na ganki kuwa? Farha nasan kinsan menake ji, domin ke ba yarinya bace, kuma kinsan muhimmanci dad'ewar mutun bayada mata, bayan kuma yasan muhimmancin matar a rayuwarshi, toh wallahi ni kad'ai nasan yadda nake ji a kanki, hakan yasa nakeson na mallakeki a matsayin matata, mufito aiki tare, mu koma tare "
Duk'ar da kanta farha tayi, harda jawo hijab d'inta na uniform ta rufe fuskarta, domin yazo da sabon Al-amari zuwa gareta, tasan dai soyayya domin tayita amma batasan wani zance wanda yake fad'iba, domin bata ta'ba aikatashiba bale taji ya dameta tana nema, sai dai ita macce ce mai yawan sha'awa wanda tasan da wannan case d'inta tun kafin ta auri Anwar, da wannan zancen da oga hisham yayima farha, da zance ta rufe fuska ta bar office d'in nashi don kunya.
Kiranta yakeyi amma bata dawo ba, hakan ya k'yaleta tare da cewa.....
"Zan koreta ita kunyar a next month mai zuwa.
★★★★★
Watan Abdul-jabbar goma bai dawo gida ba, yana abuja zamansa, domin gudun fushin umma ya hau kanshi, tare da tilastashi abunda baiyi niyyar yiba, asashi yayi a halaka, domin duk wadda zai aura cutar ta kawai zaiyi, domin babu ita aranshi.
Hakan yasa koh yaushe cikin bugama baba waya yakeyi akan basu k'asar ne baki d'aya course aka turasu, amma da yadawo zai wucikke gida baki d'aya, kuma a gurin baban anan yake samun labarin gida da kuma yadda Ikram take, don har zancen shigarta school sai da yajiya gurin baba.
Baba yasan Abdul-jabbar zance ne kawai yakeyi, domin yasan yana nigeria, kuma shi yasan abunda yake ji akan rashin mata domin shima a tension d'in yake, don haka baya ganin laifin Abdul-jabbar, sai dai idan sunyi waya dashi yana jamashi kunne da nasiha akan ya kiyaye mutuncinshi, banda neman matan banza domin ba girman mutuncinshi bane, kuma idan yayi hakan bai kyautama kushewar Iman ba da Ikram, da kuma mahaifiyarshi, da hakan baba zai d'auki tsawon lokaci yana yima Abdul-jabbar fad'a, domin yasan yadda Abdul-jabbar ke da mugunyar sha'awa wadda tazamar mashi ciwo, sannan ya horeshi da yadaina umfani da pills d'in da yake sha, gudun gada su illatar mashi da gaba.
Idan baba yak'asa yima Abdul-jabbar fad'a, shima Abdul-jabbar d'in sai yayi godiya, sannan sai ya shaidamashi cewa, shi koh macce bayason gani bale har yaji suna burgeshi, insha'allah shi bayada niyyar tarewa da matar da ba muharramar shi bace, kuma zai kare mutuncin wa'yannan bayin Allah da ya ambata.
Kamar kullum yadda suka saba wayar, yauma Abdul-jabbar shine ya kira baban, lokacin baban yashigo gidan Umma tana shaida mashi zancen neman Auren farha da hisham yace zai kawo sadaki a cikin satinnan, baba yayi murna sannan yayi masu addu'ar dace na k'warai.
Yana cikin zancen cewa, shida yayan baban Abdul-jabbar zasu kar'bi sadakin insha'alla, kiran Abdul-jabbar shi ya katse zancen da baban keyi da umma.
'Daukar wayar yayi, sannan suka gaisa,hakan yasa baban kareshi da cewa.....
"Abdul-jabbar yau kenan kasamu sarvice d'in koh? Toh ga ummar ka ku gaisa, yanzu nashigo zancen auren k'anwarka farha "
Dum! Dum!!Dum!!! Gaban Abdul-jabbar ya fad'i, wanda yarasa menene dalilin fad'uwar gaban nashi hakan, amma yasan d'ayan zancen shine, idan tayi aure harda Ikram za'a bata? Toh wallahi bazai iya wannan aikinba.
