rasa inda zaki sa kanki saboda surutan mutane, gara ayi surutan akan su biyu ya aura, da ai surutan kin hana Auren, da azo daga baya taje suyi miki aika aika, dan ni na tsorata da yadda suke son juna, tunda tazo gidana hutu, na gane ba ƙaramin so take masa ba"
Jiki a sanyaye Maman Ilham tace "shikenan Yaya Atine, amma ya zan gayawa Ihsan? Ina jin tausayinta sosai"
"Ki ƙyaleta karki gayamata yanzu, naga kamar tana cikin damuwa yanzu haka, kuma zata iya bijirewa tace ta fasa auren, kuma abunda bama so kenan"
Haka Yaya Atine taita kwantarwa da Maman Ihsan hankali..
Imran kuwa har suka je gidan Alhaji Hashim, be kuma cewa uffan ba, sam baya nadamar dukan da yaiwa Amira, saboda ƙiriniyarta da rashin jinta yai mata yawa, duk da kusan ƙarfe sha biyu na dare, suna zuwa gidan Alhaji Hashim aka buɗe musu gate, dayake Abba ya sanarwa da megidan zuwansu.
A harabar gidan, suka tarar da Alhaji Hashim, ya ƙaraso inda sukayi parking ɗin mota, Abba ya fito suka gaisa ya kalli Abba yace "Ali lafiya dai ko? Meke faruwa ne haka?"
"To lafiya amma ba lau ba, Imran ne ya kama Amira ya zaneta wallahi, yanzu gaba ɗaya jikinta ya ɗau zafi, nayi tunanin kaita Asibitin da me ɗakin ka take aiki, se kuma na tuna sunje gurin Dinner ɗazu, kuma ba lallai tana night duty ba, kuma daɗin daɗawa dai, gobe in Allah ya kaimu za'a ɗaura Aure, bana son a samu wata matsala sam"
Alhaji Hashim yace "Eh gara daka kawota nan ɗin, dukda dama munyi da kai bayan an ɗaura zata zauna a nan ne.
Ya ƙarasa gaban motar ya kalli Imran yace "Imran meyasa ka dakarmin 'ya ne, ka fiye zuciya da saurin fushi, dole ka rage wasu abubuwan da kake yi, tashe ta naga kamar bacci take yi, ka shigo da ita, bari in taso matar gidan"
Abba yace "Afuwan fa, zamu takurata"
Alhaji Hashim yace "No karka damu, ai ita tana nan tana jiran zuwan Amira dama, bari in mata Magana"
Imran ya buɗe ƙofar motar ta baya, ya daddaki Amira yace "Malama ki tashi"
A hankali ta motsa, dan baccin wahala ne ya ɗauketa, ga jikinta yayi zafi zauu, ko ina na jikinta Banda raɗaɗi, ba abunda yake mata.
A hankali ta fito daga motar, jiri na kwasarta, ta jingina da jikin motar, taji yadda jikinta ke zugi, ta tuna yadda Imran ya dinga jibgarta ɗazu kawai ta fashe da kuka, harda sheshsheƙa.
Abba yace "yi haƙuri Amira, zaki iya tafiyar ko a riƙeki?"
Ta girgizawa Abba kai, Alhaji Hashim ya fito yace "Bismillah ku shigo"
Abba yace "Imran riƙe hannunta karta faɗi" takaici ne ya kama shi ganin yadda Amira ke wani sake lanƙwashewa, tana tangaɗi.
Baya son yin musu da Abba, dan haka ya riƙe hannunta, suna tafiya a hankali amma kuka take, Abba yai gaba ya rigasu shiga, Amira ta fuzge hannunta daga nasa, taƙi shiga cikin falon ta tsaya ƙyam a waje tana kuka.
"Zaki wuce ki shiga ko sena ɓarar dake a gurin nan?"
