gwanda Billy akan Mommy a ganin shi.
A can gidan Ɗan liti kuwa Munir ne ke sallama da Saddeqa bayan ya shiga sun gama sallama da Baabaa dan kuwa a ranar yake so ya koma aka yi wannan kiran, tsaye take a jikin motar shi suna yi wa junan su alqawarin kasancewa da junan su dik rintsi duk wahala,a haka Innoh da Mommy suka qaraso sai tada qura suke yi duk inda suka wuce kamar wasu shanu,cike da takaici Innoh ta tsaya a gaban su tace,
"Ku gama iskancin ku dole ne ka dawo ka auri Ameerah saboda 'yata ba zata mutu a banza ba saboda kai,ke kuma zaki shigo ki same ni ne,"
Ta wuce tabi bayan Mommy da ko kallo su Munir basu ishe ta ba,cike da damuwa Saddeqa ta sauke kanta qasa tana jin wani irin tsoro na taso mata tin daga zuciyar ta yana bayyana a saman fuskar ta,cikin sigar lallashi Munir yace,
"Kar ki damu da barazanar ta inshaa Allahu Munir na Saddeqa ne ita kaɗai, ina zuwa zan cewa Abbah ya zo ayi maganar nan a wuce wajen tinda na samu Ummee ta sanar da shi kuma ya yi farin ciki da hakan, kin ga yanzu dik wata fargaba bamu da ita ko?"
D'aga masa kai tayi tana aro jarumta ta sanya a fuskar ta saboda kar ya tafi yana tunanin damuwar da ya barta a ciki.
Kuɗi ya bata kamar kullum yau ma qin Karb'a tayi sai da ya dinga yi mata magiya da roqo sannan ta Karb'a tayi masa godiya ya tafi cike da kewar ta.
A can gidan su Billy kuwa.........
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 33:
Tinda suka koma gida Billy ke yi wa mahaifiyar ta kuka akan ta san yanda zata yi a aura mata Abdul in dai ana so ta ci gaba da zama a qaunyen Ba Mugu in ba haka ba zata koma inda ta fito ba za su sake ganin ta ba,ita kuwa Ummah ta rasa inda zata sanya ranta ta ji sanyi saboda kukan Billy na qona zuciyar ta,duk yaran ta tafi son Billy a cewar ta ta fi su tausayi dan kuwa gashi har fita neman na kai tayi dan kawai taga ta wadata su da abubuwan arziqi su fita daga quncin talauci da ke damun mutanen Nigeria baki ɗaya.
A d'akin Billy suka yi masauki gaba ɗayan su, Ummah ce tace,
"Yanzu Bilkisu baza ki yi shiru ki ji wanne hukuncin zan yanke akan wannan maganar ba? Ki duba ki ji yanda kan ki ya ɗauki zafi saboda fitinannen kukan da kike yi?"
