Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kamar kuma ba daga bakin shi suka fito ba, saboda su duka biyun suna bukatar jinsu, daya taka ya karasa yana zama gefen gadon, sai hawayen da suke yawan kwace ma Julde a cikin kwanakin nan suka sake kwace masa yau, a karon farko, a gaban Nawfal. Sai dai ya zaiyi? Ya zai rage Lubna sufyan Hausabook.com 532 nauyin da yake danne da zuciyar shi? Ba zai boye har abada ba ya sani, amman so yake ya boye, daya fadin nan baiso ya tashi ba, ya sone ace da suka dauke shi, rami ne suka sauke shi a ciki suka bi da kasa yanda ba zai sake motsin da za'ace saiya fuskanci kowanne a cikin su ba. Amman idan fa akace rami, a matsayin shi na musulmi kalma ce mai nauyin gaske, kalma ce da take dauke da tarin ma'anoni, hakan na nufin a binne shi, idan akayi maganar binnewa ko da ba'a cika ka'idojin da musulunci yazo dashi ba kabari bahaushe zai kira inda duk aka zira shi akabi da kasa, kabarin shi, kuma a cikin yan kwanakin nan ya fuskanci tarin zunuban da suke kan shi, ya kuma kara sanin idan shekara dari aka kara masa ba zai taba jin sun isheshi aikata aikin alkhairin da za'a binne shi babu wasi-wasi a zuciyar shi ba, babu taraddadin ko Allah ya karbi tubanshi ko bai karba ba. Idan har tunanin fuskantar yaran shi na razana shi haka, fuskantar su da zunubi kwara daya da yake tunanin shi kadai suka san yayi kokarin aikatawa bai san yanda zai fuskanci Allah a filin qiyama ba, a gaban taron da zai kasance na duk Lubna sufyan Hausabook.com 533 wata halitta da aka taba wanzarwa a duniya, mala'iku, aljanu, mutane da ma halittun da Allah daya halicce sune yabarwa kanshi sanin wanzuwar su. Kunyar duniya ce kawai wannan? A cikin tashi duniyar ma ta mutanen da yasan zasuyi komai don ganin asirin shi ya rufu? Itace kadai ta gigita lissafin shi haka? Ta saka hawayen shi suke ta zuba kamar ba zasu taba tsayawa ba? Saboda a cikin shekaru masu yawa, a karon farko yaji kamar ya dawo cikin hayyacin shi, kamar abinda yake daure dashi ya sake shi tun ranar, da ya bude ido ranar, da baiga kukan da Saratu takeyi ba, da batace masa "Kamar mata sun kare a duniya Julde? Na waje basu isheka ba? Idan sun kare a Kano kana da halin da zaka bisu wajen Kano, baka ga kowa ba, sai ita? Sai Madina? Sai Madina kamar ba daga jikin Yelwa ta fito ba? Zunuban da kake dauka kullum basu isa su binneka ba sai ka kara da nauyin wannan?" Zai iya dauka komai ya faru ne a mafarki, mummunar mafarki da idan akace ya bada Lubna sufyan Hausabook.com 534 abinda ya mallaka duka don ya guje ma faruwar shi a gaske zai mika batare da yayi dogon tunani ba "Baka so ka aureni ba nasani, ka fadamun da bakinka, tun daga ranar dana shiga gidanka zuwa yau, Julde ka shafe kaso mafi girma na ranakun wajen tabbatar mun yanda baka so na, kayi duk wani kokarin ganin ka rabani da kanka na jure, wannan... Ba zan iya ba... Ba zan iya ba Julde, so da aurenka ne kaddarata, da yardar Allah ba zasu zama ajalina ba..." Ta karasa tana saka hannu ta goge hawayenta da kamar ta bawa wasu damar fitowa, jikinta na wata irin kyarma da bata da alaka da zazzabin tashin hankalin da ya lullubeta kamar bargo, dakyar ta iya