Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kadan, taya zata tattara abinda ya faru a kwanakin nan, ta takaita shi harta sanar da Julde? "Babu wata matsala" Shine amsar da takan bashi duk idan ya tambaya, saboda babu, matsalar ba irin wadda yake tunani bace ba. Kuma da yanda yake nuna akwai uzururruka a gabanshi sai ta zabi barin shi ya tafi don korar wannan uzurin da yake Lubna sufyan Hausabook.com 394 gabansa. Ba sai da matsala ba, wasu rabakun labari ne iyaye zasu so su baka, abinda ya faru dasu na farin ciki, abinda ya faru dasu mai muhimmanci da akasin hakan, wani abu daban wanda daga kai harsu dinma baku da alaka dashi. Babu kalar labaran da baka basu ba, suka saurara, badon basu da abinda yafi labaran naka muhimmanci ba a lokacin kuruciya, sai don soyayyarka data danne komai. A yayin girmansu, reshen ne yake juyewa, sune suke bukatar wannan kulawar ko da bata kai rabin wadda suka bayar ba. Duk halin ko in kula da Datti yake nunawa akan Julde abin yana damun shi, yana ci masa rai fiye da yanda zai iya misaltawa. Dije tace kuskuren nasu ne, nashi kason yafi na kowa, daga ranar har zuwa yanzun akwai wani bangare na zuciyar shi da kalamanta suka zauna suke nukurkusa. Ta saka shi maimaitawa kanshi tambayoyi da dama. Akan Yelwa, a batunta da Kabiru, a zancen aurenta da Modibbo. Baya son amsa ko daya da yake samu, saboda duka suna kamanceceniya da juna, idan aka dunkule ma'anarsu zata zagaya ta dawo kan yanda komai yake laifin shi. Lubna sufyan Hausabook.com 395 Amman akan Julde fa? A ina ya kuskure? A gadarar da yakeyi ta yafi karfin ya haifi mazinaci? Yafi karfin dauda irin ta zina ta rabi ahalin shi? Ko aibata iyaye tare da yaran da suka tsinci kansu cikin irin halin da yake yanzun? Shi kam yayi kuskure, Dije ta fada masa yayi kuskure, sauran iyayen yaran fa? Kuskuren sukayi suma? Ko kuwa kaddarar da yake ganin kamar katin gayyata ake bawa marar kyauce ta yi musu ziyarar gayyar sodi? Me yake faruwa? Duk da ba ilimi gare shi ba, a kasan zuciyar shi yasan wasu tambayoyin ko karen hauka ya cije shi huhun shi ba zai busama sautin shi iskar da zasu rabo kirjin shi zuwa makoshin shi har harshen shi ya furta su a matsayin sauti ba. Saboda hakan zaiyi dai-dai da fitar dashi daga musulunci. Sai dai shin duk wannan laifin nashi bai cancanci Julde ya sake bashi hakuri ba? Ya nemi yafiyar shi tare da kokarin gyara alakarsu ba? Idan ya gaishe dashi ya dauke kai shikenan? Bai isa ya sake bashi hakuri ba, bacin rai da karyewar zuciyar daya ja masa. Ko kuma bai ga shi kadai ya rage masa bane? Duk da kullum sai zuciyar shi ta tabbatar masa da cewa duk inda Lubna sufyan Hausabook.com 396 Yelwa take tana da rai, babu yanda za'ayi ace baiji a jikin shi ba idan har ya rasa ta. "Idan Yelwa ta rasu a wani wajen fa? Idan hakuri ya kamata mu ba zukatan mu a maimakon duban hanya fa? Ya zamuyi?" Dije ta tambaye shi wani dare suna kwance, hannunta ya laluba ya damtse a cikin nashi "Su biyu ne dani, su kadai suka rage mun a fadin duniya kaf da zan kalla in kira nawa Dije... Babu yanda za'ayi in rasa Yelwa jikina bai bani ba, zata dawo" Gyara kwanciya tayi, hannun shi da ta kara dumtsewa cikin natane kawai shaidar