Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ba ta samu dama ba. Cikin yaqe ta buɗe baki ta ce, "To Allah ya sanya alkhairi," Yah Maheer ne ya yi mata addu'a da fatan alkhairi Baban Ameerah kuwa tunda muka doshi wajen ya kafe mu da kallo, Yah Maheer ne ya matsa gefe ya na bi na da kallo, wayar shi ya zaro a aljihu ya yi rubutu ya Kalle ni muka haɗa ido ya nuna min na duba waya ta, na ji shigar saqo a lokacin amma se na dauka MTN ne ban duba ba, ina duba wa se na ga saqon shi kamar haka. 'Gaba daya matan wajen nan kin fi su kyau wallahi ba wai ina yabon kai na na iya zaben mata ba, na fad'i iyakar gaskiya ta ne' Murmushi ne ya subuce min wanda ya taso tun daga qasan rai na har labbana, kallo na Maman Ameerah ta yi suka shige mota ta na faɗin, "Sarakan soyayya se a yi ta fama" Ban ce mata komai ba na daga masu hannu suka fice daga gidan, se na ji kamar an sauke min wani qaton nauyi da ke kai na, nan muka je waje na ga motar Hafsat na yi mata addu'a sosai Baban Ameerah da Yah Maheer ma haka, nan ta sa na shiga muka ɗan zazzaga ta dawo da ni gida, suka min sallama suka tafi suka bar ni da kewar su. Da magariba bayan mun idar da sallah mun yi azkar Suwaidatu ta bani labarin da ya bani dariya sosai........ Mu tara zuwa gobe Inshaa Allah ko anjima iya comment iya typing less comments less typing....and please ban cika maraba da comment d'in PC ba a yi comment a bainar nasi inda na yi posting wataqila wata ma na da abin faɗa se a qaru da juna baki daya. *Mutanen kwarai masu albarka in an karanta a dannan min star hilis sannan a yi sharing saboda wanda basu karanta ba su antayo ayi da su..ina maraba da comments ɗin ku, amma a yi hakuri banda zafafawa domin wannan labari na gaskiya ne kamar yanda na sanar da ku tun farko...Thank you my fiful* 💅 MAHREEN 💅 WRITTEN BY HAERMEEBRAERH PAGE 28: "Ki na nufin dai ba su gan ki a wajen ba ko kuma sun gan ki kawai suka ci gaba da hirar su" na faɗa cikin dariya. "Oho musu, amma da alama ba su kula da ni ba ma kwata-kwata,sun gigice da ganin su Aunty Hafsah Maman Najeebu sai tambaya ta ke wai, Wagga kuma daga ina? Ke suhwa ta daura wallah (ke super ta daura wallahi) ke ga kunnen ta, ke ji hannun ta zobbunan gwal sun ka saka, d'iyan wana ? ('ya'yan wane ne? Ke baki ga yanda suka gigice da tambaya ba saboda kawai su na son su ji su waye suka zo wajen ki," "To da so suke na mutu da kaɗaici ko? Su sun guje ni se na zauna ban da me kula ni a birnin Kebbi ko? To ai Allah ba haka yake lamarin shi ba, yanda suke so ba za su samu ba har abada," Hira muka ci gaba da yi da Suwaidatu daga qarshe na ke ba wa Hafsat labarin abinda ya faru zuwan su ta waya, mu kai ta dariya. Hafsat na daga mutanen da suka qaunace ni domin Allah ba dan ina da wani abu ba ko su na tunanin zan ba su wani abu, hatta da mahaifiyar ta da na je gaishe ta ta nuna min qauna kamar ta jima da sani na dama haka ta tarbe ni, mutane ne su masu karamci da mutunta ɗan Adam. (Allah ya gafarta wa mahaifin ku) Wata iriyar rayuwa muka dasa me 'yanci a gidan, ba takura ba sa ido ba kuma tsoron wasu za su gani su ji haushin mu, mune wasan guje-guje, mune 'yar gala-gala, mu ne carafke, duk wani wasa da zai sa mu nishad'i yin shi mu ke da iyalai na ba tare da tunanin wani zai gani ya ji haushi ba. Mutanen unguwa kuwa na sake tsame