tasamu miji mai aminci tayi auren ta huta, domin shi kad'ai zai kareta da duk wata fitina, gashi dama tana fama da ciwon mara, kuma anshaida mata aure shine maganin hakan, toh gara ta nemi maganin hakan, da wannan waswasin nata, tafurta cewa.....
"Ya Allah, kasadani da miji nak'warai, mai mutunci, mai k'aunata, wanda zai dubi maraicin rayuwata, da girman nadamar laifina na farko, ya Allah kazabaman muji nak'warai "
Da wannan addu'ar takai bakin toilet don yin alwallah tayi sallah.
Umma cikin fushi ta d'auki wayarta domin kiran Alhaji Aliyu, cikin sa'a yad'auka, ta shaidamashi yazo don Allah idan baya komai tana nemanshi anjima kad'an, ya amsa dazaizo insha'allah daya fito gurin aiki zai shigo.
Umma ta ajiye wayar, sannan ta wuce d'akinta batare da tacema Abdul-jabbar k'ala ba.
Baba natasowa aiki ya zarcikke nan gidan, umma takira Abdul-jabbar a waya tace yazo tana nemanshi a cikin gida.
Alhaji Aliyu yace...
"Lafiya kuwa dai koh?"
"Eh dasauk'i dai, inason ne muyi magana dashine akan wani abun, kuma nasan zancen dakai shine dai-dai, don kaxama shaida "
"Toh shikenan umma Abdul bari yak'araso muji "
Rufe bakin baba dai-dai da shigowar Abdul- d'in da sallamarshi, ya gaisa dashi sannan ya zauna k'asa, domin baisan dalilin kiran nashi ba.
Umma ta kalleshi cikin fushi tace....
"Toh uban marasa hak'uri da tawakkalli, inason kafad'aman cewa kai ba ajizi bane, kuma kai baza'a ta'ba yimaka laifi anemi yafuwarka kayafeba, toh kasani A yau ba sai gobe ba Ikram zata dawo hannunka, sai dai wallahi ni bazan rik'ataba, kuma ni bazata zauna a gidanaba, sai dai kayo aure matar tarik'a maka 'yar da kake ikirarin d'iyarkace kai kad'ai, kuma na rantse yau sai Ikram ta kwana hannunka insha'allah "
"Haba! Haba!! Umman Abdul, menene abun rantsuwa akan wannan zancen kuma? Shin idan ya kar'bi Ikram yaje da ita ina kuma? Wanda bashida mata, kuma bashida yar renon rik'ata, kuma hassali Ikram bata yarda da kowa sai farha, idan akayi hakan ai wata damuwace kuma aka tayar mashi da ita fa"
"Hmmm Alhaji wannan dakake gani shine ke tayar da duk wata fitinar da aka manta da ita, toh don haka abashi 'yarshi koh zamu samu sauk'i "
"Umman Abdul, wata matsalarce wadda bansantaba kuma?"
"Eh, nima bansan Abunda yafaruba, amma farha tadawo gidannan da kuka bayan sunje tare gurin kai ikram asbiti, shine take shaidaman zata bashi Ikram domin tasamu kwanciyar hankali akan Abunda yake yimata, toh tunda baisan girman karamci ba, da hak'uri a rayuwarshi ba, toh za'a mik'amasa 'yarsa sai itakuma ta huta, ni na'aza a dalilin sonda 'yarsa keyima farha ya manta da duk wani 'bacin rai na baya, amma duka wannan bai zamo silar hak'irinshi ba, toh gara ta kama kanta abunda zai zama tashin hankali gareta, indai kan 'yarsa ne, toh daga yau babu ikram babu farha, kuma yafitar da matar da zai aura nan da sati biyu, domin koh macce ce shi yafita takabar mutuwa, bale yana d'a namiji "
"Don Allah umma Abdul kiyi masa hak'uri, kitsaya da fad'an mu fuskanci inda wannan al-amari ya dosa, kai Abdul-jabbar menene yafaru hakan ne?"
Duk'ar da kanshi yayi, sannan yafara magana a hankali yace.....