daya samu cewar taji abinda ya fada, sai kuma yanayin numfashinta da alamar kuka takeyi. Amman batace komai ba. Har bacci ya dauketa tana barin shi da juyayin tambayarta. Shisa wata asabar din daya tashi ya kwana da zazzabi, ya sake jera hakan har talata Dije tace masa "Ba zan aikama Julde sako ba kuwa yazo ya daukeka zuwa asibiti?" Lubna sufyan Hausabook.com 397 Kai ya girgiza mata, baya so ya furta, baya so ya fada mata yanda yake jin kamar yana gab da cike iya kwanakin da aka dibar masa zaiyi a duniya. Ya sha jin karshen duniyar yazo masa, akwai dararen daya kwanta yayi mamakin bude idanuwan shi da safe, saboda bai kwanta da sa ran zai tashi ba. Yayi rashin lafiya da tafi wannan zafi, amman yanajin wani sanyi cikin kasusuwan shi duk da zafin zazzabin da yake jikin shi. Sannan koya ya mike sai yaga garin yana jujjuya masa. Ga shi larabar daya kwanta, alhamis saiya tashi harda ciwon kai. Abinda duk yaci a yinin ranar saiya dawo. Yanayin daya daga hankalin Dije ba kadan ba. Da yammaci likis, yayi kokarin tashi zaune, bayan ya gama jin yanda take jaddada masa Julde na zuwa juma'ar asibiti za'a kai shi ko ya amince ko bai amince ba, tunda har kayan sirace an samo tayi masa zazzabin bai sauka ba. Baiyi kokarin musa mata ba, saboda yanaji a jikin shi bama zai kai juma'ar da take kira ba, duk kuwa da tsakanin su da juma'ar awanni ne ya rage da za'a iya kirgawa da yatsun hannu, musu da ita bashi da wani amfani. Kallonta dai yakeyi, kallo Lubna sufyan Hausabook.com 398 cikin sigar daya dauki wasu shekaru baiyi mata irin shi ba, kallonta yakeyi yanajin kwanakin da ya rage a tsakanin su, sai yakejin son rike ko da hannunta ne, ya kara bar mata abubuwan da zata tuna shi dasu. "Idan ba Dije ba, babu wanda zai iya zama da kai Datti" Ya tuna zancen Hammadi a yau, yana ganin gaskiyar da ya kasa gani a wancen lokacin. Dije, matar shi, amanar shi, uwar yaran shi. Yaran da halin shi ya raba shi dasu amman Dije tana nan tare dashi, kamar yaran ba daga jikinta suka fito ba. Dije da take shanye duk wani mugun halin shi "Dije..." Ya tsinci kanshi da kiran sunata, saita dago kai ta saka idanuwanta cikin nashi "Hamma ya sha fadamun idan bake ba babu macen da zata iya hakurin zama dani, da gaske ne, da ban gani ba, amman yanzun na sani. Ban taba miki godiya ba ko?" Lubna sufyan Hausabook.com 399 Wani abu ya canza a cikin idanuwanta, ya hangi fargaba da tsoro a cikin su, amman saiya dake "Nagode, nagode da yanda kika dinga hakuri dani duk shekarun nan, duk da halayena sun kawo mu inda muke yanzun... Idan nace ki yafe mun duk abinda nayi miki naso kaina da yawa ko?" Hawayene cike da idanuwanta wannan karin "Bana jin kinmun wani abu da na rike ki dashi a iya zaman mu, amman idan kinyi mun din, ko menene na yafe miki" Hawayenta ne ya zubo "Kaga kukana kashi-kashi Datti, bai isa ba saika kara sakani wani yau? Waye yace kamun wani abu dana rike ka? Ka daina maganganun nan kamar kana mun bankwana, kayi ciwo da yafi wannan kuma ka tashi, da wa zaka barni ma to in ka tafi? Ko dai dabara ce aure zaka kara kake son karya mun zuciya da batun mutuwa?" Dariya yayi, dariyar daya kwana biyu baiyi ba, dariyar da sautinta bai gama karade