barni in koma Nigeria,"
Mommy ta qarasa maganar ta cikin ihu da kuka da tare da kai wa baturen nan wani irin duka da naushi sai da ya tafi taga-taga kamar zai faɗi amma ya yi saurin cakewa da qasa da takalmin shi baqi sau ciki mai matuqar tsada, cikin haɗe haqoran shi waje ɗaya da fushi mai tsanani Alex ya furta,
"You filthy bich ! you are going to pay for this,"
Da hannu ɗaya ya hau jan Mommy dan ya shigar da ita cikin gidan amma ya kasa, nan take ta nuna masa renon qauye cin tuwon dawa da shan kunun gero daban da kurb'ar costard,duk yanda yayi ya ja ta zuwa cikin gidan kasawa yayi, ganin tana so ta bashi kunya a gaban ma'aikatan shi ne ya sanya shi duqawa ya sab'e ta a kafad'ar shi, da kyar yake tafiya ciki da ita saboda yanda take mutsu-mutsu da zillo tana neman sauka qasa daga jikin shi,suna shiga cikin gidan aka rufe da key ya kira ma'aikatan shi maza suka ɗauki Mommy tana ihu tana harbe-harbe da qafafu suka maida ta benen da take, a qasan dakin da aka sauke ta suka watsar da ita kamar abun banza suka ja qofar suka bar wajen, a guje ta isa jikin qofar d'akin tana ci gaba da ihu da neman agaji, cike da fushi Alex ya karb'i allurar da aka riga aka haɗa masa tin kafin ya isa cikin gidan, dan sun riga da sun san halin shi ya saba drugging duk wata yarinyar da ya siya ya mayar da ita abar shaqatawar shi,shi dai kawai ya gansu cikin maye tofa abun yafi bashi nishad'i,sannan yana sawa ya samu sauqin sarrafa su ba tare da sun yi masa musu ko gardama ba.
Yana shiga d'akin ya tarar da ita a takure a gefen gado tana gunjin kuka tare da neman taimakon a fitar da ita tana so taje gida ta gaji,murmushin mugunta yayi ya isa gaban ta hannun shi ɗaya a bayan shi,yana zama ya shammace ta ya zurkud'a mata allurar nan be zare ba sai da ruwan ya qare a jikin Mommy,nan take kuwa ta yanke jiki ta faɗi a wajen, cikin farin ciki Alex ya d'aga ta daga qasa ya kwantar a gado sannan ya fara rage kayan jikin shi.
Abinda yayi mata yau yafi wanda yayi mata a farkon haɗuwar su, dan kuwa ya yi wa Monmy dukan tsiya ya fitar mata da jini sosai a jikin ta kafin ya hakura ya kyale ta.
Miranda da ta shiga gyara ta kuka ta dinga yi tana tausayawa Mommy da bata san inda kanta yake ba, tana gama gyara ta ta fita ta bar d'akin ta wuce zuwa na Alex ,cikin kuka da ihu baturiyar ke yi masa faɗa akan idan ya kashe ta fa? Ya fa kashe mata biyar kenan fa,hakan be ishe shi ba? Cikin harshen turanci yace mata,
"Eh be ishe ni ba, kuɗi na na sanya na siye ta baiwa ta ce ! dika baqaqen fata bayin mu ne ! abun wasan mu ne su ! ki fita ki bar min nan kafin kema na yi miki abinda na yi mata, ban ɗauke ki aiki dan ki faɗa min abinda zan yi ba,ki tabbata ta ji sauqi a cikin kwana biyu saboda zata yi baqo na musamman...Mike ne zai zo shima ya yi nishad'i,"
Miranda na jin sunan da Alex ya ambata jikin ta ya hau rawa, tabbas idan wannan azzalumin yazo sai dai buzun Mommy dan kuwa ba zata qara moruwa ba har abada, shi har ta baya neman mata da maza yake yi,cike da ladabi ta bashi hakuri ta bar wajen.