Umma kar'bar wayar tayi kamar babu abunda yafaru, suka gaisa, ya tambayi Ikram, gudun gada ummar tace wani abu, harda farha d'in aka tambaya, Ummar tace "farha na gurin aikin, Ikram na makaranta"
Yace "alhmdullh"
Sannan ummar tace mashi, "Next month bukin Auren farha, don haka gudumuwar ka ga auren shine, kai zakayimata duk abunda uba keyima 'yarshi gurin aure, kuma umurnine ni nabaka, don haka koh a ina kake, k'arshen wannan watan kazo gida "
"Toh Umma insha'allah zanzo, kiyi hak'uri, kuma zanyi yadda kika ce, zan fara turo kud'in a fara sayamata abunda takeso goben"
"Toh Allah yayimaka albarka sai munjika "
Tamik'ama Alhaji Aliyu wayar sukayi sallama da Abdul-jabbar ya kashe wayar sannan yayi sallama da ummar ya wuce gida.
Sati d'aya dayin hakan mahaifin Doctor hisham ya kawo sadakin farha naira dubu d'ari, wanda saida baba ya nemi da arage sadakin domin yayi yawa amma mahaifin hisham yace su haka sukeyin sadakinsu, baba yayi addu'a tare da fatar Allah yasanya alkhairi a rayuwar auren, anan suka tsayar da ranar Auren 25 ga wata mai shigowa shine watan June, abu yayi dad'i domin iyayen Hisham sun tabbatar da uwayen farha mutanen k'waraine.
"Amarya kinsha k'amshi"
Furucin hisham kenan ga farha da yakirata a office nashi domin duba mashi patient nashi da case d'inshi yazamo mashi abun tsoro, shine tashigo yake zolayarta da kalmar "amarya kinsha mai, koh nace Amarya takusa shan mai "
"Hmm nifa banason wannan kirarinfa, gada kadinga hanani zuwa Asibitin nan, saboda tsoron zancen ka"
"Eyee, hakan kike burin yi ai naganoki, toh dake da hutu asibitin nan sai hutun cin amarcinki next month, yanzu dai kirik'aman takardun nan muje ki fara tayani aikin patient d'in nawa "
Kar'bar takardun tayi, tare da duba sunan patient d'in, nan take sunan ya hau saman idonta 'baro 'baro *ANWAR BALARABE NAIRA* Nan take tafara duba case nashi har da H.I.V ciki toh anan tafara shakkun ba wanda tasanin bane, sai dai duk wanda keda hankali zai fara tunanin wani abu akan rikicewar da farha tayu.
"Banason yawan tunaninki fa, gada ki sakani nima cikin damuwa, plz muje Nurse d'in doctor"
Murmushi farha tayi sannan suka jera zuwa shiga d'akin da Anwar yake kwance.
A nesa Hisham ya hango motar family nasu a k'ofar d'akin, nan take mamaki ya kamashi wanda sai da farha ta tambayeshi lafiyar hakan, yace mata "motar gidan mu nagani bakin block d'incen,shine nake mamakin faruwar hakan "
"May b sunsanshi, kaine baka sanshiba"
"Kuma hakane, mu k'arasa "
Shigarsu tabbas ya isko mahaifiyarshi da k'annensa guda biyu cikin d'akin, ga momyn Anwar nata rusar kuka.
Farha shigowa tayi, ta duk'a har k'asa suka gaisa da mahaifiyar Hisham cikin mutunci, itama nan take ta fahimci cewa itace farha d'inda aka kai sadakin aurenta, farinciki ya kama mahaifiyar hisham, domin farha ta ko ina tayi, tilon d'anta k'waya d'aya yayi dacen matar aure yanzu, domin ko ba komai daganin yarinyar akwai tarbiyya da kunya.
'Dagowar fuskar momyn Anwar sukayi ido biyu da Farha, ita firgita itama firgita, sakin bakin farha tayi tare da mamaki sannan ta koro mata tambaya cikin gaggawa, tacewa.....
"Waye bayada lafiya halan?"
Nuna mata Anwar tayi dake kwance baya gane kowa bale wanda ke tare dashi, hakan wanda yashigo idan yasan Anwar farko, A yanzu bazai ce shine ba, farha k'ara tambayar ta tayi cikin gidimewa.....