mikewa, ya riko hannunta, saboda a karon farko a rayuwar shi, a cikin abubuwan daya samu ya kuma rasa, babu guda daya da baya tare da Saratu, akwai mutuwa ya sani, amman ko ita bai taba hasaao zata rabashi da Saratu ba, saboda a wautar tunani irin tashi zai rigata tafiya. Itace abu kwara daya da yake da yakinin babu wani abu da zai faru tabar bangaren shi. Ko akan yaranshi bashi da Lubna sufyan Hausabook.com 535 wannan tabbacin kamar yanda yake dashi akanta. Ba dan yana sonta ba, ba don auren soyayya sukayi ba, amman mutanen duk da yaso din wanda yaba dalili da wanda bai ba wani dalili ba haka suka barshi, suka barshi ita tana tare dashi, shisa yanzun da yaji daga bakinta, ya ga alama a cikin idanuwanta wani irin kadaici mai tare da firgici ya daki duniyar shi yana barazanar ruguza abinda yayi saura "Ke kadaice Saratu, ke kadaice baki taba guduna ba duk dalilin dana baki, karki fara yau, karki fara yau da nake jin na rasa komai, a ciki harda yardar yara na...idan kika tafi shikenan, bani da komai... Da gaske komai zai zo mun karshe tare da tafiyar taki" Ya karasa cikin wata murya da ta sake karya mata zuciya, saita koma ta zauna, yana kallonta tayi kuka kamar ba zata daina ba, tayi kuka har bacci ya dauketa hannun shi yana cikin nata, nashi hawayen basu fara zuba ba sai da duhun dare ya mamaye sauran hasken da yake gari, sai daya rufe idanuwan shi hoton shi tsaye akan Lubna sufyan Hausabook.com 536 Madina da nufin keta duk wata yarda da aminci da ta dauka ta danka masa, tsallake kallon da take yi masa na wanda ya maye gurbin mahaifin da ta rasa ya rusata ta hanyar da ba zata taba komawa dai-dai ba har karshen rayuwarta, sai da wannan hoton ya dawo masa yana saka numfashin sa ya fara yi masa barazana sannan ya tashi zaune. Yaja iska ta kasa kai masa inda ya kamata balle yayi kokarin fito da ita, a tsakanin wannan kokawar da yakeyine hawaye masu dumi suka fara saukar masa kafin wani irin wahalllen gunjin kuka ya kwace masa "Hamma ina son ka, ka sani aiko?" Muryar Yelwa ta zabi ta dawo masa a dai-dai wannan lokacin "Shisa banda wata damuwa Hamma, saboda nasan abinda ba zaka mallaka mun ba, abinda baya karkashin ikonka ne kawai" Ta takan fada duk idan ta nuna tana son wani abu ya samo abin nan ya bata shi, ya sani, Yelwa ta tabbatar masa da haihuwar shi Daada tayi, Lubna sufyan Hausabook.com 537 amman idan aka saka soyayyar su a ma'auni zaiyi wahala wadda take masa batafi ta Daada yawa ba. Me ya same shi da zai kokarin rusa gudan jininta? Ko daya saba tsallake halarcin shi ya rungumi haram da hannayen shi a bude, ya kamata ace akwai haram din da tafi karfin shi, akwai layuka ko a haramcin da bai kamata yayi kokarin tsallakawa ba irin yanda yayi. Sai yake neman ranar da zuciyar shi ta fara haska masa Madina a matsayin mace dan ya koma yasa wuka ya ciro zuciyar ya yarda ita ya huta, amman ranar saita bace masa a cikin sauran ranaku. A cikin ranakun daya shafe awanni yanajin kamar wani abu yana bibiyar rayuwar shi, wani abu da idan ya cimmasa komai zai iya zuwa masa karshe. Ashe da gaskene, gashi nan da komai yazo karshe sai yake danne shi, da Saratu ta tashi ta rike shi ma