da hankali, bayan rashin imani harda shirme, wai waɗan nan sojoji ne taɓ"
"Sojojin ne marasa hankali?"
Amira tace "eh sune, kuma hadda Yayanki, su marasa hankali shi mara Imani, na faɗa tashi kije ki gaya masa, tun da nazo ƙyaleki kawai nakeyi, kuma ina ji a zuciyata in ba wani iko na Allah ba se Amira ta bar miki babban tabo, kallonki kawai nake sokuwa da baki kamar jaɓa"
Wata ƙawar Minal tace "kinga taso mu bar gurin nan, wannan'yar jaraba ce wallahi, neman abokin yi take nema, Minal ƙyaleta mu farinciki ne ya tara mu ba tsiya ba"
Minal tace "kamar kuwa kin san 'yar matsiyatan ce, shiyasa take abu a haka, ni ba inda zanje, ina nan idan ta faɗi ɗaya in gayamata goma"
Tun Anty Fa'iza tana ƙoƙarin shiga tsakani ta rabasu, Amma abu ya gagareta, Minal ta kasa gane Amira tana sane take kunnata tana bala'i, seda ta tabattar ta ɓatawa Minal rai yadda ya kamata sannan ta miƙe ta nufi filin rawa, inda yake ango da Amarya ne kawai a tsakiyar filin, Imran yanawa Ihsan liƙi tana sunkunyar da kanta ƙasa.
Tana tunakarar inda suke, Ihsan ta ɗago kanta, aikuwa sukayi ido huɗu da Amira, Amira ta sakar mata murmushi, tunda Amira ta taho hankalin mutane Ya dawo kanta.
Takaici ne ya kama Imran ganin yadda ta taho jikinta babu ko mayafi, Amira na ƙarasowa ta fara dariya, se dariyar da take tai mata wani mugun kyau, ta kalli Ihsan tace
'Yayata liƙi nazo yi muku, Allah ya sanya Alkhairi, ya baki ikon haƙuri da juriya akan halin mutumin da kika aura"
Nan gaban Ihsan ya shiga harbawa, ta ɗaga kai tana wa Imran kallon tuhuma, gaba ɗaya Imran ya rasa mema zeyi.
Amira ta buɗe jakarta ta ɗakko kuɗi, ta fara liƙa musu, tana yi tana murmushi, gaba ɗaya Ihsan tausayi da dariya take bawa Amira, a ƙalla Ihsan zata kai shekaru Ashirin da biyar, amma ƙirjinta kamar 'yar shekara sha huɗu, siririyace sosai sedai fara ce tas ajin farko.
Khalid ne ya hau kan stage ɗin yace, "Amira matsa kusa dasu in muku hoto"
Amira tace 'to bari a temaka musu, suyi hoto da celebrity"
Wani sojane ya ƙaraso shima, yace Amira ta kawo wayarta a ɗaukar mata hotunan, se cewa tay "Allah ya kiyaye ta ajiye hoton Imran a wayarta"
Imran ya kalleta kawai ya ɗauke kai, ta tsaya a jikin Imran, yayin da ya tsaya yana kallon Amira, Ihsan kuma tanawa Amira kallon tsana da takaici.
Imran ya kalli Amira yace "malama ina mayafin kayan da na haɗa miki dasu?"
"Ni ajiye shi" ta bashi amsa
"Dama dan ki ajiye na baki?"
"Kaga malam karka takuramin mana, haba ka barni in huta nagaji da wannan ƙarfin halin naka"
Imran kawai ya bita da kallon mamaki da takaici.
Aka dinga hotuna, Khalid seda yasan yadda yayi yaiwa Imran hotuna akan high table harda Amira, saboda itama Amrayar ɓoye ce.
Ana gama hotuna ta sakko, an saka waƙar da take so, nam ta fara takawa, cikin salonta na burgewa da jan hankali, sedai bata girgiza jikinta wannan karon, amma rawar ta ta ta bada kala.
Nan fa ta fara shan liƙi, Imran ya dafe kansa yana fesar da numfashi, Ihsan kamar zata fashe da kuka tace "Imran wace wannan yarinyar?"
"Amira ce" ya bata amsar kai tsaye.
"Amma Imran, kai kace min yarinya ce, kuma na nuna maka hotonta kace ba ka santa ba, ashe ita ce Amiran, itace kake zuwa gurinta a Kano? Imran dama zaka iya ɓoyemin wani abu?" Hawaye suka fara bin idon Ihsan.
