Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Bayan kece ke yima wasu wa'azi akan su daina,amma gashi ynx kin fara, toh ki daina kiyi mata addu'a shine abu mai kyau, kuma kune ya kamata kubama mama hak'uri akan rashin da tayi, ba ku k'ara saka ta kukan ba, kiyi hak'uri Allah yayi mata rahama " Share mata hawayen yayi sannan ya zaunar da ita, yace ta d'auko mayafinta su shiga gidan umma suji yadda tafiyar zata kasan ce, ya koma kitchen ya kashe komai da komai, tun da dama ta k'arasa aikin wanke kayan da ta'bata ne take yi,banda yaje ya dameta da tuni ta k'arasa. Dawo wa yayi ya rik'a hannun ta suka shiga part d'in umma, Ikram na ganinshi da gudu ta zo yi masa oyoyo, ya d'auke ta, koh da suka shiga gidan d'akin umma suka shiga, lkchn tana had'a kayan ta a k'aramar jikka, domin zasu kwana biyu basu dawo ba. Abdul- jabbar yayi sallama ya shiga da shi da iman, umma ta d'ago ta kalle su tace.... "Dama baban ku yace ku d'aga tafiyar nan taku ga yau, sai jibi sai ku tafi, tun da ga rasuwa anyi, kaga bai kamata ace iman bata je ba, kuma kaima ya kamata kaje ayi komai da kai, don haka ku shirya yadda zamuyi tafiyar, don ynx baban ku na nan tafe sai zamu wuce" "Toh ummah, gsky ni daga yau idan ban koma Abuja ba zanyi hasarori masu yawa, domin tun shaikaran jiya ake ta kirana ina bada hak'uri akan yau zan shigo, toh tun da har hakan ta kasan ce, ni ayi man uzuri na koma,ita sai aje da ita, insha'allah idan nadawo _next to week_ sai mu wuce tare kuma nayi gaisuwar, ynx zan yima mama da baba idan sun shigo " "Toh babu komai tun da uzuri ya shigo ciki, kuma sai ayi bayanin rashin zuwan naka, kuma dama farha nasan bada ita za'aje ba, domin tana jarabawar k'arshen aji,wadda daga ita sai fara aikin ta na nurse, kuma itama za'a fad'i nata uzuri domin idan taje kuma ta dawo baya, kuma hakan yayi tun da mu munje ai shikenan " Ahakan aka kai k'arshen tafiyar ta su, shi bada shi za'a je ba, idan yadawo sai ya wuce da iman d'in. Iman ta fara magana da cewa... "Umma dama mun yanke shawarar yaye Ikram sbd wasu matsaloli da suka gitta yasa ba muyi ba, amma yanzu tun da ba da yaya farha za'ayi tafiyar ba zan bar ta gurin ta har mu dawo, kin ga koh da zamu dawo ta manta da nonon baki d'aya, duk da bata damu da shi ba " Abdul-jabbar da sauri ya dubi iman da cewa "ya za'ayi hakan? Bayan kinsan cewa tafiya zakiyi sannan kuma ki barta?" Da sauri umma tace... "Ah ah babanah, baka san uxurin ta ba akan yayen, domin nima naga dacewar hakan, sbd nafara ganin alamun ciki ga gare ta, toh ka koh ga gara a rabata da nonon da wuri, kuma hakan shine yafi,koh da zata dawo ta manta, kaga sai ku koma abujar cikin sauk'i batare da kun wahala ba " Sai ynz abdul- jabbar ya gane nufin umma, _it means_ dai iman na da juna biyu at bata shai da mashi ba? Shiru kawai yayi sannan yace.... "Toh shikenan umma , nima 4:pm jirgin mu zai tashi, nata bucking d'in sai a changr shi, kuma zan bar kud'i duk abun da ya kamata sai ayi, ita kuma ikram d'in a saya mata abun da ya kamata " Umma tayi godiya sannan, sanna ya ciro kudd'in masu yawa ya bama umma , sannan ya k'ara akan wayan da za'a saya ma ikram abincin da take