"Umma don Allah kiyi hak'uri, wallahi nima narasa gane kaina akan wannan al-amarin, idan natuno rayuwata ta farko har izuwa yanzu, toh idan nakalli farha wani bak'in ciki nakeji, narasa meyasa hakan,amma ninasan da cewa na dad'e da yafe mata tuntuni kawai dai halin rayuwa ne, dakuma idan na kalleta natuno da k'iyayyar da tayi man farko, amma don Allah atayani da addu'a bazan k'araba,kuma zancen Aure don Allah baba kuyafeman, wallahi babu maccen danake iya ganin zan iya zaman aure da ita a yanzu "
"Koh kak'ara, koh gada ka k'ara, yau dai Ikram gurinka zata kwana, wajibine yau kagano mahimmancin reno a rayuwarka, sannan kuma Aure wajibine kanka tunda mu ba mutanen banza bane "
"Innalillhi wa'inna ilaihirraji'un! umma don Allah kitausayaman banason na bijirema buk'atarku akaina, sai dai kisani zan kar'bi Ikram yau takwana hannuna gobe zan koma, sai nadawo da ita hannunku"
"Umma Abdul kiyi hak'uri, da wannan zafin fad'an akanshi, ni nasan me Abdul keji, domin ni d'a namijine, kekuma bazaki gane nufinsaba, don haka mubi a hankali zai kawo wadda yakeso nan gaba kad'an "
"Hmmm naji, toh tunda hakane, kai kabashi lokaci ya kawo matar don abashi 'yarshi, mu huta da tijararshi, domin itama mai rik'on na 'yar tashi aure zatayi insha'allah "
Anan yabada hak'uri, kuma bazai sake abunda yake yiba, sai dai don Allah ajaye mashi zancen Aure kusa domin duka yanzu matarshi koh shekara batayiba kuma a tayar mashi da zancen Aure, don Allah ak'ara masa lokaci.
Baba zancen Abdul- jabbar dariya yabashi, domin yasan waye Abdul-jabbar a sha'awa tunda itace tata'ba kwantar dashi asibiti, amma wai yanzu kuma bayason Auren bayan ya d'and'ana zancen auren, baba yak'arabawa umma d'in hak'uri akan ta k'aramasa lokaci zuwa wata d'aya, a lokacin idan babu wani zance, toh shi da kanshi zai yimasa hukunci, aka kai k'arshen zancen tare da bada hak'uri akan abun da yafaru, umma tace anjima yazo yad'auki Ikram domin yau dole su kwana tare, baba yace anjima yaxo ya d'auketa domin cika umurnin nata.
Ahaka aks kai k'arshen zancen cewa anbashi 1month ya kawo matar aure, domin su samu lafiya, kowa ya watse, amma zuciyar Abdul-jabbar kamar ta fashe don bak'in cikin rashin matarshi mai sonshi, gashi yanzu an tilastashi kawo abur da baisan inda zai samu kalar wadda yake soba, shidai wallahi tun fara soyayyarshi har yanzu bai samu kwanciyar hankali mai d'aurewa ba, toh koh ya zaiyi yanzu?
A haka ya yini acikin part nashi.
Da dare yaje cika umurnin umma, amma wallahi Ikram tak'i yarda dashi koh kad'an, a hakan yayi dubarar d'aukarta, yafito da ita, sai dai me, Ikram ta hanashi barci bale yazauna ya huta, a yau kuma yagane cewa farha rufin assirice gareshi, koh ba don komai ba, sai don Shak'uwarta da Ikram, Amma wallahi har yanzu koh kad'an bayason ganinta kusa dashi, domin shi kad'ai yadan girman tsanarta a rayuwarshi.
Tunda asuba Abdul-jabbar ya maida Ikram part d'in umma, domin yasan ta wahala da kuka shima ya wahala, don haka bai bari umma ta ganshiba, ya koma ya shirya don barin garin baki d'aya.
★★★★★
*AFTER 5 DAYS*
Doctor Hisham yakawo ziyara gidansu farha, bayan wayar dasukayi da ita, tabashi dama akan Yazo, domin taji k'udurinsa akanta, A hakan ta sanar da umma zuwansa, itama umma tayi farinciki tare da addu'ar dace ciki.
Isowarshi kenan, Farha ta gabatar mashi da kayan ci da sha, sannan ta samu guri ta zauna daga nesa dashi suka gaisa.