"Bazan shiga ba ɗin, ba ɓararwa ba yanka ni zakayi, Mugu kawai"
Muryarta ta shaƙe saboda kuka, ko fita bata yi sosai amma bakin yaƙi mutuwa.
Aikuwa ya shige ya barta a gurin, yana shiga ya tarar har matar Alhaji Hashim ta fito falon, Abba yace 'ina Amiran kuma?"
"Tace ba zata shigo ba, tana tsaye a waje" ya basu amsa.
Abba ya girgiza kai ya taso ya fito wajen, tana tsaye jikinta nata rawar sanyi se kuka takeyi, Abba yace "Amira ki shigo mana, dubaki za'ayi a baki magani ai"
Girgiza kai tayi tace "dan girman Allah a maidani gida, dan Allah kayi haƙuri ku maida ni gida kafin ɗanka ya kasheni, dan Allah kayi haƙuri ku kaini inda zan hau mota in koma gida"
Abba yace "naji amma ki tashi mu shiga a duba lafiyarki, nan gidan Alhaji Hashim ne fa, kin tuna shi"
Matar Alhaji Hashim tace "Ohh dama wannan ce 'yar tawa? Ai na ganta ɗazu a gurin biki, kizo mu shiga ciki kinji"
Maimakon ta tashi, sema ta zube akan gwiwowinta tana yiwa Abba magiyar ita dai a maida ita gida, sedai kan Abban ya kuma magana, Amiran ta faɗi a gurin sumammiya.
Gaba ɗaya sukayi kanta suna kiran Innalillahi wa innalillahi raji'un.
Imran ne ya ɗauketa ya shiga da ita falon aka kwantar da ita, ta ɗakko ruwa me sanyi tana shafawa Amira a fuska, ta cirewa Amira hijjabin jikinta, seda Imran ya ɗan tsorata ganin illar da yaiwa Fatar Amira.
Duk fatarta tayi taruwar jini, harda wani sashe na fuskarta, akwai almar duka.
Hajiya Nafisa matar Alhaji Hashim, wadda suke cewa Anty ta ɗago ta kalli Abba tace "waye yai mata wannan dukan haka?"
Abba yace 'gashi nan ɗanki ne Imran"
Anty tace "da wani ne ba kai ba Imran, da tabbas sena kai ka Human rights, haba Imran kamar ba wayayye ba? Ya zaka zage ƙwanjinka akan mace kamar haka, kuma ma wadda zaka aura, 'yar uwakka ce fa, ai kamats yayi kowani kaga ze mata haka, ka tsaya mata amma kai da kanka, dan abun kunya, kuma da alama jikinta baya son duka, dan shine ya samata wannan zazzaɓin, amma karku damu zata farfaɗo insha Allah, zanyi amfani da wannan damar ma, a ɗibi jininta a daren nan a kaishi lap, ayi mata duk gwajin daya dace"
Abba yace "to shikenan Nagode sosai, Allah ya saka da Alkhairi ya bar zumunci"
Suna nan zaune a daren, aka sakawa Amira ruwa bacci ya ɗauke ta.
Haka nan a daren Abba da Imran suka kuma komawa gida, suna tafe Abba yana ƙara yiwa Imran Nasiha.
Ammi kuwa bata ga kiran Maman Ilham ba se bayan sha biyun dare, bata bi kiram ba saboda a ganinta dare yayi, tace bari ta bari seda Safe ta kirata.
Imran kam kasa bacci yayi, yana tunanin ya Ihsan zataji idan taji labarin su biyu ze aura, ya tabbata maƙaryaci kuma mayaudari kamar yadda ta faɗa, tun farko yakamata ace ta sani, ba yanzu da lokaci ya ƙure ba, Amira ta ɓata masa komai, ga Yadda ran Abba ya ɓaci saboda dukan da yai mata, wannan yarinyar a sanadinta Komai na tafiya ba yadda ya so ba.
