Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
& # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 [07/12/2025, 13:34] Uwar Batoorl✍️❤️🥰: 💔NAUYIN BAKI....👄💔 Na Uwar Batoorl. 𝗕𝗜𝗦𝗠𝗜𝗟𝗟𝗔𝗛𝗜𝗥 𝗥𝗔𝗛𝗠𝗔𝗡𝗜𝗥 𝗥𝗔𝗛𝗘𝗘𝗠 اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 🅿️ 31 _ 35 ⭐️ Ringing guda layin da Hajiya ta aika wa ƙira yayi aka ɗauka, "Assalamu alaikum." "Wa'alaikissalam Hajiya barka, ya kuke? Ya shirye-shirye?", aka faɗa a ɗaya ɓangaren. "Alhamdulillah Nadiya, yaushe kayakinnan za su iso? Alhaji ya ce a satinnan yake son a kai lefe, fatan kin yi yanda na ce?" "Nayi Hajiya, kuma in sha Allah nima zuwa jibi ina Nigeria", faɗin Nadiya a ɗaya ɓangaren. Hajiya ta ce, "To Allah ya kai mu, Allah ya kawo ki lafiya." Sai da suka yi magana akan abinda ya shafi business nasu, sannan suka yi sallama, daga haka Hajiya ma ta bi lafiyar gado ta kwanta. ⭐️ RAYFIELD SADIYA POV *** Tun da Dr Saddam ya bai wa Sadiya taimakon da ya kamata, bacci take har sai goshin la'asar sannan ta farka, cikin rashin ƙwarin jiki da too much of headache. Slowly ta fara blinking eyes nata saboda nauyin da suka mata, rapidly ta buɗe su gaba ɗaya tare da yatsine fiskanta with a pain, saboda ciwon kan nata har jijiyan idanuwanta take jin shi, a hankali ta lallaɓa ta tashi daga kwancen da take ta zauna with her hands on her head, looking soo painful. Mama da fitowanta ɗaki kenan, ganin Sadiya ta tashi har ta iya tashuwa ta zauna da kanta, hamdala tayi tare da cewa, "Sannu da tashuwa ko, fatan ba abinda ke miki ciwo?" Sadiya shagwaɓe fiska tayi tare da sake dafe kanta ta ce, "Kai na Mama." "Sannu Sadiya, Allah ya baki lafiya ya yaye miki wannan lalura." Mama ta faɗa with a pity voice. "Amin Mama", faɗin Sadiya idanuwanta na tara ƙwalla, saboda tuno yanda ta kalli Yaya Sadeeq nata a asibiti, yanda yake kwance har da oxygen maƙale a hancinshi kaman wanda bai da rai, looking very unconsciousness, a sanyaye hawaye ya silalo mata, yanzu wa zai kuma yarda ta je asibiti wajan Yaya Sadeeq nata? Ba mai sake yarda, kuma tana son sake kallonshi ta roƙe shi ko zai yi haƙuri ya samu sauƙi ya dawo gida, she can't bear his being in hospital, and she definitely knows ba mai barinta ta ma je ta sake duba shi, this is soo bad to her. "Tashi ki lallaɓa ki je kiyi sallah kin ga har la'asar ta kawo kai", faɗin Mama tana katse wa Sadiya tunanin da take, saboda yanda ta ga Sadiya ta tsurawa waje guda ido tayi shiru ga hawaye na silalo mata a cheeks nata, ta tabbata to tunani take yi. In a low motion Sadiya ta lallaɓa ta mike duk da jiri-jirin da take ji, maimakon ɗakinta sai ta wuce na Mama a nan ta yi alwala ta tada sallah, tana idar da sallah ta kama addu'a da kuka, Mama ta shigo ɗakin kenan ta ji kukan Sadiya, girgiza kai tayi tare da cewa, "To ai ba kuka za ki yi ba, addu'a za kiyi da hamdala, mai babban suna dai ya farfaɗo Alhamdulillah, ina da tabbacin zuwa yanzu ma ya tashi baccin da ɗazu Ummanku ta ce mini yana yi." Da sauri Sadiya ta dakatar da kukanta tare da cewa, "Mama da gaske Yaya Sadeeq ya tashi? Mama kin gan shi kuwa? Mama kin ga