Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
son wani akan shi, baya so sam, shisa take kokarin danne yanda take kaunar Bukar dan batason Lubna sufyan Hausabook.com 179 wannan kishin na Julde ya gifta tsakanin su. Bukar dinma a gaban Julde saiya daina bata labarin Hamman shi "Daada baki ji karatun da Hamma yake yi ba, kamar ya sammun wani sashi na kwakwalwar shi" A yanayin yanda yake yawan maganar Hamman shi ne tasan irin girman kaunar dake tsakanin su. Duk da Bukar ne, kowama so yake, kowa ma nunawa kauna yake. Amman kaunar da yakeyi wa Hamman nan nashi daban take, kuma da alama yana daga cikin manyan 'yaran Baabuga da yakan tura neman karatu gari-gari, cikin wanda zamanta bai tsawaita a gidan shi ba balle ta san su. "Hamma Am fa ya haddace sittin, rubutawa yake yi yanzun" Bukar ya karasa maganar da yanayin nan mai cike da alfahari, a yanayin yanda yake yawan maganar Hamman shi ne tasan irin girman kaunar dake tsakanin su. Duk da Bukar ne, kowama so yake, kowa ma nunawa kauna yake. Amman kaunar da yakeyi wa Hamman nan Lubna sufyan Hausabook.com 180 nashi daban take, tunda ya fara mata zancen shi alamu suka nuna yana daga cikin manyan 'yaran Baabuga da yakan tura neman karatu gari-gari, cikin wanda zamanta bai tsawaita a gidan shi ba balle ta san su. Duk wannan kaunar bata dameta ba, a hankalima sai ta bude ido taji tana taya Bukar son 'yan uwan shi, son Hamman nan nashi. Da ta sani, in da tasan cewa wannan kaunar zata kawo su inda suke yanzun da tayi komai a karkashin ikonta ta yanke wannan kaunar "Ina so zan bi Hamma Maiduguri inda yake karatu wannan karin Daada, ina burin yin karatu mai zurfi kamar na shi" Maganganun Bukar suka daketa, irin duka na ruwan saman da baka ga haduwar hadarin shi ba, bakaji yayyafi ba, karfin ruwan daya dirar maka kawai kaji "Ke na fara gayawa" Bukar ya dora kamar hakan ya isa ya dai-dai jirkitar da yayi ma duniyarta gabaki daya Lubna sufyan Hausabook.com 181 "Idan shawarata kake nema bana so kaje, idan ra'ayina kake son ji babu inda nake so kaje. Idan kuma gayamun kakeyi saboda ban isa ba Bukar kayi abinda kake so" Tace tana mikewa tabar masa wajen. Ta dauka zai hakura, har kasan zuciyarta ta dauka zai hakura saboda Bukar na da gudun bacin rai, nata fiye da na kowa. Amman kaddarar da take fisgar shi saita rinjayi komai. Da yaga daga Hammadi har Abu sun kasa shawo masa kanta saiya nufi Baba, Baba da yayi bata umarni a maimakon ya tausheta "Me yasa zaki hana shi tafiya tunda yana so? Namiji ne, idan karatu baisa yayi nisa da gida ba, wata rana neman na kan shi zai iya nisanta shi da gida. Ki godema Allah daya baki yaro mai hankali irin Bukar, ke in ba rashin hankali ba ai abin murna ne ace ya dawo da sittin akan shi" Hawaye takeyi da tun daga ranar har zuwa yau take jin sun kasa tsagaita mata. Banda nisan Maiduguri da Marake babu abinda take hangowa, yanda duk suke labarta mata kaurin sunan da yankin yayi a wajen ilimin addini mai Lubna sufyan Hausabook.com 182 inganci kunnuwanta basa karasawa da zancen zuwa zuciyarta. Shima Bukar din da yace "Ida na tafi ba saina gama zan dawo ba Daada, irin yanda Hamma yakeyi