zuciyarta har tayi dogon nazari kan ranar karshe da taji Lubna sufyan Hausabook.com 400 dariyar shi haka ba, muryar da ko da Datti bai yanke kauna da sake jinta ba, ita kam Dije ta dauki wannan hanyar tayi musu kutse cikin tunanin su tana girgiza duk wani bango na ruhinsu "Baba..." Yelwa ta kira muryarta na rawa, idanuwanta tsaye akan shi, shima ita yake kallo. Yelwa ce, yar shi, tilon yar shi da duhu da kuma ramar da tayi bata boye kyawun fuskarta ba. Yar shi ce da yake da yakinin ko fuska aka canza mata zai ganeta. Sosai yake kallonta, atamfa ce a jikinta da wata hijabi da asalin kalarta ya kode kamar hijabin jikinta. Daga duk inda ta fito rayuwa ta tara mata gajiyar wasan cikar shekara. Karasawa tayi, yanajin sautin takunta a cikin zuciyar shi kamar tambari. Hannunta ta mika da Datti baiko yi tunani ba ya kama, ta lumshe idanuwanta, wasu siraran hawaye na zubo mata, ta bude idanuwanta akan Dije da batama san hawaye takeyi ba "Daada... Daada Am" Lubna sufyan Hausabook.com 401 Yelwa tayi maganar cikin karyewar murya kuma a wahalce, har lokacin hannunta na cikin na Datti. Sai da tayi kokarin zama, yanayin yanda take yin hakan da dabara, tukunna daga Dije har Datti suka sake kallonta, kallo fiye da na mamakin ganinta, kallo daya wuce canjin da fuskarta tayi, sutturar jikinta da kuma tarin tambayoyin da suke yawo a kawunan su, kallo na son gane dalilin da yasa take dabara wajen zama. Kusan a lokaci daya sakon abinda idanuwan su ya gani ya karasa har cikin kansu yana saukowa zuwa zuciyoyin su. Ciki ne a jikin Yelwa, ciki tsoho, idan Dije bata kuskure ba, yanayin yanda cikin ya dunkule waje daya ya kuma yo kasa, ko yanzun ciwon nakuda ya kama Yelwa babu wanda zaiyi mamaki, saboda ko meye a cikinta gab yake da fitowa duniya. Babu jaka ko daya a hannunta, sai yar karamar leda mai layi layi da take sakale a tsintsiyar hannunta, har bayan zamanta kuma batayi kokarin ciro ledar ba balle ta ajiye. Numfashi dai take ta kokarin saukewa kamar zaman ma aikine. Ta kuma kara matsawa yanda zata iya Lubna sufyan Hausabook.com 402 dora kanta a kafadar Daada tana wani irin sauke ajiyar zuciya. "Nayi kuskure Daada... Nayi kuskure mafi girma a rayuwata" Ta tsinci kanta da furtawa wasu sababbin hawayen na saukar mata. Sai dai an rasa wanda zai fara korar shirun daya biyo bayan maganarta a tsakanin su. Sai kiran sallar Magriba daya karade gidan. Har aka dire babu wanda ya yunkura, sai da Daada taji alamar an kira sallar tukunna ta iya samun karfin mikewa. Ita tayi alwala, roba da buta ta kawo ma Datti da bashi da karfin tashi har inda yake. Yelwa ce ta karba, ita ta dinga zuba masa ruwan yana alwalar. Shi yaba Dije damar shiga daki ta dauko wata tabarmar ta shimfida harta tayar da sallah, yelwar ma inda Datti yayi alwala tayi tata. Daga zaune ya gabatar da tashi sallar saboda yana kara jin sanyin nan ya kara lullube kasusuwan shi, sai yaga kamar daya idar zai iya farkawa daga mafarkin da yakeyi na dawowar Yelwa. Kamar zai ga komai ba gaskiya bane ba, da idanuwa Datti yake rokon Dije ta rike Lubna sufyan Hausabook.com 403 tambayoyinta, shima yana da tarin su, ta dan basu lokaci zuciyar su ta gama gamsuwa da cewa Yelwa ce