Nan take zuciyar ta ta d'arsa mata lallai zata taimaki Mommy ta bar gidan koda kuwa hakan na nufin rasa tata rayuwar ne, abinda uban gidan nata yake yi yayi yawa.
Haka ta dinga bawa Mommy kulawa ta musamman dan kawai ta samu ciwukan jikin ta su warke, cikin ikon Allah kuwa Mommy ta fara iya takawa da qafafun ta tana zuwa band'aki a kwana na biyu da faruwar wannan mummunan rashin imanin da Alex ya gwada mata.
Tin da sassafe Miranda ta yi wa Mommy bayanin abinda take so tayi mata,Mommy bata wani gane ba sosai amma tinda taji kalmar escape ta san kub'utar da ita Miranda ke son yi, ai kuwa da sauri Mommy ta rungume ta tana godiya,Miranda kuwa fita tayi ta yi wa saurayin ta da ke cikin ma'aikatan gidan alama da komai ya zama ready.
D'akin Alex Miranda taje ta na yi masa tambayoyi akan irin shiga da kwalliyar da yake so a yi wa Mommy yau saboda zuwan baqon shi na musamman.
Nan take Alex ya saki baki yana yi mata lissafin abinda yake so a yi wa Mommy da ko sunan ta be sani ba,shi dai kawai ya san ya sayawa kanshi abun nisha'di, suna nan suna ta lissafe-lissafe saurayin Miranda ya fitar da Mommy daga gidan cikin wata boyayyiyar hanya, suna fita daga gidan ya bata kuɗi da wata takarda yace idan ta samu taxi ta basu sannan ya lullub'a mata rigar sanyi mai kauri a jikin ta, qafar ta na sanye da takalmi sau ciki me kyau, gudu kawai Mommy take tana so ta bar unguwar ta yi nesa da gidan sosai.
Taxi ta gani ta tsayar ta faɗa tare da miqa masa takardar da aka bata haɗe da dala guda ɗaya kamar yanda saurayin Miranda ya yi mata nuni, babu b'ata lokaci driver ya ja mota ya hau kwalta suka miqa, Mommy bata kwantar da hankalin ta ba sai da ta ga sun yi nisa sosai da gidan sun shiga jama'a sosai dan kuwa can unguwar su Alex unguwa ce ta masu hannu da shuni, gaba ɗaya layin ma gida uku ne a wajen maka-maka kamar ginin wata babbar makarantar.
A bakin wani hotel motar ta tsaya Mommy ta buɗe ta sauka, canjin ta ya bata ya yi gaba abun shi, cikin qanqame jikin ta ta hau tafiya tana waige-waige tana zubar da hawaye,yunwa take ji sosai amma bata jin zata iya tsayawa cin abinci,waje ta samu ta rakub'e ta dunqule waje ɗaya ta fashe da kuka tana faɗin,
"Ya Allah na tuba, Allah ka gafarta min ba zan sake fita yawon karuwanci ba, ba zan sake kallon fina-finan banza ba ko karanta littafin banza balle har na yi sha'awar kusantar zina,Allah ka kawo min dalili mafi alkhairi da zan koma qasata, Allah ka shiga lamurana, La'ilaha'illalla anta subhanaka inni kuntu minazzalimin,"
Tun Mommy na kuka da hawaye har hawayen suka dena fita ta samu waje ta sake takurewa saboda sanyin dake ratsa ta, mutane kuwa idan suka zo wucewa wasu sai su wurga mata kuɗi a zaton su mabaraciya ce,tana nan zaune wani security ya fito daga cikin hotel ɗin ya tashe ta yana yi mata magana akan ta bar wajen ko ya kirawo mata police,cikin d'aga kai ta hau cewa,
"Dan Allah ni ka kira min 'yan sandan ma su maida ni qasata ko haqqi na ba zan tsaya a bi min ba mun haɗu a qiyama da mugu,"
Tura ta mutumin ya dinga yi har saida Mommy ta bar wajen ta samu wani wajen ta zauna tana ci gaba da rawar sanyi.