zan dingayi nima. Duk bayan wasu watanni zanzo gida inyi sati kamar yanda yakeyi" Jin shi kawai tayi, nisan da take ji yayi da zuciyarta na kara tsayi yana barin wani fili da batasan me zatayi da shi ba "Dan Allah Daada, bana so in tafi zuciyarki bata aminta da zuwan ba" Nan ma babu abinda tace masa, saboda karya bata taba shiga tsakaninsu ba, bata so ta fara. Ba zatace masa ta aminta ba, ba zata ce masa zatayi komai don yabar wannan tafiyar ba. Hankalinta bai kara tashi ba sai da tagan shi da kullin kayan shi, da tarkacen da Abu ta hada mishi, duk abinda take tunanin zai bukata, ita babu wani abu data tanada, tunanin ma baizo mata ba saboda tanata addu'ar Allah ya canza mata zuciyar shi, da kanshi yace ya fasa. Lubna sufyan Hausabook.com 183 "Daada me yasa zai tafi? Dole sai can? Nan babu makaranta?" Yelwa ta karasa maganar idanuwanta cike taf da hawaye "Shi ka zaba ko Bukar? Bayan nace maka ni kadai ne Hamman ka" Murmushi Bukar din yayi yana girgiza ma Julde kai "Bashi na zaba ba Hamma, karatu na zaba" Su duka basa so, zuciyoyin su basu aminta da tafiyar ba. Babu yanda zasuyi da Bukar ne tunda ya kafe, suna ji suna gani ya tafi yabar su da kewar shi da suka fara tun kafin a kwana. Yelwa ma Saratu ce ta jata suka shige gidan Abu saboda kukan da takeyi, Julde ko raka Bukar kinyi yayi daga baya, sai da yaga ya bace mishi, ya sha kwana sannan ya bishi da gudu, ko ya dawo ba gidanta ya shigo ba, sai dai in ya shiga gidan Abu ne. "Kiyi hakuri Dije, ki taushi zuciyarki tunda yace duk bayan wasu watanni zai dawo" Lubna sufyan Hausabook.com 184 Yanda Abu ta karasa maganar da wani nisantaccen yanayi a muryarta yasa Dije dagowa ta kalleta. Akwai kyallin hawaye a idanuwan Abu da taketa kokarin dannewa. Bukar ba daga jikinta ya fito ba, daga farko ma tana son yaronne saboda ya fito daga jikin Dije, saboda kaunar da takeyi wa Dije mai girma ce. Amman daya dawo hannunta sai ya tabbatar mata ko da Dije, ko babu Dije idan hanya ta hadasu zata kaunace shi, zata so shi wata irin soyayya da ba zata kwatantu ba. Rabon da tayi baccin kirki tun ranar da Bukar yazo mata da maganar yana so ya bi Hamman shi. Amman sai ta danne nata ciwon, ta danne nata zafin zuciyar saboda ta tausashi Dije. "Adda" Dije ta kira muryarta a karye, kunyar Abu na kamata, tunda aka soma maganar tafiyar Bukar ta manta cewa a hannun Abu yake, tama manta cewa itama Abu zata iya jin ciwon tafiyar Bukar din ko da bai kai nata ba. "Muyi masa addu'a kawai... Allah ya tsare shi ya taimake shi" Lubna sufyan Hausabook.com 185 Kai Dije ta daga mata, tana sake share hawayen da suka zubo mata "Bari inje gida, yamma nayi in dora tuwo" Kan dai Dije ta sake dagawa, duk da taga hawayen da Abu tayi saurin daukewa da yatsa. Gara taje gida tayi nata kukan ko zata samu sauki itama. * Rigar da Datti ya cire bayan ta dawo ta dauke daga kan gadon tana kokarin ninketa, sai taji kamar goro a cikin aljihun, hannu tasa ta ciro, harda dabino ma "Ina ka samo goro da dabino?" Ta tambaye shi, tana kallon inda yake zaune yana kokarin saka zariya a jikin wandon sakin dake hannun shi. Lokaci ya koya mata gujema duk wata magana