kai na daga cikin su, tunda abinda aka sanar da su akai na ba yanda zan na goge shi a zuciyar su tunda ban san mene ba su kuma ba su mu'amalance ni ba balle su san wacece ni, Se na kyale su akan kowa na da ra'ayin yarda da abinda ya ji ko kuma ya yi bincike dan sanin gaskiya, dan haka sai na maida rayuwa ta daga gida, sai gidan Maman Ameenah dattijuwar kirki wadda ta ɗauke ni a matsayin 'yar ta ita da Baban Ameenah,ganin haka se ya sa nima na riqe su a matsayin iyaye na, har nake ba wa Mama da Baba labarin su, su kuma su yi ta yi musu addu'ar alkhairi, nakan ce wa Mama yanda ki ke kula da yaran wasu a garin da ba su da iyaye ba su da dangi shi ne nima Allah ya haɗa ni da mutanen kirki. Ana haka muka samu labarin za mu yi sabbin 'yan haya, a cikin watan da muke ciki suka fara dawo da kayan su bangaren Maman Ameerah wanda ya ci wani irin dattin da kamar debo bola akai aka zuba,dan haka ba qaramin gyara wajen ya sha ba kan ya dawo hayyacin sa, duk wanda ya gani ba zai gane cewa wannan shine gidan da aka ci dafdala a cikin shi ba. Waje nan da nan ya ɗauki haske da kyalli kamar za a saka sabuwar amarya, a da duk mun gwada buga qusa a jikin ginin se ta qi zama saboda qarfin ginin gidan, komai qarfin qusa in aka Saka ta a ginin se ta yi wuta ta fice, dan haka da na ga an sa wa sabuwar maqociyar mu labule se na sa hope din nima zata bugu ne in aka sa naci dan zama ba labulen ba dad'i musamman yanda aka fara iskar damuna se mutum ya ji kamar a sahara yake tsabar yashin da ke cika waje. Da misalin 7;40pm ina tsaye a saman kujera ta ina ta qoqarin cigaba da gwada sanya labule na ko zan samu ya shiga muka ji qarar motoci na tsayawa a bakin gate ɗin gidan, shiru mu ka yi dan mu tabbatar da ko nan ɗin ne duba da cewa dare ya yi bana tsammanin wasu baqi, mun tabbatar da nan gidan ne a lokacin da aka buɗe qaramar qofar gate ɗin aka shiga, hayaniyar mutane muka ji sosai kamar ana biki, hijabi na na dauka na sanya saman kayan bacci na masu guntun wando,na sauka daga saman kujerar da na haye ina gwada buga qusa, sannan na leqa waje, hasken fitilun waya ne suke ta walwali a cikin duhun daren,nima ina tsaye ina haska tawa fitilar wayar,sallama mu ka yi wa juna da mutanen nan sannan na gane sabuwar maqociya ta ce ta ta zo tare wa, dangin ta suka rako ta kamar sabuwar amarya, nan take se abun ya burge ni na qara washe baki ina masu sannu da zuwa, godiya suka min sannan suka buɗe sashen su suka shige nima na koma gida, buga qusar da ban ci gaba ba kenan har yah Maheer ya dawo daga masallaci muka ci abinci mu ka yi shirin kwanciya. Mu na nan kwance mu na jiyo hirar su sama sama, tun mu na jiyo hirar su da shewar su har muka dena ji alamun kowa ya samu inda ya dora haqarqarin shi kenan, bamu jima da kwanciya ba sosai aka kawo wuta alamu ne na sha biyu na dare ya yi kenan hamdala na yi na sake bajewa a katifar da muke bazawa a parlour dan Shan iska. Washegari da safe qamshin soye soye ne ya cika min hanci na farka daga nannauyan baccin da na ke, waya ta na ja ina murza ido na, da sauri na tashi ina addu'ar tashi daga bacci, gani na yi gari ya waye sosai qarfe wajen tara na safe, da alama Suwaidatu ce ta gama soya dankalin turawa da kwai ta dafa ruwan tea sai qaton bread da ta dora a babban faranti ta ajiye mana a kitchen ɗin tunda