"Wai waye shi?"
"Anwar ne farha, yakoma hakan "
Cikin takaici da tuno wulak'ancin da yafaru da ita kala-kala wanda Anwar yajama rayuwarta, taja sunan tare da hawaye.....
"ANWAR! ANWAR!! kaine kazamo hakan? Toh Alhmdullh Anwar tun banje koh inaba naga yadda Allah kesaka ma bayinshi, ANWAR! Allah ya isarman tsakanina dakai sai Allah ya isa "
Mamaki ya kama mutanen gurin, hakan yasa shima Anwar d'in ya bud'e ido tare da kiran sunan "FARHA! Farha.......
Kash! yakasa k'arasawa domin zuciyarshi nantake ta buga, sai wani nishi mai k'arfi tare da ajiyar zuciya yace ga garinku nan.
Dasauri farha tafita d'akin tana kuka mai tsanani wanda batasan sadda labarin baya ya dawo mata farko ba.
Fara dubashi doctor hisham yayi, yagane ai Anwar ya rasu a dalilin shak'ewar da yayi, ya shaida masu sannan yafita da sauri zuwa gurin farha domin yaji wanene Anwar a rayuwarta da take yimasa Allah ya isa, kuma menene dalilin hakan?
Ko da yafito baiga farha ba, sai cen ya hango motar ta tafita asibitin da sauri, office nashi yakoma domin d'aukar wayarshi ya kirata.
Fitar Farha da Hisham yasa mahaifiyar Hisham tambayar Momyn Anwar cewa....
" Halan menene tsakanin Anwar da Farha wanda take jamasa Allah ya isa hakan, kuma shima da ganinta kawai gashi ya rasa rayuwarshi, meke tsakaninsu Hajiya ?"
Momyn Anwar saida tatsaya da kukan nata sannan ta d'ago tace.....
"Itace tsohuwar matarshi wadda suka rabu "
Mahaifiyar Hisham ta zaro ido, domin zancen yazo mata a bazata...........
Toh fa! Anwar anwuce da kaya bisa kai, Allah yajik'anshi toh, kuma ga wani rikici zai 'bullo kai.
Toh dai gamu ji da gani yanzu.
_Nagode da addu'oin ku, nasamu lafiya sosai, don haka gani gareku masoya na, ku 'ballani ga'ba ga'ba_🤣🤣
_page biyu ne guri d'aya, na jiya da yau da gobe ma😝_
*Bee Been Masoya*💞
💧💧💧💧💞💧💧💧💧
*SO NE......*
*DALILIN HAWAYENAH😭😭*
💧💧💧💧💞💧💧💧💧
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
©®
Khadija bee bee
Khadijabeebee@gmail.com
My wattpad user name.... *khadijabeebee......*
My Facebook page....
*beebeenmasoya*
*I LUV YOU ALL MY FANS*
💋💋💋💋💋
★TRUE LYF STORY★
★★★★★★★★★
*I have the "I",I have the "L",I have the* *"O",I have the "V",I have the*
*"E",... so pls can I have "U"?*
_Answer
Mee my funny lovers_😂😂😂
Page...
★5⃣4⃣★
Da sauri farha ta fad'o gida tana kuka,Umma da sauri ta tareta domin ita kad'ai ta ganta bataga Ikram ba.
" Farha lafiya, menene haka?"
"Umma Alhmdullh! Umma A yau Allah ya amshi addu'a ta, Alhakina yafita gurin Anwar, umma a yau naga yadda Anwar yakoma qasqantace a duniya, duk wanda yasan Anwar abaya, a yau bazaice shine ba, k'arshe kuma ni nasan bazai rayuba, domin cuta ukku nagani file nashi yau, don Haka ina murna a yau kuma ina bak'in cikin tarihin rayuwar danayi a baya ya dawo man sabo Umma"
"A Ina kikaga Anwar d'in?"