ta Bukar a tsakanin su. Saboda hakan baya jan komai sai fadan da suke shafe kwanaki bai kare ba, koma tace Datti yake shafe kwanaki bai daina ba. Bata da karfin biye masa, ta kowacce fuska sai da ya tabbatar ta gane fada ko jayayya dashi babu wata riba. Ko Lubna sufyan Hausabook.com 186 na rana daya bai nuna mata yasan Bukar ya tafi Maiduguri ba, baima nuna ya kula da baya nan ba, abin yayi mata ciwo na ban mamaki. Amman a zaman su yana abubuwa da yawa da suke mata ciwo, abubuwan da ta koyi shanyewa tunda ko tayi magana a kai ba zai sauya komai ba. Hammadi da kan shi ya saka su Julde a makarantar allo, amman Julde sai yayi sati biyu baije ba, randa Datti yaga sawun Bulala kwance a damtsen hannun Yelwa yayi tashin hankalin da har saida Hammadi ya biye masa "Saratu ce kake son nuna mun ban isa da ita ba, sai kasa taje makarantar ita, amman ni dai nawa yaran dana isa dasu sun gama zuwa. Babu katon banzar da zai kamamun yara yana duka saboda karatu" Hammadi kyale shi yayi, sai dai Saratu ta nuna ma Hammadi cewa abinda Datti yake so itama shi take so, abinda baya so itama bata so. Ko Abu ta tirsasa mata tafiya makarantar sai tayi rashin kunyarta da babu wanda ta cirewa hula banda Datti, sannan zata tafi, idan ta tafin ma ba Lubna sufyan Hausabook.com 187 makarantar take zuwa ba, waje take samu tayi zamanta har sai lokacin tashi tukunna "Mtswww" Tsakin da Datti yaja ya maida hankalin Dije kan shi "Hamma ne fa ya jani auren nan na wajen yar Dammud'o....lalataccen aure ma irin wannan" Kallon rashin fahimta Dije tayi masa "Kad'o fa ya dauka yaba, yana bafullatanin usul ya dauki yarinya ya hadata da bahaushe, Allah tsine wannan hadin. Kinga son da nakewa Yelwa ko? Gara in binneta da in hadata aure da bahaushe, inyi kuka in hakura" Wannan karin a tsorace Dije ta kalle shi, maganganun shi na taba zuciyarta. Tasan baya son hausawa, wata irin kiyayya yake musu da batasan tushenta ba. Tunda a iya saninta babu abinda bahaushe yayi masa banda bambancin yare, bai kuma taba bata labari ko akwai wani abu daya taba faruwa tsakanin shi, ko wani nashi da bahaushe da yasa yayi musu wannan tsanar ba. Itama zuwa yanzun ta tabbata da bata Lubna sufyan Hausabook.com 188 biyo Innarta ba, da batayi kama da fulani ba, da bai yara mata yaji ta fahimta ba, yaji ta amsa shi, tun ranar farko daya ganta ba zai taba amincewa da aurenta ba. Yaron da yake magana Dije ta tabbata in dai haihuwa da kuma girman Marake ne zai wahala ace bayajin fulatanci. Saboda cudanya da juna tasa har hausawan cikin ma suna yarawa, duk da kanayi Datti yake gane kai ba bafullatani bane, yakan ce suna bata wasu kalaman wajen furtawa "Bafa yare ake dubawa ba a wajen aure Datti, kyawun hali ake dubawa" Daga kai yayi yana dubanta "Yare zan fara dubawa, ko Julde ba zai auri bahaushiya ba" Murmushin takaici tayi "To ai kai ka auri bahaushiyar, kuma jinin hausawa na yawo a jikin su Julde" Shima murmushin yayi Lubna sufyan Hausabook.com 189 "Allah ya tsare su, bangarenki na fulani ne kawai tare da 'ya'ya na Dije, bangarenki na fulani na aura, da kuma shi kadai nake cudanya" Sai taji ya bata dariya. Dariyar da shigowar