har a wannan lokacin ina kwance a parlour ne inda muke bajewa mu ci abincin daga nan ta wuce makaranta, godiya na yi ga Allah da na koya mata girki da wuri ba dan haka ba yanda na makara ba su tashen ba wa zai mata? Tashi na yi na daga katifar da kyar ina jin bani da wani qarfi a jiki na, daga baya na naji an kama katifar tare da dukan kafadata sannan aka mammatsa min ita, cikin jin daɗin tausar da ya ke min nake bin dukkan wani motsi da hannun sa ke yi a kafad'u na, ina sauke ajiyar zuciya kamar wadda ta yi wani qaton aiki ake mata tausa, ido muka haɗa da Yah Maheer da ya fito daga dakin Suwaidatu bayan ya ajiye kayan shi da ya cire ya saka a wajen wanki,murmushi ya min ni kuma na kyabe baki irin na shagwababbun nan na ce, "Shine baku tashe ni ba ko? Yunwa ce ta tashe ni ina bacci na ji qamshi shine na miqe" "Kin san dai bana so ki na bacci ana tashin ki, tunda ba koda yaushe ki ke samun baccin ba, baki ga har tokare qofar na yi ba dan kar ta dinga qara ta dame ki? Maza ki je ki wanke baki ki zo mu ci abinci yunwa nake ji" "To gani nan zuwa, ni fa ina idar da sallah na san dai na yi istighfari uku daga nan ban san me na sake cewa ba se gani na na yi anan" Dariya ya yi ya shige da katifar ba tare da ya amsa ni ba, bathroom na shige na watsa ruwa na wanke baki na, hayaniyar da na jiyo ana hira ne ya sa na tuna cewar ba fa mu kaɗai bane ashe a gidan, murmushi na yi a raina ina jin inshaa Allahu wannan baiwar Allah daban take za mu zauna lafiya da ita. Ina fitowa na shige d'aki na sanya kaya masu dama dama a cikin kaya na saboda akwai mutane bana son zama ba wadatattun kaya a jiki na. Abinci muka ci muka qoshi sannan na ce wa Yah Maheer bari na leqa maqotan mu mu gaisa, ya ce ya kamata saboda sun zo ya ce musu ina bacci. Koma wa na yi na zauna ina fuskantar shi da kyau, dan ina so maganganu na su shiga kunnen shi da zuciyar shi, cikin marairaice fuska na ce, "Dan Allah Yah Maheer ina so na roqi wata alfarma a wajen ka" Kallo na ya yi shima da kyau dan ba wa magana ta mahimmanci. "Dan Allah ina so ka rage yawan kulawar da ka ke min gaban mutane, ka ga ina kyautata zaton ita ta jawo mutane ke jin haushi na, ka na gani ko a can gida Bauchi qiri qiri za ka ji ana nuna ba me dorewa bace in dai namiji ne in dena sake jiki, ko a ce na mallake ka da sauran su, dan Allah mu na yin komai baya baya" Tashi ya yi ya shige d'aki ya bar min wajen dan tunda ya ji inda magana ta ta dosa ya ja guntun tsaki ya maida hankalin shi wajen shanye tea din da ya rage a mug din shi, galala na sake baki na bi bayan shi da kallo, wato wannan ba abu bane me mahimmanci a wajen shi ko? Shine har ina masa magana ze min tsaki ya shige d'aki to da kyau, na tsani tsaki a rayuwa nan da nan kuwa na ji rai na ya ɓaci, da qarfi na furta. "Allah baka sa'a ka ci gaba ina ruwa na ni" Shima da qarfi na jiyo muryar shi ya na ban amsa har da buɗe qofar d'akin wato na ji shi da kyau ya ce, "Da ruwan ki mana, ke kuwa ki ke da ruwa yarinya, in be dame ki ba meye na magana?" Murgud'a masa baki na yi na yi fari da ido Ina wawwatsa 'yar rashin kunya ta yanda na ga dama, murmushi kawai ya yi ya rufe qofar ya barni tsaye ina b'ab'atu. Tattare wajen na yi na gyara sannan na leqa maqota na masu yawan fara'a muka gaisa, anan na gane mutanen Sokoto ne amma su na zaune