saita sa wani kukan ya kwace masa, kuka yake kashi-kashi, kuka yake akan abubuwa da yawa, musamman damar daya samu a tare da Datti ya kasa zuwa ya zube a gabanshi ya roki ya yafe masa, ya ianye kalaman shi akan shi, ya roke shi akan gwiwoyin shi Lubna sufyan Hausabook.com 538 komin tsayin kwanakin da zai dauka har saiya yafe masa, saiya fada da bakin shi ya yafe masa sannan. Baiyi haka ba, ya dauka yanda lokaci ya tafi da Datti zai tafi da duk tsinuwar da ya dinga yi masa, zai kuma tafi da tasirin bakin shi yabar holokon kalaman kawai. Ashe suna nan da nauyin su kamar jiya ya furta masa su, kunyar da ya nemar masa yaji ta, ya kunyata a gaban mutanen da suka fi komai muhimmanci a wajen shi, yaji kunyar da yake da tabbacin lokaci kawai ba zai tafi da ita ba "Ka daina boye mana Daddy, ba zai canza komai ba" Cewar Nawfal yana kallon shi, kai Julde ya daga yana saka hannu ya goge hawayen shi. Shi da kanshi Nawfal ba zaice ga asalin abinda suka fada ba, ya dai san Julde ya maimaita masa babu abinda ya faru, kuma ya yarda dashi tun ranar, ya maimaita masa ya yafe masa fiye da yanda ya maimaita masa babu abinda ya farun, ya rasa meya rike masa harshe, meya hana shi yace masa ya yafe masa, ko dan yafiyar ba abu bane da zai faru lokaci daya? Watakila sai a hankali, Lubna sufyan Hausabook.com 539 tare da ciwon yardarsu da ya karya, yanda bai koyi kokarin danne zuciyarshi ya nuna mata abinda take so abune da zai rusa zuciyoyin su duka ba. Yana kallon shi ya sauka daga kan gadon ya bude wardrobe din shi, a ciki ya janyo wata jaka, a cikin jakar ma alamun shi sun nuna akwai abubuwa da yawa daya bude kafin ya dauko takardar da take hannun Nawfal din yanajin nauyinta a duka jikin shi, ya damka masa ita. Numfashi yaja yana fitar da iskar ta bakin shi, jikin shi na rawa ya bude takardar, yana tsintar kanshi da saka dayan hannun shi ya shafi rubutun, kafin ya rike da duka hannuwan shi biyu kamar yana rike da hannayen Bukar da suka bace a cikin tunanin shi, tayi kama da wasika, sai dai wasikar duniya duka daya sani, da wadda aka koya musu a farko babu wadda ta fara da sunan marubucin ta kamar yanda wannan ta fara dashi: Bukar, Abubuwan da zan fada ji nakeyi sunfi karfin littafi balle in tattara jimilarsu a yar takarda Lubna sufyan Hausabook.com 540 guda daya, banda tabbacin mutum daya da nake son rubutun nan domin, idan nace abinda na haifa dole in naqalta jinsi a tare dashi, sai dai hakan ba zai yiwu ba, 'yata zance ko 'dana tunda ban kai da ganin su ba. Ina rubutun nan ne saboda zuciyata na rawa akan abubuwa da yawa, ciki harda rashin tabbacin zanyi tsayin ran da zanga abinda yake cikin matata. Cikakken sunana Bukar Baabuga, dan asalin kauyen Marake, da ga Dije matar Julde, idan kaje Marake duka ka tambayi Julden Hammadi ba za'a rasa wanda suka sanshi ba, idan kuka same shi zaku samo mahaifiyata, zaku gano Daada. Na biyo Hamma na da sunan karatu, sai dai dalili yasa ban tsaya makarantar da yayi ba, yanzun nake fahimtar a cikin dalilin nan harda kaddarar haduwa da Kaltume, saboda mahaifinta ya zabeni satika biyu da zuwana Borno a cikin tarin almajiran da suke karkashin Malamin mu, da fadin