Mahaifin Billy kuwa cewa yayi,
"Kar ta yi shirun tinda akan ta aka fara irin hakan, ni kun ga fitata ma,amma ina so ku buɗe kunnuwan ku da kyau ku jini,maganar Sarki dai ta zauna dole a bita Bilkisu ki samu waje ki zauna daga yau babu ke babu komawa birni aikatau,kar kuma in samu labarin kin kori saurayi idan an zo zance wajen ki, ki tsaya ki bawa duk wanda yazo zance wajen ki dama ku fahimci juna, idan yayi miki sai a yi da shi, idan be yi maki ba sai ki sauya wani daga nan zuwa qarshen shekarar nan in Allah yaso zan aurar dake kin ji na faɗa miki,"
Yana gama maganar shi ya shuri takalman shi ya bar gidan, yana fita Billy ta saki wani uban ihun da ya janyo hankalin qannen ta maza guda biyu, nan take mahaifiyar su ta kora su waje, ta zauna a kusa da Billy da ta ɗora hannayen ta aka tana rusa kuka tace,
"Wai ni bana ce ki yi shiru bane? Ina sane da kalar son da kika taso kina yi wa Abdul tin kina qarama ba kuwa zan zuba ido ya kub'uce miki ba, na yi miki alqawarin sai kin auri Abdul hankali na da naki zai kwanta,zuwa dare kafin baban ku ya dawo daga shago zan je na samu Yaaya mu tattauna akan wannan maganar,Abdul naki ne ke kaɗai dan ko kishiya ba zan bari yayi miki ba bayan ya aure ki,"
Billy na jin haka ta fara rage kukan ta, dan kuwa ta jima tana son Abdul bata jin zata iya haƙuri da shi ya auri wata ma balle Mommy, ai ko da take tafiya yawon banzan ta ba zai hana watarana ta yi aure ba, Abdul kuwa shi ta ajiye wa kan ta a duk sanda ta gama yawon barikin ta ta aura,ba wata 'yar hau ɗin da zata aure mata shi ta kyale ta, Mommy ta tabbata ta kula da kan ta dan kuwa yanzu qazamin yaqi zai b'arke a tsakanin su.
Wayar ta ce take ta ringing amma tana katsewa dan kuwa bata son amsa wayar Man Ummah na kusa da iya dan kuwa yana iya faɗin wata kalmar da zata bayyana ko ita wacece a harkar bariki, shi yasa take so Ummah ta tafi dan ta samu ta amsa kiran nashi, amma Ummah taqi tashi so take ta zauna da 'yar tata ta kwantar mata da hankali sosai.
Rashin ɗaukan wayar Billy kuwa a wajen Man ɗin nata ya jawo masa shiga babban tashin hankali, dan kuwa irin haka bata taɓa faruwa a tsakanin su ba, a sukwane ya fita ya bar gidan har yana mantawa da wayoyin shi,direct gidan Hajiya K'waisa yaje ya tarar dasu an saka musu bandage a hannu da wuya, cikin hanzari ya isa ya zauna a kusa da Samuel dake ta lallashin Hajiya K'waisa akan ta ci abinci amma taqi sai tararar da hawaye take yi tana faɗin,
"Shikenan asiri na ya tonu yarinyar nan ta rusa min duk wani shiri da tanadi na da nayi akan ta zuwa qarshen shekarar nan, Allah ya tsinewa wannan yarinya albarka ya hana ta morar kan ta matsiyaciya,yanzu dole na je a cikin waɗannan yaran da na saka a tsohon gidana na duba na ga wacce zan d'akko na rena kafin new year,ina murna ga yarinya 'yar shila komai yaji natural ba artificial ba shine ta watsa min qasa a ido,"
"Na ji baby an yi maki ba dai-dai ba amma ki yi hakuri ki ci abinci ki sha magungunan ki, ni da kaina zan sama maki wata ki yi hakuri kin ji?"
Da kyar Hajiya K'waisa ta buɗe baki Samuel ya sanya mata abinci ta hau taunawa kamar bata so, tissue paper ya zaro a cikin k'walin ta ya goge masa hawayen shi, Man da ya gaji da ganin dramar 'yan daudun ne yace,
"Wai ni Hajiyar mu me yake faruwa ne? Wa ya b'ata wa sarauniyar kyawawa rai yanzu na ɗauki mummunan mataki akan shi? Samuel me ya same ku haka ko hatsarin mota kuka yi ne na gan ku da bandage?"
Wani mugun kallo Samuel ya sakar wa Saurayin Billy daga baya ya kauda kai, dan ya ji kishin kirarin da aka yi wa K'waisan shi a gaban shi,sake d'iban abinci yayi ya bawa K'waisa ta Karb'a tana yatsina tare da yin wani mugun tari,shafa bayan ta Samuel yayi, a hankali tace,
"Hummm ai gwanda hatsarin mota da yarinyar nan ta kafa maka hauren ta ɗaya a jikin ka,yanda kasan dafin maciji ko kunama haka dafin dake jikin haqorin ta yake, yanzu haka zazzaɓi ne a jiki na,"
"Ah ah ! Wacece haqorin ta yake da dafi haka har ta kai ku da nad'e hannu da wuya da bandage?"