anan Kebbi gidan da suke ciki ne ambaliyar ruwa ta ci shine suka dawo nan da zama, fatan alkhairi na mana sannan na fito ina santin yanda suka gyara wajen kamar d'akin amarya ga shi itama matar ta sha gayu tsaf da ita,ba fara bace kuma ba za a ce mata baqa qirin ba, ta sha qunshi da kitson ta, ta sanya doguwar riga armless, ire iren shiga ta, nan take na ji son matar a raina na ce inshaa Allahu wannan za mu je da ita domin da alama duk wani zaɓi na shine zaɓin ta, tin daga kan kujeru da jeren ta na gane mu na da ra'ayi ɗaya. Baqin basu tafi ba sai yamma lisss suka bar gidan daga baya me gidan ya zo ina daga bakin kofa mun shimfida carpet ya shiga gidan da sallama tun kallon farko da mukai wa juna ba mu sake kallon juna ba ya shige sashen shi ni kuma muka sake matsawa baya da shimfid'ar mu inda ba za a na gano mu ba sosai. Haka muka fara sabuwar rayuwa da sabbin maqota na, a hankali shaquwa na shiga tsakani na da Maman Abdurraheem, ta ɗauke ni kamar qaramar qanwar ta, ni kuma ina mata kallon Addah Ummuna saboda sa'anni suke, duk abinda ban iya ba za ta koya min, haka duk abinda ta gani a waje na bata iya ba zata tambaya na koya mata bata da girman kai kwata kwata. Labulaye na da suka qi kafuwa kuwa da kan ta ta koya min yanda zan taka fridge na soka a jikin silin ɗin parlour da d'aki na, kasa sawa na yi ta kuwa karba ta haye se gashi ta saka da qusa da tabarya ta qarama da yake doguwa ce ita. Sharar tsakar gidan nan haka za ta fito ta fara watarana kafin na zo saɓanin da da sai dai na yi ta shara ni kaɗai in ba Allah ne ya taimake ni 'yan mutuncin na nan ba a taya ni, ga gidan da shegen girma, ga bishiyoyin darbejiya/maina manya gaba da backyard ɗin mu Baban Ameerah kan su tashi ya shuka zogale masu yawa kuma duk sun kama, a jikin bishiyoyin muka daura igigoyin shanyar wankin mu. Watarana ta yi Shara ita kaɗai wata rana mu yi tare, watarana na yi ni kaɗai, ana haka saboda zaman da akai a baya se Yah Maheer ya yi qoqarin saka Langa Langa aka raba tsakanin gidajen indan muna son had'uwa se dai mu bi ta backyard ko mu zagaya Langa langar. Hatta da kitso Saude wato Maman Abdurraheem ita ke min watarana,bana manta wa akwai sanda ta ce na zo ta min kitso, har cikin rai na bana son kitso ni sosai, gashi na samu gashi na ya fara dawowa saboda qurajen zafi da suka tafi sakamakon tsayawar damina da saukar sanyi da aka fara, tun muna kitso a zaune se da ta kai na koma na kwanta saboda qanana ta d'ebo, qarshe dai dakin Abdurraheem muka koma, ina kwance a saman gadon ta tsabar yanda ta ke gatanta ni ita kuma ta na min kitso, mu na tsaka da hira na ji qauri na tashi a gidan, saboda ni Allah ya min baiwar yawan jin qamshi ko wari, nan da nan na juya na ce mata, "Qauri nake ji mene ne ke qonewa?" Yanda ta nuna ba komai se ya bani mamaki, dan ban ga alamar tsoro a tattare da ita ba, cikin nuna halin ko in kula ta ce, "Ba fa komai bane kettle ce na jona ruwan zafi ita ce take wannan qaurin" "Tabbb! To ai da kashewa ki kai irin haka se ta qone ai" "Batta kawai haka take yi" Shiru na yi ban sake magana ba, ta ci gaba da yi min kitso na, ko da muka gama se na yi mata godiya na miqe zan tafi ta ce, "Saura duk wannan wahalar da ki ka sha kwana uku ko huɗu ki tsefe shi" Dariya na yi sosai, dan kuwa ta san hali na tabbas, ni kitso ya