Julde ta katse mata "Daada hannuna zai kone, ki fito ki karba" Yake fadi, don sallama bata cikin abinda yake yawaita yi don zai shiga waje, musamman idan yayi daga farko, to a wajen shi ta dauke ta yini guda ko zai shiga ya fita gidan sau goma "Ya za'ayi ka rungumo kunu a langa?" Dije ta fadi tana karbar kwanon daya dauki mugun zafi daga hannun shi tana ajiyewa a kasa, baiko saurareta ba ya fice yana komawa inda ya fito. Harya shiga gidan murza hannuwan shi yakeyi a jikin rigar shi cikin yanayin da yasa Saratu fadin "Me ya sami hannun?" Tana daukar kosai ta kai bakinta "Konewa nayi" Lubna sufyan Hausabook.com 190 Ya amsa a takaice, radadin da tafukan shi sukeyi na shiga har kwanyar shi. Tashi tayi daga inda take zaune tana karasawa inda yake tsaya, batare da tace masa komai ba ta kamo hannun shi guda daya tana ware tafin hadi da saka nata a ciki ta murza masa. Nata hannun yake bi da kallo da kuma yatsunta, yatsunta da suke dauke da farata farare qal, yanayin taushin su a cikin nashi kamar bata taba aikin wahala ba tunda take. "Sannu... Muga dayan" Ta fadi tana sakin wannan, tsintar kanshi yayi da mika mata dayan hannun nashi, ta murza masa kamar dayan, tana cikin yine Yelwa da taje kai ma su Dije kosai ta dawo "Me ya same ka?" Ta fadi tana karasawa ta janye hannun shi daga cikin na Saratu tana dubawa, sai dai bata ga komai ba "Konewa yayi" Saratu ta amsata, sosai Yelwa take duba hannun nashi, ko da bai kone ba jar fatar shi tasa bata ga Lubna sufyan Hausabook.com 191 wani bambanci ba ita. Daga ido tayi tana kallon fuskar shi, amman ba ita yake kallo ba, hannunta yake kallo, a zahirance yafi na Saratu kyau, yafi shi komai. Amman baiji abinda yaji da nata yake cikin nashi ba. Shisa ya zare hannun nashi, so yake ya kara rike na Saratun, yaji ko yanayin zai kara dawo masa, yaga ko zai gane dalilin da zaisa yaji abinda yaji a karo na farko bayan ya tuna lokutta masu yawa da ya rike hannunta, amman a rijistar kwakwalar shi babu wannan yanayin. Babu dumin nan da yaji ya ratsa ta cikin hannun nashi yakai ko ina na jikin shi. Ya taba hannun Yelwa yanzun baiji dumin ba. Hakan na nufin a na Saratu kawai yake kenan? Ji yayi yana so ya gwada, yana so ya sake jin dumin nan, yana kuma so yasan idan a hannun Saratu hakan ya tsaya ko kuma akwai wasu mata da hannuwan su ke da dumi kamar nata. Jin idan ya tsaya zai koma inda Saratu take ya riko hannunta yasa shi juyawa ya fice daga gidan. Sai dai fitar shi ba zata sake kaddara ba Fitar shi ba zata sake komai ba Lubna sufyan Hausabook.com 192 Komai da yanzun ne zai fara Yelwa take kallo, idanuwanta a rufe, Saratu da take gabanta tana mata kwalliya, ta diga mata kwallin daya fara tun daga goshinta zuwa karan hancinta, da alama digon zai dire ne har habarta cikin kwalliyar su ta fulani, bakinta ma a zane yake da bakin kwallin daya zauna das yana kara fito da hasken fatarta da kamar tana girma yana kara fitowa ne, girman su harya daina bata mamaki. Ba son kai Dije zatayi ba idan tace kaf kauyen babu mai kyawun Yelwa, ko da bata fada ba, mutane da yawa sun fada, ita da kanta wasu lokuttan gani takeyi kamar ba daga