ya yarda da natsuwata, ya aminta da cancantata daya daga cikin yaran gidan shi. Mahaifin Kaltume bai rikeni a dan aikaceaikacen gidan shi kawai ba, haduwata dashi Lubna sufyan Hausabook.com 541 saita kara inganta rayuwata, sai yake jana har wajen kasuwancin shi, a hankali saina fahimci babu shiri a tsakanin shi da 'yan uwan shi duk kuwa kasancewar kowannen su karkashin kulawar shi, cikin ni'imar tarin dukiyar da Allah ya azurta shi da ita, yau da gobe na san cewa mahaifi suka hada, shi kadai mahaifiyar shi ta haifa kafin rasuwarta, mai rabon ganin badin da ake fada ce ta kasance akan shi, sai kuma Allah ya ware shi a cikinsu ya azurta. Akan dukiya, shine karona na farko da nagani ba naji labari ba, 'yan uwa na neman rayuwar dan uwansu, rayuwarshi suke nema amman ni da nake kusa dashi, da lokaci ya koyawa kaunar shi ni nakejin tsoro. Yanda yake shi kadai a wajen mahaifiyar shi, haka Kaltume take ita kadai a wajen shi. Naje marake, na dawo na samu rasuwar matarshi mahaifiyar Kaltume, na same shi yana wani ciwo da rayuwa ba'a hannuna take ba amman zuciyata na fadamun ba zai tashi ba, a cikin ciwon ya danka amanar Kaltume a hannu na, a cikin ciwon ya bukaci bayason kasa ta rufe idanuwan shi ban amshi aurenta ba. Daga ni har ita an daura mana aure Lubna sufyan Hausabook.com 542 bayan na rana daya bamu taba hango kasancewa karkashin inuwa daya a matsayin mata da miji ba Ba Kaltume kawai ya dankamun amana ba, harda dukiyarta da tashi ce, saiya rasu, kasar dai ta rufe idanuwan shi yana barina da Kaltume, yana barmun nauyin zame mata abubuwa biyu masu muhimmanci da ta rasa, ya bar mata gadon arzikin shi, ya barmun na kiyayyar 'yan uwanshi da gari ya dauki zargin da sa hannun shi a jinyar da ta zama ajalinsu shi da matar shi, ni da Kaltume munyi ciwo, munyi jinya kala-kala muna tashi, kamar yanda ta roka, nayi yunkuri, nayi duk wani kokari na mubar Borno zuwa Marake sai wani abu ya danne ni, sai in kasa. Haka kawai nakejin kamar cikin jikinta ba zanyi tsayin kwanan ganin shi ba. Baya takardar Nawfal ya juya, babu cigaba, baisan abinda yake ji ba, ya mike tsaye, ya koma ya zauna, kafin ya murza takardar saboda yaji alamar kamar guda biyu ce, sai ga dayar ta fito, yana rike da numfashin shi ya soma bin wasikar Lubna sufyan Hausabook.com 543 Bukar, Da gaske babu abinda addu'a ta bari, a ciki harda yau da muka hada kayan mu duka, bayan shekara hudu, yau mun hada kayan mu tsaf da nufin barin Borno babu wanda ya fita daga hayyacin shi, tun azahar, ga dare na neman rabawa, amman daga zuciyata nake jin zamu iya barin Borno a safiyar gobe da yardar Allah, babu abinda zai faru, zamuyi nisa da kowa da komai, zamuyi nisa dasu. Wannan karin har dayar takardar Nawfal ya dauko ya sake murzawa, ya zazzaga amman babu komai, su biyun ne kawai. Bayan Bukar, suna daya kawai ya karu, sunan mahaifiyar da ko a tunanin shi ba zai iya tunata ba, Kaltume, ya dauka takardar dauke take da wasu sirrika, wasu bayanai da zasu amsa masa tarin tambayoyin da yake dasu bawai su sake jefa shi cikin sabon rudani ba Kwanaki biyu kenan, da Nawfal ya same shi ya mika masa wasu takardu guda biyu, kamar yaki karba, kamar