Sanye take cikin atamfa doguwar riga,sannan tad'aura d'an kwalinta dai-dai kanta, irin d'aurin zamani wanda farha tasabayi shi tayi, sannan tayi kwalliyarta dai-dai yadda takeyi bata k'ure zuwa ga wadda take haukata 'ya'ya mazaba, domin har ta manta da ita.
"Wooo my best choice, kinyi kyau sosai, koba kwalliya ke ta dabance fatima, bari gada na zurfafa yabon tauraruwar bayan banji _accepted_ d'in _requesting_ d'in nawaba, da farko dai duk da kinsan da sunana amma gara na kammalashi da tarihi na_____
_sunana Hisham Bello Ard'o Gombe, ni d'an asalin gombe ne, sai dai aiki yakawo mahaifinmu nan kuma muma zaman mu yadawo nan kaduna, nayi aure amma munrabu da matar saboda Rashin mutunci nata da kuma izgilancin wulaqanci ga mahaifana, bamu haihu da ita ba, tun lokacin bank'ara sha'awar auren wata macce ba sai ke farha, tunda na ganki naji gabad'aya komai nawa ya sauya,nayi maki magana, kikace ke matar aurece har da d'iya tare dake, daga baya na bincika naga ashe kin rufene don bakison damuwa, wlhy farha gabad'aya akanki komai nawa ya sauya please ki aminta dani, domin na hango zuciyarki da kalar damuwa irin tawa, mubama zukatanmu farincikin da muka rasa, baki haihuba, a binciken da nayi, naji ance yarinyar k'anwarkice da tarasu, please ki aminta dani mu share hawayenmu tare, sai inkuma nine d'in banyi makiba, amma kuma ki tambaya kaf kaduna wallahi babu wanda baisan family namu ba, akwai mutunci da karamci aciki, don haka inajiran sakamakon zancena gareki yanzu"
"Hmmm Oga Hisham, anan banida wani za'bi sai za'bin Alla akaina, kabani 2days insha'allah zakaji result d'inka daga zuciyata, amma yanzu bansan me zance makaba, domin duk abunda zance gaskiya k'arya kawai zanyi, domin babu nazari ciki, amma next 2 morrow da kaina zan kiraka "
Ya aminta, suka d'an ta'ba fira cikin mutunci, tare da tambayar waye Abdul-jabbar agareta halan? Tabashi amsa da yayanta ne, kuma Abban Ikram ne, k'anwarta ya aura wadda ta rasu, daga nan sukayi sallama cikin jin dad'i da alkhairai irin na soyayya ya kawo mata.
★★★★
★ *WAI WAYE ADON TAFIYA, SHIN YA LABARIN ANWAR DA IYAYENSHI?* ★
*Bee Been masoya*💞
💧💧💧💧💞💧💧💧💧
*SO NE......*
*DALILIN HAWAYENAH😭😭*
💧💧💧💧💞💧💧💧💧
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
©®
Khadija bee bee
Khadijabeebee@gmail.com
My wattpad user name.... *khadijabeebee......*
My Facebook page....
*beebeenmasoya*
*I LUV YOU ALL MY FANS*
💋💋💋💋💋
★TRUE LYF STORY★
★★★★★★★★★
_Page d'innan duka nakune, Marubuta gidan Hira✍🏻, inayinku ina k'ara yinku😍 kuna saka bee bee nishad'i, a wanne hali take,ta ganku kawai zata fara 😂 *Love you All Gidan Hira*_❤
Page...
★5⃣3⃣★
*~LABARIN ANWAR DA TAWAGARSA.~*
Tun ranar da Anwar yasaki Farha bayan taka masu suna aikata iskancinsu da abokinshi da kuma jamila k'awarta a d'akinta, bai k'ara zama inda mahaifinshi zai ganshiba domin labarin sakin yazo mahaifinshi a kunne,hakan yasa ya had'a duk wani abu nashi mai muhimmanci yabar garin tare da abokan iskancin nashi.
Mahaifiyar Anwar babu yadda batayi da mahaifinshi ba akan ya nemo mata Anwar, domin shi kad'ai ke gareta rayuwar duniya.
Mahaifin Anwar ya nunamata cewa, dama da hannunta a lalacewarshi don haka idan batayi a sannuba har ita zai iya yafeta ba Anwar kad'aiba, hakan hankalinta yayi mugun tashi da wannan furuci, nan take ta gano cewa lallai dadyn Anwar zai iya yin komai Akan hakan, sai takama bakinta tayi shiru, amma kud'd'inta nashan kashi gurin neman Anwar, amma shiru babu Anwar bale labarinshi.
