Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
haƙuri Baba, in Allah ya yarda ba zan ƙara aikata kuskuren ba, Kuma zan yi yadda ka ce amma zan so ka sa mata abin wuyan da kanka, zan sa Yara su kai ka gidanmu da ga nan sai ka gaisa da Mamarmu." Baban Halima ya ce "To Ɗan nan ba zan ce a'a ba." Miƙewa Shahbeer ya yi ya nufi hanyar fita ya na sharar ƙwallah, jiki a sanyaye su ka mara masa baya, har su ka isa gida in banda sharar ƙwalla ba abin da su ke yi, dukansu ba wanda ba ya kuka. Tin da Mommy ta gansu cikin wannan yanayin jikinta ya yi sanyi, cikin sauri ta fara tambayar Lafiyarsu. Cikin muryar Kuka Shahbeer ya ce "Mommy yanzu lokacin Rabuwata da Halima ya yi." gabanta ne y yanke ya faɗi cikin zaro ido ta ce "Me??? Shahbeer ina nutsuwarka ta tafi??, me baiwar Allahn nan ta yi maka da zaka rabata da mu?" girgiza kai ya yi ya ce "A'a Mama zan maida ita gurin Mahaifinta ne, muna tare da shi tin da daɗewa sai yanzu na gaya masa gaskiya." jaɓar ta zauna akan kujera ta shiga jero salati, "Yanzu Shahbeer sai da mu ka shaƙu da yarinyar nan sannan zamu rabu?, me yasa ba ka mayar da ita tin farko ba sai da ta gama shiga ran kowannenmu??, ban ji daɗin haka ba Shahbeer." ta ƙarasa maganar tare da fashewa da kuka. durƙusawa ya yi a gabanta ya riƙo hannunta cikin sigar rarrashi ya ce "Don Allah ki yi haƙuri Mamma ba yadda na iya ne dole hakan itace Mafita, da zarar Babanta ya zo za su tafi tare, ki dena kuka Umma." Ta ce "Yanzu shi ma Shahzad rabamu da shi za ka yi??" waro ido ya yi akanta cike da mamakin da kuma tambayar yaushe ta Ƙaunaci Shahzad ɗin har haka da ba ta son rabuwarsu?, girgiza kai ya yi kafin ya ce "Ba zan iya rabuwa da abu biyu masu muhimmanci a gareni ba kuma lolaci ɗaya, zan riƙe Ɗana shi ma ya ɗauki tashi." Mommy ta ce "To Allah ya sa hakan shi ne mafi Alkairi a garemu." 04:00Pm Abeer da Baban Halima ne su ka yi sallama a Falon su Shahbeer, Inna da ke tsaye ta ce "Ku shigo sannunku da zuwa." Bayan sun ƙaraso sun zauna Inna ta ce "Ina wuninmu?" Baban Halima ya amsa da "Lafiya Lau Baiwar Allah." Shahbeer da ya ci kuka ya ƙoshi ya na gefe sai lullumshe idanunsa ya ke da ƙyar da ƙyar dan kuwa wani mugun Zugi su ke yi masa, cikin disashshiyar Murya ya ce "Sannu Baba; Inna ki ce Mommy ta zo su gaisa Malika kuma ta kawo mini Shahzad." Inna ta ce "To" sannan ta fice. bayan wani ɗan lokaci su ka shigo tare dukansu har da Halima, kai tsaye kusa da Shahbeer ta nufa ta zauna sai rarraba ido ta ke yi ta na kallonsu Musamman Baban nata da Zuciyarta ta ke raya mata abubuwa da yawa akanshi. Bayan sun gama gaisawa Shahbeer ya miƙawa Baban Halima Zobukan sannan ya kama hannunta ya kaita gabansa ya durƙusar da ita, ido kawai ta ke binsu da shi gaba ɗaya ta kasa fahimtar me su ke shirin yi, Baban Halima ya riƙo hannunta ya na ɗan murzawa, ya yi murmushi me ciwo kafin ya ce "Tabbbas Ƴata ce; Sannu Halimatu." kallon Shahbeer ta yi gami da cewa "Waye??" ya ɗan goge ƴar ƙwallar da ta ke neman zubowa kan kumatunsa, sai da ya numfasa sannan ya ce "Baba ne." ta maida hankalinta kan Baban Halima ta yi masa ƙuri da ido. Abin wuyan nata wanda ya koma na Zaren Gold da Shahbeer ya saka wa Zobukan guda biyu, ya ɗaura mata bakinsa ɗauke da Addu'o'i. wani