A can gidan Alex kuwa Miranda ce ta gama sauraren shirmen shi sannan ta duqa alamar gaisuwa ta bar wajen nashi ta nufi wajen Mommy, tana shiga d'akin ta tabbatar da an kub'utar da mommy sai kawai ta k'walla qara mai qarfi tare da kwasar gudu ta hau benen da Alex yake, a hanya suka haɗu da shi ta hau numfashi tana nuna masa hanyar benen Mommy, a gigice ya bi bayan ta suka shiga d'akin,gani yayi be gan ta ba, sai ya shiga har band'aki ya hau neman ta amma be same ta ba, qarshe dai babu inda ba a duba ba amma babu mommy babu kayan ta, cikin Kuka Miranda ta hau cewa,
"Yanzu ina ta tafi gashi bata san kowa ba kuma bata da lafiya ina jin tsoron kar ta haɗu da 'yan iska su yi mata fyad'e,"
Kuka ta dinga yi da ya sanya Alex cire zargin da sanya hannun ta a gudun mommy wanda nan take ya tuna ma ai tana sashen shi d'azun itama komawa tayi ta ga bata nan.
Nan da nan fa bature ya dinga masifa yana kiran dika ma'aikatansa dan gano wanda ya kubutar da mommy a gidan.
A can cikin gari kuwa Mommy na nan nata watangaririya a gari bata da kowa da zai taimake ta ta koma Nigeria, sai dai ma kyara da nuna mata ita ɗin ba kowa bace da zata dinga zuwa tana rab'ar su har da zata nemi taimako a wajen su.
***************************
"Ohhh ni K'waisan alheri na shiga uku, wai a yi mutane dan ruwn zumar soyayyar da suke kur'bawa na da zaqi se a dena ganin su online? Kin ga bama Mommy kaɗai ba har da ɗan tijarar nan ma baya hawa ko TikTok ne in fact account d'in shi da na sani babu shi yayi b'atan dabo,"
Wayar shi ya sake kangawa a kunnen shi da alama kiran waya yake yi amma shiru, ba alamar ma tana shiga balle ya sama ran za a ɗauka, tsaki ya ja me qarfi yace,
"Baby ni fa ina jin tsoro, haka kawai zuciya ta ke bugawa da ta tuna bawan Allahn nan da ko cikakken sunan shi ban sani ba, million sha uku muka ci nashi banda wanda yake kashewa yarinyar nan, kana ganin dai wayar da ya sai mata ta milliyoyin nerori,nif ko sunan sabon resort ɗin nashi da yace zai buɗe ban sani ba, anyaaaa?"
Samuel ne ya kama hannayen Hajiya K'waisa cikin sigar lallashi yace,
"Kwantar da hankalin ki my love kar ki d'aga hankalin ki ki fara quraje a fuska,'yan bariki ne fa dik inda suka je za su dawo gida ne,ita waccan uwar gantalin ina ta tafi ban ganta ba?"
"Hummm wani customer ne ya taya shine ta tafi ita ai kaga tana kirana a gaisa a san halin da take ciki, amma banda waccan uwar tinb'elen,"
"Kar ki damu zata dawo lafiya ki bata kwana uku idan bata dawo ba sai a baza hotunan ta wajen mutanen mu wataqila a samu wanda ya ganta,"
"Allah ya sa a gan ta lafiya ba a gutsire ko a yanke ba, duk sanda kuwa na ɗora ido na akan ta se na sa tsinin farce na na sace mata leb'en nan,"
Dariya Samuel ya sanya yace,
"Ragadada kenan,"
"Heeeee ragassss !"
Hajiya K'waisa tace suka tafa da Samuel suna dariyar shaqiyanci.