Dan wata muguwar tsana da kishi ne suka baibayeta, ba namijin daze wa Amira kallo ɗaya ya kauda idonsa, mussaman surar jiki da Allah yai mata, amma a haka Imran ya dinga ce mata ai Yarinyace ƙarama, kuma yazo yai mata ƙarya, Amira 'yar galace luma Karuwa, kallo ɗaya zakayiwa idonta kasan fitsararriya ce.
Wani irin gumi ya shiga tsatstafowa Ihsan, hawaye wani na bin wani
Imran yai ƙasa da murya yace "dan Allah Ihsan kiyi haƙuri, zan miki bayanin komai"
"Bana buƙatar bayaninka Imran, ka bani kunya wallahi" tai maganar kanta a ƙasa tana goge hawayw ta cikin mayafinta.
Hankalin mutane yana kan Amira, dan haka ba kowa ya lura da abunda ke faruwa ba.
MC ne yace "kai Masha Allah, 'yar baiwa muna godiya da wannan gudunmawar ta hanyar nishaɗantar damu da kikayi, ga tsabar farinciki Amarya tana zubar da hawayen farinciki, Amarya Wannan rana ce me girma ya farinciki a gareki, dan haka be kamata aga kina hawaye ba, ango yakamata ka Share mata wannan hawayen mana.
Imran kam ji yayi gaba ɗaya taron bikin ya fita daga ransa, yaji dama Amira bata zo gurin taron ba, Abba ne ya matsa Lallai taje, ga abubuwa na shirin kwaɓewa, yana ƙoƙarin ya rarrashi Ihsan amma a hasale tace masa "dan Allah malam ka ƙyaleni"
Yana ɗaga kai ya hango Amira a zaune, Matasan sojojin nan zarata, sun kewaye kujerar da take, suna ta mata surutu, wani lokacin tayi murmushi wani lokacin kuma ta bisu da kallo.
Wayarsa ya ciro yaiwa Khalid message ya maida ita cikin Aljihunsa, Ƙannen mahaifiyar Ihsan suka je suka kamo hannunta daga kan high table, suka sakata a tsakiyar filin rawa suna jujjuyata suna mata liƙi.
Maman Ihsan ce tace "ke Ihsan wannan wane irin sakarci ne haka, sekace wadda za'aiwa Auren dole? Kukan me kikeyi haka?"
"Ahh ki ƙyaleta, ze iya yuwuwa kukan farinciki ne, kuma ze iya yuwuwa tana tunanin sabuwar rayuwar da zata shi ne" cewar ƙanwar mahaifin Ihsan.
Aka shigo da Imran ma tsakiyar filin, Ammi da su Minal suna masa liƙi.
Khalid ya ƙaraso inda Amira take, yace yana son Magana da ita, tana ganin mutuncin Khalid dan haka bata musa masa ba, ta tashi suka koma gefe ya kalleta yace "Imran yace a maida ke gida yanzu"
"Saboda me, naga ba'a tashi ba?"
"Eh haka dai yace min"
"Gaskiya bazan tafi yanzu ba, kowa yana nan a maida ni gida ni kaɗai, wallahi bazan tafi yanzu ba se an tashi"
Khalid ba yadda beyi da Amira ba, amma tace fafur ba zata koma gida yanzu ba.
Khalid ya zaga yaje kunnen Imran ya gaya masa yadda sukayi da Amira, Imran yaiwa Khalid raɗa a kunne, Khalid ya koma inda Amira take, Imran ma ya koma gefe.
Imran ya kira wayar Khalid, Khalid kuma ya bawa Amira, Imran yace "Malama ni nace a maida ke gida yanzun nan, ki bar gurin taron nan"
"Wai saboda me? Naga dai bani nace zanzo ba, kasa aka kawoni, kuma kowa yana nan sekace a maida ni gida, wallahi bazan tafi yanzu ba, sedai in tashi akayi"
Imran yace "ni kike gayawa haka?"
"Toni me nace, idan kuma baka son in zauna seka zo ka maida ni gida, Amma baza'a maida ni gidan nan inje in zauna kamar mayya ba"
Yana ƙoƙarin sake yin Magana, Amma Amira ta katse kiran ta bawa Khalid Wayarsa.