Tunda anwar yabar kaduna, sai ya tare a wani babban hotel da ke garin Abuja, inda yanzu abun nashi yaci gaba, domin yana homosexual ne saboda yasamu kud'd'i.
Ranar da ya tashi barin kaduna bayan ya rabu da farha, ranar ne yabama jamila k'awar farha kud'd'i masu yawa, hakan yasa jamila taji zata iya binsa akoh inane domin itama tak'ara samun kud'd'i, domin akan kud'd'i babu abunda bazata'iya aikatawaba, don haka da ita akayi wannan tafiyar.
Iyayenta sun nemeta har sungaji sunsakama sarautar Allah idanu.
Anwar abun nashi yaci gaba, domin yanzu manyan masu kud'd'in Abuja sune abokan hark'allanshi, hakan yasa sai jamila takoma tamkar matarshi, girkinshi, tayar mashi da sha'awarshi, amma bai yarda da sex da itaba domin baya gabanshi, sai dai usman ke d'an ta'ba mu'amala da ita, duk da hakan ta za'bi zama dasu, domin tasamu mak'uddan kud'i da yawa a k'ark'ashinsu, tunda har motar kanta gareta, hakan yasa ta manta da wata rayuwar kaduna, masha'arsu kawai sukeyi, wanda yanzu gida garesu na kansu, itama da nata miyagun matan a nan gidan suke tasu harkar.
Mahaifin Anwar yabada sak'o a sanar dashi cewa, ya cire Anwar daga tsatsinshi, koh bayan ya mutu Anwar baya gadonshi domin shi ba d'anshi bane a yanzu, idan ya rasu yafi farincikin dukiyarshi a baitil mali da Anwar ya gadeshi, domin ya samu labarin abunda yake aikatawa, mahaifinshi yayi kuka har yagaji domin Anwar shi kad'aine Allah ya mallakamashi a jinin jikinshi Amma gashi yayi yayi yakoma mutumen k'warai yak'i ya koma, domin duk wasu kayan maye da d'an adam kesha su bugar dashi Anwar zaishasu yanzu, hakan yasa mahaifin anwar d'auko d'an yayanshi domin ya cigaba da gudanar da kular mashi da wasu al-amuran da yake aikatawa a nan gida nigeria, gaba d'aya ya manta da tsarin Anwar a rayuwarshi, kuma yaje har gidan mahaifan farha ya basu hak'uri akan abunda ya faru, domin shi baiso hakan ba, koh lokacin da yaji rasuwar mahaifiyar farha saida mahaifin Anwar yazo yayi mashi gaisuwa da yashigo nigeria.
Mahaifiyar Anwar tak'i takoma jidda domin bazata iya tafiya tabar anwar acikin wannan halinba, domin koh ba komai tasan hadda hannunta a lalacewar Anwar d'in tun farko, domin komai yakeso zata tilasta mahaifinshi yayi mashi koh ransa baisoba, don haka dole ta tsaya ta nemi inda Anwar d'in yake.
Wata shidda da faruwar hakan, momynshi ta shirya domin taje abuja ta nemi gurin da yake zaune, bata wahalaba domin wayanda suka sanshi su tanema, taci sa'a yana nan kuma lokacin a cikin halin yake na bad'alar tashi.
Shigowarta gidan taga jamila zaune a shiga ta rashin mutunci, ga 'yan mata nan zazzaune sai firar banza sukeyi, shigowa momyn Anwar tayi da sunan tambayarsu inda Anwar d'in yake, kafin ta fara tambayar sai wata macce dake zaune gefen jamila tafara tambayarta da koh tazo d'aukar watace daga cikinsu? Momyn Anwar kallonsu kawai tayi saboda takaici, sannan tace.....
"Ina Anwar yake?
Sai a lokacin jamila tagane mahaifiyar Anwar ce domin fuskarsu d'aya da Anwar babu bambanci, nan take ta mik'e domin zuwa d'akin da yake, knocking tafarayi sannan yazo ya bud'e domin aikin yakeyi itakuma zata katsemashi jin dad'i, don haka da sauri ya bud'e tare da hasala yafara tambayarta.....