abubuwan da aka jona mishi a jikinshi? Mama har da oxygen fa na'urar taimakawa wajan numfashi, he's in coma Mama, farkawanshi won't be possible by now", ta ƙairshe maganan with very hopeless face. "Inkin gama surutun naki, sai kiyi hamdala ki shafa addu'a, maza ki zo ki sha ga kunu na dama miki, sannan ki sha magun-gunanki", faɗin Mama da ta juya ta fice a ɗakin. Ta kuma cigaba da cewa, "Allah na gode maka, yarinya ce uwa ƴar shekara uku, Allah ka shirya mini Sadiya ka mata albarka." Fiska ɗauke da tsantar jin daɗin maganan farfaɗowan Sadeeq, Sadiya ta ɗaga hannayenta sama tare da jero godiya ga Allah, ta kuma bi da wasu addu'o'in sannan ta shafa, ta lallaɓa ta miƙe ta naɗe praying mat ɗin, ta kuma aje wa Mama hijabinta, ta juya da niyan ficewa a ɗakin sai wayan Mama ya kama ringing, tura baki tayi tare da dawowa ta ɗau wayan a kan gadon Mama «Umar», sunan layin da ke ƙira, sanin lamban Yaya Umar ne sai bata ɗauka ba ta nufi ficewa a ɗakin, da sweetness and slimmest voice nata take faɗin, "Mama ana ƙiranki Yaya Umar." Mama daga kitchen take cewa, "To ki kama mana dan mai anguwan garinku, ko sai ya tsinke hankalinki zai kwanta?" Sadiya tura baki tayi tare da cewa, "Mama ni kam Yaya Umar idan ya ji nice zai mini faɗa." "Tun da ga ashi ayagi ko? Kedai Sadiya Allah ya shiryaki, baki da lafiyan ma ba za ki bar kasa halinki ba, to na ma fi tunanin Ummanku ce ba shi ba, dan ɗazu ma da wayarsa muka yi magana da ita wai ta mance nata wayan a gida, Allah dai ya sa mai babban sunan ne ya tashi", faɗin Mama tana ɗaukan kofin kunun da ta sako wa Sadiya, ta fito kitchen ɗin. Kamun Mama ta gama magana, tuni Sadiya ta ɗau ƙiran da ke daf da tsinkewa, cikin zaƙuwa ta rangaɗa sallama da jinyatacciyar siririyar muryarta, "Assalamu alaikum." Amsa sallaman nata Umma tayi, tare da tambayar jikinta. Sadiya shagwaɓe murya ta yi tare da cewa, "Da sauƙi Umma, am okay now, wai da gaske Yaya Sadeeqna ya tashi? Umma Allah zan iya sake zuwa na gaishe shi ma ba komai na warke", in a begging way ta yi maganar, with soo much hope that Umma za ta amince ta sa baki a barta ta kuma zuwa, cause she can't believe it wai Yaya Sadeeq ya farka daga coma, sai ta gani da idonta ko ta ji muryan shi. *** Umma a ɓangarenta murmushi ta saki mai kyau, tare da cewa, "To haka muke son ji, Allah ya ƙara muku lafiya ke da yayan naki, daman ciwon naku na haɗin baki ne ai, ga yayan naki shi ma ya tashi." Da waitless expression Sadiya ta ce, "Umma ba shi wayan to dan Allah." Umma murmushi tayi tare da miƙa wa Umar da ke a kusa da ita wayan, tare da cewa, "Umar miƙa wa Sadeeq wayan, Auta na son magana da shi." Umar amsan wayan yayi yana faɗin, "Umma idan aka biye shirmen Sadiya ba za a yiwa Mama maganan kunun ba, kinsan shi kuma biye mata yake", ya ƙarishe maganan yana sanya wayar a kunnenshi. Ya ɗaura da cewa, "Ke bai wa Mama waya bana son rubbishness ɗin ki." Sadiya tana ɗaukin Umma za ta bai wa Yaya Sadeeq waya, amma tana jin Umma ta ambaci Umar first, kindly and slowly ta cire wayan a kunnenta, tana tura baki tayi taking steps to Mama while she's