ci, domin tym zai k'ure idan yace yaje ya siyo. Suka mik'e, amma ikram koh tayi alamar zata bisu, zaman ta tayi gurin umma tana wasa da kudd'in da abban ta ya bada ynx, umma ta kalketa tayi murmushi tace "takwaran umma kin fi sona da iyayen ki koh?" Dariya ikram tayi, domin bata san me take cewa ba. Abdul- jabbar duk yaga iman ta yi wani sukuku, da alama rasuwar duk ta shiga jikin ta sosai, kuma gashi yaji umma tace iman nada ciki, toh koh tafiyar zata iya yin ta kuwa? Domin baya son abun da zai ta'bi cikin da lfyr matar tashi guda d'aya tak, k'arasawa yayi gurin da take tana cire kayan tafiyar, ya riqa hannun ta cikin hikima ya fara magana.... "Momy ikram! Me ke damun ki ne wai? Idan bakya iya tafiyar abar ta mana, naga duk kin bi kin wani changr, ni ban damu ba amma ke duk kin damu, fad'aman meke da munki?" 'Dagowa tayi da fuskar ta ta dube shi, sannan ta mik'e daga had'a kayan zuwa saman jikin shi tace... "Abban ikram nifa koh rasuwar hajiya ne, ta shiga jiki na sosai, sannan kuma ina tunanin yadda mama take ji yau na rashin mahaifiya, duk da nasan ldan lokacin mutun yayi dole sai ya tafi, amma mama kawai nake tunani, kuma kaima nafi son muyi tafiyar nan tare, wlhy banason ba ina nesa da kai, domin kazama jinin jiki nah, hasali kuma ga new babyn ka da nasan ynx yana cikin 1month, kuma kasan babyn nan wlhy tun da na same shi, bai ta'ba hana ni naji ina buk'atar ka kusan ceni ba, shi da ban yake da na d'iyar ka ikram wanda yabaka wahala sosai, hakan yasa koh yaushe, jinka nakeyi har cikin raina, kasan ynx nasan dad'in abun fa " Sakin baki yayi yana kallon iman, yaushe tazama haka? yaushe iman ta iya wa'yannan kalmomi haka? Murmushi yayi sannan yace... "Momyn ikram! Kece kuwa? Domin kin fara mantar da ni inda nake, anya bazasu tafi ba, na kaiki da kaina ba, idan dare yayi na kama hanya ta ba, ga bad'aya naji bazan iya barinki ki tafi hakan ba, dole mugana da sweet babyn da aka 'boyan ba'a fad'aman ba " "Hmmmm! Koh ba kace ba, nima sai na baka kaina, nima ka shayar dani zumar da zanje amsar gaisuwar mutuwa ina tuna ka, don haka gani gare ka kafin su mama su k'araso, tun da na gyara " Abun kamar wasa, domin Abdul- jabbar ya d'auka wasa iman take yi, shiya sa ya tsaya yana kallon ta cikin mamaki, cije le'bensa na k'asa yayi yana kallon ta, mik'ewa tsaye iman tayi sannan ta juyo zuwa gare shi, ita da kanta ta kamo kan shi ta saka bakin ta cikin nashi, tafara wasa da halshen shi cikin k'warewa, nan take abdul-jabbar ya kar'bi sak'on iman, domin abun nema yasamu, a farko ya d'auka wasa take yi, amma wannan alamar kad'ai ta tabbatar mashi da gskyr zance. Rik'ota yayi sosai, tare da mayar mata da martanin abun da take yimashi, nan take duka jikin su ya amsa sak'on masoya, jikin abdul- jabbar har rawa yake yi sbd tsananin buk'atar hakan, Rik'o iman yayi sosai, tare da mayar da ita saman gadon nata, yayi mata runfa da jikin shi, nan yafara changr salon wasar izuwa nema rabata da kayan jikin ta, itama hakan tayi ta taimaka mashi suka cire baki d'ayan su, daga su sai numfashin su domin shi kad'ai ne kariyar samun k'arfin su anan. Iman najin dad'in abun sosai, domin abdul