"A asibitinmu, doctor hisham shine likitan dake dubashi, hakan ya umurceni da na tayashi duba patient nashi, ina shiga d'akin sai naga momyn shi, anan nagane Anwar ne, kuma ya ambaci sunana, umma bazan iya yafema Anwar ba"
"Ah ah farha, ai shi Allah gafururrahim ne, gada kice hakan, ki zamo cikin masu yafiya a rayuwarki ta duniya, ki tuna shi yasaki aikata duk laifin da kikayiwa iyayenki baya, kuma kika gane kuskurenki aka kuma yafeki, sannan kuma yanzu gashi kinfishi komai a rayuwar duniya, kin d'ara Anwar tako ina, don haka ki furta kalmar yafiya gareshi, koh zaki samu babban rabo nan gaba farha"
'Dago fuskarta tayi, itama umma ta kalleta, sannan umman tayi murmushi, nan take farha itama sai taji sanyi a zuciyarta tace......
"Umma na yafe mashi, domin Anwar bazaikai labari ba a yadda naganeshi yau"
"Toh kingani farha nah, Ina d'iyarki? har 12:30 ba'a d'aukota ba "
"Subhanallah! Wayyo Ikeey nah! Wallahi umma duk na rud'e, domin ita na fito d'aukowa amma duk tunane ya mantar dani, zan koma yanzu na d'aukota "
Fita tayi da sauri, abun mamaki! Kuma sai ga hisham da Ikram a gaban motarshi, tsayawa farha tayi tana murmushin ganin Ikeey d'inta, bud'e motar yayi ya d'auko Ikram tare da lunch box nata ya mik'ama farha ita, Ikram sai murna takeyi itama uwar tata murmushi tayi tare da yimata one kiss a goshinta.
"Ikeen Aunty farha, uncle ya fanshi Auntynki koh?"
Dariya tayi da nuna mata abunda ya siyamata a hanya, murmushi farha tayi tare da kallonshi, shima shi yayi mata, sannan yace....
"Ki kaita gurin umma, kizo muyi magana "
Ba musu farha ta shiga da ita ciki, sannan ta cire mata kaya tare da watsa mata ruwa ta bata abinci tace ta zauna gun umma yanzu zata dawo, ikram d'in ta yarda.
Fitowa tayi, sannan ta bud'e mashi gurin da bak'i ke sauka kamar yadda suka saba kullum, sannan ta zauna ita.
Duban farha d'in yayi, sannan ya k'ara duban ta cikin so da jin amsar tambayoyin da zaiyimata.
"My teemah wanene Anwar a rayuwarki?"
Farha juyar da fuskarta tayi gefe tare da zubar da hawayen idonta kafin ta juyo ga Hisham, d'agowa tayi tana sharar hawayen nata, da sauri hisham ya taso inda yake don matsowa kusa da farha, domin yaji answer d'in dai-dai, duk'awa yayi sannan yace.....
"Kibani answer d'in tambayata farha, ina cikin gid'emewar wannan al-amari fa"
"Anwar shine mujin da na aura farko "
Bud'e ido Hisham yayi, sannan yaji duk'i ya kasa d'aukar k'afafunshi, don haka ya koma ya zauna, ya k'ara dubanta yace.....
"Farha tsohon mujinki fa kikace?"
"Eh shine, amma duka auren namu baifi 5month ba muka rabu,saboda bashida mutunci?"
"Innalillhi wa'inna ilaihirraji'un! Farha Anwar na d'auke da cututtuka har ukku fa, wanda a sanadin sex duka ake samun su, kinsan da hakan domin kin karanta a file nashi, toh ya zamuyi yanzu ?"
"Dame hisham? Kana nufin duk inada cutar da yake da ita kenan? Saboda na ta'ba aurenshi?"
"Koh d'aya farha, hassali sonda nake yimaki,wallahi ko da ace kinada d'aya daga cikin cutar zan iya aurenki, sai dai matsalar kuma mahaifiyata da nasan dole taji dalilin Allah ya isar da kikayima Anwar, wanda dole wannan zancen zai biyo baya, kuma wallahi ni nasan mahaifiyata Irin sonda take yiman ba k'arami bane, amma a irin wannan zan samu wuyar shawo kanta farha "
"Innalillhi wa'inna ilaihirraji'un! Anwar Allah ya sakaman, gashi ka 'batan suna da martabata, tun banje koh ina ba, gani zargin abunda banida shi zai bini a duniya, Allah ka sakaman tsakanina da kai "
"Farha ba kuka bane mafita a rayuwarmu ba, mafita itace, mutashi muje asibiti a yimana test kawai, domin a gano inda matsalar take "
Mik'ewa farha tayi da sauri, tare da rufe bakinta da kuka ya fito mata bata shiryaba tace......