saying, "Ga wayanki Mama ." Mama amsan wayan tayi tana kallon yanda Sadiya ta kyaɓe baki hawaye sun cika idanuwanta, girgiza kai kawai Mama tayi tare da bai wa Umar amsan maganan da yayi tunda ya tsammani wayan na hannun Sadiya, "Ni ɗin ce Umar, ya aka yi? Ina Umman taku? Ya kuma jikin mai babban suna?" Umar a ɓangarensu ya ce, "Ga Umma nan, Sadeeq ma jiki da sauƙi dan ya tashi har ya samu ya yi sallolinshi, yanzu ma shi ne wai ba zai ci abinci ba kunu zai sha, Umma ta ce na ƙira na faɗa miki." Washe baki Mama tayi cikin farinciki ta ce, "Kai to ma sha Allah! Alhamdulillah, Allah ya ƙara mishi lafiya da ƙarfin jiki, aikuwa daman yanzunnan na dama irin kunun nasu da suke so wa Sadiya, dan haka zan saka a flask na taho da shi yanzu." "To Mama Allah kawo ki lafiya", faɗin Umar cikin girmamawa. Mama ta ce, "Bai wa mai babban suna wayan mana naji shi kamun na iso." Ba musu Umar ya tashi ya ƙarisa wajan Sadeeq da ke zaune a kan darduma ya zuba mishi mayatattun miskilallun idanuwanshi, miƙa mishi wayan yayi without saying a word. Sadeeq tun da ya ƙurawa wayan Umar da ke kare a kunnen Mama ido, yake jin wani irin strong feelings, he has to be more unconsciousness than before, he see no reason for him being alive, in dai zai rasata, and he hasn't had any option to go for, he already ruined his opportunity, and yanzu ba ta yanda zai yi ya same ta, dole ya yi haƙuri ko da haƙurin zai zame mishi abinda zai yi na ƙarshe a rayuwarshi, saboda rasa ta shi ne ƙarshen rayuwarshi, ya tsara abubuwa da dama amma ba wanda ya zo mishi as he pleases, komai ya lalace a ƙanƙanin lokaci, jinkiri da yayi da kuma nauyin baki ya maida dukkan mafarkanshi fake, mafarkan da kullum yake addu'a da fatan tabbatar su, ashe ba rayuwa zai yi da ita ba, mutuwa zai yi ba tare da ya mallaki ko da sirin gashinta ba balle ita gaba ɗaya. Wani irin kama wa zuciyarshi ta yi, the pain ended what's in his mind, bitting lower lip nashi yayi very had yana faɗin, "Auchhh", ciki-ciki yayi making sound ɗin idanuwanshi a kan Umar da ke riƙe da phone yana miƙa mishi. Umar ganin irin kallon da Sadeeq ke mishi, da kuma expression na yanayin da yake ciki da yayi, gently ya ce, "Sorry bro, Mama ce on phone." Sadeeq da left hand nashi ya miƙa ya amshi wayar, saboda right hand nashi na a dafe da saitin zuciyarshi, cikin ƙoƙarin daure ciwon da yake ji ya sanya wayar a loudspeaker, sai da ya runtse idanuwanshi sannan da jinyatacciyar muryarshi ya ce, "Mamaa." Wani irin tausayin Sadeeq ne ya ƙara rufe Mama, jin yanda muryarshi ya nuna raunin ciwo da yake ciki, a sanyaye ta ce, "Allah ya maka albarka mai babban suna, Allah ya baka lafiya wadatacciya ya yaye maka abinda ke damunka." "Amin Mama na gode", cikin girmamawa yayi godiyan kuma a taƙaice. Mama ƙwallan da suka taru mata a idanuwanta ta goge tare da cewa, "Ga Sadiya za ta maka sannu", ta faɗa tana miƙa wa Sadiya da ke zaune wayan. Sadiya daman all her eye's are on Mama and the way she react da take magana da Sadeeq, Mama na miƙa mata wayan ta amsa eagerly, while her weakness eye's full of painful tear's, manna