**************************
"Ranka ya dad'e ni dai da an bi shawarata an yi musu had'in zumunta da yarinyar nan Bilkisu kaga shikenan an yi tuwona mai na kuma dakan d'aka shiqar d'aka tankad'en bakin gado lomar kwanciya,"
Murmushi mahaifin Abdul ya yi har sai da haqoran shi suka fito kafin ya kalli matar tashi me tsananin biyayya, amma wannan karon tana so ta cusa wa yaron ta ra'ayin auren zumunta wanda shi kuma baya son hakan,
"Amma dai qarshen hausar nan ke kika qarata ko ? Dan dai a shekaru na sittin da uku ban taɓa jin ance wata lomar kwanciya ba sai yau,"
Dariya ta yi mai sauti kafin tace,
"Wai ai dan in tabbatar maka da kusancin alaqar ne idan ka manta,"
Gyara zaman shi yayi sosai sannan yace,
"Laminde ba wai ina gudun yaron nan ya haɗa zuri'a da qanwar ki da kuke uwa ɗaya uba ɗaya bane, ina guje miki kar a zo zumuncin ku da kuke riritawa na shekara da shekaru kuna bawa kowa sha'awa ya rushe azo ana dana sani a lokacin da bashi da amfani, da ace ita macen ce tace bata so iyayen ta na iya tursasa ta kuma tayi hakuri ta aure shi,se ki ga saboda rauni irin na mace daga baya ta saki jiki ta fara son mijin, amma Lami akwai matsala akan auren da namiji ne baya son mace aka tursasa shi, abun be cika haifar da da'me ido ba,amma yanzu abinda zamu yi shine,mu dage da yi masa addu'a Allah ya zab'a masa mace ta gari mai albarka,"
"Maganganun ka gaskiya ne ran sarki ya dad'e,kuma in Allah ya so zan dage da yi masa addu'a Allah ya shige mana gaba,"
"Yauwaa matata 'yar aljannah da izinin Allah, wato saurin fahimtar ki da hakurin ki tare da kawaicin ki na sawa a kullum in ji ina sake son ki da qaunar ki,"
Wani murmushi tayi tana sunkuyar da kai irin na jin kunya, a haka suka ci gaba da hira a tsakanin su suna magana akan makarantu biyu da Abdul ɗin ya bada kwangilar a gyara,tare da hirar Saddeqa da ɗan nasu ya sa qanin shi Sultan ya gano masa a wane gida take a qauyen.
****************************
Duqe take a bakin wata shara tana leqa kan ta dan ta ga ko mazan da ta ga suna kallon ta daga qarshe suka fara bin ta sun tafi? Daga can nesa idanun shi ya sauka akan idanun ta dake tsiyayar da hawaye tana leqe wanda da dikkan alama a tsorace take....................
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA: HAERMEEBRAERH
PAGE 29:
Wani irin bugawa zuciyar shi tayi da qarfi, ya sake saurin duba inda yake ganin idanun Mommy dake zubar da hawaye, shin tsabar yawan tunata da yake yi ne ya sanya take yi masa gizo a irin wannan yanayin da ya ganta a ciki ko kuwa ya abun yake ne?
Zuwa suka yi daf za su wuce ta kusa da drum ɗin zubar da sharar Abdul ya kalli Bilal yace,
"Guy kana ganin abinda nake gani ko kuma ni kaɗai nake ganin akwai mace acan tana lab'e tana kuka?"