Khalid yace "Amira ki dena yiwa Imran haka baze ji daɗi ya baki umarni kiƙi bi ba"
"To me nayi masa, kawai ina zaune yace sena koma gida haka akeyi?"
"Yi haƙuri, baki san dalilinsa na faɗar hakan ba, kiyi haƙuri a maida ke, nida kaina zan maida ke gidan ma"
Amira ta tura baki irin bata so ɗin nan ba, Khalid yace "yi haƙuri Amaryarmu, tashi muje karya miki faɗan nasa idan kuka koma gida"
'Amaryarku kuma? Wuce nan ga amaryarku can bushashshiya kamar karan dawa"
Tai maganar tana jujjuya idonta, tuna sakin layin da yai yayi, yai saurin cewa "Ai kyan da kikayi baza'a banbanceki keda Amrayar bane"
"To bari in kira su Yaya Fa'iza, se ka maida mu tare"
"A'a, akwai motocin da zasu maidasu, keɗin dai ki taso mu tafi"
"To ai banci Abinci ba, kuma ina jin yunwa dan azabtar dani yai tayi, sedai ya bani cake, ko abunda bazan ƙoashi ba"
Khalid yai dariya yace "an ajiye miki komai naki, yana mota taso muje in kaiki"
Haka ta miƙe tai gaba, jikin nan nata bako mayafi suka fita daga hall ɗin, seda suka fita akan idon Imran sannan hankalinsa ya kwanta, amma ya ƙule ƙwarai da Amira yau, dan ji yai tamkar ya maƙureta a gurin nan.
Har cikin gida Khalid ya shiga da motar, sannan ya fito ya buɗe mata motar ta fito, ya bata babbar leda cike da duk wani abu da'aka raba a gurin nan, ta karɓa ta kalli Khalid tace "Nagode sosai Allah ya saka da alheri, kana da kirki sosai ba kamar wancan masifaffen ba"
Khalid yace "ba ruwana kumfi kusa"
"Ba wani kusa, waze raɓi wannan masifaffen, seda Safe" tana gama faɗin haka ta tafi.
Khalid yai murmushi, wato gaba ɗaya Amira simple ce, babu babban abunda yake biyar da ita cikin sauƙi irin rarrashi, bata son faɗa dan shi ke sata taurin kai, sedai kuma Imran is very serious Man, be fiye son shirme ba.
Khalid ya hau motarsa ya koma gurin bikin, sedai yana zuwa ya tarar Dangin Ihsan sun ɗauketa sun tafi da ita gida, dan ta kasa kwantar da hankalinta kuka kawai take, ga jiri yana ɗibarta, ƙarshe ba Amarya aka ƙarasa dinner, seda Ammi ta tambayi Imran ko dai wani abun yai mata, yace shi be mata komai ba.
Haka aka tarkata kowa ya fara kama gabansa, saboda dare yayi ga Amarya ta tafi.
Su Sadiya da Amina aka samu banza, Abinci kamar zeyi Magana haka suka dinga lodar Abinci, suka dinga fakar idon mutane, suna kwashe lemuka da kajin da 'yan gayu suka bari, Ummma kuwa dama teburi teburi ta dinga zagawa, Sauran cake ne ko donut ko kaza haka ta dinga tattaresu a leda, shinkafa kuwa duk haɗamarsu seda syka tureta, haka lemuka ma suka sha iya shansu, suka dinga saye sauran.
Amira kuwa kayanta na ɗakin Imran, tana son ɗaukar doguwar rigar daya sai mata ta saka, ta canza wannan kayan na jikinta, Amma ɗakin na rufe dan haka ta haƙura.
Akwatin Anty Fa'iza ta gani a wani ɗaki, taje ta buɗe sega shi hadda kayanta irin wanda take zuwa ta bari a gidanta tazo mata dasu.
Tai murmushi ta ɗauki wata riga da wando na bacci, taje ta watsa ruwa ta sauya kayan jikinta, ta cire wannan leshin daga jikinta, tai alwala tai sallar magariba da isha'i taci Abincin ta, sannan mutane suka fara dawowa gidan daga gurin dinner.
Taje ɗakin Ihsan, ta kwantar da wata katifa, ta ɗauki bargo akan gadon Minal ta kwanta, ta ciro wayarta ta hau chatting.