wayan tayi a kunnenta tana sauƙe numfashi like someone run after her, jin shiru ba a ce komai ba, gently ta ce, "Yaayaana." Sadeeq tun da Sadiya ta amshi wayan ya ji haka a jikinshi, numfashin da ta sauƙe har ƙoƙon ranshi ya ji ya dake shi, sake runtse idanuwanshi yayi bai iya buɗe baki to say a word ba, har ta ƙira shi yanda take ƙiranshi, har sannan ma bai ce komai ba, sai wani cool and hot water da ya ji kaman an watsa wa zuciyarshi at same time, he can't express how he feels, neither happiness nor sadness, jin muryanta ya kawo sanyi but remembering that in a few day's coming za ta zama mallakin wani ba shi ba, yayi making zuciyarshi very bad and weak. Sadiya jin yayi shiru, hawayen da ke tare a idonta ne suka samu chance na silalowa, she's trying her very best to hold the cry inside her, but she can't hold it anymore, kukan kawai ta fashe da shi sosai-sosai, kuka take kaman za ta shiɗe. Sadeeq yana jin sound na kukanta a kunnenshi, a take zuciyarshi ta yi wani irin bugawan da ya sanya ciwon da ya kama shi ya sake shi, he's trying to say something, but before he open his amazing lip's to utter a word, sai ji kawai yayi Umar ya amshe wayar ya kashe ƙiran, da sauri Sadeeq ya wara jinyatattun idanuwanshi tare da aikawa Umar da wani kallo, wanda ke nuni da akan me zai mishi haka? Umar da Umma dama idanuwansu a kan Sadeeq yake duk abinda yake, kuma musamman da wayar ke a hands free, duk iyayin da Sadiya take a cewar Umar, suna ji, yana jin ta fara rubbishness nata ya miƙe ya amshi wayarshi tare da ɗaure fiskanshi, without bothering at the looks Sadeeq is giving him. Umar miƙewa yayi tare da ficewa a ɗakin yana jin ranshi na ɓaci sosai, Sadiya kan wai akwai motsi a kanta ne? She'll be acting like this despite that ta san condition da Sadeeq yake ciki tun da ta kalle shi da naked eye's nata, «amma sakamakon ya nuna farfaɗowanshi na da dangantaka da wani abu, wanda ya same shi wanda yake so ko yake ƙi, lallai wannan yarinyar da ta faɗa jikinshi, tana daga dalilin farfaɗowanshi cikin ikon Allah, walau ta kasance maganin cutarshi ko kuwa cutar tashi gaba ɗaya». Maganan da likita yayi musu shi da Abba ne yayi clashing a kan shi, hannayenshi both ya saka ya kama waist nashi, a fili ya furta, "Me hakan ke nufi? Kenan Sadeeq na ɓoye wani abu? Why is he acting like this?", wani irin iska mai huci Umar ya busar, a cikin ruɗu yake matuƙa, cause he don't want to think about what his heart is telling him, saboda he believes ba abinda Sadeeq zai ɓoye mishi, nomatter what indai something like what his mind is telling him ne, to ba shakka Sadeeq would let him know since the first day's, he'll be the first person to know before su Umma sef, Sadeeq ba zai yi hiding important abu haka wa kowa ba, but abinda ya ruɗa shi a nan shi ne, abinda likita ya ce first, secondly reaction na Sadeeq, his eye's looks so terrible that there's something he's hiding, menene? Me Sadeeq ya ɓoye mishi bayan basa ɓoye wa juna komai? Safa da marwa kawai Umar ya dinga yi a entrance da yake tsaye, he just ended up with headache, dan