jikinta Yelwa ta fito ba. Yanda take yanzun, kyawunta kamar an cirota daga cikin zane. Kallon ta Saratu ta danyi "Yawwa an gama" Bude idanuwa Yelwa tayi tana saka su cikin na Saratu "Nayi kyau?" Lubna sufyan Hausabook.com 193 Ta tambaya tana duba gefenta in da ta ajiye dan mudubin da ta dauka ta haska fuskarta, tana danyin farr da idanuwa cike da son ganin yanayin yanda kwallin ya zanu cikin idon nata. Kayan sakine a jikinta farare da suka sha ado, sai sarkar su ta fulani shake a wuyanta, ta daura dankwalin da harya fara soshewa amman son da take masa yaki bari ta iya bayar dashi, Abu ce ta bata shi, ta manta ko tun yaushe. Amman tana son dankwalin, zanen ganye ne a jiki da koren su ya fito sosai "Muje?" Ta fadi tana duban Saratu, ba zaka kirata mummuna ba, amman idan har tana tare da Yelwa babu yanda za'ayi ka ga nata kyawun, bata da hasken fata kamar na su Julde, amman kuma ba baka bace ba. tana da madaidaicin tsayi, yanzun da alamun 'yan matanci ya fara nunawa a jikinta zaka ga kalar cikar halittar da take da shi, batayi sirantaka irin wadda aka san akasarin fulani da ita ba. Sai dai kallo daya zakayi ma yanayin fuskarta da bakinta da bata cika sauke labban ba, a dage suke kusan ko da yaushe, alamar dake nuna saurin fushinta da Lubna sufyan Hausabook.com 194 yanda take a shirya da ta mayar maka da magana idan har bukatan hakan ta taso. "Wai Daada babu abinda za'a siyo miki?" Yelwa ta sake tambaya a karo na ba adadi tana mikewa "Babu fa, kuma yawo ne zai kaiku ba don akwai abinda zaku siya ba" Kafin Yelwa ta amsa Saratu data juya idanuwanta ta karbe zancen "Ita fa kasuwa baka sanin kana bukatar wani abin saika shiga" Numfasawa Daada tayi batace komai ba, lokutta da yawa bata cewa komai in dai har zancen ya zamana tsakaninta da Saratu ne, tana da hakuri, amman bata son raini, tun kafin Saratu tayi girman da za'a daina amfani da yarinta ana ma rashin kunyarta uzuri bata cika son yarinyar ba. Zuciyarta ta kasa natsuwa da ita, sai halayenta suka hadu suna kara sakawa ta fita harkarta in ba ta kama dole ba. Ko Abu ta yiwa rashin kunya kau da kai takeyi. Tunda idan ta shigama babu Lubna sufyan Hausabook.com 195 wani abu da hakan zai haifar, saima fadan da Datti zai rufeta dashi idan yaji. Akan Saratu sai ya manta wacece Abu, saiya manta yanda a ko ina ya kamata ace ya kasance cikin mutanen da zasu iya bada shaidar halayen Abu, sai ya manta cewar ko Saratu bata fito daga ciki Abu ba, ko da ba ita take riketa ba ya kamata ace tafi karfin Saratu ta kalleta ta mayar mata da magana ko don dattako da cikar kamalar da suke shimfide a fuskar Abun. Rashin kunyar Saratu irin ta Datti ce, babu wanda ya wuce ta a wajen su muddin tunaninsu ya basu cewa anbi takan sune. da farko Dije ta dauka Abu kadai take yiwa, sai a hankali ta kula da har Hammadi ma bai wuce ta mayar masa da magana ba, baifi ta hade rai tana surutai kasakasa idan yayi mata fada akan wani abu ba "Allah ya shiryeki Saratu, Allah ya shiryeki" Ya kan fadi cike da wani yanayi a muryar shi, komai. Banda fatan shiriya babu wani abu da zaka iya bin Saratu da shi. Sai kuma ido, kamar yanda ta bisu da shi daga