Ji tayi hayaniya na ƙaruwa, alamar mutane nata dawowa, yau a shirye tale da duk wani Iskanci na Minal, yau idan ta taɓata ba zata ɗaga mata ƙafa, shiyasa ma tazo ɗakin ta kwanta.
Aikuwa babu jimawa sega Minal ta shigo, ta kunna fitilar ɗakin sega Amira tayi lumui a cikin bargo, akan katifa ga wayarta tana chatting.
"Kan Uba, ubanwa ya baki izinin shigomin ɗaki harki kwanta"
"Ubanki ne" ta bata amsa, sannan ta maida kanta kan wayarta.
"Ni kike cewa Ubana?"
Amira tai mata banza, bata kulata ba.
"To wallahi sekin bar ɗakin nan, ai ba da babanki aka haɗu aka gina ɗakin ba, Karuwar banza data wofi, har zaki zo ki naniƙarmin bargo haka, mara mutunci mara tarbiyya, kece me kushe mutane da raina mutane, bayan kece me abun faɗa*
Jin hayaniya yasa Anty Hadiza ta shigo ɗakin tana faɗin "Ke Minal, ke da wa haka? Muryarki kawai ake jiyowa kina masifa, lafiya?"
"Ina fa lafiya wannan ƙaramar karuwar tazo ta kwantamin a ɗaki, wallahi seta barmin ɗakina, mar tarbiyya kawai baki ji yadda ta dinga zagin Yaya Imran ba, tana kushe Ihsan, dan tana taƙama da ƙaramin Iskancinta"
Amira ta miƙe ta kalli Minal tace "karki ƙara cewa ina taƙama da ƙaramin iskanci, da babban nake taƙama, kuma na zagi Imran ɗin waye yace yamin abunda zan zageshi? Ki kiyayeni wallahi" Amira tai maganar cike da kashedi tana nuna Minal.
"Bazan kiyaye ki ɗin ba, kuma kema na zegeki karuwa kawai 'yar gidan karuwai mara tarbiyya"
Amira tace "Naji nagode, amma nikaɗaice Karuwar, banda iyayena"
Ta koma ta kwata, Anty Hadiza tace "gaskiya banji daɗin abun nan da kukayi ba, kamar ba 'yan uwa ba da giemanku da komai kamar wasu ƙananan yara, Minal karki kuma ce mata karuwa kinjibna gayamiki"
"To Anty Hadiza ba karuwar bace? Ai karuwar ce mara amfani, kai kuma wallahi seta barmin ɗakina"
Tai kan Amira, ta janye bargon jikin Amira, tana ƙoƙarin fizgo Amira akan katifa, aikuwa Amira ta shaƙoata, take kokowa ta ɓarke a tsakaninsu
Anty Hadiza da sauran mutanen dake gurin suka kasa rabasu, aka samu wata taje ta gayawa Ammi, wadda dawowarta kenan, aikuwa a sukwane Ammi tai ɗakin Minal, jin ana can ana tumurmusar autarta.
Tana zuwa taga an taru akansu, amma sunƙi rabuwa, da an rabasu Amira ta haƙura se Minal ta kuma dako tsalle Lallai seta rama abunda Amira tai Mata.
Shikuwa Imran tunda suka taho da Khalid, baya jik me Khalid yake faɗa, dan hankalinsa baya jikinsa sam, tunani daban daban ya cika masa zuciya, harya rasa wanne zeyi ma.
Suna zuwa gida Imran ya fito daga motar, sega Anty Hadiza tace "Yawwa, gara da Allah ya kawoka, wallahi Amira da Minal ke dambe tun ɗazu an kasa rabasu"
"Kamar yaya dambe kamar wasu maza"?
"Ni dai zo muje, ƙil in suka ganka su bari"
Cikin sauri ya shiga cikin gidan, Ammi na ganinsa tace "maza zoka ƙwatarmin 'yata daga hannun wannan azzalumar da kuka haɗa kai da mahaifinka kuka kawomin gida, ta saba dambe da maza a bariki shiyasa take da ƙarfi kamar namiji, nibkarta kashemin 'ya dan idan ra kashe ta bazan yadda ba"
Imran wani takaici ya mamaye zuciyarsa, yaje yana ƙoƙarin janye Amira da gaba ɗaya idonta ya rufe, Amma ta gasa masa wani lafiyayen cizo a hannunsa, aikuwa yasa hannu ɗaya ya fizgota a jikin Minal, yai jifa da ita gefe guda.