Haka ya wayi garin Allah duk da tarin gajiyar da yake ɗauke da ita, amma ya kasa bacci, ranar ɗaurin Aurensa ne, amma sam baya murna da ranar, gaba ɗaya jikinsa a sanyaye yake.
Da Safe wajen ƙarfe takwas da rabi, aka takurawa Ihsan taci Abinci, haka nan gabanta yake ta faɗuwa, maimakon tayi farinciki da ranar ita ma faɗuwar gaban ce ke damunta.
Bayan ta gama cakalar Abinci, ana cewa me kwalliya zata zo ta mata kwalliya, kafin 'yan ɗaurin Aure suzo, Yaya Atine taje ta sameta ta cewa ƙawayenta su ɗan basu guri, aikuwa suka fita suka basu guri.
Ta rufe ƙofa ta dawo ta zauna a kusa da Ihsan tace
"Ihsan ina son ki buɗe kunnuwanki da kyau ki saurareni, ina son ki ɗau abunda zan gaya miki a matsayin ƙaddara kamar yadda muka ɗauka ni da mahaifiyarki, jiyavda daddare wan Mahaifinki yazo bayan an dawo daga gurin Dinner, ya gaya mana wani abu da ya girgiza mu, amma kamar yadda na taushi mahaifiyarki ta haƙura ta kwantar da hankalinta, kema haka nake so kiyi haƙuri ki kwantar da hankalinki, kamar yadda kika sani anjima za'a ɗaura miki Aure da Imran, sedai ku biyu zaku aure shi"
Ihsan ta kalli Yaya Atine tace "Kamar yaya kenan?"
"Eh, haka wan mahaifinki yazo ya gaya mana jiya daddare, amma dan Allah ki kwantar da hankalinki, amma keda abokiyar zamanki za'a ɗaura Aurenku yau"
"Innalillahi wa innalillahi raji'un, meyasa Imran zemin haka? Dama abunda yake shiryamin kenan? Duk yadda na bashi yadda amma shi ba haka bane a gurinsa, dama nasan za'ai haka, tuntuni nake ganin take takensa amma soyayya ta rufemin ido, to yaje ya auri duk wadda yake so, amma Aure ni da Imran babu shi, na haƙura na barwa kowa cece na bar mata Imran, na haƙura, bazan Auri Imran ba wallahi na haƙura!!!"
Tai maganar cikin kuka me ban tausayi, Yaya Atine tace "Ihsan karki wa kanki biyu babu, wan mahaifinki yace ɗayar Umarnin mahaifinsa ne yasa ze Aureta, kiyi haƙuri ki kwantar da hankalinki"
"Ni ba wani hankali na da zan kwantar, an cuceni an yaudareni, idan 'yarsu ce ni zasu min haka ne, ba wani Auren biyayya dama can an shirya wulaƙantani ne, ni ba zan zauna da kishiya ba, na haƙura da Imran na fasa Auren"
Nan da nan Ihsan ta birkice, ta dinga koke koke tana bori, tace Allah karta ba zata auri Imran ba, jikinta ya riga ya gama bata Amira ce matar da ze Aura su biyu.
Rarrashin duniya amma Ihsan fafur taƙi sauraren kowa, se kuka da takeyi kamar zata shiɗe, nan da nan idanunta suka kumbura, ta fita hayyacinta kamar wadda akace za'a kashe.
Imran kuwa ya kasa komai, se aikin tunani harya faɗa saboda damuwa da tashin hankali, ga tausayin Ihsan da yake ji, saboda yasan yadda take kishinsa da ƙaunarsa, yasan tabbas an mata ba daidai ba, haka Khalid yazi ya same shi a kwance a ɗakinsa.
"Imran meye hakane? Anjima fa ɗaurin Aure amma kana kwance kamar wani ruwa, dan Allah tashi mana"
Imran ya tashi zaune yai ajiyar zuciya ya dafe kansa yai shiruu.