ya cewa Nawfal din ya fara fada Lubna sufyan Hausabook.com 544 masa abinda yake cikin takardun kafin ya karba, sai yayi karfin halin mika hannu ya amsa, ya bude ya karanta, nauyin abinda yake ciki na kara danne shi tare da sauran abubuwan da yake fama dasu a cikin kwanakin nan "Ba zakaje Borno ba, ka sani ai ko?" Ya fadi yana daga ido ya kalli Nawfal din "Idan tunanin da yake cikin kanka kenan ka fitar dashi, ba zakaje Borno ba. Waya baka wannan ma?" Kafadu Nawfal din ya dan daga masa batare da yace komai ba, kamar babu muhimmanci a sanin wanda ya bashi, tunda dai ya rigada ya gani "Bajjo ba wasa nakeyi ba" Ya fadi yanajin wani abu yayi masa tsaye a waya da yanayin kallon da Nawfal yake yi masa "Idan naje Borno ta ina zan fara? Ko ina so inje bansan ta inda zan fara ba Hamma, ni Marake zanje...zamuje da Hamma Khalid...kace zakaji da Madina, mu zamuje Marake" Lubna sufyan Hausabook.com 545 Numfashi ya sauke yana jinjina ma Nawfal din kai, takardun ya karba daga hannun Salim yana juyawa batare da ya sake cewa komai ba, shima Salim din ya bude baki amman sai ya rasa abinda zaice, ya karbi duk lambobin wayar da yake bukata. Ya kuma gama shirin duk da zaiyi, asibiti ya samu wanda baiji a muryarsu sun nuna alamun ya takura su ba daya bukaci su karbar masa shift din shi, tunda ya sha yi musu nasu na dare babu adadi. Idan komai ya tafar masa yanda yake so, kwana daya ya tsara yi a garin Abuja. Duk da bai daga burin shi akan komai ya tafi yanda ya tsara ba, dan jikin shi ya gama yin sanyi da yanayin rayuwa yanzun. Sai yasha mamaki, yanda komai yazo masa da sauki, saiya kara mamaki akan wani mamakin lokacin da idanuwan shi suka sauka akan Kabiru, kafafuwan shi suka soma yi masa barazanar kasa daukar sauran gangar jikin shi, da gaske ne, ana kama, har zakaji wasu na cewa "Ai kuwa idan wane ya bace to tabbas 'yan uwan shi da dangin shi duka ba zasu taba yarda ba kai bane ko kece, saboda yanda kukayi kama" Lubna sufyan Hausabook.com 546 Shima wajen mutum nawa ya fada masa ya taba ganin me kama dashi, amman mutumin da yake tsaye a gabanshi, ko yayi rantsuwa ba zaiyi kaffara ba jinin Madina ne, da yayi murmushi sai Salim yaji zuciyarshi ta doka "Kullum ina duba hanya, a cikin fuskoki da yawa ina neman wanda zaiyi shige dana Yelwa ko zan rike shi in tambayi labarin 'yan uwanta, in samu in hadata da ahalin dana rabata dasu, yaro nazo nan cike da taraddadi, nazo nan da zuciyata a tafin hannu na saboda bansan abinda zan gani ba. Bayan shekaru masu yawa, a tsakanin haduwa da fulani kala-kala, yau naga fuslar Yelwa a cikin taka" Salim ya bude bakin shi, labbanshi sun motsa,amman muryar shi bata karasa cikin kunnuwan shi ba, bai san meya tambaya ba sai da yaji amsar Kabiru "Neman wanda ya daura mana aure ne abu na farko da muka fara yi da Yelwa bayan motar data dauke mu daga Marake ta sauke mu" Kabir ya karasa maganar da wani kyalli da Salim din ba zai iya fassarawa ba kai tsaye a Lubna sufyan Hausabook.com 547 cikin idanuwan shi, kyallin yana masa kama da dana sani, yana masa kama da shekaru cikin wani ciwo na zuciya da babu wanda zai fahimta, yana kuma yi masa kama da firgici, kwatankwacin