Juyawa dai-dai wajen da Abdul ya kalla yana magana Bilal yayi, kafin Bilal ya bashi amsa suka ga ta yanko da gudun tsiya ta qanqame Abdul ta na fashewa da wani irin kuka mai ban tausayi, cikin kukan tace,
"Dan Allah yayana ka taimake ni kar su kama ni,sato ni aka yi aka kawo ni qasar nan, na samu na kub'uta daga hannun mutumin da ya siye ni yanzu kuma wad'ancan 'yan daban na bina za su kama ni,"
Hannun ta Abdul ya kama ya janye ta daga rungumar da ta yi masa,cikin wani irin yanayi na tashin hankali ya ce,
"Saddeqa right ? Ya aka yi aka sato ki daga qauyen Ba mugu aka kawo ki wannan qasar? Waye a kaf qauyen nan yake da zamar aikata hakan ba tare da an sani ba? Innalillahi wa inna'ilaihirraji'una, muje masaukin mu sai ki bamu labari da kyau,"
Ganin shigar da ke jikin Mommy bai sa ya ji k'yamar ta ba ko yayi zargin wani abu mara kyau daga gare ta, hasali ma tausayin ta da mamakin ganin ta a wannan qasar shi yafi damun shi, tabbas idanun ta da girar ta ne suka tabbatar masa da cewa wannan Saddeqa ce, amma kuwa duk wanda aka kama da wannan aika-aika sai ya hukunta shi hukunci mafi muni kuwa a rayuwar shi.
A bangaren Mommy kuwa jin ya ambaci Saddeqa sai ta shiga rud'ani da tashin hankali, a ina wannan bawan Allah'n ya san sunan qanwar ta? Tayaya zai kalle ta ya ce itace ma Saddeqa bayan Saddeqa bata da wannan mugun bakin nasu na gado da suka gado wajen Ɗan liti? Cikin zuciyar ta take ayyana,
'Wataqila idanun mu ne suka yi masa kama, babu ja akan kamannin idanun mu saboda gaba ɗaya yaran gidan mu irin idon Baba muka d'akko'
Har suka isa Mommy bata dena zubar da hawaye ba da rawar sanyi, sanda suka shiga d'akin nasu na hotel ne taga Abdul na cire rigar shi ta sama sai wani irin tsoro ya kama mommy,nan take ta fara ja da baya ta na yarfe hannu, Bilal ne ya cire tashi rigar saboda tsabar tsokana sai ya fara taku ta saitin inda Mommy ta nufa wanda nan ne gadon shi yake, kafe ta yayi da ido yana murmushi, nan take Mommy ta kurma ihu ta zube a qasan wajen a sume,gaba ɗaya ta gama saddaqar da ta kawo kanta hannun masu fyad'e.
Abdussaboor ne ya ga abinda Bilal ya aikata sai ranshi ya baci ya hau yi masa masifa, shi kuwa dariya kawai yake yi yana kumawa, daga qarshe ya haye saman gadon shi yana dariya yace,
"Se ka watsa mata ruwa ta miqe sannan ka san yanda za ka yi da ita, ni ba ruwana a wannan chakwakiyar da kake neman jefa kan ka,kana da tabbacin gaskiyar abinda ta faɗa shine ya faru ba qarya take yi ba? Haka kawai na ji a zuciya ta akwai lauje cikin nad'i a maganar ta,ka dai bi a hankali, ka kalli jikin ta da kyau da surar da Allah ya bata, kana da tabbacin sato ta aka yi ba itace ta kawo kanta ba?"
Da sauri Abdul ya dakatar da Bilal ta hanyar nufar gefen gadon shi ya dakko ruwa ya watsawa Mommy, kafin ta farfad'o Abdul yace,
"Ka dinga kyautata wa mutane zato Bilal, kai a komai sai ka kawo nagetive though a ciki,wa ya faɗa maka jikin ta na da nasaba da zuwan ta qasar nan? Mu jira muji daga gare ta, iya sanina da yarinyar nan mahaddaciyar qur'ani ce kuma nitsattsiya, itace yarinyar danake faɗa maka na saka Sultan yi min binciken gidan Iyayaen ta,"
Tana gama buɗe idon ta taga Abdul tsaye a kan ta, da sauri ta hau taɓa jikin ta tana so ta ji shin kayan ta na nan a jikin ta ko sun cire mata,ji tayi kayan ta na nan a jikin ta sai ta yi wata ajiyar zuciya ta ja da baya ta shige lungun gadon su Abdul ɗin tana ci gaba da kukan ta, a hankali Abdul ya isa gaban gadon ya zauna yace,
"Sanar dani ya aka yi aka sato ki nan, iya sanina ke yarinya ce nitsattsiya mai ilimin alqur'ani na je gida na gan ki na kuma baro ki lafiya me ya faru?"