ita har Yelwa har suka fice daga cikin gidan hannuwan su cikin na juna, Lubna sufyan Hausabook.com 196 bambanci shekarun su bai rage shakuwar da take tsakanin su ba, duk da kowa yasan kauda kan Yelwa na daya daga cikin abinda yasa ba'a yawan jin kansu. Suna karya kwanar gidan suna hango Julde, zuciyar Saratu ta doka a cikin kirjinta, dokawar da ganin shi kawai kan sa hakan ta faru. Tun kafin ya karaso yake musu murmushi, ko tace yake yiwa Yelwa murmushi. Farin wandone a jikin shi da rigar saki, ya tara suma a tsakiyar kan shi, yayi kitso dai-dai a kowanne gefe na kan shi da ya saka sauran sumar a tsakiya, sai sarka ta wuri da take daure a wuyan shi. Banda kwallin da yake idanuwan shi babu zanen komai "Kai ba bororo bane ba..." Datti yace masa ranar farko da yayi kitso, kujera yaja ya zaunar da shi, yasa almakashi yana saita masa sumar da ya tara ta daga gaba tafi sauran cika, ba kamar sumar Bukar da take luf ba, tashi a cunkushe take, kuma yafi sonta a hakan. Idan ya kalli sa'annin shi a Marake, ya kalli fuskokinsu yaga tsagun fulani reras saiya kara Lubna sufyan Hausabook.com 197 godewa Datti da bai musu wannan zanen a fuska ba. Daya taba tambaya haka yace masa "Da muna da tsage na gado da na ganshi a fuskar Babana, ko ta Inna ta, da kuma anyi mana kagani a fuskata... Fulanin yankin da muka fito daga shi sukanyi adon sune da kaloli daban daban a fuska a maimakon tsagar... Idan kana so sai in koya maka" Dariya kawai yayi, bayason komai banda kwalli a fuskar shi, wani lokacin Yelwa da ita take masa kitson kan saka masa wuri guda biyu ko hudu a jikin kowanne kitso, bashi da zuciyar da zai hanata "Hamma Am" Yelwa ta kira shi tana fadada murmushin ta, tana kallon shi kamar duka duniya bata da wanda yafi mata shi. Shima murmushin yake mata, tilon kanwar shi da zai iya komai dominta "Ina zaki je?" Ya tambaya kamar baiga Saratu tare ita ba, abinda yayi mata ciwo har kasan ranta. Da zata iya da ta dinga share shi irin yanda yake Lubna sufyan Hausabook.com 198 shareta, da tayi watsi da lamurran shi kamar yanda yakeyi da nata. Da ta ganshi taki ganin shi, ta ji shi taki jin shi. Amman ta kasa, idan ta gan shi babu abinda take so irin ya kulata, idan bai kulata ba zata kula shi ko da ba zai amsa ba. Ta taso tana jin labarin soyayyar dake tsakanin Hammadi da Abu, da ta fara hankalin fahimtar wannan soyayyar da bata boyuwa ga kowa sai taji tana son kwatankwacinta tare da Julde. Tana hankali tana kara rage abubuwa da yawa da suke kawo musu rashin jituwa tsakanin su, sai dai yana nuna mata kamar lokaci ya kure. Yanzun fiye da lokuttan baya, yana tsaye a gabanta kamar yau din sai ta dinga jin tamkae idan ta kai hannunta zata iya dangwalo nisan da yake tsakanin su, nisan da kan sata farkawa cikin dare ta kasa komawa bacci. Yanda duk zatayi tunanin aure, tunanin kwana da tashi a gida daya da wani namiji, hoton Julde ne a wannan tunanin. Hoton da girman shi ya hana mata ganin duk wani matashi dake kauyen, wadanda suke son samun dama a wajenta da wanda ma bata gabansu. Lubna sufyan Hausabook.com 199 Wani zare ta hango a gefen wuyan Julde da batasan lokacin da ta mika