yasan ta yadda yake sarrafata har sai ta fara sauken nata feeling d'in sannan shi yafara ga batar da nashi. A soyayyar junan su, suka tafi, abdul jin iman yake yi kamar yau ne rana ta farko da ya ta'ba shiga jikin ta, domin acikin ni'ima ya taru yayi kwance, sabbatu yake yi wanda shima bai san me yake cewa ba don dad'i, hakan itama yau dana ta sabbatun wanda takasa rik'e kanta domin nishad'i. Abdul-jabbar addu'a kawai yake zubo ma iman tare da sanya mata albarka, tare da yi mata alk'awalin da ita da umma hajjin bana dasu ciki, kuma yana zancen da gsk amma kuma tsananin k'aunar iman itace ke bayar da kyautar a halin ynx, domin dama yayi niyyar hakan. A hakan suka gusar da sha'awar junan su cikin qwarewa, amma duk da hakan Abdul-jabbar yakasa sakin k'irjin iman domin ga ninsu yake kamar sabuwar duniya, kamar bata ta'ba shayar wa da su ba. Iman bayan ta natsu, sannan take ce masa a cikin kunne.... "Ka sakan hakan mana, gada su mama su iso ban fita ba, kuma kaga idan suka zo bani da damar yin wanka, sai dai nayi alwallah kawai muje, idan naje nayi wanka a cen,kuma kaga babu kyau zama da najasa" "Momyn ikram, zan yarda da tafitar nan kuwa? Wlhy da ba dole bane, iman bazan iya rabuwa dake ba yau, a haka zamu kasan ce, ki yi ta yiman kalar abun da kika yiman ynx, naji dad'insa sosai wlhy, har ji nake kinfi koh yaushe dad'i, amma dole na hak'ura har ku dawo, nazo na d'au keki" "Ni ai nafi ka jin dad'in ka, domin yau lokacine na bak'in ciki, na mun rasa kakar mu, amma kuma ranar farin ciki ne gare mu kuma, domin gashi kayi mana kyautar kujerar hajji ni da umma, ai farin ciki nah babba ne a yau, sai dai dole na 'boye hakan sbd girma ta'aziyyar da zamuje,amma Abban ikram yasani cewa Iman yak'arasa mata komai aduniya, kuma k'aunar sa, ako da yaushe k'aruwa take yi, sai dai kuma iman na k'ara shai da mashi ta tsani kishiya, ta tsani wata tazo ta ra'bi wannan ni'imar indai ba iman ba, domin sandar girma sandar amincin nan gare ni kad'ai take da umfani, duk wadda ta kuskura ta ra'beta ba komai zata k'aru da ita ba, indai bada izini na ba" Dariya abdul yayi wadda k'ila tun da aka haifeshi bai ta'ba yin irin ta ba, domin yau iman ta zauce sosai, lallai yayi aiki, wai sandar girma, sandar aminci, _it means_ tana nufin alk'alamin rubutu na kenan, ya rubuta mata kishi a gidan girma, hakan yasa ya kasa cewa komai, sai jinjina kai kawai yayi zancen ya shigeshi iya matuk'a. Iska ya shaqa ya furzat da bakin shi, sannan ya d'auke ta sai toilet, acen ma wanka akayi da yad'a k'auna suka fito, shine ya shirya iman da komai da komai da zata je da shi, sannan ya cire kud'i masu yawa yasa ka mata a hand bag, shima ya gyara nashi kayan tafiya, sannan ya duk'o zuwa gare ta yace.... "Babu wata matsala koh?" "Eh komai nomal Abban ikram, sai dai zan bar makullan part d'ina a hannun yaya farha, sbd idan ikram na buk'atar wani abu daga kayan ta, duk da tana da su a cen gidan, amma zan bar shi sbd kada yafad'i ma, kuma kai ma baka nan bare na bar shi hannun ka " "Duk yadda kika so hakan za'ayi, sai kuma menene?" "Sai ka raka ni part d'in umma " "Abincin fa?" "Ai ka ciyar da ni da guri mai mar taba " "Duk da hakan ki k'ara wani gada baby ya wahalar man da ke " Ta miqe ba musu har zuwa dining, anan suka ci suka sha sukayi hamdala, anan ringin d'in wayar shi ya shigo, kiran baba yagani ya d'aga, baban yace... "abdul ku ake jira mun iso kufito" Amsawa yayi, tare da shiga yad'auko bag d'in iman, ya riqa hannun ta suka yi part d'in umma. Shigar su suka ga kowa da kowa atsaye, ikram na jikin farha hankalin ta kwance, mama fuskar ta tayi jawur sosai, sbd kuka,iman duka ranta 'bace yake kuma tasan hakan dalilin rasuwar ne da damuwar mama a hakan, farha ma taci kuka iya matuk'a domin ita har k'uduri gare ta na taje ta gano ta idan sun k'arasa wannan mugunyar exam d'in, amma Allah bai yi ba. "Toh Abdul-jabbar zamu wuce, domin da la'asar za'ayi jana'izar, kuma muna son musamu, ace kai bazaka samu zuwa ba sbd aikin naka da babu uzuri gobe, kuma kayi niyyar zuwa da matar ka, gashi uzuri ya hana tafiyar, toh sai kayi hak'uri, idan andawo, ni da kaina zan sakata jirgi sai ka tare ta a cen insha'allah, kuma ance za'abar amarya ta gurin mamar ta, toh Allah ya taimaka yasa anyi cikin yawan cin rai, ita kuma hajiya Allah yayi mata rahama " Duka suka amsa da ameen, sannan umma tace... "Nayi magana da Talatu mak'wabciyar mu, akan tun da mijinta ya rasu, kuma ba wani aiki take yiba, ta dawo nan tana taya farha zama duk da ba dad'ewa zamuyi ba, amma zama mutun d'aya babu dad'i " Kowa yayi na'am da hakan, kuma shawar tayi, a ka shirya fitar da kayan domin driver shine zai kaisu, sbd asamu sauk'in tafiyar. Iman da sauri ta k'arasa gurin farha, tabata makullan d'akin ta, sannan ta rik'a hannunta tace... "Yaya farha zamu tafi, ga makullan d'aki na nan idan akwai abun da kuke buk'ata na ikram, duk da nasan baza'a rasa komai ba, amma kuma ai gara na barshi gudun gada ya fad'i, ikram toh momy sun tafi gaisuwa, banda yima yaya farha rigimar nono domin bata dashi na baki,kuma nono kin yafe ma k'annenki masu zuwa koh?" Wangale baki tayi tana dariya wanda sai da dimple nata yafito, iman tayi mata bye bye, kuma koh ajikin ta ta damu, domin dama bata sha mata kai ba. Farha nat biyo bayan iman har suka shiga mota, su ukku baya baba da driver gaba, Abdul- jabbar gefen da iman take anan ya tsaya, sannan ya duk'o ta yarda ba za'a gane ba, yace ma iman a kunne tare da riqo hannunta yace..... "My sweet safe journey" Murmushi tayi ta kalleshi tace, "ameen tanx" Ya rufe k'ofar aka tada motar suka bar get d'in, juyowa yayi yaga ikram hannun farha, sai yayi kamar bai gansu ba, ita kuma sai so take yi a ajeta taje gurin shi, farha ta sauke ta qasa, da gudu taje gurin shi ya bud'e hannu ya d'auke ta, sai dariya take yi, farha barin su tayi taje part nasu domin gyara gurin da ikram ta 'bata, shikuma ya wuce da ita part nashi domin gyara tashi tafiyar. Nan take yaji gidan gabad'aya ya ishe shi, nan take ya gyara komai a jikkar shi, domin rasuwar nan tazo mashi da tikas wlhy, duban ikram yayi tanata wasar ta hankali kwance, tana cin biskit d'in da ya bata, kuma sai tadawo jikin shi ta zauna. Kissing nata yayi a goshi, sannan yace.... "Ikeeyn Abba, hankalin ki kwance, momyn ki tayi tafiya,amma abban ki duk