"Wai meye hakan dakike yiman jamila?"
"Anwar ina tunanin mahaifiyarka ce fa tazo gidan nan yanzu?"
"Eyee! Toh wai su meyasa zasu dameni bayan na barmasu gidansu, Amma kuma suna biyar didiqina? Kawai kice mata bananan baki ganniba, kuma ki wuce kibani guri plz"
Jamila takoma tasanar da ita baya nan, itakuma yarda ne batayiba, hakan yasa tabi hanyar da jamila tabi domin gani da kanta idan gaskiyane, k'ofar ta tsaya tare da knocking, nan take yafito da niyyar rashin mutunci amma ganin mahaifiyarshi yasa ya tsayar da hakan.
"Anwar kaza'bi kazauna acikin wannan halin mara amfani daka zauna damu a matsayin iyayenka masu sonka koh?"
"Momy.........
" Dakataman! Anwar akan ka babu wahalar da bansha ba akakan kaji dad'in rayuwarka, na d'auki kud'in mahaifinka bai saniba domin kaji dad'in rayuwa, nayimaka a kud'd'in dake jikina, amma wai karasa zama mutun wanda iyayensa zasuji dad'in k'aruwa da kai, Anwar kasani ni kad'ai yanzu ke sonka domin nice mahaifiyarka, mahaifinka ya dad'e da mantawa da kai a rayuwa saboda aikin da kake aikatawa "
"Momy kikoma gida, gobe zanshigo kaduna nasameki, yanzu akwai aikin da nakeyi gada contract d'ina ya rushe, domin tare nake da honourable, zanzo "
Turo k'ofar yayi yabarta nan tsaye, Ahakan ta kwashi bak'in cikinta ta koma kaduna, wanda takejin zuciyarta zata iya bugawa akan hakan.
Tunda hakan yafaru momyn bata k'ara neman Anwar ba kuma shima bai nemetaba.
*Bayan shekara biyu, da faruwar hakan.*
Anwar ciwo yake fama dashi, wanda duk wa'yanda ketare dashi duka sun gujeshi, Usman yad'an tsaya yana kula dashi, Amma daga lokacin da yaga Anwar wasu ruwa na fitar mashi daga cikin jikinshi masu wari, sai shima ya fara guje mashi, bayan yakaishi asibiti anduba ance bashida magani ciwonshi, kuma wanda duk yayi wata mu'amala dashi macce koh namiji ciwon na iya faruwa dashi, domin shima d'aukarta yayi jikin wani, tundaga nan Usman da jamila suka tsere suka barshi, ciwo nata cinshi shikad'ai wanda har tsutsa tafara fito mashi a jiki.
Watarana mai gadin gidan da Anwar yake, yaga kowa yashigo gidan gudu yakeyi, shima sai ya shiga yaga menene hakan d'in?
Shiga yayi domin duba halin da akeyima gudu, ganin anwar kwance tare da tsutsotsi a jikinshi, yasa mai gadin rufe hancinshi domin ya taimaka mashi.
Anwar number mahaifiyarshi yabada domin yasan ita kad'ai zata iya taimakonshi, mai gadin yakirata ya shaidamata halin da yaronta yake ciki, hartayi kamar gada tazo kuma sai soyayyar haihuwa tasata d'aukar mota domin ganin halin da dayake ciki.
Isowarta gidan taga yadda anwar ke wari ga ruwa nayi mashi zuba masu tsutsotsi da wari, sai hankalinta ya tashi, nan take ta rufe hancinta tana hawayen danasani, mai gadin ya rik'a mata aka wanke masa jikinshi sannan akasamu jallabiya aka saka mashi, tare da saka barguna da leda kamar ta 'yan haihuwa k'ark'ashin jikinshi ta dawo dashi asibitin nan kaduna, layin 'yan yoyon fitsari, domin su harsunfishi, don shi a duburarshi abun ke fita.
Kafin su kar'beshi federal hospital d'in sai da momyn Anwar ta zube masu 100k sannan suka bashi gado a wani wulak'antaccen d'aki.