Khalid ya dafa shi yace "Imran ya dai? Akwa matsala ne?"
Imran yai ajiyar zuciya yace "Khalid, wallahi sam bana murna da wannan ranar, ina jin tausayin Ihsan, ina ji a jikina ban mata adalci ba, na cutar da rayuwarta, na ɓoye mata abubuwa yanzu tana min kallon mayaudari maƙaryaci, ban san wace irin karɓa zan samu a gurinta yau ba, gefe guda waccan mahaukaciyar jiya dan rashin nutsuwa suka hau dambe da Minal, a gaban mutane jiya a gidan nan, naje na rabasu amma yarinyar nan taƙi jibharda cizona, zuciya ta ɗebe ni, na mata duka jiya, a daren Abba yasa muka tafi kaita gidan Alhaji Hashim, kusan a sume ta kwana, saboda ko kafin mu bar gidan nan, zazzaɓi ya rufeta tana ta layi, yanzu haka Abba kusan fushi yake dani, ni ji nake dama ban ɗakko maganar Aure ba, komai ya kwaɓemin ya lalace".
"No karka faɗi haka, ka kwantar da hankalinka komai ze wuce, tabbas Ihsan abar tausayi ce ta cancanci a tausaya mata, duba da irin son da take maka, amma a zahiri Amira ce abar tausayi, kuma gaskiya dukan ta da kayi baka kyauta ba, dan ba shine mafita ba sam, ni dai ina baka shawara da kaji tsoron Allah Sannan ka kamanta adalci a tsakaninsu duk da nasan Amira ba zaɓinka bace zaɓin Abba ce, amma kayi haƙuri Auren Amira da zakayi tamkar Jihadi ne, ko da baka sonta ka ji tausayinta ka riƙeta tsakani da Allah, ko dan Saboda maraicinta da kuma 'yan uwantakar dake tsakanin ka da ita"
Imran yace "ita wannan yarinyar tana tausayin kanta ne ko duba maraicinta, ni ina tsoron zamansu Guri ɗaya da Ihsan ta cutar min da mata a banza"
"Itama ai matarka ce, kuma bana jin duk abunta idan Ihsan bata kulata ba ba zatayi mata ba"
"Kaga Khalid ƙyaleni, bata wannan nake ba, ni ta Ihsan nakeyi itace a raina"
"Ita waccan ɗin daka sumar bata gabanka kenan?"
"Wallahi ko tausayinta banji ba, ina dukanta tanamin Allah ya isa, kai Yarinyar nan idan mutum ya biye mata, seya kusa kasheta ma"
"To kai waye yace ka dake ta? Baka san irin Amira rarrashi suke buƙata ba"
Tsaki Imran yayi ya miƙe ya nufi banɗaki, dan ko zancen Amira baya son ji, a ganinsa a dalilinta ne yake neman rasa farincikinsa.
Amira se wajen ƙarfe Bakwai ta farka, ta ƙarewa ɗakin da take ciki kallo, tunanin tayi ta tuna abunda ya faru jiya da daddare dukan da ta sha a hannun Imran, da kuma yadda suka zo wannan gidan, ta tashi zaune a hankali, ɗakin ɗan madaidaici me kyau, ta kalli hannunta taga ruwa a jikinta, ta sunkunyar da kanta tai shiru tana jiran taga ta inda wani ze shigo ta nemi yadda zatai, tayi salla.
Turo ƙofar ɗakin akayi, aka shigo da Sallama wata matace ta shigo, ta kalli Amira tace "ashe kin tashi ya jiki?"
"Da sauƙi" Amira ta amsa a hankali.
Ta ƙarasa shiga cikin ɗakin tace "bari in cire miki ruwan, ki shiga banɗaki kiyi wanka kizo kiyi salla kafin Antyn ta fito"
Amira ba tace Komai ba, ta cire mata Ruwan, ta nuna mata banɗaki, ko ina na jikinta yayi tsami se raɗaɗine ke ratsa fatarta.