yadamu da rashin ta kusa, toh Allah yadawo mana da su lfy koh?" Dariya kawai tayi, sannan ya duba gurin da yagama murzar iman yanxu yayi murmushi, yace.... "Missing love, yau zan kwana abuja takure wlhy " Gyarawa yayi sannan ya rufe koh ina da koh ina na gidan tare da kashe glubs d'in gidan, ya d'auki ikram ya shiga ciki da ita, shigar shi yaga wata a zaune, da alama talatun da akace ne zata taya farhar zama,suka gaisa da ita, sannan ya bama ikram ledar sweet d'inta da kumz biskit da drinks ciki, sannan sauran ya ajiye a nan falo, ya mik'ama ikram d'in makullan part nasu yace.... "Ki kaima aunty " Sannan yafito ya kira wanda zai kaishi air port d'in, sbd adawo da motar gida, yazo suka wuce. Farha ta amshi kayan da makullan ta ajiye su in da ya kamata, domin karatu zata yi gobe akwai exam mai zafi, a haka ta yini cikin karatu, ikram na gurin talatu tana yimata wasa. ★★★★★ Alhmdullh sun sauka lfy, wanda kuma sun samu jana'izar, inna hajiya tasamu jama'a domin dama mujin ta tsohon malamin makaran ta ne a nan zamfara d'in, hakan yasa kowa yaji rasuwar, kuma tasamu shaidu na k'warai wanda kowa yaxo zai yabi halin boyar Allah d'in, ga karamci ga managarci ga tsoron Allah, da haka kad'ai inna hajiya ta yi dace rayuwar ta, sai dai juyayi na d'iya da jikoki domin sunyi rashi, ahakan dai suka sami dangana da hak'uri a rayuwarsu. Kwana ukku da addu'a umma da baba suka shirya dawo wa sbd shi ga aiki, ita kuma umma tunanin ta akan farha da yarinya da tabaro gida, hakan yasa mama tace su wuce, har da iman domin ita zata tsaya har mutane su k'arasa zuwa in yaso idan aka kwana biyu sai tadawo. Kowa ya aminta da hakan, sai umma ta buk'aci da iman ta tsaya sai su dawo tare, tunda koh banxa tayi yaye, kafin su koma ta manta da nonon baki d'aya, baba shima ya ga hakan d'in yayi idan suka koma sai ya cika alk'awalin shi na tura ta gurin mujinta, kuma zaman zaisa ta k'ara gane wasu, domin sun fi sanin farha akan ta. Aka zauna akan hakan, kuma itama taji dad'in hakan,kuma yayen ikram ciwon nonon komai batayi ba domin cikin da at gareta, don haka da sukayi waya da Abdul-jabbar shima yace hakan yayi kyau. Su umma suka iso lfy k'lau, ikram murna kamar kace me, taga abokiyar wasar ta tadawo, talatu kuma umma tace tunda ba yara gare ta ba tayi zamanta kawai, tun da da wuri,a haka suke zaune cikin jin dad'i, ikram tunda tayi kukan nono sau d'aya bata k'araba, sbd bai dame taba, da ta nuna alama aka bata madara shikenan ta manta da komai. 💧💧💧💧💧 Sati d'aya da gama amsar gaisuwa, kowa ya watse, har k'anne mama d'in sun watse, sai k'anwar su k'waya d'aya wadda bata yi aure ba, mama tace da ita zatazo, aka shirya tafiyar da ita da kayanta. Abdul-jabbar najin da wowar su, yabuga ma wani driver waya akan yaxo gida ya amshi mota ya d'auko su, domin bai yadda iman ta shiga motar kasuwa ba, hakan akayi shi ya d'auko su, suka kamo hanya. Ba'a 2 mnt abdul- jabbar bai kira iman yaji ina suke ynx ba, har yakai chaging wayar tata duka ya k'are, sai neman tambayar ya tsaya. Sunata shan hanya duk da 2hour ne tsakanin kaduna da zamfara, amma akwai xama, ga tafiyar ta d'anyi marece sbd 3:pm suka taso, kuma