Mahaifiyar Anwar takira mahaifinshi ta shaida mashi ciwon nashi, amma cewa yayi tacireshi a harkar Anwar domin shi baisanshiba, kuma naira d'inshi bazata shigo asbiti da sunan ciwon Anwar ba, momyn tayi kuka wanda yake kuka domin harda ita gefen 'bata rayuwar Anwar da mugunyar tarbiyya, su gasu masu kud'd'i yaronsu ya wataya yadda yakeso, toh yau ga k'arshen gata yazo, domin duk wanda yasan Anwar wallahi bazai ta'ba cewa d'an gayun yaron nan ne ba Anwar Naira, domin yakoma Anwar mutuwa.
_Toh Allah ka'iya mana, kabamu tarbiyya ta k'warai, da kuma 'ya'ya nak'warai, kabamu ikon yimasu tarbiyyar hali na k'warai ba tarbiyyar nuna jin dad'in duniyaba, ka karemu ka kare musulmi baki d'aya da rayuwa irin wadda Anwar yayi kuma yanzu yake ciki, ameen ya Allah.👏🏻_
A Federal hospital anan aka kawo Anwar, doctor hisham shine likitan da ke duba anwar, shima yana iya k'ok'arinshi akanshi domin anzube masu kud'd'in aikinshi yadda ya kamata, mahaifiyar Anwar waya tabugama mahaifinta dake cen jidda akan yayi mata taimako da kud'd'i domin samama Anwar lafiya.
Kasancewar mahaifinta naji da ita batasamu mishkila anan ba nantake ya turo mata kud'd'i masu yawa domin samama jikanshi lafiya tunda jidda bazasu amsheshi ba koda yace azo dashi, don haka suka tsaya nan Nigeria, mahaifiyarshi na iya k'ok'arinta amma ciwo yak'i ci bale cinyewa.
Doctor Hisham ciwon na Anwar har mamaki yake bashi sosai, domin yasan ciwonshi na farko masu mu'amalar homosexual suke fama da kalarshi kuma idan dai za'a jure shan magani da cire kud'd'i asayi maganin toh may b a samu d'an sauk'i domin warkewa kuma babu, tunda a duburarshi ake mu'amalar, cuta kuma tarigada tashiga babu wani saf sauci ciki, amma abun mamaki sai ga wasu k'uraje damk'an acikin jikinshi sunfara fitowa, aka bada text a duba akaga Anwar d'auke da cutar H.I.V positive, wanda wanda kedashi sukayi tarewa ya lak'amashi shi, hakan doctor hisham yafad'amasu tare da basu result d'in sugani, ya wuce.
Momyn Anwar taci kuka har batasan metake cewa ba, haka shima mai ciwon sai yanzu yafara gane Illar abunda ya aikata,amma nadama yanzu ai bata aiki Anwar kabar girma tun ranar haihuwarka.
💧💧💧💧
Farha anfara aiki a federal hospital, yanzu cikin 2 month take da farawa, Rayuwarta yanzu cikin jin dad'i da annashuwa, domin kuwa ta aminta da doctor hisham sone na tsakani da Allah yake yimata, kuma aure yakawoshi ba wasaba, domin yanzu ko wanne 'bangare na iyayensu sunsan da zancen neman Auren Doctor Hisham da farha, hakan yasa yanzu shak'uwar soyayyarsu nasaka farha mantawa da komai.
Ikram ta saba da doctor hisham, domin duk sanda zaizo, wajibine sai yayo mata tata tsarabar ta musamman,sannan kuma suyi fira da ita kamar ba 'yar shekara biyu da rabi ba, hakan nasaka soyayyar Ikram ga kowa wanda ke tare da ita, saboda wayo da kuma gane karatu, domin ansakata free nursery yanzu, idan farha zataje gurin aiki take ajiyeta sannan ta wuce, kasancewar yanzu umma ta tilastata akan tadinga d'aukar mota da kanta tana driving, saboda ai bata kowa bace ta ummar ce, hakan yasa yanzu take driving da kanta da sunan motar umma tunda ta iya dama.
Kamar kullum haka yauma tashirya fitar Ikram makaranta, sannan itama tashirya tata fitar, rataya jikkarta tayi sannan tarik'a lunch box d'in ikram a hannu d'aya sannan ta rik'a ikram d'in a hannu d'aya, suka shiga d'akin umma ta shaidamata sunwuce, umma tayi masu addu'a sannan tace....
"Ikeen Aunty farha harkar babu bye bye?"