Cikin hargowa K'waisa yace,
"Kai ka ishe mu da surutu ka barmu mu ji da tashin hankalin dake gaban mu, tashi ka tafi dan Allah ita kanta Billy bana son ganin ta kar ta dawo min nan, bana son harka da 'yan hau, Amy dik iskancin ta bata taɓa yunqurin saka hannun ta a jiki na ba har ta bar gidan nan sai wannan me wakeken bakin kamar qofar gari,dama bahaushe yace man kad'e be saba da tandu ba, wasu alheri sam be kamace su ba sun fi son tsiya to taje can ta qarata, Sallau ! Sallau ! Ka haɗa min jakunkunan da na ce ka haɗa ko?"
Da gudu Sallau ya fito daga kitchen ya tsaya gaban K'waisa yace,
"Eh na haɗa Hajiyata,"
"To d'akko ka bawa wannan bawan Allah'n dika jakunkunan ɗaya ta Billy ɗaya ta Mommy bana so na sake ganin ɗaya daga cikin su,a kai wa wani sarkin gari da yawa maye ba zai ci kan shi ba,shi yini da arziqi ai ya fi kwana da tsiya, zan nemo wasu su maye gurbin su, mata fa kullum kawo kan su suke yi ni ce ma na ke qin kulawa masu buqatar taimako na ware masu gida na musamman suke baje haja da kolin su,ina zuwa wajen su na ce ina neman wadda zan mayar 'yar gata kamar yanda nayi musu zan samu masu son zama kamar su ko ma fiye da su ma, dan haka tashi ka bar min gida kafin raina ya fi haka ɓaci,"
Duk yanda saurayin Billy yaso ya baiwa Hajiya K'waisa hakuri qi tayi ta dinga mafisa da bala'i qarshe Samuel ya shiga suka yi masa kaca-kaca suka kore shi,jiki babu k'wari haka ya zuba jakunkunan a motar shi ya bar gidan,direct hanyar qauyen Ba Mugu ya ɗauka dan kuwa be ga ta zama ba irin wannan mummunan abun ya samu masoyiyar shi, wataqila shi yasa ma bata ɗaukan wayar shi.
***************************
Mommy ce kwance a d'akin Innoh a saman gadon ta mai rumfa tana ta tsiyayar da hawaye,ta gaji da kukan amma ya qi dena zuwa bata taɓa nadamar zaman ta 'yar bariki ba sai yau,irin nadamar nan da mutum ke jin dama za a dawo da hannun agogo baya da be aikata abinda yayi ba mara kyau, mommy bata taɓa sanin soyayyar Abdul ta ci qarfin zuciyar ta kamar haka ba sai yanzu da ya furta ya tsane ta baya son sake ganin ta, idan baya son ganin ta ai ita tana son ganin shi ko? Ya zata yi da soyayyar shi? Wa zai aure ta yanzu?