ya kasa gane komai, kawai ya yanke yiwa Sadeeq magana a yanayi na fahimta, if Sadeeq keep's hiding what he's hiding already, so zai bincika da kanshi and he'll let Abba and Umma knows what's is going on. Sai da ya gama yanke abinda zai yi sannann ya fice zuwa harabar asibitin, duk da magrib ya kusa amma ya san Mama sai ta zo, shiyasa ya yiwa direba magana akan ya je ya ɗaukota, saboda ya ƙira other driver ɗin, and he told him he's with Abba. Direba shigewa motar yayi tare da mata key ya kama hanyan Rayfield dan ɗauko Mama, Umar kuma daga haka ya wuce side da masallaci yake, ya samu waje ya zauna tare da ciro wayarshi yana dannawa, duk da gefe guda na zuciyarshi tunani ne na daban. A cikin ɗaƙin kuma, kaman yanda Umar ke kallon Sadeeq har ya fice, in same way Umma ma ta zuba wa Sadeeq ido, ta san ba haka yake yi wa Sadiya ba no matter how the cause of pain he's bearing, zai yi making peace at Sadiya's heart, he'll talked to her ko da kuwa ba zai yi wa kowa magana ba, zai rarrasheta ba ya bari tayi kuka, amma yanzu ta ƙira shi bai amsa ba, ta yi kuka bai ce komai ba har Umar ya amshi waya, babban abun ma shi ne yanda ya yi yanayin kaman ciwon ƙirjinshi zai motsa, Umma ba tare da ta janye idanuwanta a kan Sadeeq ba ta ce, "Me ke faruwa Sadeeq?" Shiru Sadeeq yayi bai cewa Umma komai ba, har ya ƙoƙarta ya miƙe tsaye, haƙoranshi taune da lip nashi, taking steps nashi yayi zuwa gado, sannan ya kwanta in a simple way, ya lumshe idanuwanshi yana jin yanda ƙirjinshi ke mishi zafi matuƙa, ga bugun da zuciyarshi ke yi very fast. Umma tana bin shi da ido har ya kwanta, sannan ta kuma cewa, "lafiya kuwa Sadeeq? Ko dai jikinne?" Ciki-ciki Sadeeq ya ce, "Am okay Umma." "To Allah ya kara sauƙi", faɗin Umma tana sauƙe ajiyan zuciya. Sadeeq idanuwanshi a lumshe ya furta, "Ya Hayyu Ya Qayyum", tare da dafe saitin zuciyarshi yana ƙara taune lip nashi, saboda muryarta tana kuka yake ji har yanzun a kunnuwanshi yana mishi amsakuwwa. ⭐️ RAYFIELD SADIYA POV *** Kuka Sadiya take yi billhaƙƙi kaman wacce ake yankewa wani sassa na jikinta, a haka Mama da ta shiga kitchen ta dawo ta samu Sadiya,da mamaki kuma da tunanin me ya samu Sadiyan ta ce, "lafiyanki kuwa? Jikin naki ko kuma jikin Sadeeq ɗin ne?" Sadiya kukan kawai ta cigaba da yi without giving answer to Mama, ƙarshe ma tashuwa tayi ta wuce ɗakinta tana kan kukan, tana shiga ɗakin ta faɗa kan madaidaicin gadonta tare da making her crying sound more louder, saboda ji take kaman ta fire ta ganta a hospital ɗin. Mama da kallo ta bi Sadiya har ta shige ɗakinta, numfashi Mama ta sauƙe a lokaci guda kuma ta girgiza kai tare da cewa, "Allah ka shirya mini wannan yarinyar", daga haka Mama ma ta wuce ɗakinta dan ta shirya ta samu ta tafi asibitin. A gaggauce mama ta sanyo hijabinta ta fito ta wuce kitchen, komai da ya kamata ta hada a madaidaicin basket sannan ta wuce dakin Sadiya, ba tare da ta bi ta kan kukan Sadiyan ba ta ce, "ki kula sosai bari naje na dawo, kema Allah ya ƙara miki lafiyan", daga haka mama ta juya ta yi tafiyanta, tana ficewa a gidan ta yi kwana ta nufi