Matar ta bata hijjabi da towel, Amira ta shiga banɗaki, ta haɗa ruwa me ɗumi ta fara zubawa a jikinta, wani irin zafi ya ratsa ta, kawai ta fashe da kuka, ƙarshe da ƙyar tai wankan ta fito.
Tana fitowa ta samu an ajiye mata ƙaton Hijjabi da sallaya, ta zira hijjabin nan tayi salla, ta idar ta zauna tayi Azkar.
Sedai jikinta ba ƙwari sam, ta miƙe ta nufi gaban mudubin dake ɗakin, ta cire hijjabin jikinta ya zama daga ita se towel, ta soma ƙarewa jikinta kallo fatarta tayi ruɗu ruɗu tayi ja, wani gurin a kumbure ya fashe, kawai ta fashe da kuka, hakan yai daidai da shigowar Anty, tana faɗin "Amira Ashe kin tashi?"
Ta tarar da Amira a gaban Mudubi tana kuka, ko ba'a gayamata ba tasan dalilin kukan nata, dan haka ta ƙarasa inda Amira ke tsaye tace "haba Amira ya kuka haka? Kiyi haƙuri nasan Boss be kyauta ba daya dakeki, nima ya bani haushi amma kiyi haƙuri kinji"
Tai maganar tana kamo hannun Amira, ta zaunar da ita a bakin gado tace, ga kayanki nan ki saka, yanzu za'a kawo miki abun karin kumallo da magani, ki dena Kuka kinji yarinyar kirki?"
Amira ta jinjina mata kai, tana cigaba da Share Hawaye, ta kalli Anty tace "dan Allah ki bugawa Abba waya, kice yace wa Su Anty Fa'iza su taho mu tafi gida, koni kisa a kaini tasha in koma gida, dan bazan ƙara zuwa garin nan ba, wannan ne karo na biyu da nayi dana sanin zuwa garin nan" tai maganar tana sake fashewa da kuka.
Anty tace "yi hakuri Amira, insha Allah wannam zuwan naki Kaduna, shine zuwa Mafi Alkhairi kiyi haƙuri". Haka Anty ta zauna taita aikin rarrashin Amira.
Abba yana ta shirinsa, sega Ammi ta shiga ɗakinsa ta sha shadda, tayi rasa da ita kamar ba ita ta haifi su Imran ba.
"Gani naga ka aika a kirani"
Abba yace "eh, dama na aika a kiraki ne dan in sanar dake wata mahimmiyar magana, yakamata tuntuni ki san maganar amma sanin halinku ku mata musamman ke yasa ban gayamiki tuntuni ba"
'meye halin nawa da kake kashedi a kai?"
Abba yace "ba wannan ba, kamar yadda a baya naso in riƙe Amira amma kika ƙi yadda shi......
"Abba nifa maganar yarinyar nan ta isheni haka wallahi, naga ƙarewa ka ɗauketa bata kwana a gidan nan ba, yau za'a gama biki ta tarkata tabi 'yan uwanta su koma gida mungode Allah yasaka da Alkhairi, nifa ban riƙe Yarinyar nan a baya ba, a yanzu fa bazam riƙe ba gaskiya"
"Inke ba zaki riƙe ba ɗana Imran ze riƙe"
'kamar yaya kenan? Yaron daze Aure yanzu za'a kwashi wannan kwazgwamemiyar Baligar a kai masa gida, gata Karuwa, ina Ihsan zata iya riƙe Wannan yarinyar, da yaya Ihsan ta girmeta? Ba tafi Ihsan girma ba, dan Allah Abba ka dinga faɗar abunda ze yiwu mana, 'yan uwa ta ma ba zasu yadda ba, nima bazan goyi bayan hakan ba"
Abba ya kalleta yace "Amira ba a 'yar riƙo zata je gidan Imran ba, a matsayin matarsa zata je ita ma"
"Kamar Yaya? Kana nufin Imran ze auri Karuwa ya haɗa da 'yar mutane?"