Hasken da ya haske idanun ta ne ya sanya ta rintse idanunta ta juyar da kan ta ɗayan bangaren ta ci gaba da kukan ta,cikin halin ko in kula Innoh tace,
"Au wai har yanzu kukan kike yi ? Lallai iska na wahal da mai kayan kara, ba nace ki dena kukan ba zan ɗauki mataki akan matsalar taki ba? Na kula da ke da Ameerah kashe kan ku kuke son kuyi ku huta, ni a duniyar nan akwai wanda soyayyar shi zata kai ni kwance ne? Ko uban ku da muka yi soyayyar yarinta har ta kai mu ga aure yace baya sona gaba na zan kama balle wanda be aure ni ba,Ita tana can kwance wata da watanni tana fama da son maso wani,kema shine zaki zo ki jibge min ku zama biyu ko? To ni ba uwar wahalallu bace miqewa zaku yi kuyi sharafin ku yanda kuke so aure ne sai an yi shi,bari ma ki gani, Ameerah ! Ameerah miqo min waya ta in kin gama kiran wahalar da kika sa kan ki, na faɗa maki wannan yaron jikan kafaffiyar tsohuwar nan ba zai amsa kiran ki ba ko me zaki yi,"
Ameerah ce ta fito daga d'akin ta daga ita sai ɗaurin qirji,fuskar nan ta faɗa daga manyan idanu sai dogon baki, wuya ya zurma ya yi qashi k'wandala-k'wandala, yawu ta zubar ta shiga d'akin Innoh bakin nan se tashin wari yake yi tace,
"Gashi,"
"Um um umhhhh ! Fitar min a d'aki shegiya qazamar banza, duk qazanta ta yarinyar nan kin shallake tunani na, kan uban can gunnusuru, Ameerah kashe kan ki zaki yi da wari ko? Kece tsamin hammata da warin baki ga uban warin dake fitowa a jikin ki kamar wadda bata tsarkin kashi? Kaiii subhanallahi"
Waje Innoh ta fito ta tsirtar da yawu ta koma d'akin ta tana ci gaba da masifa ta danna kiran Naja, kamar wadda take jira kuwa ta ɗauki kiran,babu sallama Innoh tace,
"Ke 'yar uwa ki zo ki yi min rakiwa ina zaune za a sabauta min yara,ki zo maza ina da buqatar ki raka ni wajen me kankat,"
"An gama kuwa dama jiran kiran wayar ki nake Ameerah ta kira ni tana kuka tace min wancan matsiyacin yaron ya tafi ko neman ta be yi ba balle suyi sallama sai ma fita da Saddeqa da yayi a mota kuma suka dawo a mota ya wuce babu ko sallama"
"Hummm ke dai bari, dik da bana son haɗa zuri'a da waccan 'yar tsurut ɗin tsohuwar ina ga dole na bawa Ameerah abinda take so in ba haka ba halin da take ciki ya ta'azzara mutuwa zata yi, warin da take yi kaɗai ya isa ajalin ta,"
Dariya Naja tayi sannan tace,
"Gani nan zuwa Yaya kar ki yi wa 'yata mugun baki, Allah ya tsare ta da mutuwa akan d'a namiji"
"To Ameen ki yi sauri muje mu dawo da wuri,"
"To Yaya,"
Suna kashe waya ta miqe ta hau shirin fita, Saddeqa kuwa tana can gaban murhu tana hura wutar dora abincin rana, tana yi tana sharar hawaye saboda rashin mutuncin da Innoh tayi mata da zagin Yadikon Sule da bata ji ba bata gani ba da ta gama kafin ta bata umarnin ɗora abincin rana.
A gaban idanun ta Ameerah ta zauna a bakin rijiya ta saka hannu a ruwan tukunyar da ta jawo dan ta ɗora girki ta kurkure bakin ta ta zubar,tana ganin sanda na qasan yayi tsalle ya koma tukunyar, dole ta zubar ta sake d'auraye tukunyar ta zuba wani,ji tayi zuciyar ta na tashi a lokacin da ta tsaya kusa da Ameerah tana d'iban ruwa, nan take amai ya yunquro mata saboda warin hammata da wani hamamin da bata san daga ina yake fitowa ba a jikin Ameerah, ganin Saddeqa na son yin amai ne ya b'ata ran Ameerah cike da rashin mutunci ta shaqo Saddeqa ta saka a hammatar ta tana duka tare da zagin ta, nan take kuwa Saddeqa ta wanke Ameerah da aman da take ta qoqarin dannewa,ashar Ameerah ta d'ura ta sake kamo Saddeqa da ta galabaita ta shaqe ta tana duka, Innoh na ganin su taqi kula su balle ta raba, Naja na zuwa ta ja ta suka fita suka bar gidan a cewar ta ai Saddeqa ce tayi wa Ameerah rashin kunya, dan haka a bar su ta lallasa ta gobe bata qara ba.