gidan su Sadeeq ɗin, dan ta yiwa direba magana ya kai ta tunda ta san ko abin hawa ta fice za ta nema to za ta bata lokaci ne kawai saboda yamma ta yi, balle ma Abba ya ce muddin direba na nan ko ina za su to direba ya kai su amma bai yafe ba su hau abin hawa na haya alhalin direba ko yaran suna gida, wannan yana ɗaya daga cikin karamci da mutuncin su Abba da zuri'arsa gare su. Mama bata tarar da direba ko guda ba a gidan, mai gadi ne bayan sun gaisa ya sanar mata cikin girmamawa kan cewa direbobin duka biyu sun fice, hakan ya sanya Mama ta jinjina kai tare da yiwa mai gadi godiya ta fice, hanya ta miƙa da niyan ƙarasawa bakin hanya ta nemi abin hawa, dan dama ba su da rata da bakin hanya sosai, kawai samun abun hawan ne ke wahala musamman da yanzu magrib ya kusa. Mama na tafiya cikin natsuwa kanta a ƙasa har ta isa baki hanya, tana ta ƙoƙarin tare masu adaidaita sahu, amma ba wanda ya tsaya ko guda, tana kan tarewa sai mota ya parker a gabanta, direba da umar ya yiwa magana ne ya hangi Mama tun da ya tinkaro junction na anguwan nasu, hakan ya sanya ya daidata motar a dai-dai gaban Mama tare da sauke gilashin motar saboda ta gan shi, sannan cikin girmamawa direban ya fito tare da miƙa hannu ya amshi basket na hannun Mama yana fadin, "Afuwan Hajiya Mama hanyar ne da yake yamma yayi ababen hawa sun yawaita sosai shiyasa na bata lokaci." murmushi Mama tayi tare da shigewa bayan motan inda ya bude mata ya kuma kulle da ta shiga, sai da ya aje basket din a cikin motar sannan ya zagaya mazauninshi ya ja motar, yana kuma bai wa Mama hakuri. Mama murmushi ta kuma yi tare da cewa, "Ba komai Iliyasu, ai dama yamma ta yi to hanya sai a hankali tunda kowa na hada-hadan komawa gida ne duk antashi ayyuka, fatan dai Allahu ya kai mu lafiya." "Amin Hajiya Mama", faɗin direba tare da mai da hankalinshi ga tuki dan su samu su isa kamun a shiga sallan magrib da aka soma ƙiraye-ƙirayen shi a wasu masallatan. A ma'adana motoci direban ya daidaita sahun motar, bayan da suka shiga harabar asibitin, sannan ya fito cikin hanzari, dai-dai Mama ma ta fito, hakan ya sanya ya ɗauko basket ɗin tare da rufe ƙofan bangaren Mama sannan ya wuce ya mara wa Mama baya suka nufi ɗakin da Sadeeq yake. Da sallama Mama ta tura ƙofan ɗakin ta shiga direba ya rufa mata baya, sannu ya yiwa Umma tare da tambayan ya mai jiki, ta amsa mishi sannan ya aje basket ɗin ya juya ya fice, direct masallacin da ke a asibitin ya nufa yana ida alwala ya ji muryan Umar na tambayanshi har ya ɗauko Maman? cikin girmamawa ya jinjina wa Umar kai tare da cewa, "Na kawo ta suna ciki da su Hajiya Umma." Jinjin kai Umar yayi, sannan suka shige masallacin, bayan sun ida salla suka fito, direba ya tsaya nan waje wajan mota shi kuma Umar ya nufi ɗakin da su Sadeeq suke, bakinshi ɗauke da sallama ya tura ƙofan ɗakin ya shiga. Mama sannu ta yiwa Umma bayan shigowanta, Umma na murmushi ta cewa Mama, "Sannunku da hanya Maman Sadeeq, kin taho kin baro mini auta ita kaɗai, ai dole ma na tashi na koma gida na kula da autata." Mama na ƴar dariya ta ce, "Autanki ko rigima