dogon numfashi ta ja tare da shaƙuwa sai kuma ta fara tari, a gigice ta miƙe ta na baya-baya har sai da ta kai bango sannan ta zube a sume. Baban Halima ya ce, "Ku barta na ɗan lokaci sannan a yayyafa mata ruwa." Kamar yadda ya ce hakan aka yi, bayan ɗan lokaci aka yayyafa mata ruwa, ta farka a firgice ta na kiran Babaaa!!! Babaaaa!!!!. Baban Halima ya ce "Alhamdulillahi" Zumbur ta tashi lokacin da ta yi tozali da Idanun Shahbeer, ta ƙwallara ƙara kafin ta fara kuka ta na cewa "Ka ƙyaleni Ramadan, Wallahi ba zan yafe maka ba Mugu azzalumi, kuma sai Allah ya yi mini sakaiya." Baban Halima ya riƙo ta ya na cewa "Kwantar da hankalinki Ƴata ina kusa da ke, faɗa mini meke faruwa?? waye Ramadan???" Da yatsa ta nuna masa Shahbeer. ya nuna ƙirjinsa gami da cewa "Ni????" ganin Su Shahmeer ya sa ta ƙara sakin wata ƙarar ta na cewa "Baba su na da yawa don Allah ka zo mu gudu." ganin ba shi da niyar guduwar ya sa ta fallatsa da gudu don neman tsira. Inna ta ce "Bawan Allah anya kuwa Ƴar taka ta dawo daidai? ko dai wata sabuwar haukacewar ta yi??, amma mu ƴaƴanmu Biyu Aminullahi, Biyu Mukhtar haka sunayensu su ke. _________ _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu 'batawa kai lokaci🙏🏻_ _*infection*_ _Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye! infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu'amula mussaman ga ma'aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za'a dace_ _*SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI*_ _07084653262_ *INDO* [1/1, 10:06 AM] INDO CE: *WATA HANYA* 30 Ayeesha Abdulkareem *(Indo ce..)* ELEGANT ONLINE WRITERS. 1/1/2023 Baban Halima ya ce "Haka ne, nima kaina bansan akan wa ta ke magana ba. Cike da dauriya Shahbeer ya ce "Baba, Za ka koma gida tare da Abeer da Halima, amma don Allah a kula da ita don gudun faruwar wani abin." Baban Halima ya ce "To Ɗannan ina Abeer ɗin ya ke ?" "Ya Fita na ce ya rarrasheta ne ya sa ta a Mota don nasan cikinmu ba za ta iya fahimtar kowa ba. Baban Halima ya ce "Haka ne, To kasan ni fitata sai da Ɗan Jagora tinda ban san kan gidan ba." Hannunsa Shahbeer ya riƙe su ka fara tafiya, a sannu a sannu har su ka isa wajen da Abeer ya ajiye Mota, Ya samu da kyar ta shiga bayan ya lallaɓata akan zai maida ita gidansu, ta na ganin Shahbeer ta ƙara fashewa da kuka ta na ƙoƙarin fita Baban Halima ya dakatar da ita da cewa "Ki samu nutsuwa Halimatu ba abin zai faru da ke da izinin Allah." Cikin kuka ta ce "Baba ba su cutar da kai ba? su waye su ka kawo ka nan kai da ba ka gani? ko dai kashemu za su yi?" da temakon Abeer ya shiga Motar, bayan ya gyara zama ya ce "Duk yadda ki ke tunani ba haka bane, da farko dai Shahbeer ne silar zuwana ɓangarensu yanzu kuma Abeer ne ya rakoni wannan gidan, su ba masu cutarwa bane ki kwantar da hankalinki." Ba ta yarda da kwantar da hankalin ba don haka ta yi shiru Da maganar ta ci gaba da ɓarza kuka. Shahbeer ya ce "Abeer Hanzarta ku tafi do Allah." ya ce "To YaYa." cikin gida ya koma har lokacin duk su na inda su ke sai ma zama da su ka yi kowa ya na jimanta al'amarin. Mommy ta ce "Shahbeer ka ji abin da Halima ta ke faɗa?" ya ce "Na ji Umma." ta ce "TO Waye Ramadan?" Shahmeer ya ce "Mama shi ma Babanta bai san