Yanda Ameerah ke jijjiga jikin ta tana aikin qarfi haka warin jikin ta ke qara fitowa, kafin wani lokaci Saddeqa ta galabaita cikin ta taji yana juyawa kamar zata zaga gashi ta kasa k'watar kanta a hannun Ameerah dake ta jibgar ta tana kuka,salati Baabaa da ta idar da Sallar azahar ta doka tace,
"Yanzu Ameerah kashe marainiyar Allah zaki yi? Ina fa ji dan rashin adalci uwar ki ta gama zagin ta tasss har da mamaciyar dake qasa sannan aka haɗa ta da aikin girki, be ishe ku ba shine kike ta dukan ta kamar kin samu jaka yanzu me tayi maki kike mata wannan.......subhaballahi shin meye ya mutu a tsakar gidan nan me wari haka...uhum uhummm me yake wari haka mun shiga uku,"
A galabaice Saddeqa ta janye jikin ta daga na Ameerah dake cika tana batsewa tana jin kamar ta shaqe Baabaa itama, wanne wari take yi haka har da kowa ke magana akai ne? Ita fa bata jin warin da ake magana akai,ta sani wulaqanci ne kawai ake yi mata ba komai ba.
Da sauri Baabaa ta duqa ta ja Saddeqa dake kwance cikin tab'o da datti,ruwa ta ja a rijiya ta dinga kwara mata daga qarshe ta shiga d'akin Yadiko ta samo mata wasu kayan ta ce ta shiga tayi wanka ta sauya.
Baabaa da kan ta ta ɗora masu abinci tace se dai a haɗa da na dare dan ba shegen da zai sake saka marainiyar Allah girki da almuru.
Saddeqa ta jima a band'aki dan kuwa tana tsugunnawa a shadda ta dinga zawo, cikin ta gaba ɗaya ya burge, da kyar ta samu ta gama abinda zata yi tayi wanka ta yi alwala ta wuce d'aki sanye da kayan da Baabaa ta bata,sallah ma a zaune tayi ta saboda rashin k'warin jiki, Ameerah kuwa na nan tsakar gida tana qunquni da zage-zage,Baabaa ce ta juya ta qanqance ido tace,
"Idan baki deb'i ruwa kin shiga wanka ba ruwan nan na tafasa zan d'iba da zafin shi na yi miki wanka Ameerah, kin dai san idan aljanu na suka tashi ko uwar ki da take ji da qiba ba qarfi na tafi ba ko? Shashashar yarinya kawai, a hakan ne Mannirun zai so ki kina wannan mugun warin?"
Tana jin Baabaa ta ambaci sunan Munir Ameerah ta miqe ta kindimi ruwa ta wuce bayi tana zumb'ura baki,a haka ta samu ta yi wanka sama-sama ta fito, ko kallon inda take Baabaa bata yi ba ta ci gaba da aiki, fatan ta taci qarfin aikin kafin Innoh ta dawo daga yawon nata ta hau Saddeqa da masifa.
Zaune suke gaban Boka ya gama dube-dube da tsubbace-tsubbacen da zai yi ya kalle su cike da tashin hankali yace......
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA: HAERMEEBRAEH ✍️✨
PAGE 34:
"Ran boka ya dad'e akwai matsala ne?"
"Gagaruma ma kuwa, domin kuwa wannan yarinya Ameerah auren ta da wannan yaron Manniru zai yi wahala indai dole sai an mallake kakar shi za a yi auren, amma ba zan ce ba zai yuwu ba gaba ɗaya saidai ko zai yuwu ɗin to fa za a sha wahala,"
"Boka wai waye zai sha wahalar ne? Ni ko 'yata ko kuma su iyayen yaron ko wannan matsiyaciyar Saddeqar?"