"Ƙwarai kuwa, idan ke ban isa dake ba, na isa da ɗana, dan haka Imran ze Auri Amira"
"Amma kaima kasan wannan abun bame yuwuwa bane, wallahi in dai da raina Imran baze Auri wannan fitsararriyar ba, yaje ya auro duk wadda yake so, amma Banda wannan yarinyar".
"Aikin gama ya gama Jamila, saboda a gurin ɗaurin Aurensa da Ihsan, za'a ɗaura Auren sa da kuma Amira!.
Aikuwa a kiɗime tace "akan me zaka yanke wannan ɗanyan hukuncin saboda me? Nima fa ina da haƙƙi akan Imran kamar yadda kake da shi, saboda me zaka min haka? Baka gudun lafiyar ɗanka da na 'yar mutane daze aura, kuma ka kasa sanar dani tuntuni se daidai wannan lokacin da awanni suka rage a ɗaura Aurensa, saboda me zaka yimin haka? Akan me? Wallahi baka min adalci ba kuma ba kayiwa 'yar mutane Adalci ba kum....
"Ya isheki haka Jamila, da Imran da Amira duk 'ya'yana ne, kuma na yanke hukuncin da naga ya dace ba wanda ya isa ya canza min, this is my final decision"
Wani irin gumi ya dinga karyo mata, fuu ta koma cikin gida ɗakinta ta wuce, tana zuwa ta ɗau wayarta ta kira Maman Ihsan, ta kirata ya kai sau Uku Sannan ta ɗaga a hasale tace "Wai meye kike ta kirana haka? Ni da na kiraki jiya kika ƙi ki ɗaga se yanzu zaki isheni da kira, bayan kin san abunda kuka ƙulla ke da ɗanki, kun shirya wulaƙanta mun 'ya"
"Dan Allah Murja kiyi haƙuri, ashe ke kinma san meke faruwa, to ni Wallahi Allah kenan ban sani ba se yanzu, Yanzu da suke shirye shiryen tafiya ɗaurin Aure sannan ya gayamin, saboda yasan idan ya gayamin bazan bari duk yadda zan se na hana, shine be gayamin ba se yanzu, wallahi gaba ɗaya hankalina a tashe yake"
Maman Ihsan tai ajiyar zuciya tace "to Ihsan ma yanzu aka gayamata, gaba ɗaya ta birkice tace ita ta fasa Auren, ta haƙura da shi ta barwa waccan ɗin, naji tana cewa wai Yarinyar Karuwa ce"
"Eh Karuwa ce wallahi, 'yar ƙanwarsa ce, Yanzu haka jiya da daddare baki ga dukan da Imran ɗin yai mata ba, amma dan Allah ki tasuhi Ihsan ki kwantar mata da hankali, nasan matakin da zan ɗauka akan lamarin, amma dan Allah kuyi haƙuri, ban san da Maganar nan ba se yanzu, ku ƙyaleni dasu, ai Imran ni na tsuguna na haifeshi, ba inda Auren nan zeje nina gayamuku, ki kwantar mata da hankali dan Allah, kuyi haƙuri nasan ba ai muku adalci ba"
"Shikenan Allah ya kyauta, ni dai tsorona kar a sawa yarinyata wata cutar daban"
"Wayace miki za'a kai ga nan ma? Ki bar komai a hannuna kawai kuyi haƙuri"
Suka gama wayar, ta kira Imran, Imran na ganin kiran Ammi gabansa ya faɗi, ƙirjinsa ya finga bugun uku uku, yasa hannu ya ɗaga wayar.
"Kana ina ne?"
"Ina gidansu Khalid" ya bata amsa
"Kana sane da Mahaifinka ze aura maka wannan Karuwar Yarinyar?"