Cikin kuka Minal tace "Na faɗa na kuma, Karuwa 'yar gidan Karuwai, ballagaza mara tarbiyya kawai"
"Shut up!" Yaiwa Minal tsawa yace "banzaye sekace karnuka, dambe a gaban jama'a dan abun Kunya, Ke Minal ubanwa yace ki biye mata kin san ba ƙarfinku ɗaya ba, ta fiki girma ita faɗa a cikin ta kamar Karya, tai da maza tayi da mata"
"Niba karya bace, karka sake cemin karya, dan ban taɓa faɗa da maza a titi ba, kuma wallahi ta kuma zagina sena maƙure mata wuya, kuma in kana da zuciya ka ƙyaleni in tafi gidanmu a daren nan, dan nan ba gidan ubana bane kamar yadda ake goranta min"
'ni kike gaywa haka?" Yai maganar yana nuna kansa.
Cikin kuka tace "eh na faɗa ɗin"
Hanyar waje yayi ya ƙyaleta, ta zauna tana kuka, Minal ma kukan take tana cigaba da mita se Amira ta bar mata ɗaki, mutane kuwa kowa da abunda yake tofawa, ai sega Imran ya dawo da wata wayar wuta a hannunsa, ya rufe ɗakin nan, wanda suke ciki suna ciki ya soma zuba musu ita su biyun.
Dama gashi a ƙule yake da Amira, yau duk ransa a ɓace yake.
Minal na ihu tana bawa Imran haƙuri, tana kiran Amminta tana bashi haƙuri, Amira kuwa Ihu take tana Allah ya saka mata.
Hakan kuwa ya fusata shi, ya koma kan Amira ya dinga zuba mata wayar nan a jikinta, ga kayan baccin jikinta Nylon ne, ta ɗora hijjabi a kai.
Amma tuni hijjabin yai nasa guri ya bar Amira, "Allah kaga abunda wannan bawan naka yakemin, Allah ka sakamin wallahi na barka da Allah"
Kowa na gudun tunkarar Imran ya ƙwaci Amira, saboda duk wanda yazo gurin ze iya haɗawa da shi, Ammi ta window ta dinga kiran sunan Imran tana karya kashe mata 'ya, Amma be saurareta ba.
Anty Fa'iza ma da tuni suka dawo, ta dinga masa magiya akan ya ƙyale Amira, dan ta san idan ze kashe Amira ne bakinta baze mutu ba, dan Amira akwai taurin kai, kuma bata son duka sam.
Allah ya temaketa ta buɗe ƙofar ɗakin, tai waje da gudu jikinta na tsuma, saboda ta daku ba ƙarya.
Abba kuwa daga part ɗinsa ya dinga jiyo hayaniya sama sama, yaji abun yaƙi ƙarewa dan haka ya fito, yana fitowa yaga Amira ta fito da gudu tana kuka, tayi hanyar waje sedai tana zuwa har an rufe gate ɗin dan haka Abba ya samu damar cin mata, ya riƙo hannayenta yana faɗin "Amira lafiya kuwa? Meyasameki haka?"
Kasa magana tayi se kuka da take kamar ranta ze fita, Anty Fa'iza ce ta ƙaraso ta cewa "gaskiya ba zamu kwana a gidan nan ba, tunda munzo anyi biki Allah ya amfana, Imran ze iya illata Amira"
Cikin rashin Fahimta Abba yace "meyafaru ne?"
"Faɗa ne ya haɗa su da Minal ya dake su, Amma dukan da yai wa Amira ya wuce tunani, tana mace be kamata ya mata wannan dukan ba, kalli jikinta fa"
Gwanin ban tausayi, fatarta duk ta tara jini, wani gurin ya farfashe se rawar sanyi take tana kuka.
Abba yace "Innalillahi wa innalillahi raji'un, Imran ɗin ne yai mata haka?"
Dukda dukan da Imran ɗin yai mata, sam be huce ba ransa a ɓace yake sosai, yana fitowa harabar gidan yaga Abba a tsaye riƙe da hannun Amira, Mutane duk a tsaye a gurin.
Gabansa ne ya faɗi ya ƙarasa gurin, yana zuwa zeyi magana Abba ya dskatar dashi yace "base kace komai ba Imran, nagode gara da ka nuna min irin riƙon da za kai Mata nagode sosai"
"Abba ba haka bane, walla...