wanda ya dandana a 'yan kwanakin nan. Yayi tunani kala-kala, akan abinda ya tambaya, amman ya kasa tunawa. Ya dai san amsar Kabiru ta saukaka masa wani abu daya jima kulle da zuciyar shi, ya sauke numfashin da baisan yana rike dashi ba tun randa ya karanta wasikar Yelwa a hannun Madina. "Za muzo, zan dauko ta muzo" Shine kalman karshe da suka hadashi da Kabiru, suna masa yawo a cikin kanshi ya koma Kano, suna masa yawo har kwanaki uku da yayi amfani dasu wajen binne kanshi da aiki a asibiti dan ya janye hankalin shi daga kiran Kabiru, ya kuma ji dadi da Madina ma duk wayar da sukayi bata daga masa maganar ba. A safiyar kwana na ukun ne da yake jin hakurin shi yana gab da karewa Kabiru ya kirashi ya fada masa suna hanya, bai tambayi daga inda zasu taho ba, ya Lubna sufyan Hausabook.com 548 dai cire farar rigar jikin shi, ya kuma dauki mukullin motar shi ya fita daga asibitin "Kaci abinci Hamma" Sakon Madina ya shiga wayar shi lokacin daya fita daga asibitin, ta saba tuna masa yaci abinci saboda tasan in dai yana aiki saiya wuni da yunwa. Yau yana da karfin cin abincin, duka a kwanakin nan zai amsata ne, amman saiya saka abincin a gabanshi yaji ko kadan bayaso ya kai shi baki, idan ya tura abinda zai iya yanayin hakan ne don jikinshi yana bukatar abincin, amman baya gane dandanon ko kadan. Sai ya rasa abinda zai siya, bayason shiga bangaren Saratu, har yanzun bai shirya ganinta ba, balle kuma abinda zai hadashi hanya daya da ganin Julde. Yana cikin wannan tunanin ne yaji alamun kira ya shigo wayar shi "Adee" Ya fada bayan ya daga ya saka wayar a kunnen shi "Ka manta kana da kanwa ne Hamma?" Sai murmushi ya kwace masa Lubna sufyan Hausabook.com 549 "Yanzun na fito daga asibiti, abinda zanci nake nema Adee" Ya furta a madadin amsa korafinta "Fanke zan soya ni, ka biyo ka karba mana to, ina da Zobo da kunun aya a fridge, jiya nayi, in kuma da tea zaka hada to" Numfashi ya sauke "Yanzun sai nazo har unguwarku saboda fanke Adee?" Yanajin dariyarta "To me kake so sai in dafa maka? Kaji? Dan Allah kazo, kaga rannan da naje gida baka nan, banganka ba" Sai da yayi kamar ba zai amsa ba, saboda tunanin da yakeyi, yana hango tsayin tafiyar da zai hada shi da gidan Adee daga inda yake "Bari in karbi fanken" Bai amsa surutun da takeyi ba ya kashe wayar. Ya danyi fama da cunkoso daya juya dayan hannun, tunda ranar aikice, ga kuma yan Lubna sufyan Hausabook.com 550 kasuwa da sauran al'umma da suka fito dan gudanar da uzurin ranar. Sai yaga komai ya kara kala a idanuwan shi yau, har iskar da yadan bude gilashin motar tana shigo masa jinta yakeyi daban, kamar duk wani abu da zaici karo dashi yau ya san girman abinda yake shirin faruwa dasu. Da wannan yanayin ya karasa gidan Adee, yanda duk tayi dashi ya shiga ciki yakiya, motar shima a bakin kofa yayi parking dinta bayan ya juyata hannun da zai fitar dashi daga unguwar "Hamma wannan ba zuwa kayi kaganni ba" Cewar Adee data fito jikinta sanye da hijab, tayi masa kyau, alamar akwai kwanciyar hankali a tattare da ita, hakan kuma yayi masa dadi, duk gidansu idan akwai wanda ya cancanci ya samu natsuwa fiye da kowa to Adee ce, saboda nagartattun