Imran yace "wace Karuwar kuma Ammi?" Yai maganar a saɓule.
"Wace banda wannan sheɗaniyar 'yar ƙanwar tasa"
Imran yace "Na sani Ammi"
"What! Dama ka sani amma baka gayamin ba? Kuma ka amince zaka Aureta?"
"Ammi ya zanyi? Abba be taɓa roƙata wata alfarma ba se wannan, se ince bazan masa ba? Ni kaina bana son Auren nan ba yadda zanyi Ammi.
"Dalla rufemin baki, Shashashan banza, algungumi ni zaka gayawa baka son Auren? Da baka son Auren ai da tuni ka sanarmin, musan matakin da zamu ɗauka, amma ba a tashi gayamin ba se Yau, ya rage awanni a ɗaura maka Aure da Ihsan kawai se inji hadda wannan Yarinyar, ka bani kunya ka bani mamaki Imran, gashi can kasa 'yar mutane a damuwa tana ta haƙura da kai ta fasa Auren, Yarinya me nutsuwa da tarbiyya kayiwa kanka, indai karuwace gaka ga ta nan"
Cikin karaya Imran yace "Ammi dan Allah ki saurareni kiji" kashe wayarta tayi ta ƙyaleshi.
Ya ajiye wayar ya zauna Ya dafe kansa, ya easa mema zeyi yaji daɗi.
Khalid ne ya dinga rarrashinsa, yana kwantar masa da hankali.
Tuni sakamakon gwaje_gwajen da akayiwa Amira ya fito, bata ɗauke da Kowace matsala da ka iya kawo tangarɗa ga Aure, kama da gwajin cuta me karya garkuwar jiki wato HIV, ciwon hanta HEPATITIS B, Rukunin jininta BLOOD GROUP, Genotype, Gwajin ciki, PREGNENCY TEST gaba ɗaya lafiyar Amira ƙalau.
Ɗaurin Auren da aka saka ƙarfe sha ɗaya, ƙarshe se bayan da aka idar da sallar Azahar aka ɗaura shi, masallaci ya cika maƙil da manyan mutane, waliyyan Ihsan sun ɗanyi jinkirin zuwa ga mutane sun fara ƙosawa, dan haka aka bada sakamakon gwajin Amira aka fara ɗaura Auren Imran da Amira, ana cikin ɗaurawa ne waliyyan Ihsan suka ƙaraso, bayan an gama na Amira aka ɗaura na Ihsan da Imran.
Amma Ihsan tana can gida tana bori akan ita lallai bata son Imran yanzu ta barwa Amira shi, dan ko an ɗaura an kaita seta dawo.
Seda "yan ɗaurin Aure suka dawo Sannan mutanen gida suka san mata biyu aka Aurawa Imran, ciki harda Yarinyar da ya zane jiya da daddare.
Nan gida ya ɗau cece kuce, su Fa'iza sam basu san meke faruwa ba, ita gaba ɗaya hankalinta yana kan ya Amira ta kwana, ga jakarta da wayoyinta duk a nan ta barsu, ita Fa'izan ce ta ɗauke mata su.
Duk yadda abokan Imran sukayi dashi akan suje gidansu Amarya ayi hotunan ɗaurin Aure ƙi yayi, dan be san da wani idon ze kalli Ihsan ba, da suka dawo gida ma, suka yi walimarsu ta angwaye sam baya walwala, kuma ya kasa shiga cikin gidansu, wanda basu san mata biyu ze aura ba se ranar suna ta zolayarsa, suna ya akai ko a gurin Dinner Amarya ɗaya suka gani, se ranar ɗaurin Aure suji Amare biyu ne.
Shi dai Imran ba wanda ya tankawa, dan shikaɗai yasan meke damunsa.
Gida ya cika da jama'a, ana ta shiga ana fita, ana Allah ya sanya Alkhairi, Abba yasa Anty Hadiza ta nemo masa Fa'iza.