"Kece wadda zata fi shan wahala a lamarin kafin 'yar ki ta biyo baya,amma kuma kar ku manta maganar bahaushe da yace...yi yafi rashin yi wai qazama tayi tsarki da ruwan d'orawa,daga qarshe dai za a ce tayi tsarki,"
"Da ruwan ɗorawar boka? Ai gwanda ta zauna babu tsarkin,ina sam ba zata sab'u ba,a bar wannan aikin a kama na babbar 'yata boka, ina so 'Ya ta Mommy ta auri wannan yaron Abdussaboor ɗan sarkin garin nan, sannan idan an sake binciko wata hanyar mai sauqi a taimaka min a na Ameerahn ma yarinyar nan kashe kanta take so tayi akan yaron nan Boka,"
"Kar ki damu ai ke kina sakin kuɗin aiki dan haka za a yi miki aiki da kyau,ko da ba ta samu auren wannan da kuke so ta aura ba za mu yi mata abinda zai sa ta manta shi ta samu wani tayi auren ta baki alekum,"
"Ni dama haka za a yi da nima hankali na yafi kwanciya dan har yanzu zuciyata bata son haɗa zuri'a da tsohuwar nan,idan yaso ita yarinyar nan Saddeqa a hana yaron auren ta kowa ya rasa,"
"Zamu yi me yuwa ku dai ku saki kuɗin aiki ku ga aiki,"
Su Innoh basu baro wajen boka ba har sai da suka tabbatar da za a sama masu mafita akan matsalolin su domin sun yi imani da shi, muddin suka kai masa damuwar su komai girman ta yana yi masu maganin ta,dan haka suka baro wajen shi ran su fess Naja ta wuce gida Innoh ma ta yi nata gidan.
Ko da ta iso gidan la'asar ta jima da wuce wa, domin kuwa qarfe shida na maraice yayi, Sule ta tarar yana zaune yana cin abinci sai zuba santi yake yi yana fad'in,
"Ni fa Allah na gani nafi son girkin Yadikona tin da can, sai kuma na Saddeqa da Baabaa, in dai Innoh tayi miya se ka ji gishiri ya zarce ko kuma wajen son a burge baba se a zabga mata shegen maggi, watarana kuma kaga mai nashe-nashe kana leqawa ka hango fuskar ka kamar madubi, tuwon kuwa idan ka yanko zaka iya jifa da shi goshi ya tsage tsabar tauri kaii....."
"Goshin uban ka na jefa da lomar tuwo ya tsage sule, nace goshin uban ka na jefa, shege sallamamme kwasasshe,ina can ina fafutukar yanda zan samawa 'yan uwan ka farin cikin su kai kana nan kana ɗebe min albarkar abincin da dashi ka ci ka girma, Sule idan baka fita a ido na ba na rufe se na....."
"Assalamu alaikum, Mommy na nan?"
Billy ta katse Innoh dake ta faɗa ta hanyar doka sallama, faram-faram ta shiga gidan kamar babu abinda ya faru ɗazu,Innoh na ganin ta da qatuwar jaka itama ta washe baki ta hau fad'in,
"Lale maraba da Bilkin Mai dusa, bismillah tana cikin d'aki na ko Sule? "
Ta qarasa Maganar ta da tambayar Sule inda Mommy take dan kuwa bata da masaniyar inda take a yanzu tinda itama dawowar ta kenan gidan daga yawon bin bokaye,Mommy ce ta fito tsakar gida ido yayi mata luhu-luhu saboda kukan da ta sha,tsayawa tayi tana kallon Billy da wani mugun kallo tace,
"Billy me ya kawo ki gidan mu kuma? Kin ga dan Allah ki tattara dik wani abinda ya kawo ki ki bar min nan bana son ganin ki,bana so na sake yin wata alaqa dani da ku har abada, kun koyar dani darasin rayuwar da ba zan taɓa mantawa da shi ba, dan haka bana buqatar duk wani abu dana same shi daga wajen ku,ki juya ki koma ki kaiwa wannan qaton banzan kayan nan dan kuwa bana so,"
Cikin wani irin yanayi Billy ta isa gaban Mommy ta riqe hannun ta ta qura mata idanu, kafin ta buɗe baki tace,
"Mommy ki kwantar da hankalin ki,shi kan shi k'waisan ya kore ni da kan shi, Man ne ya kawo mana kayan mu na gidan ta, ki Karb'a ki duba na tabbata duk wasu kuɗin ki suna ciki dan kuwa nima na ga nawa a ciki, kuma ATM ɗin ki ma na ciki kar ki yi wa kan ki da 'yan uwan ki asarar dukiyar da na tabbata basu taba riqe irin ta ba, ki...."