shi ba bare mu." Shahbeer ya ce "Abin da ya fi ɗaure mini kai kenan, na ma kasa yin Nazari akan lamarin." Malika ce ta miƙo masa Shahzad tare da cewa "Tin ɗazu ya ke son ya bi ka ya ce gurinka zai je." riƙo hannunsa ya yi ya jawo shi jikinsa gami da cewa "Har da kuka ka yi?" Shahzad ya ce "A'a Baba ne ya na kuka" girgiza kai ya yi gami da cewa "Baba ma ba kuka ya ke ba hawaye ya ke yi." Shahzad ya ce "Hawaye?'' kai ya gyaɗa masa kafin ya ce "Zan sa ayi mini bincike a can yankinsu waye Ramadan ɗin." Shahzaib ya ce "Hakan ya yi." Inna ta ce "Ni fa na fi tunanin wata Duniyar haukan yarinyar nan ta faɗa, ga dai Ɗa me kama da kai sakk amma ace kuma wani ne Ramadan daban? ko dai kaine Ramadan ɗin Shahbeer? nasanka da fuskoki da yawa." Shahzain ya ce "Ku ji Inna fa, ba ki san mutum ya na kama da mutum ba tare da sun haɗa alaƙa ta jini ba??" Murmusawa Shahbeer ya yi ya ce "Inna haka ne amma a wannan ɓangaren ba ni bane, ni sunan ma bai yi mini ba bare na yi amfani da shi." Mommy ta ce "Allah kaɗai shine masanim abin da zai faru da wanda ya faru, to don haka mu miƙa komai gareshi idan lokaci ya yi komai zai baiyana tinda gashi Allah ya kawo mu wannan lokacin jiran da za mu yi nan gaba ai kaɗan ne." Shahmeer ya ce "Ƙwarai kuwa Allah ya sa mu ji alkairi." su ka amsa da "Amin" Shukriya yau Duniyar duk ta gama yi mata zafi, ta rasa me yasa Dada ta zage sai ta Aura mata wanda ba ta so ba za ta iya rayuwa da shi ba. ta zuba tagumi hannu bibbiyu sai sharɓa gumi ta ke yi. Abida ce ta katse mata tunani da cewa "Anti Shukriya ya kamata ki manta da Shahzain tinda me faruwa ta riga ta faru, Dada dai ta ce dolen-doliya a ɗaura Aurenki da Ya Maalik a cikin Sati ɗaya to inaga fa gwara mafi sauƙi ki manta da Shahzain kawai." "Abida to ke me yasa ba za ki Auri Ya Maalik ɗih ba?" "Ai ni ba ni ya ke so ba ke Yake so. "Ashe ba ki da hujjar cewa ni in ƙyale wanda na ke so in Auri Maalik; tin da na ke ban taɓa jin wani abu me kama da so ko burgewa ma a tattare da Maalik ba, na yi iya ƙoƙarina wajen bawa kaina haƙuri har na koyawa kaina son shi amma hakan ya ci tira na kasa, ba na jin zan iya son Maalik har bayan raina, ko da An Aura mini shi zan rayu da shi ne a cikin ƙunci da damuwa ba zan taɓa farin ciki ba domin an rabani da wanda na ke so kuma an haɗa ni da wanda ba zan iya son shi ba, Abida ba zan iya mantawa da Shahzain ba har sai naga an ɗaura mini Aure da wani a hakan ma ba zan cire tsammani ba domin indai Rabona ne zan Aure shi, ki dena tunanin zan manta da shi cikin sauƙi, ni bansan me ya sa ma bakya tausaya mini ba Abida. Abida ta taɓe baki kafin ta ce "Ai ba rashin tausayi bane ni na fi yi miki sha'awar Auren Maalik don shine ɗan-uwanki ba wasu bare ba wanda ma ba'a da Tabbacin Ƴaƴan Halak ne ko na Haram." "Abida da bakinki ki ke faɗen haka?" "Me zai sa ba zan ce haka ba tinda ta kama?, Ke fa ba komai ki ke yiwa ba sai kuɗi da Daula, daga haɗuwa sau ɗaya sai soyayya in ba ƙaryar banza ba?" cike da mamakin kalaman Abida ta ce "Wallahi ban taɓa son Shahzain dan kuɗinsa ko Daula ba, idan kuma ƙarya na yi miki kar Allah ya bani ikon ƙara yin magana, kinsan ai rantsuwa ba wasa bace, kuma ko da ba'a kamuwa da son mutum lokaci ɗaya ni dai na kamu da sonshi