Ko da Fa'iza taje Abba ya sanar da ita halin da ake ciki seda ta girgiza, tasan tabbas akwai daru, nan ta shiga tunanin ko ya Amira zata iya zama da Imran, shi zuciya ita taurin kai da rashin kunya, ta wani fannin an temaki rayuwar Amira, amma ta wani ɓangaren akwai ƙalubale.
Abba yace "Yanzu ki ɗakko mata kayanta da tazo dasu nan, direba ze kaiki Gidan Alhaji Hashim, ki kai mata kayanta, za'a maida ku Kano, sannan zanzo da kaina har Kano, in yiwa su Yadikko bayani in Basu haƙuri akan hukuncin dana yanke ba tare da saninsu dangin mahaifinta ba"
Ita dai Fa'iza ta kasa cewa komai, jiki a sanyaye taje ta tattaro kayan Amira, da nasu kayan Aka haɗasu da direba zuwa gidan Alhaji Hashim.
Har suka tafi hanya basu san meyafaru ba, sun ɗauka zasuje su ɗakko Amira ne su tafi gida.
Suna ta murna da irin shatara ta Arzikin da aka basu, da wanda suka sato a gidan, sam dukan da akayiwa Amira baya gabansu, sema murna da sukayi suna Allah ya ƙara.
Da sukaje gidan Alhaji Hashim kuwa, dama direban sojan nan ne daya kai Amira gurin make up, yace "mutum ɗaya ce zata shiga, dan ita kaɗai aka san da zuwanta ku ku zauna a Mota"
Amina tace "ooh ji wani makirin iyayi".
A sanyaye Fa'iza ta shiga gidan, a falo ta tarar da Anty suka gaisa tace "dama nice wadda nazo gurin Amira"
Anty tai murmushi tace "Sister ɗinta ce ke?"
Fa'iza tace "Eh"
Aka nuna mata ɗakin da Amira take, Amira na ganin Fa'iza ta miƙe ta fara share hawayenta tace "Yawwa muje, dama tun ɗazu ke nake jira, gara mu bar garin nan kan a kasheni"
"Amira ba dake zamu tafi ba, kayanki na kawo miki, keda Garin Kano sedai kije da ziyara"
A fusace Amira tace "Kamar Yaya? Me kike nufi?"
"Saboda yanzu ke Matar Imran ce, an ɗaura Masa Aure dake da Ihsan!!!"
SHARE PLEASE
(Nayi dogon page yau, am expecting your Comments.
Ko ya Amira zata karɓi Wannan batun Auren? Ku kasance da Alƙalamin Marubuciyarku wato Ayshercool, domin gyara Sharhi ko shawara ku tuntuɓeni akan 07063065680 or Follow me on watpad@ Ayshercool7724)
[1/21, 6:08 PM] Ayshercool: 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥
WUTA A MASAƘA
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P. W. A
*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA)
*BAƘIN TABO (Labarin gasa)
*AƘIDATA (Paid Book)
* WUTA A MASAƘA
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in
❌❌❌
Ƙirƙirarren labari ne, ban yadda ayi amfani da kowane sashi na labarin ba ba tare da izinina ba.
(INA WA INNALILLAHI RAJI'UN, NA SADAUKAR DA WANNAN PAGE GA YARAN DA AKA SACE AKA MUSU KISAN GILLA A KANO DA KUMA ZARIYA, UBANGIJI ALLAH YAI MUSU RAHAMA YA KAWO MANA TSARO A ƘASAR NAN, ALLAH YA BAWA IYAYENSU HAƘURIN JURE RASHIN SU)
*_Masha Allah, gaskiya ina jin daɗin yadda kuke Comment da nuna soyayyar ku ga littafin WUTA A MASAƘA, nagode sosai Ubangiji Allah ya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 12 Chapter of 31