Kasa sanar da shi Mommy tayi ba itace Saddeqa ba sai kawai ta fara magana,
"Ni kaina ban san me ya faru ba, ina hanya ina tafiya kawai na ji kamar an shaqa min wani abu, ban sake farkawa ba sai a jirgin ruwa, daga nan ina ta kuka ina yi musu ihu suka sake shaqa min wani abu ban sake sanin inda kaina yake ba sai a wannan qasar, a gaban mu aka yi cinikin mu kamar kaji sannan aka sanya mu a mota,a gidan wani Bature mai suna Alex aka sauke ni, shine...shine...shine ya ke..."
Kuka sosai Mommy ta fashe da shi har jikin ta na rawa, da jin haka su Bilal suka fuskanci inda maganar ta ta dosa nan take Abdussaboor ya ji wani irin matsanancin kishi da baqin ciki sun mamaye shi, a fusace ya tashi yana faɗin,
"Zaki iya gane gidan shi?"
Da gudu Bilal ya sakko daga saman gadon shi ya damqe kafad'un Abdul ya girgiza shi da qarfi cikin d'aga murya yace,
"Kaii ka nutsu ! Nan qasar ba Nigeria bane ba kuma qauyen Ba mugu bane inda kuke mulka, nan qasar waje ne qasar wajen ma ta turawa, shawarata anan kawai ka zo mu duba online mu koyi yanda za a yi reporting b'atan passport ɗin ta, sannan mu yi dik yanda zamu yi mu tafi da ita shikenan,wani fushi da nuna jarumta ba naka bane a qasar azzaluman mutane irin wannan, yanzu ita se a sake ta su yi maka d'aurin goro,"
A hankali Abdul ya fara rage fushin dake cin zuciyar shi,sai suka kunna laptop suka duba yanda za su cike form din DS-11 dan su sama mata sabon passport cikin sauqi.
Suna kammalawa Abdul yayi waya aka kawo abinci da abubuwan sha da shayi, sannan ya duba a kayan shi ya samo mata T-shirt da wandon shi da zai iya yi mata, band'aki ta fara shiga tayi wanka sannan ta sanya kayan da ya bata ta fito tana rakub'ewa a jikin gini, Bilal banda kallon ta babu abinda yake yi, haka kawai yaji be yarda da ita ba, babu qarya yarinyar na neman taimako, amma zuciyar shi na sanar dashi akwai abinda take b'oyewa.
Haka Monmy ta qarasa gaban abincin nan ta zauna ta hau ci tana shan lemo da shayi dik a lokaci ɗaya,kana ganin ta ka san a wahale take kuma a yunwace take,bata kyale abincin nan ba sai da ta gama ci tasss sannan ta samu qasan gadon inda ta rakub'e ta kwanta tana sauke ajiyar zuciya.