hannunta da nufin cire masa ba, ta gefen idon shi ya ganta yayi saurin rike hannunta yana saukewa hadi da kallonta, wani irin kallo da yasa tsikar jikinta mikewa tanajin kamar an buge mata gwiwoyinta ta baya saboda sanyin da sukayi. Ya sha kallonta, ba zata iya kirga adadin lokuttan da idanuwansu suka sarke dana juna ba, amman bai tana mata kallon da yake mata ba yanzun. Numfashi yaja ya mayar a hankali yana sakin hannunta, yanajin yanda sakin hannun nata shine karshen abinda yake son yi. Me yasa zatayi kokarin taba shi? Ko dan bata san yanda yake kokawa da kan shi a duk rana ba yanzun na ganin bata shiga cikin jerin matan da yake tabawa ba? Saboda ita ce, saboda tabata zaiyi dai-dai da tonuwar sirrin da yayi shekaru hudu yana binnewa yanzun. Sirrin da babu wanda ya sani "Ba fa zaka bi motar Ikko ba Julde, ba zakayi wannan nisan ba" Lubna sufyan Hausabook.com 200 Datti ya fadi cike da yanayin da yasan bashida wajen musu. Yanzun ana kai musu amfanin gona da dabbobi har garin Kano, nacin daya dinga yi sai da suka hadu shi da Hammadi sannan suka shawo kan Datti ya bar shi ya fara bin motar Kano din, amman ba ko da yaushe ba, saboda in sunje din anayin har sati daya ba'a dawo ba, su kuma duk bayan watanni biyune ake kai musu kayan Kano. A garin Kano, iyakacin su Miltara da Dawanau. Zuwan shi na biyune ya shiga gari yawo shi da wani yaron babbar mota da suka hadu anan Miltara da ake kira da Danjuma. Yace ma Julde shi dan asalin Zamfara ne wani kauye da Julde ba zai tuna sunan shi ba. Almajiranci aka turo shi kauyen Badume, fadi tashi yasa shi fara neman na kanshi harya soma bin motocin dake zuwa kudu, a haka ya zama yaron mota, da suke daukar kayan masarufi daga nan Miltara zuwa Legas da sauran jihohin kudu. Cikin irin wannan hirarrakin da suketa ba Julde mamaki har ya fara bashi labarin kauyen Tafa da yanda sukan yada zango anan idan zasu je Lagos ko garin Lokoja. Anan yaji labaran da tunanin shi bai taba kai shi ba, tare da Danjuma Lubna sufyan Hausabook.com 201 suka soma shiga sabon gari, Danjuma ya rike hannun shi ya hada dana Ladi a cikin sabon gari. Ladi da yake tunanin zai wahala idan bata girmi Daadar shi ba. Sai dai tarin shekarun nan ta ajiye a gefe ta bude masa ido da wata irin rayuwa da ta amsa masa tarin tambayoyin da suka dade suna masa yawo a kai, suna kuma bude masa wani shafin guda na sababbin tambayoyin da ya kosa da yasan amsar su a lokacin. Duka matane kamar Ladi? Ko suna da bambanci? Da duk komawar da zaiyi Kano da yanda yake samun amsar tambayoyin shi. Sai dai kalubalen na tare da yanda yake son Datti yabar shi yabi masu zuwa Ikko, saboda ya leka yaga ya rayuwa a can yake, idanuwan shi su gane masa labaran da Danjuma yake ta bashi. A cikin Marake kawai akwai mutane mabanbanta, haka ma yanda suke gudanar da rayuwar su. Amman idan ka duba akwai kamanceceniya saboda duka kauyen nasu da mutanen ciki bayajin sun kai yawan al'ummar daya gani a sabon gari. Idan kana waje daya babu abinda zaka gani, tun randa ya shiga mota suka hau titi zuciyar shi take gaya masa an haife Lubna sufyan Hausabook.com 202 shi a Marake, ya girma a Marake, amman