"Hisham kaima zargin ciwon nashi zaka fara a kaina kenan? Tun kafin jama'ar duniya susan da abun da ke faruwa?"
"Ah ah farha, ki tuna aikinmu d'aya dani da ke, koh ba don wannan zancen ba, wajibi muyi test d'in junanmu akan kariyar kanmu baki d'aya, farha na fad'amaki, wallahi koh kinada wannan cutar duka da ke jikin Anwar, wallahi zan iya aurenki, kuma zan nema mana maganin da zai zamo kariya garemu baki d'aya, burina shine, koh da zancen yaje kunnen iyayena nabasu test namu shaidar ba kida komai da zasu so bincike ciki "
"Maganar zance itace hisham, ni Anwar baita'ba sanina a matsayin macce ba, hakan wani ma, ban ta'ba sa'bama Allah anan ba, Inason kasan cewa Anwar d'an homosexual ne, tsawon zamana da shi baita'ba kusantata ba akan wannan mu'amalar, domin ba itace gaban shiba, kuma zan bika muje muyi test d'in,amma ba wai don kowa ya yarda da zancena ba, sai don kai kagane gaskiyar zancen da nayi maka "
"Farha kina nufin alak'ar aure bata ta'ba had'aki da Anwar ba?"
"Ehh, ni ba ta'ba yin wani abu irin wannan ba "
"Alhmdullh! Farha Alhmdullh! Don Allah kiyi hak'urin tuhumar danayi maki, wallahi nima a rud'e nake fatima domin gudun gada muyi aure a duhu, amma duk da hakan koh don mahaifana zamuje asibiti a yimuna test, please fatima don Allah gada ki bari wannan abun ya zamo wata damuwa a zuciyar ki, wallahi ni inasonki ko da kuwa kinada wata cutar a ciki bale kuma baki da koh d'aya, please my teemah kishare hawayenki, ni zanzamo maki sanyi a rayuwar ki, ki fad'ama umma zamuje mudawo, amma bazaki shiga gida kina wannan share hawayen ba, ki zauna na sakaki dariya "
"Hmm! basai na shiga ba, domin Ikram zata lik'emani, amma zan kira umma d'in sai na fad'amata "
Haka akayi kuwa, ta kira umma ta fad'amata zata koma asibiti, amma yanzu zata dawo, Umma tayimata Allah ya kiyaye hanya.
Motar doctor d'in suka shiga, don zuwa lab. d'in.
Shigarsu asibitin ana fita da gawar Anwar d'in, sai a lokacin hisham ke shaidama farha rasuwarshi tun d'azun, "Alhmdullh!"
Furucin farha kenan da tayi kawai.
Suka shiga lab. Duk da tsoron Allurar da farha keyi, amma a wannan lokacin komai batajiba, doctor hisham shi ya d'ibi jinin farha da kanshi aka fara yimata gwajin a gabanshi itama a gabanta.
Alhmdullh! farha test nata ko ciwon maleria ba'a ganiba ciki, don har nashi test d'in shi hisham anga fever ciki, toh ita komai babu tare da ita.
Hisham yayi farin ciki, haka itama sannan suka fito tare da test d'in hannun hisham, ya d'auketa sai gida ya ajiyeta.
Tunda akayi rasuwar Anwar, hisham bai k'ara zuwa gidan mahaifanshi ba, domin shirin lefen farha da yakeyi, ya had'a komai da komai sai abunda ba'a rasaba aciki, wanda koh ya tambayi farha d'in sai tace yayi duk abunda ya kamata ita komai yayi ai so takeyi.
A yau yashirya domin zuwa gidansu zancen kai kayan auren farha gidansu, shigarshi gidan yafara shiga d'akin mahaifiyarshi suka gaisa, sannan yafara yimata bayanin abunda ya kawoshi, nan take ta amsa da gobe sai akai insha'allah, sai kuma ta k'ara kiran sunan hisham d'in tace....