Dik yanda Abdul yayi akan ta hau gadon shi zai koma na Bilal su kwanta tare qi tayi tace nan qasa ya ishe ta,Bilal na jin furucin ta ya gyad'a kai yace,
"Ka gani? Bata wani son gado kawai ka je ka kwanta abun ka malam ni kar ka wani matse ni,"
Abdul na jin haushin yanda Bilal yake magana a gaban Mommy yana nuna baya son zaman ta a tare da su,babu yanda ya iya dole ya kyale ta bayan ya wurga mata pillow da abun rufa, kasa qarasa rufe jikin ta tayi saboda baccin da take ji,munsharin ta me kama da husir ne ya sa Bilal dariya har yana fad'owa daga gado,tsaki Abdul yayi yace,
"Ka ji jiki kai dai,"
"Ahhh dole na ji jiki mana,ashe qauyen ku akwai qauraye ji yanda yarinya ke busa husur ɗin fita farauta,"
Duk yanda Abdul yaso ya haɗe rai kar ya yayi dariya amma da mommy ta ja wata sarewar munshari dole shima ya kece da dariya har yana hawaye, kusan raba dare suka yi suna dariya da tattaunawa akan yanda za a samawa Mommy takardar barin qasar cikin 'yan kwanakin da ya rage musu su tafi tare da ita.
Washegari da asuba Bilal ne ya fara tashi ya shiga band'aki ya kama ruwa yayi alwala sannan ya fito ya tashi Abdul domin ya yi alwala su yi jam'i a tare.
Abdul na fitowa daga band'aki sai ya tada Mommy dan ta yi alwala duk suyi sallar a tare, wani irin juyi tayi ta yaye bargon ta banqaro jikin ta tana miqa a suk'wane Abdul ya bar wajen yana zaro idanu waje be sake komawa inda take ba ya tada sallah Bilal ya bi bayan shi yana ayyana,
'Allah ya qara waya aike ka karambanin tashin mace daga bacci dama?'
Ko da suka idar da sallah sun jima zaune suna azkar still mommy bata farka ba,dik cikin su babu wanda ya sake bi ta kan ta suka yi wanka suka shirya suka bar mata takarda da rubutu jiki suka kulle d'akin suka fita yin abinda ya kawo su.
Mommy kuwa bata farka ba sai qarfe 11am ta tashi da miqa tare da hamma mai tsawo tana kalle-kalle, ganin inda take ne ya tuna mata da dik abinda ya faru a jiyan, da sauri ta tashi daga inda take ta ga babu kowa a d'akin,wata takarda ta gani a ajiye a saman gadon Abdul hannu ta sanya ta ɗauka,cikin kyakkyawan rubutun shi ya sanar da ita idan ta farka ta kira wannan No da ya rubuta a kawo mata abinci sannan tana iya duba cikin inda ya ɗaukar mata kayan sawa jiya ta ɗauki wanda zata sauya ba za su dawo ba sai dare.
Murmushi tayi sannan ta yi tsalle ta haye gadon Abdul ɗin tana juyi,a haka ta isa jikin landline phone ɗin dake ajiye a side drower ɗin gadon nashi ta sa hannu ta ɗauka ta hau duba takardar nan tana danna No dake jiki, tana gamawa ta kanga a kunnen ta, abinci ta sanar da akawo mata.
Cikin qanqanin lokaci ta shiga wanka ta wanke bakin ta ta duba kayan Abdul ta sauya zuwa wasu riga da wandon ta ninke wanda ta cire ta ajiye masa a saman gado.
Ba jimawa aka kawo abinci taci ta samu waje ta sake kwantawa a saman gadon ta hau bacci ko sallah bata yi ba.
Haka Mommy ta dinga rayuwa a cikin su Abdul suna kyautata mata, ita kuma ta na qoqarin nuna musu ita ta Allah ce dan su taimake ta ta koma Nigeria,a haka sai da suka shafe sati ɗaya ana cuku-cukun samawa mommy takardun da zasu bata damar barin qasar.
A can gidan Alex kuwa sun qudurta niyyar nemo Mommy ko ta halin qaqa dan kuwa be taɓa samun macen da ta yi masa ba irin ta, shi da abokinsa Mike sun qudiri aniyar ɗaukan mummunan mataki akan Alhaji da ya siyar masu da matsala a farashi mafi tsadar gaske.
*****************************
Alhaji na haɗa kan kud'ad'en shi ya sallami duk wanda zai sallama sai ya tattare ya koma
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 70