sai da iman ta kira farha ta shai damata sun taso, don Allah talatu ta taimaka ta share mata gidan kafin tazo, ta fad'ama farha ita kuma ta fad'ama umma sbd gada rainin yayi yawa, taga ba a kyauta mata ba, umma ta fad'amata ba musu ta je ta gyara gidan lfy qlau. Sun kawo, zaria anan aka fara kiran sallah la'asar, mama tace a tsaya suyi sallah sannan, nan sukayi sallah sannan suka kama hanya. Barci ya d'auki iman, kuma taji dad'in barcin, acikin barcin taji ana kiran..... "Innalillhi wa'inna ilaihirra'un! La'illaha illallah, muhammadan rasulullahi sallahu alaihi wasallam!!!" Muryar mama kenan da ta tayar da ita,koh da ta bud'e ido kawai zata iya tunawa, amma sauran zancen bata sanshi ba, domin wata k'atuwar mota burkin ta ya katse aguje ta tunkaro motar su,hakan driver d'in yayi k'ok'arin kaucewa, itama wata k'aramar motar tayi gudun tsira, sai d'ayar motar ta bugi motar su Iman gaba d'ayan su suka fad'a wata gada dake tsakanin zariya da jaji. Tun da mutane masu wucewa suka hango hakan nan take aka kai d'auki cikin ramen da mota biyun ta fad'a, ita kuma babbar motar jejin ta mik'a ta bugi icce ta kama da wuta. Da sauri mutane suka fara fitar da mutanen da abun yafaru da su, driver d'in su iman da mutanen motar su gaba d'aya sun rasu nan take, saka makon bugun da kansu yayi a wani babban dutsi. Mama da ihsan duka sun ji jiki, domin basu san inda kansu yake ba, samira k'an war mama itama allah yayi mata cikawa itama, nan take wani ya jawo jikkar da yagani, ya duba last call na wayar mama, yakira Alhaji Aliyu yake shaidama shi su had'u assibitin shika, domin ita ce kusa, kuma ya fad'amashi hatsari ne ya faru su had'u assibitin. Nan aka kwashe su a motar assibiti tare da yn sanda, zuwa emergency, domin duka in ba ka sansu ba bazaka shai dasu ba. Baba sauri yayi, yaje ya d'auki umma ba tare da ya fad'amata komai ba, suka kama hanyar assibitin....... _Ubangiji Allah yabaku lfy, ya jik'an wayan da suka rasa rayuwar su, kamar sameera k'anwar mama da driver d'in su, da mutanen d'ayar motar, da ake ganin family guda suma, Allah kabama iman lfy da mamar ta_😭😭😭😭😭 *Bee Been masoya*💞 [2/24, 10:46 PM] ‪+234 803 932 4068‬: 💧💧💧💧💞💧💧💧💧 *SO NE......* *DALILIN HAWAYENAH😭😭* 💧💧💧💧💞💧💧💧💧 ® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_* _ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_ # WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM # *IG PML WRITERS* # https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 # http://maryamsbello.blogspot.com ©® Khadija bee bee Khadijabeebee@gmail.com My wattpad user name.... *khadijabeebee......* My Facebook page.... *beebeenmasoya* *I LUV YOU ALL MY FANS* 💋💋💋💋💋 ★TRUE LYF STORY★ ★★★★★★★★★ *Asragfirullah, wa'atubu ilaihi,Astagfirullahu lazee man lazee la'illaha illah huwa alhaiyyul k'ayyum wa'atubu ilaihi*🙏🏻🙏🏻 Page... ★4⃣7⃣★ Abdul-jabbar a tsiyace ya kawo zaria, assibitin yashiga tare da neman gurin, nan take aka nuna masa, nan take ya gane, ta hanyar hango umma zaune ita kad'ai azuciya yace "mutuwa mai yanke zumunta, ji umma ita kad'ai " Dasauri ya k'arasa tare da tambayar ta gurin da iman take, koh gaisuwa babu sai tambaya, sbd