jima akai na ya yi kwana biyar ko shida ya na wahala ya cika bakwai,amma ina iya watanni sama da biyar se dai na yi ta gyarawa ko na yi guda biyu akai na. A kwana a tashi ni da Maman Abdurraheem kullum sai samun shaquwa muke duk da qoqarin ja baya da nake yi saboda ina tsoron kar na zarme a zo a samu matsala daga baya, nan take ta nuna min in saki jiki na ita ba ta da wata matsalar da zan kame kai na daga wajen ta, a haka kuwa na samu na saki jikin nawa, yaron ta ɗaya Abdurraheem yaro me qiba ga kyan jiki Masha Allah,yaro ne mai shiga rai ya na qaunar mu ni da Yah Maheer,in ya baro sashen su ya zo wajen mu sai ya jima kafin ya koma. Saudee mace ce me tsananin biyayya ga miji duk abinda yake so ta na so, duk abinda baya so ta bar shi kenan har abada,ina kula sosai da yanda take tafi da gidan ta, ni ina ganin ina koya daga gare ta ita ta na ganin ta na koya daga gare ni. Ana haka muka kusan shekara tafiya gida ta kama mu, shirye-shirye muka fara ba kama hannun yaro, ranar tafiya muka yi sallama da maqota muka tafi gida, a Kano muka sauka, na ji dad'i sosai dan ganin iyaye na da 'yan uwa na da nake jimawa ban gani ba,a wannan zuwan ne Yayana Abdulhaleem ya bani wata wayar shi me kyau saboda nawa na samun matsala, godiya na dinga yi masa ina kumawa saboda ko ba komai ni ma na faso gari, dan kuwa wayar babbar waya ce kuma me kyau da ban sha'awa a ido. Baba kuwa ba shi da burin da ya wuce na ya ga na rage qiba dan a cewar shi yawan qiba ma zai iya zama sanadin rashin haihuwa ta, rashin haihuwa ta na damun shi kwarai, shi ne dalilin da ya sa duk muka haɗu se ya min nasiha da kwantar da hankali saboda kar na shiga damuwa akan rashin haihuwar da ban ba, wata ranar ma ni ke kwantar masa da hankali na nuna masa babu komai ni na fi son zaɓin Allah Akan son zuciya ta, da haka yake hakura da yawan nanata nasihar shi a gare ni da jan ayoyin qur'ani dan kwantar min da hankali. Washegari mu ka tafi Bauchin Yakubu muka yada zango gidan Hussaini, mutane da yawa a gidan saboda mu dangin mu Masha Allah akwai yawa,bayan mun kwana biyu muka tafi liman Katagum mu ka yi hutun mu muka d'akko hanya muka sake komawa Bauchi, tun zuwan mu na fahimci sauya sauyen halaye daga wajen matar Hussain amma se na yi kamar ban gani ba, na bata uziri na ce dan Adam tara yake be cika goma ba, dole na qara hakuri da ita ni da zan zo na tafi ma se a shekara ba a ganni ba? A haka na hakura da duk wani abu da na gani ko na ji mu ka koma Kano, daga Kano mu ka dawo kebbi. Mun samu tarba me kyau daga wajen Maman Abdurraheem, daga nan kuma na fuskanci ita da Hauwa'u suna mutunci sama sama har wata rana ta ce mu je gidan bana son zuwa amma haka na daure na je aka gaisa,ni Kuma ba wani mugun hali ne ya sa bana son hulɗa da ita ba se dan saboda abubuwan da suka faru se na ke janye jiki na da Hauwa'un. Gidan Maman Ameenah kuwa da na ke son zuwa sosai ita kuma ba sosai ta ke son zuwa ba, a nan ne ra'ayin mu ya sha banban. Watarana mu na zaune mu ka ji qarar mota, ba mu motsa ba dan koma waye ai zai shigo ne, dan haka mu na nan zaune na ga wata mace doguwa fara me aji ta shigo gidan ta na taku ɗaya ɗaya saboda gayu, ta sanya atampa me kyau fara me ratsin ja wadda duk da ban san kuɗin kaya masu tsada ba na tabbata me tsada ce, ta ɗora mayafi Shara Shara a saman