a ganin farko, ta yuwu ni wata irin halittar ce daban ba mutum, amma ni dai nasan ban taɓa yiwa wani Namiji irin son da na ke masa ba, kuma wallahi ban taɓa tunanin Dukiyarsa ba ba na kallon duk abin da ke gefensa shi kaɗai kawai na ke gani, ina son mutum me gaskiya kuma da tsoron Allah, amma babu wannan a tsakankanin wasu mutanen waye Maalik in ba Mazinaci ba? Na taɓa son Safyan tin lokacin da ban san So ba amma tin da na gane ba ya tsoron Allah shi ba me gaskiya bane ba Adali bane sai na ji bani da abin da na tsana kamar shi; A da tabbas bansan So ba amma yanzu na san shi akan Shahzain, ya kamata ki fahimceni Abida kece ƙanwata idan ba ki fahimce ni ba waye zai fahimce ni?" tsaki Abida ta yi ta tashi ta bar ɗakin cike da takaici da baƙin ciki. Shukriya ta fashe da kuka, Allah kai ka ɗora mini jarabar son Shahzain kuma ina roƙonka ka yaye mini, abin da ta ke maimaitawa kenan a cikin ranta. Shahbeer Juye-Juye ya ke faman yi akan Gado gashi ya na jin bacci amma ya kasa rintsawa sai wasu ƴan ƙananun mafarkai ya ke yi, duk ya rasa meke masa daɗi, ba abin ya yi kuka ya ce ya huce ba nan ma ƙarin wani zafin ne ga kansa ya na wani mugun ciwo. ya na cikin wannan halin Malika ta farka a tsananin firgice, jikinta sai kakkarwa ya ke yi lokaci ɗaya gumi ya fara yanko mata ta ko'ina, sai da ta numfasa sannan kuka ya kufce mata. Da kyar ya yunkura ya tashi zaune cike da ƙarfin hali ya ce "Me ya ke faruwa Malee?" da sauri ta rarrafo kusa dashi ta rungumeshi ta ƙara fashewa da wani sabon kukan, Zuciyarsa ta shiga dukan sittin saba'in, ɗan bubbugar bayanta ya shiga yi gami da cewa "Ki yi shiru, ki faɗa mini me ya faru?" Cikin shashshekar kuka ta ce "Wata Mata ce amma ba mutum bace irin kamannin Aljanu gareta, shine ta danne ni wai sai ta cinye ɗan dake cikina, Wallahi sun wahalar da ni Shahbeer na zata ma na mutu ko da na farka." "Ɗa??" ya yiwa kansa tambayar gami da kallon fuskarta da ta yi wujiga-wujiga "Malee Dama ki na da Juna biyu ne?" "ni ma ban sani ba, ka temaka mini kar su rabani da Ɗana Shahbeer. Mamaki da Al'ajabi gami da Tsoro sun gama daskarar da shi, ƙara rungumeta kawai ya yi ya ma rasa me bakinsa zai furta, in ya Fahimta daidai bala'in da Mahaifinsu ya jawo musu ne ya ke neman dawowa kan Matarsa da ɗan cikinta, Shahzad ne ya faɗo masa a rai hakan ya ƙara haɓɓaka tsoro da razaninsa, kenan shima Shahzad ya shiga cikin waɗanda hatsabibin mutumin nan zai sha jininsa?, "A'a, Ba zai yuwu ba" ya faɗa cikin matuƙar kaɗuwa. Addu'o'i ya shiga jerowa har ya samu nutsuwarsa ta dawo, bayan wani lokaci bacci me nauyi ya yi awon gaba da Malika, ya gyara mata kwanciya sannan ya tashi Domin gabatar da Nafila. Salim Matashin da ya ke kulawa da Baban Halima, Kira Baban Halima ya ke ƙwala masa akai-akai har ya sai da ya iso ya ce "Gani Baba" sannan ya dena kiran nashi, cike da tarin damuwa ya ce "Yaro ka duba mini Halimatu anya kuwa ta na nan? na ji shiru kuma ina ta magana ban ji ta ce komai ba." To ya ce sannan ya tashi ya fara dube-dube, a cikin Ɗaki ya hangeta ta raɓe a jikin gado ta yi tsumu-tsumu. Cikin tausayawa ya ce "Baiwar Allah Baba ya na kiranki." ta ɗago idanunta da su ka sauya kala sabi da kuka ta kalleshi tsaf sannan ta ce "Me ya sa