dawwama a cikin Marake ba nashi bane ba. Saboda idan duk yabar kauyen babu wani abu da yake kewa banda 'yan uwan shi da iyayen shi. Idan zai dauke su subar Marake yana da yakinin ko na rana daya ba zai taba kewar komai daya danganci Marake ba. Sai dai yanzun ba zuwa Ikko bane babban kalubalen shi, yanda zaiyi da sabuwar rayuwar da ya koya. Yanda yake tashi da safe yaji babu abinda yake so daya wuce ya rabi mace. Macen da tafi kusanci dashi itace Saratu. Duk idan ya ganta sai yaji kamar tana kara hura masa wutar da take cine a cikin jikin shi. Shisa ya rage shiga gidansu, amman idan shi bai shiga ba ita tana shigowa nasu gidan. Yana ganin giccinta, ko bai mata magana ba zatayi masa ita, muryarta na fitowa a hankali kamar a tsorace take saboda bata da tabbacin zai amsata ko ba zai amsata ba "Julde" Takan kira wasu lokuttan, dan tun lokacin yarinta yasha buge mata baki akan ta kira sunan shi gatsau kamar shidin sa'anta ne, rashin Lubna sufyan Hausabook.com 203 kunyarta da son ganin ta kular dashine yasa ta cigaba har ta fara sabawa, kafin tace masa Hamma ana daukar lokaci. Idan ta kira sunan shi da wannan muryar sai yaji yana so ta maimaita, yana so yaji ta kara maimaitawa kamar yanda yake jin mata da yawa sun maimaita a lokutta mabanbanta a yanayi iri daya amman cikin muryoyi daban-daban. "Hamma..." Muryar Yelwa ta kutsa cikin tunanin shi "Kuje abinku... Karku dade amman" Kai ta daga masa tana riko hannun Saratu da ta daga ido ta kalli Julde, sai taga kamar launin idanuwan shi sun canza, kamar akwai wani abu a cikin su da ya girmi fahimtar ta. Yelwa da take janta tabi suna nufar hanyar kasuwar. Har lokacin tana jin jikinta a sanyaye, hirar da Yelwa take janta da itace tasa harta dan warware kafin su karasa kasuwar da aketa hada-hada. Da yake sanyi ya fara zuwa ga sabuwar goruba nan da magarya kamar ba'aso "Yelwa kinga magarya" Lubna sufyan Hausabook.com 204 Cewar Saratu don tana so, duk da tana da sauran wadda Datti ya kawo mata, wannan din sai taji ta shigar mata ido "Wai dan Allah dadin me kikeji a abin nan? Nifa na tsani ki shata cikin daki wallahi, duk saiya gume da wari kamar an bude daddawa" Dariya Saratu tayi "Magaryar ce take warin daddawa? Saboda bakya so? To sai na siya" Saratu ta karasa wajen mai magaryar daya bajeta a cikin buhu "Aifa sai kiyita siya. Da rake ma muka karasa mukai cinikin sanda aka yayyanka mana muka tafi gida da yafi wannan magaryar" Saida ta siyi magaryar tukunna ta dago tana duban Yelwa dake tsaye tana ta bata fuska "In dai rake ne mu zagaya a duba me kyau mu siya... Daga shigowar mu harkin fara mu tafi gida kamar bake kika damu da muzo ba" Sake bata fuska Yelwa tayi, ita duk yanda zataji tana son shigowa kasuwa, da ta tako kafarta Lubna sufyan Hausabook.com 205 taga mutane cunkushe sai taji hayaniyar na shigar mata har tsakiyar kai. Bata cika son shiga mutane da yawa haka ba. Baki ta bude da nufin yin magana, abinda bai taba faruwa da ita ba ya faru lokacin da idanuwanta suka gifta ta gefen kan Saratu suna sauka cikin nashi, kalaman ta fara ji sun koma mata cikin makoshi tare da wata irin iska da tasa

Chapter 8 of 27