halayen da take dashi "Baka fadamun zobo zaka sha ba ko kunun aya, na dai saka maka duka biyun" Karbar kwandon da ta mika masa yayi yana ajiyewa kan kujera a cikin motar Lubna sufyan Hausabook.com 551 "Naganki, kinganni nima ina lafiya. Ki gaishe da mijin ki" Ya karasa yana murza mukullin motar "Hamma..." Ta kira da sauri, sai ya daga ido ya kalleta, duk ta daburce lokaci daya, kashe motar ya sakeyi yana kiran sunanta "Adee" Numfashi taja ta fitar "Da naje gida, akwai abinda ya faru ko? Na tambayi Nanna tace bakomai banda Daddy da bayajin dadi kuma shima jikin da sauki, naga da sauki, har hira munyi... Daga Bajjo har Khalid sunce mun bakomai" Sosai ya kalleta wannan karin yana ganin sauran kalaman da bata furta ba kwance akan fuskarta "Akwai abinda ya faru, ki yarda dani rashin saninki yafi muhimmanci" Lubna sufyan Hausabook.com 552 Ta dauki wasu dakika, har saida ya fara tunanin musu ne abinda zai fito daga bakinta sannan tace "Abinda ya farun? Ya wuce? Komai ya koma daidai?" Kai ya girgiza mata "Amman babu abinda lokaci baya tafiya dashi right?" Murmushi tayi tana dan daga masa kai "Zamuyi waya" Kan dai ta sake daga masa, sai kuma hannunta bayan ya rigada yaja motar, ta mudubi ya hangota tana tsaye har lokacin. Babu ma'aunin da zai iya daukar girman son da yake yiwa Adee. Tun suna yara yakejin duk wani abu kafin ya sameta zai fara wucewa ne ta cikin shi, saboda ko menene zai same shi tsaye a gabanta, yana bata duk wata kariya da take karkashin ikon shi. Waje ya samu yayi parking, ya saka ruwa ya wanke hannun shi ta murfin motar, sannan ya bude robar fanken, harda soyayyen nama ta zuba masa. Yayi mamakin yanda ya kusa cinye, Lubna sufyan Hausabook.com 553 dakyar ya rage guda hudu, yanka nama biyu. Gida ya wuce ya watsa ruwa ya sake kaya, yadine ya saka bula, Nawfal ne ya sai musu, duk wani kaya da yake dasu masu kalar yawanci kyautar Nawfal ce, kamar a duniya babu wata kala da idanuwan shi suke gani sai ruwan sararin samaniya. Saiya wuce gidan Daada, kamar kullum a bakin kofa ya tsaya ya kira Madina, ta fito, sai da ta zauna cikin motar tana hamma kamar bacci bai isheta ba sannan ya kula da wani takalmi mai kaza da ta sakama kafafuwanta, irin mai gashin nan, murmushi ya kwace masa "Ina kwana" Ta furta kowacce kalma a tsakanin Hammar da takeyi, tana mika hannu cikin kwandon da dauke kafin ta zauna, ta kuma ajiye shi akan cinyarta "Menene wannan? Ina ka samu zobo mai sanyi da safen nan?" Yana kallo ta dauki roba daya tana juyawa, data kwance ta kurba Lubna sufyan Hausabook.com 554 "Adda ta baka?" Ware idanuwa yayi cikin mamaki "Kasan zobon Adda fa ba irin shi a garin nan, dana sha saina gane nata ne, nace ta koyamun dame-dame take sakawa, nayi amman sai naji bai dai kai nata ba..." Komai nata, komai na Madina yayi masa, harda surutun ta "Fanke? Ya naga guda hudu?" Ta karasa tana bude robar ta dauko guda daya "Rage miki nayi" Ya furta yana jingina jikin shi sosai da kujerar motar ya juyar da kai yana kallonta, yanda da yaganta duk wata gajiya da yake ji, wadda ya sani da wadda bai sani ba take danne shi yana bashi mamaki, ko bacci yakeji daya ganta saiya karu, saboda