aka kawo ni nan?, Ina Ramadan?" Salim ya ce "Bansan wanda ki ke magana akansa ba, ni dai Me-gida Shahbeer ne ya sani kulawa da Babanku, yanzu ma Baban ne ya ce in nemo masa ke hankalinsa duk ya tashi." Cikin rawar murya ta ce "Kar ku ƙara cutar da ni don Allah ku barmu mu koma gidanmu." Salim ya ce "Ba abin da za mu yi miki don ba aikinmu bane cin zarafin mutane, Ki taso mu je Baban ya ganki ki ganshi. cikin sanɗa ta tashi ta na takawa da kyar da kyar, har inda Baban Halima ya ke zaune Salim ya rakata ya gyara mata gurin zama sannan ya ce "Baba ga ta nan kusa da kai." ya ce "To na goda Yaro Allah i yiwa rayuwa Albarka. ya amsa da Amin sannan ya basu guri, Baban Halima ya ce "Halima!" cikin disashshiyar murya ta amsa, ya ƙara da cewa "Shin nima guduna ki ke ne?, tin da mu ka dawo gidan nan kin ƙi yi mini magana ashe ma tashi ki ka yi ki ka barni." "Baba ba zan gujeka ba, Ina neman yafiyarka Don Allah ka yafe mini Baba, tin da na fita ashe ban dawo gida ba. "Ƙwarai ba ki dawo gida ba Halima har an kwashi lokaci kusan shekara uku kenan. "Baba shekara Uku na yi ba na gida? to ina aka kaini? ya akai Ramadan ya ɗakko ni ya kawo ni nan??" ''Ki fahimta Sadiya, su waɗannan Ƴan-huɗu ne sunansu Shahbeer Shahmeer Shahzaib Shahzain, kuma su ba sa cutar da mutane, wanda ki ke magana akansa daban waɗannan daban, sai dai abin mamakin meye alaƙarsu?, Kinsan cewa kina da Ɗa? Shekararsa biyu sunansa Mukhtar Laƙabi Shahzad, ya taso a hannun Shahbeer ne shi ne ya raine shi. fashewa ta yi da kuka ta na cewa "Wallahi Baba ni ba Mazinaciya bace, wallahi Ramadan ne kuma sai Allah ya tambaɗar dashi tin da ya zalumce ni, Komai tsananin da zan shiga ban taɓa irin wannan tunanin ba bare na aikata, wallahi ya cuceni tsakanina dashi sai dai Allah ya isa." "To wai Sadiya waye Ramadan ɗin nan ne??, kuma abin da zai baki mamaki Yaron da ki ka haifa ba abin da ya bari a kamannin Shahbeer hakan ne ma ya sa Duniya ta ke kallonsa a matsayin uban Ɗan" "Nima bansan asalinsa ba Baba, ƙila ma shine wannan ya ke nuna kamar ba shi bane, ni dai ba zan taɓa yafe masa ba Duniya da Lahira, kuma ba zan taɓa Son shi ba, ba zan so ɗan nashi ba dukansu na tsanesu. "To Halima idan kin tsani Ɗanki ai bashi da laifi kune masu laifin, ya kamata ki dawo nutsuwarki kuma ki nemi yafiyar Allah, kuma dolenki ki bani labarin Alaƙar da ke tsakanin ke da wani namiji har da Ɗa ya shiga tsakaninku ba tare da Aure ba. ta ƙara fashewa da kuka gami da cewa "Na shiga uku na lalace." "Ya-isa haka Halima kukan nan ciwon kai zai ƙara miki, ki dawo nutsuwarki ki bar kuka. ba ta yi magana ba ta ci gaba da ɓarzar kukanta. Ta ko'ina hada-hada ake yi domin kuwa bikin Yallaɓai Maalik ya kusa, Hajiya Dada ba zama ta tsaya a tsaye don ganin ta fitar da ɗanta. Mami kuwa ba wani murna ta ke da Auren ba don kuwa ta na Tausayin Shukriya. Abba ma dan dai ba yadda zaiyi ne dolensa ya haƙura. a cikin Kwanakin nan da su ka wuce, kullum cikin Ƙunci da koke-koke ta ke, idan ta ji alamar su Shahbeer sun zo sai ta ji kamar ta shaƙe kanta ta mutu sabi da baƙin ciki da tsananin ƙiyayyarsu, Shahbeer kuwa duk son shi da ganinta ya danne ya basar ko tambayar Lafiyarta ma da kyar ya ke yi. Zaune su ke a Falo su na hira Su duka