kafad'ar ta shima ja ,hannun ta ɗaya riqe da makullin mota dayan Kuma jaka ce me kyau da tsada qafar ta sanye da dogon takalmi mai tsinin gaske kalar jakar hannun ta wanda daga gani tare aka yi su, direct wajen mu ta nufa ta na murmushi........... *Mutanen kwarai masu albarka ya kuke gani in na raba wannan novel gida biyuuu kashi na biyun ya koma paid book? Ina son jin ra'ayin ku domin ko na siyar ko ban siyar ba fata na kowa ya amfana da abinda na rubuta na alkhairi abinda yake ba me kyau ba kuma kowa ya guje masa....sai na ji ra'ayoyin ku mutanen kwarai....dan Mama ta riga ku bada shawara ina dai so na ji naku ra'ayin tukunna😂* 💅 MAHREEN 💅 WRITTEN BY HAERMEEBRAERH PAGE 29: Gaba ɗaya hankali na ya tafi wajen kallon ajin da matar ke tattare da shi wanda ya sanya idanu na cika da ganin kyan ta duk da cewa ba wata kyakkyawa bace sosai, yanayin shigar ta da ajin ta ne ya qara fito da kyan ta, gaishe ta na yi sannan na maida hankali na gefe guda ina tunanin yanda Maman Abdurraheem ta ke ta murnar ganin matar da alama ta na da mahimmanci a wajen ta, bangaren Maman Abdurraheem suka shige su na ta murnar ganin juna, ni kuma se na tashi na tattara kaya na na shige nawa bangaren na yi alwala na yi sallah sannan na hau girki, ina yi ina karatun wani novel da na aro wajen Aunty Sumayyah, (Maman Amirah) ban gama girki na ba Maman Abdurraheem ta shigo muka zauna mu na hira, anan take sanar da ni qawar ta ce ta zo nuna mata motar da mijin ta ya sai mata kwanan nan,hirar maganin mata ta hau yi min har kalar wanda qawar ta ta ke amfani da shi,mamaki duk ya kama ni, daga Shan maganin mata se a maka kyautar mota? Ko dai dama can mijin ya yi niyya ne? Daga sama na jiyo muryar Maman Abdurraheem ta na cewa, "Na taya ta murna, amma mu da mazan mu ba su da halin siyan mota ko albarka aka saka mana ai mun gode" Dariya mu ka yi a tare, ina ci gaba da jinjina lamarin. "Ke bari ma zan baki wani magani ki gwada ya na da kyau, sannan akwai lalle da zan baki ki qunsa a qafar ki, da wani ruwa, ke in ki ka sha ruwan nan ko? Hummmm ba a cewa komai, ki bari kawai zan baki su ki gwada mugun tsada ne da su in ya qare se kin nema" "To ni ina na ga kuɗin siyan maganin mata musamman me tsada? Ai kedai kawai ki bani domin Allah na sha a samin albarkar nima " Dariya mu ka sake yi, cikin zuciya ta ina addu'a kar Allah ya bata ikon bani maganin nan, musamman lallen. 'wanne irin lalle ne na mallaka ko farin jini? Me aka saka a ciki? Sannan menene a cikin ruwan da zan sha ina aka samo shi? Ba zan iya sha ba gaskiya' A fili kuwa ina ta biye mata mu na magana, nan take na tuna wani maganin mata da karambani na ya kai ni na sha shi da jimawa, awanni kaɗan da sha Yah Maheer ya dawo, sai da komai ya kankama na hau zubar da jini ba qaqqautawa ba tsayawa se da na yi kwanaki biyar sannan ya tsaya, na zaci period ne na sake gwada sha, jini ya sake balle min har da guda guda, abun tun ya na ban mamaki ya dawo bani tsoro,duk sanda na sha maganin mata za a yi abu d'ayan uku ne. Ko na dinga zubar da jini har se aikin maganin ya qare a jiki na. Ko na dinga qunci da yawan neman faɗa da masifa da bala'i Dan a Kula ni na yi fushi na qi bada haɗin kai. Ko kuma qatoton qurji ya fito min guda ɗaya tall raina kama ka ga gayya wanda motsin arziqi ba zan iya

Chapter 23 of 30