"Shuy up! Meye ba hakan ba, da ka kasheta fa? wane irin duka ne wannan, waye ma yace kasa hannu ka daketa? Ka kyauta ba abunda zance maka se godiya"
Abba yace a kawowa Amira Hijjabi, ya tafi da ita sashinsa, aka kawo hijjabi ta saka, amma still jikinta rawa yake, Anty Fa'iza zata bisu yace bakomai base ta bisu ba.
Abba da kansa ya ɗakko bargo ya lulluɓeta, ya nemi guri ya zauna yana tunani, Imran ya rasa abunda zeyi gaba ɗaya Aurensa yazo masa a baibai.
Ammi ce ta shiga sashin Abba tana faɗa "wallahi Abba ka bani mamaki, ko takan Minal baka bi ba bayan itama ya daketa, se wani abu kake akan Yarinyar nan, zan sake jadadda maka wallahi ba zata zauna min a gida ba, ka basu kuɗin mota gobe su tafi, ta kama min 'ya ta daka kuma shima yazo ya haɗasu ya daka, amma kai ta ita kawai kake baka ta 'yarka.
Abba bece mata uffan ba, ya kalli inda Amira take, jikinta na cigaba da rawa se surutai take, yaje inda take kwance ya ɗan ɗaga bargon ya dafa goshinta, jikinta ya ɗau zafi sosai.
Ran Abba ya sake ɓaci sosai, ya ɗau wayarsa ya kira Imran, ba'a daɗe ba sega Imran yazo jiki na rawa.
Abba yace "kaga sakamako abunda kayi ko?"
Imran ya sunkunyar da kai ƙasa.
"Gidan Alhaji Hashim zamu tafi Yanzu, ka kaita mota gani nan fitowa"
Amira ta tashi tana jiri, tabi bayan Imran, ita dai bata san ma yadda akayi taje mota ba se ganinta tai a Mota, Ammi tana ta masifa tana tambayar meye ba'asin zuwa gidan Alhaji Hashim a daren nan, amma Abba ya shareta ya fice.
Suna tafe Abba na yiwa Imran faɗa
"Imran idan bazaka iyayimin alfarmar da na nema a gurinka ba, tun wuri ka gayamin in nemi wani yayi min"
"A'a Abba zan iya"
"Aini na tsorata da lamarinka ne Imran, ka bani mamaki sosai"
"Abba dan Allah kayi haƙuri, yarinyace sam bata da kunya, dambe fa sukayi ita da Minal a gaban mutane"
"Du da haka, mata lallaɓasu akeyi, karka kuskura ka saba musu da duka mutuncinka ze zube a idonsu, mussaman duk irin wannan na rashin imani, duk randa ka kuskura ka daki wata a cikinsu duk hukuncin da nayi maka kai ka janyo shi"
"Insha Allah bazan sake ba"
Amarya Ihsan kuwa tunda suka koma gida take Kuka, aka rasa gane kanta sam, wani mugun kishi da haushin Imran suka mamayeta, ga tsanar Amira da take ji a ranta.
Yayan Baban Amira ne yazo, yace ai masa magana da Maman Ihsan.
"Kaine a tafe da daddare haka? Ina fatan lafiya ƙalau?"
Yace "eh lafiya ƙalau Alhamdilillah, ya hidima?"
"Hidima Alhamdilillah, muna ta fama daga gobe in Allah ya kaimu dai an gama kowa ya huta"
"Hakane, dama wata maganace ke tafe dani, kin san komai muƙaddari ne daga Allah, dan haka kafin in gayamiki koma meye, ina son kuyi tawakkali daga ke har Ihsan"
"Lafiya kuwa? Auren suka fasa kokuwa?"
"A'a ba Aure suka fasa ba, kamar yadda suka canza muku gidan da za'ayi jere hakan ya faru ne sakamakon wani hukunci da mahaifinsa shi angon ya yanke, ze aurawa ɗansa mata biyu ne lokaci ɗaya, bayan Ihsan akwai wata da za'a ɗaura Aurenta da Imran gobe in Allah ya kaimu, su biyu kenan !!!
Domin Sharhi gyara Ko shawara
Ayshercool
07073065680
[1/19, 2:13 PM] Ayshercool: 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥
WUTA A MASAƘA
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P. W. A
*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA)
*BAƘIN TABO (Labarin gasa)
*AƘIDATA (Paid Book)
* WUTA A MASAƘA
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in
❌❌❌
Ƙirƙirarren labari ne, ban yadda ayi amfani da kowane sashi na labarin ba ba tare da izinina ba.