huɗun sai Ma'arufa da Inna Mommy dai ba ta gurin, Malika cee ta salallaɓo kusa da Shahbeer murya ƙasa-ƙasa ta ce "zan je gyaran gashi." Kallonta ya yi sama da ƙasa, ta wani koɗe fayau idanunta kamar farar tsoka gaba ɗayanta kamar ta wani fiffirgice, Kafin ya yi magana Shahzaib ya ce "Ke je ki na barki, Amma ki kula." Harararsa Shahbeer ya yi, ya na dariya ya ce "Ato Boss na san ɗan nazarin nan naka na hana fita ne, to yasin sai ta je." ya ce "Allah ya tsare." ta yi saurin cewa "Amin, in tafi da Shahzad?" jim ya yi kafin ya rausayar da kai ya ce "To ku je tare don shima akwai son yawo, amma fa kar ki shagalta ki bar mini ɗa ya shiga garari." ta ce "In Allah ya yarda hakan ba za ta faru ba." Fitowarsu kenan daga gurin Gyaran Gashin su na shirin shiga Mota wani Ɗan Saurayi ya zo kusa da su ya kai hannu zai fizge jakar hannunta Shahzad ya ƙwalla ƙara da sauri ta waigo don ganin abin da ya faru ido huɗu ta yi da Ɓarawon ya tsirawa Shahzad Ido, kasancewar ba ta san abin da ya ke shirin aikatawa ba ya sa ta ce "Bawan Allah lafiya??" ya ce ''Hajiya Ɗanki ne wannan? amma fa kyakkyawa ne" har lokacin idanunsa na kan Shahzad shima Shahzad ya zuba masa idanu su na kallon juna. ɗan janye Shahzad ta yi ta rungume shi a jikin ƙafafunta sannan ta ce "A'a Ɗan Mijina ne." Saurayin ya ce "Allah ya bani kamarka yaro, gaskiya kyakkyawa ne, ya sunansa?" "Shahzad sunansa, idan ba damuwa ba mu guri mu wuce. ya ce "Allah ya tsare Hajjaju." ciki-ciki ta amsa da "Amin" sannan ta shige mota cike da mamakin abin, ta lura ba ita saurayin ya ke kallo ba Shahzad ya ke yiwa wani irin kallo na ƙurilla wanda ta kasa gane me ya ke nufi, duk ta gama tsorata tunanin irin munanan mafarkan da ta ke yi su ka shiga dawo mata. shi kanshi Shahzad ya yi tsuru-tsuru da alamu hankalinsa bai kwanta da Saurayin ba. haka cikin yanayin tsoro da mamaki su ka koma gida. Saurayin kuwa sai da ya dena ganin ƙurar motarsu sannan ya tari adaidaita-sahu ya shiga jiki na ɓari ya shiga neman wata lamba sai dai ba'a ɗaukar kiran nashi. Jiki a sassaɓule Alhaji Boza ya fito daga cikin Asibitin ya nufi gurin da ya ajiye Motarsa, har ya buɗe zai shiga ya ji an kira shi "Baba!!" ba kiran ne ya fi ɗaukar hankalinsa ba muryar wanda ya kira shi, da sauri ya ce "Shahbeer?" Ƙarasowa wajen ya yi tare da cire abin da ya ɓoye fuskarsa, Alhaji Boza ya yi murmushin Farin ciki tare da hawaye "Alhamdulillahi, yau Allah ya nuna mini ranar da Ɗana ya kira ni Baba tin kafin na mutu. "Ka yi haƙuri.. Da sauri ya ce "A'a Yaro, ko me ku ka yi mini hukunci ne, yau da ba ku nuna mini kuskurena ba da yanzu ina kanshi ina ƙara tufka tsiya, Alhamdulillahi Allah me kyauta Allah me karɓar tuban bayinsa, Ɗana me ke tafe da kai gurina?" "Temakonka na ke nema. "Faɗa mini indai har zan iya to tabbas zan temake ka. "To mu shiga mota ko Baba?" Alhaji Boza ya ce "To Shahbeer." bayan sun shiga motar ya zaiyana masa duk abin da ke faruwa....... Da gudu ya ƙarasa wani ginin gida me kama da kango, can ƙarshe ya tarar da Ogan nasu ya zube a gabansa ya na mumfarfashi. Ogan ya ce "Meye hakanne?? ka zo wa mutane wani raɓe-raɓe ina aiken da mu kai maka??" ya ce "Oga akwai matsala fa, Wallahi wani yaro na gani me kama da kai

Chapter 20 of 30