"Hisham shin kanada labarin yarinyar da zaka aura, itace tsohuwar matar Anwar dan gidan balarabe naira?"
"Eh umma, nayi bincike akaima, kuma alhmdullah, ba wani dad'ewa sukayi ba, domin kinsan bayada mutunci a lokacin, kamar yadda bincikena ya nunaman, duka 5month sukayi suka rabu, amma umma ni bansanshi agidan bala naira ba, dama yanada yaro namiji?"
"Ehh, bazaka sanshiba, domin lokacin baka k'asar nan gaba d'aya, shikuma a jidda suke zaune, sai aka dawo dashi nan gurin kakanninshi, sukuma suna cen jidda d'in, kaga ba lallai ka sanshi ba, sai dai nima bansan lokacin da yayi aure ba, duk da amincin da mukeyi da mahaifiyarshi "
"Ok toh Allah ya taimaka, anjima zan shigo da kayan, sannan zan bada kud'i abunda babu ciki sai a k'ara saya "
"Toh insha'allah za'a fad'oma gwaggwanninka sai su zo goben "
"Toh umma nagode, zan koma domin inada night duty yau "
Sukayi sallama, ya wuce, itama tayi ciki.
Iya matuk'a wannan rashin gane dalilin rasuwar Anwar yayima Hisham dad'i, domin harda takardar test na farha yake yawo a aljihunshi, amma kuma rashin sanin nata yayi matuk'ar burgeshi, da farinciki ya koma gida ya cigaba da shirin kayan domin akai a huta, yaga nawar a d'aura ya wuce gurin kawai.
Farha nashiga gida ta fara fad'ama umma rasuwar Anwar, umma tayi mashi addu'ar samun rangwame, taci gaba da aikinta, Ikram barci takeyi a kujera hakan yasa itama tayi ciki domin watsa ruwa koh zataji sanyi, duk da tana cikin farin ciki.
Week da hakan, Aka kawo lefen farha, kaya alhmdullah, komai har yafi na budurwa, suma su umma sukayi harkar karamci irin wadda akeyi idan ankawo kayan aure, komai cikin nishad'i da walwala, ango da amarya suna shauk'in junansu, domin kowa nason d'an uwanshi.
Lokacin da aka kawo lefen aunty hafsart da yan uwan mamarsu farha d'in duk suna nan, suma sunyi farinciki na yadda ba'a tsammani domin sunsan koh da suka yi rashin 'yar uwa, sunsamu madadinta, wato Umman Abdul-jabbar, hakan yasa sukazo da nasu shirin akan 'yarsu tunda sunsan ta ta'ba aure, don haka sukazo da kayan da zasu gyarata kafin lokacin.
Farha gyara takesha na k'in k'ari, domin har hutu ta d'auka domin shirye shiryen buki.
Abdul-jabbar ya cika alk'awalin da ya d'aukarma umma, domin shi yabada kud'd'in da za'ayi duk wata hidima ta auren farha, koh ba komai, tukuycin renon Ikram ya wuce hakan a gurinshi, domin tayi duk yadda akeyi, sai dai shi har yanzu rayuwarta ce kawai at bata yimashi ba, hakan yasa koh yaushe bak'in farha yake gani a rayuwarshi, domin baya manta miyagun kalamanta akanshi, zai iya manta komai amma banda zagin da tayi ma mahaifiyarshi ido da ido, hakan yasa koh yaso ya manta da abunda tayi mashi, sai yaji abun ya dawo mashi sabo.
K'arshen watan anata hidimar buki, koh wanne 'bangaren sunata hidima, hakan kuma Abdul-jabbar week d'in ne ya sauko kaduna domin cika umurnin umma, sai dai 2days zai koma domin akwai abunda zai yi, kowa yayi murnar ganinshi domin ya changr sosai, yayi kyau ga haskenshi ya fito kamar ba shiba.
Tunda ya shigo, gidan baiga farha ba, bale Ikram, suna cen suna hidimar bukinsu, domin za'a fara program, suna gidan rasheeda, duk da tanada tsohon ciki amma kuma da ita akeyin komai, domin duniya a k'awance babu wadda farha keso kamar Rasheeda, domin itama tana sonta, ahaka suketa gabatar da komai cikin tsari, farha najin dad'in yanayin domin tanason Hisham sosai, Rasheeda itama tak'ara nasihar ta akan farha, tare da zolayarta, hakan farha kesata gaba tayi ta tambayarta cewa....