yana so yayi baccin a kusa da ita, yanajin kamar duk wani hutu nashi yana jingine ne da ita "Kwara hudu Hamma?" Lubna sufyan Hausabook.com 555 Ta fadi tana dariya "Yayi dadi, dakyar na rage" Dariya takeyi sosai, ya kuwa yi mata dadin, suna da sauran shinkafa da miyar data dafa da daddare, shine ta dumama musu da safen saita dafa ruwan shayi tunda daga ita sai Daada a gidan, Murjanatu bata nan, bata tambayi inda taje ba tun jiya saboda abubuwan da take tunani sunyi mata yawan da bata da wajen kananun tambayoyi irin wannan. "Hamma karkayi bacci a motar nan, ka fito mu shiga ciki ka kwanta a kujera, Daada ma bacci ta koma" Madina ta fadi tana saka shi makale mata kafada, idan cikim gidan ya shiga, ba zaiji ta a kusa dashi haka ba, tana ma iya bar masa falon da taga yayi bacci, shisa ya sake langabewa cikin kujerar, yace yana sonta, ya fada mata yana tabbatar da taga duk wani waje da son nata ya taba a tare dashi, batace komai ba, ta kalle shi, kamar ta fahimta haka ta kalle shi "Mug..." Lubna sufyan Hausabook.com 556 Ya kira can kasan makoshi, sai da ta gyara gilashin fuskarta sannan ta kalle shi "Bakya so na?" Tambayar ta fito daga bakin shi tana dukanta, saboda batayi tsammaninta ba, daga wajen wani ma balle kuma shi, ya zai dora ayar tambaya akan son da takeyi masa bayan yana daya daga kalilan din mazan da suke cikin rayuwarta? Kuma kamar tunda suka hada jini bata da wani zabi akan son shi. Kafin kusanci ya gifta musu tana son shi saboda jinin shi da yake yawo a jikinta, da tasan wanene shi sai ya tabbatar mata ko basu hada jini ba zata so shi. Amman a kalmar so na karshe daya furta mata sai taga kamar yasha bamban da wanda take tunani, a kallon da yakeyi mata yanzun sai yake tabbatar da inda tunaninta yaje anan nashi yake zaune "Bakya sona" Wannan karin ya furta cikin son tabbatar ma kanshi, saita tsinci kanta da sauran girgiza masa kai, kaifin kallon shi na ratsawa ta cikin kirjinta Lubna sufyan Hausabook.com 557 zuwa zuciyarta, kawai dai kamar bata shirya ba take ji, ta bude baki batare da tasan amsar da tayi niyyar bashi ba, karar wayar shi ta katse musu yanayin, daya duba sai taga yanayin shi ya canza "Bari yanzun zan dawo" Ya furta idanuwan shi na kan wayar da bai daga ba, dakyar ya rabasu da wayar yana kallonta, kai ta dan daga masa tana daukar kwandon da yake kan cinyarta, yanda jikinta yake a sanyaye sai taji dakyar ta iya fita daga motar, kafin tayi wani yunkuri ya mika hannu ya rufe murfin yaja motar yabar wajen. Cikin gida ta koma, da kwandon a hannunta, saita wuce dashi kitchen, ta dauki robobin da suka rage ta saka a fridge, harda zobon data fara sha, sai sauran fanken da guda biyu taci, ta dauko robar tana fitowa falon, suka ci karo da Daada a tsakiyar falon inda take neman zama kan kafet "Wai Daada laifin me kujera tayi miki?" Madina data zauna kusa da ita a kasa ta fadi "Ke da batayiwa laifi ba me kike a kusa dani?" Lubna sufyan Hausabook.com 558 Dariya tayi tana mika mata robar fanken "Adda ce ta ba Hamma, ci kiji Daada, yayi dadi sosai, inajin gobe idan Allah ya kaimu shi zanyi mana" Murmushi Daada tayi tana daukar guda daya "Lallai

Chapter 21 of 27