baya a hayyacin shi, umma kar'bar ikram tayi sannan tace yabata wayar shi, ya mik'amata ya kama hanyar d'akin, sai da yatafi sannan takira layin wayar ta, cikin sa'a wayar na hannun farha, kamar kada ta d'auka domin numbr da tagani kuma sai wata xuciyar tace bari ta d'auka, tana d'agawa taji muryar ummar, bata tsaya amsa sallamaba, tace "kina ina?" "Ina assibiti gurin aiki?" "Kinada kud'i a hannunki?" "Eh ki hawo transport muhad'u dake assibitin shika" "Toh zanzo ynx umma,amma zan koma gida na d'auko ikram " "Ah ah gata nan tare dani kidai zo Jikin farha har rawa yake yi, da sauri ta shirya ta nemi transport nan take. Shigar abdul-jabbar d'akin yadinga dube dube domin baiga mai kama da iman d'inba, yadawo ya tambayi umma ta biyoshi suka shigo tare, inda yavari nan daine iman take, kuma itace wadda bai ganeba, kuka umma Abdul-jabbar kuka.... "Umma kina nufin haka iman ta koma!?" "Eh Abdul qaddarawar ubangiji kenan d'in, su nan da sauk'i sauran duka babu rai " Ashe idon iman bud'e kuma tana jinsu nan take tace... "Kaji umma! waye yace maki nima ina raye? Ai burina kawai nake son yacika sannan mala'ikan dake kusa dani ya wuce dani gidan da aka ginaman wanda yafi wannan a aljannah,Alhmdullh umma Alhmdullh, zan rasu ina mai farincikin zan koma hannun ubangijina kamar yadda mama ta koma masa, dama inajin duk abunda ake yi,Abdul karik'e man amanar Ikram, duk matar da zaka koma aure gada ka bari ta cutar man da ita, domin nasan dole d'iyarka zata koma hannunka wata rana,ni kuma zanje maka da wannan babyn sabon gidan mu na aljannah, sannan kacikan dukan alk'awarina bayan raina " Kuka Abdul-jabbar yasaki mai k'arfi wanda sai da ikram itama ta fashe da kukan haka umma da ita tashin hankalin da tagani ai batasan iya karshi ba tunjiya har izuwa wannan tym d'in, Abdul-jabbar ya matsa kusa da ita da sauri tare da rik'a fuskar iman wadda banda aka fad'amasa itace da bazai yar da ba, amma duk'awa yayi a fuskar ya dubi iman yace cikin sanyi wai shi ya kwantar mata da hankali, amma kuma kuka yake yi..... "Ah Ah iman ai ba haka mukayi da ke ba fa, munyi alk'awalin zamu rayu tare zamu mutu tare, kawai don ciwo ya sameki sai kice man wai zaki tafi kibarni? Nima so kikeyi na bi bayanki kenan mubar ikram ita kad'ai? Toh ki daina,ai kin fara samun sauk'i gobe gida zamuje tare,kin manta zamu koma sabon gidanmu na abuja iman? Zuwan da nayi kenan muwuce, kuma zamuje kidaina fad'in hakan don Allah, ki duba nine fa, nine Abdul-jabbar d'inki, ki tuno da farincikin da kike sakani idan muka kasance tare, iman kece ke sani nishad'i ya za'ayi kuma ki tafi ki barni duniyar nan iman?" Umma tagane shima hankalin nashi ya gushe, domin baisan ma me yake cewaba, kar'bo ikram yayi ya azota gefenta yace... "Duba ikram na ganinki kuma tanajinki kina fad'amata zaki tafi ki barmu, toh ki fad'amata wasa ce kikeyimuna zamu koma gida tare " Iman dariya tayi ma ikram sannan tace... "Haskenah kenan! Ikram ina kika baro Auntynki?" Itakam kallon farin bandeji kawai takeyi a fuska, domin batasan waye anan gurin ba, idan ita kad'aice tserewa zatayi, amma hannun abbanta take. Umma kar'barta tayi

Chapter 23 of 44