Wufff Innoh tayi ta amshe jakar ta na risinawa kamar zata duqawa Billy ta hau fad'in,
"Mun gode kedai 'yar albarka, Allah ya saka da alkhairi mun gode ki gaida min aminiyata Allah ya saka da alkhairi sai da safe,"
Billy ce ta kalli Mommy taga shigar dake jikin ta, wata riga ce mai siririn hannu an riqeta ta sama ta qasa ta baje amma dik da haka ana ganin shape ɗin Mommy fatar nan luwai da alama qasar da taje ta karɓe ta,tini ta cire gashin dokin dake kan ta asalin gashin ta ya sha parking, dan kuwa Mommy na da gashi dama rashin gyara ne ya sa yake danqarewa ta qeya ta gaba ya kwanta luwai, yanzu kuwa da ake gyara mata shi ya tashi ya miqe ya yi kyau, yawu Billy ta had'iya a ranta tana ayyana.
'Allah yasa Yah Abdul ya aure ni sai daga baya in sa ya auro ki Mommy in haɗa ku ku biyun ina morewa ta'
A zahiri kuwa sai ta dafa kafad'ar Mommy ta ɗan shafa tace,
"To Sweet H sai da safe, ki yi tunani da kyau wannan kuɗin halal ɗin ki ne ke kika nema da jikin ki, idan ma kin qi Karb'a an mayar musu a banza za su cinye ke kikai asara,dan haka sai da safen ku,"
Haka Billy ta tafi ta bar Mommy na gasgata maganar ta, dan kuwa ta san ta wahala da jikin ta kafin ta samo kuɗin to me zai sa ta bar wa su K'waisa? Da sauri ta fizge jakar a hannun Innoh ta shige d'akin Innoh ta zauna a bakin gado,ganin Innoh ta biyo ta d'akin ne ya sa tace,
"Dan Allah Innoh ki ɗan bani waje mana ina buqatar sirri kika san meye a jakar tawa? In kuɗi ne ni ba da kaina na fita nema ba dan na baku ku mora me zai sa na hana ki yanzu da aka kawo min har gida? Dan Allah ni ki fita idan na gama zan kira ki,"
Babu musu kuwa Innoh ta fita tana washe baki, Sule ne ya yage murya yace,
"Qanwata idan an gama nima ina nan ina jiran a yaga min wata salalar,"
Ba tare da Mommy ta amsa shi ba ta buɗe jakar waya da laptop ta fara gani a sama sannan ATM ɗin ta da ta bari a lokacin da zata bi Alhaji Uganda,hawaye ne suka sirnano mata saboda tunawa da Alhaji da cin amanar da yayi mata.
Tana d'aga rigar farko taga bandir ɗin dubunnai guda huɗu da sauri ta mayar ta rufe tana zare ido, leqa window tayi ta hango Sule da Innoh tsaye suna ta safa da marwa a tsakar gidan, shawara ta yanke akan bari ta d'akko bandir biyu ta boye
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 23 Chapter of 70