"Rasheeda first nyt nada wuya koh?"
Rasheeda tayi mata murmushi sannan tace...
"Eh, amma gareki tsohuwar gwarruwa mai mugun sha'awar taji yadda ake ji, ai bazaki ji wuya ba, sai dai dad'i "
"Dad'ina dake rasheeda, koh yaushe cikin sharri kike k'arema mutun magana, toh amsar ma banaso idan naje ai zangane, kuma nasan Hisham d'ina nasona bazai wahalar dani ba "
"Eh naji dai, wallahi zakiyi bayani, indai namijine, bale shida yata'ba yin wata matar kinga yasan k'ofar abun iri-ire, don haka zaki sani "
Dariya sukayi dukansu, sannan farha taja hannun ikram tare da d'aukar makullan motar da tazo da ita ta umma, da kuma rataya hand bag d'inta suka fito, Rasheeda nayi masu rakkiya har bakin k'ofar fallow d'inta.
Sanya Ikram tayi sannan ta jefa teddy d'in dake hannunta baya da bag d'inta ta tayar da motar zuwa gida.
Kafin ta wuce, sai da ta tsaya wani shop ta sayama Ikram kaya masu kyau, saboda cin buki, sanna ta saya mata ice cream da sweet suka fito.
Shigarsu gida Abdul-jabbar na harabar gidan zaune yana waya da kareema, wadda ke bala'in sonshi cen abuja, k'anwar matar Abdul-hafiez ce.
Hango shigowar motar tasu yayi, ikram ce gaba, farha na driving, cigaba yayi da wayar hankalinshi kwance, itama farha hankalinta kwance tafito motar, Ikram na hango Abbanta da gudu ta rungumeshi, farha kuma kwaso kayan tayi a hannunta tare da takowa zuwa inda yake, ta d'an tsaya daga nesa ta gaidashi tare da godiyar abunda akace shine yayi mata.
Kashe wayar yayi tare da cewa.....
"Zankiraki anjima, yanzu ina busy ne"
Tab! Wani kishin yar uwarta ya taso mata, wayyo Iman! Haka farha tace a zuciyarta, sannan ta k'ara gaidashi tare da maimaita maganar godiya, amsawa yayi sanna yace mata babu komai, ba tareda ya kalleta ba, sai ikram da ya'aza a k'afafunshi, suna fira.
2 days na cika Abdul-jabbar yafara shirin komawa Abuja, domin yanason yakai k'arshe da kareema, akan tayi aurenta gada ta tsaya jiranshi, domin bai shirya aure yanzu ba, ya sanar da umma komawarshi abuja, saboda yaga gidan duk anfara cika, ga program anfara gabatarwa, jibine d'aurin aure, gara ya tsere kafin dangin mahaifinshi su risk'eshi gidan, za'ayi babu dad'i, bale yayan babanshi.
Yasanar da umma tace babu inda zayaje domin sai anyi d'aurin auren farha da shi, yaji bak'in cikin wannan rantsuwa da ummarshi tayi, domin dole ya bi umurninta, hakan yasa tunda aka fara hidimar sai ya tare gidan basheer, domin shima yayi aure yanzu, acen yake yini sai cikin dare yake dawowa.
Ana jibi ne d'aurin aure, mahaifiyar Hisham takirashi a waya tace yazo da sauri tana kiranshi, gasunan a fallow harda mahaifinshi, ko da aka kirashi suna shirin zuwa party ne, hakan yasa ya basu hak'uri da andawo komai dare zai sauka gidansu, mamar tashi tace yanzu takeson yazo, mahaifinshi yace ta barshi idan ya tashi sai yazo, aka bar zancen akan hakan.
Bayan antashi party d'in bai 'bata lokaciba, domin farha kawai yakai gida ya wuce gurin iyayen nashi.
Shigarshi yayi d'akin mahaifinshi, nan take mahaifinshi ya fad'amashi dalilin kiran da cewa.......
"Hisham na haramta maka auren yarinyar da za'a d'aura maku aure da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 27 Chapter of 44