Ummansu, lamarin wannan yarinya taki sai addu'an shiriya kawai." murmusawa Umma tayi tare da fadin, "Allah shirya mana ita ya mata albaka." "Amin, Allah ya albarkacesu duka", faɗin Mama sannan ta ƙarasa gaban gadon da Sadeeq ke a kwance idanuwanshi a lumshe kaman mai bacci, cikin kulawa da tausayawa take kallonshi, sannan ta juyo ga Umma tana faɗin, "Mai babban suna ya faɗa sosai wallahi, Allahu dai ya bashi lafiya." "Amin Maman Sadeeq", faɗin Umma tana ƴar murmushi, dan lallaikam duk da irin kamammiyar jikin Sadeeq ta jarumai, amma fa duk wanda ya sanshi muddin ya kalle shi, to lallai zai tabbata a ɗan kwanakin ya faɗa sosai. Mama da ta zaci Sadeeq bacci yake, cikin tausayawa ta ce, "Sannu Babana, Allahu dai ya tashi kafaɗunka ya baka lafiya." Sadeeq da tunda ya kwanta ya lumshe ido yake tunane-tunenshi a kan Sadiya, yana jin komai har shigowan su Mama har maganganunsu, yana son ya yiwa Mama sannu da zuwa amma ƙirjinshi matuƙar nauyi yake mishi, hakan ya sanya bai bude ido ba balle yin magana, sai da Mama ta mishi sannu a yanzu, sannan cikin dauriya ba tare da ya bude idanuwanshi ba, a sanyaye ya ce, "Amin Mama sannunku da zuwa." Mama sanin halin Sadeeq na rashin son dogon magana ko yana lafiya balle kuma babu lafiya, hakan ya sanya ta murmusa tare da jinjina mishi kai kawai. Umma miƙewa tayi tare da faɗin, "Naji ana ta ƙiraye-ƙirayen sallah tun kamun ku shigo, bari na alwalo na zo na miƙa." "Aikam ki fito nima na samu na yi alwalan, dan nima ban yi magrib ɗin ba", faɗin Mama tana zama a ɗaya kujeran. Umma na shigewa ba jimawa ta fito da alwalanta, ta tada sallah a kan darduman da ke shumfiɗe, Mama kuma ta wuce toilet ɗin, Mama na fitowa sai Umar ya turo ƙofan ɗakin ya shigo da sallama, amsawa tayi ya iso ciki yana faɗin, "Sannunku da zuwa Mama." "Yauwa Umar, nikam me ka cewa Sadiya ne ta kama kuka kaman ka zage ta", faɗin Mama da duk lissafinta kukan Sadiya dalilin Umar ne ko ya ce mata wani abun. Umar taɓe baki yayi yana faɗin, "Wannan shirmammiyan yarinya bulala take buƙata kawai." Kamun Mama ta bashi amsa, Umma da ta ida shafa addu'anta ta ce, "To lallai kuwa watan da za a ji mu ya kama, ita autar za a zane? Yarinya abun a tausaya mata ga hidiman biki? A dai dinga sassauta mata dan Allah." "Hmmn!", kawai Mama ta faɗa tare da gyara hijabinta ta ƙarisa kan darduman da Umma ta sauƙa, ta tada sallahnta, dan ba ta da abin cewa, rigimar Sadiya sai dai Allah shiryata, musamman da ta samu ga Ummansu da Abbansu da mai babban suna suna goya mata baya. Umar cikin son ɓatar da maganan, ya ce, "Umma, Sadeeq ya tashi yayi sallah kuwa?", yayi tambayan ne dan kaucewa surutun Umma, dan yanzu sai tayi ta cewa ya matsa wa autarta. Umma girgiza kai tayi tare da cewa, "Banma ce ko sun gaisa da Mamanshi ba, taimaka mishi ya samu ya tashi ya lallaɓa yayi sallahn, tunda dai yana iya tashi yayi gwanda ya lallaɓan." Umar ba musu ya ƙarisa wajan Sadeeq, hannunshi ya kai da niyan taimakawa Sadeeq ya tashi yana faɗin, "Ka samu ka lallaɓa kayi sallah.." Kallon da Sadeeq ya watsa mishi shi ya dakatar

Chapter 8 of 32