Dariya Ikram tayi harda 'boyewa bayan Farha, sannan ta lek'o ta bayanta tace.....
"Idan uncle Hisham ya siyaman sweet da mota zan baki d'aya, nabawa Abban Abuja d'aya, motata kuma Aunty farha kawai zansaka tunda ita ke goyani "
"Ehhh, lallai Ikeen Aunty farha toh Adai yi karatu da yawa "
Farha dariya tayi sannan taja hannunta suka fita, sakata motar tayi, sannan tasaka lunch box nata da jikkarta a baya, tadawo gurin driving d'inta ta zauna.
Shigarta kenan wayarta ta fara ringing, kuma daji tasan mai kiran Hisham ne, picking tayi sannan tayi sallama.
"Amincin Allah ya tabbata agareka sanyi idaniyar teemah uncle d'in Ikram, antashi lafiya?"
"Wannan zance hakan? Ai sai kisaka nakasa fad'ar zancen dake bakina, plz ki safsautaman fa, akwai sauran time, toh qlau natashi, kefa?"
"Nima hakan"
"Toh Alhmdllh dear, dama so nakeyi kifito da wuri, domin akwai aikin da nakeso ki rik'aman na wani patient saboda aikin nad'aya daga cikin abunda nakeso ki k'ware a kai, sai dai nasanki da tausayi gada kizo kikasa fa"
"Hmmm naji zan daure ai, Ina onway ma, domin ikram kad'ai zan ajiye a school zan shigo yanzu "
"Ok kikular man da kanki kafin ki iso, sannan kibama ikram one kiss ga goshinta "
"Ank'are Oga "
Dariya sukayi dukansu, sannan ta mayar da wayar a jikkarta ta tayar da motar.
A bakin get nasu Ikram ta tsaya, tafito ta rufe motar tarik'o hannunta da lunch box nata, sai da ta tabbatar Auntyn tasu ta kar'beta sannan ta fito ta wuce.
Shigarta asibitin taje tasaka hannu a attendance ship, sannan ta duba komai wanda yakamata ta duba, sannan tafita zuwa office d'in doctor hisham.
Turawa tayi cikin sallama ta shiga, lokacin yana cike wata takarda a gabanshi, sai kuma ganinta yasa ya ajiye biron da yake rubutu yafara kallonta tare da cewa......
"Gaba d'aya nurses d'in asibitin nan, babu wadda uniform d'innan kema kyau kamar my teemah,wallahi keta dabance a jerin kyawawa farha, hakan yasa bazan bari wannan kyawon na k'arewa a duba patient's ba, har ni a dinga dubani, hakan yasa banji zan iya cika 2 month batare da anbani matata ba, don haka nashirya komai a hannuna, jiran kawai nakeyi a ce yau na iso "
"Wai kai Oga, koh yaushe sai kayi abunda zaisaka mutun dariya, gada ka manta kaga mata iri-iri a duniya, kazauna turai, ka auri shuwa'arab, don zaka Auri farha shikenan saikata zaro zance? Toh babu ruwana idan kyawawan nurses d'in asibitin nan suka jika "
"Farha kenan, dole na fad'a maki hakan, domin da sonki nake kwana nake tashi, k'arshe kuma ina burin najimu a inuwa d'ayane, kinyi auren farko nima nayi, amma wallahi jinakeyi wannan shine aurena na farko a rayuwa, don haka insha'allah a month d'innan komai zaizo k'arshe "
"Naji nidai oga tsoratani ma kakeyi, a yanzu saboda yadda kake zaro zancennan, toh mubar wancen zancen, ya batun patient d'inda za'a d'aura training d'insa akaina?"
"Hmm tunda ba kyason zancen nabari, amma ki shaidama umma next 2 week sadakin Hisham zai shigo hannun farha, sanna patient d'in anjima idan kin k'arasa aikinki zan kiraki sai muje tare koh? amma yanzu bangaji da kallonki ba, kibani 5mnt nak'are kallon flower ta "
"Haba! Wai oga menene hakan? Nifa yau tsoro kake bani, domin kafi koh yaushe rud'ewa akaina, inda da Ikram mukazo anan itama zata gane yadda ka koma fa"
Murmushi yayi sannan ya matso da sit nashi gaba, harda wani lumshe ido yayi sannan yace....
"Kinsan menake ji idan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 26 Chapter of 44