21_22
"Nifa ban fahimci abinda kake nufi ba, kamar yaya mata biyu za'a aura masa?"
"Da hausa fa nayi miki bayani, ba da Yarabanci ba, Mijin Ihsan da za'a ɗaura musu Aure gobe in Allah ya kaimu, su biyu za'a aura masa, ita da abokiyar zamanta"
A fusace Maman Ihsan tace "aikuwa ba zata saɓu ba sam, ni za'a ciwa mutunci a munafurta, daga ina wannan banzar maganar ta fito? Kuma ba'a gayamin tuntuni ba se ana i gobe za'a ɗaura Aure, dan cin fuska da cin zarafi"
"Kinga ki dakata mun dan Allah, gudun irin wannan matsalar da rashin tawwakalin yasa ban sanar muku ba, tun kafin a fara bikin nan, suka zo suka sanarmin ni nace kar su gaya muku, in ba haka ba bazaku bari ayi bikin nan ta daɗin rai ba, kuma nine matsayin uba ga Ihsan, Auren nan bau fashi za'ayi shi gobe insha Allah, kin sani sarai bana Magana biyu, idan kinso kije ki rarrasheta ki kwantar mata da hankali, idan kin so kije ki zigata ki tayar mata da hankali kisa idan taje gidan miji ta kaso Auren, ke zaki zauna da ƙaramar bazawara a gida, idan kuma kina ganin duk wannan dandazon jama'ar da kika tara, zasu watsene a fasa Auren, ke kika jiyo se yadda kuka zaɓa"
Yana gama maganar ya tashi ya fice.
"Wallahi ba zata saɓu ba wai bindiga a ruwa, dan bala'i Auren fari yarinyar ba zata zauna ta huta taci amarcinta ba, za'a haɗata da wata a auren fari, Lallai Jamila ta munafurceni, dani take zancen".
Ta ɗakko wayarta ta kira layin Ammi, sedai Ammi bata ɗaga ba, saboda tana can tana rarrashin Minal, saboda dukan da ta sha, gashi a ƙule take jiran su Abba take su dawo ayi wadda za'ayi akan Amira, Dan duk abunda za'ayi se Amira ta bar gidan nan a gobe.
Maman Ilham ta dinga surfa masifa, tace sedai a fasa Auren baza'a ci mata mutunci ba, hankalin mutane'yan biki ya fara dawowa kanta, aka fara ƙoƙarin jin ba'asin abunda ya sata masifa haka a wannan daren, bayan dawowa daga dinner.
Yayarta ce taja hannunta suka uwar ɗaki, ta rufe ƙofa tace "Ke Murja, ki rufawa kanki Asiri kamar yadda Allah ya rufa miki, karki yadda a fasa Auren nan, ki taushi yarinyar nan taje ta tsuguna a ɗakinta tunda Yaron nan yana sonta tana sonshi nasan ba'ayi muku adalci ba, da ba'a gayamuku da wuri ba, amma bari kiji bar ganin Ihsan na da wannan kyan, samun miji irin wanda ta samu yana da wuya a wannan zamanin, dan haka kuyi haƙuri, taje ta zauna sedai kawai ki tashi tsaye ki gyara 'yarki ta riƙe mijinta, ki tabattar ta zama Mowar gida, idan ba haka ba kin san yadda muke cikin 'yan Uba da maƙiya, duk dangin nan namu gashi wasunmu na da kuɗin amma babu yarinyar da ta samu miji kamar na Amira, gashi ɗan shahararren mutum, ga kuɗi da kyau suna dashi, dama Auren nan na Ibsan a wuyan wasu yake, idan kika sa aka fasa Auren nan wallahi a cikin maƙiya za'a samu wanda ze lallaɓa ya bashi tashi 'yar ya haɗa biyun, Mussaman ke da Akuyarki tayi kuka a dangi gara ki rufawa kanki Asiri"
"Amma Yaya Atine an min adalci kenan? 'yar guda ɗaya a haɗata da kishiya, kuma a kasa gayamin se ana gobe ɗaurin Aure?".
"Kiyi haƙuri, kedai ki samu tayi aure ta tashi daga gaban ki, wallahi aka fasa Auren nan sekin
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 31