a cikin gidan, Yelwa ce a tare dasu, kafin wani abu ya sake biyo baya. Suna zaune shiru kowa da magana a bakin shi amman yana tsoron ya zamana wanda ya fara korar shirun. A haka isha'i ta same su suka kuma gabatar da ita. "Ki zuba mana abinci muci" Datti yayi maganar, Dije batayi musu ba, a waje daya ta hado musu abinci, su duka sunayin kamar basu kula da duk lomar da Yelwa zata kai bakinta sai ta kai dayan hannunta ta share hawayen da suka zubo mata ba. Hawayen da Datti yakejin zafin su har a zuciyar shi, ko dandanon abincin baya ganewa, hakama Dije, sun kasa cire hannaye ne saboda Yelwa, sai da ta fara cirewa tukunna. Suka wanke hannuwa suka sha ruwa. Jin da Yelwa tayi bayanta ya amsa yasa ta kiran sunan Allah "Lafiya? Me ya faru? Baki da lafiya ne?" Datti ya riga Dije tambaya. Maimakon amsa wani irin kuka ne ya sake kwacewa Yelwa, Lubna sufyan Hausabook.com 404 kamar ta kwana biyu bata ji wani ya damu da al'amarinta ba balle ya tambayeta me yake faruwa da ita "Ba ku tambayeni daga inda nake ba har yanzun Baba... Daada baku tambayeni ba" Kauda kai gefe Dije tayi kamar hakan zai hana hawayen dake idanuwanta zubowa "Ki huta Yelwa... Gobe duk sai muyi wannan maganar... Ki huta yau, kije ki kwanta" Kai Yelwa ta girgiza tana sake matsawa kusa da Datti, kamar duk abinda zai sake rabata da shi ba karamin shiri zaizo dashi ba kafin hakan ya faru, gefen hijabinta ta saka tana goge fuskarta, amman hawayenta sunki daina zuba. Shirun da yake cikin gidan zai zaka iya tattara shi ka rufe jikinka "Da alamar hadari a garin nan, mu koma daki kar ruwa ya sauko" Dije ta fadi tana mikewa, hannun Datti ta kama ta taimaka masa ya tashi tana kaishi har daki, ta dawo ta mikama Yelwa da take kokarin tashi itama hannu, bata ki ba, ta bari Dije ta taimaka Lubna sufyan Hausabook.com 405 mata ta mike, bata jira Dijen ba ta shiga dakin da Datti ya shiga, a kasa ta zauna gefen gadon da yake kai tana jingina kanta a jiki, wasu sababbin hawayen na zubo mata. Dije sai da ta gama kayekayen da takeyi a tsakar gida saboda hadarin kara haduwa yakeyi, taurari duk sun bace a cikin shi. Ga iska na kadawa alamar kowanne lokaci ruwa zai iya saukowa sannan ta shiga dakin. Shimfidar da tayiwa Datti ita ta samu waje ta sakeyi a kasa ta kwanta, wata irin gajiya takeji tana saukar mata, yawon da tunani da ruhinta sukeyi ne tun batan Yelwa suka samu tsayawa yanzun da suka sake kasancewa karkashin rufi daya. Wata irin gajiya ce da bata da kalaman da zatayi bayaninta balle ta iya fahimtar da wani. A tsakanin yawon da tambayoyi suke mata cikin kai wani irin bacci mai nauyin gaske ya dauketa Baccin da bata san tashi daga shi zaiyi dai-dai da tarar da duniyarta a birkice ba Da tayi yaki dashi bata bari yayi galaba akanta ba Lubna sufyan Hausabook.com 406 Ba don wani ya fada mata cewar don an haifeta a marake, ta girma, tayi aure anan zata kare sauran ranakun ta a cikin kauyen ba. Kawai a jikinta take jin cewa anan din za'a binneta wata rana, ko da zata bar Marake sai dai tayi tafiyar da sunan ziyara, ba wai bari na gabaki daya ba. Duk wani abu da yake da muhimmanci a wajenta a ganinta ya fara ne daga Marake, ya fara daga tsatsonta. Ta gilashin motar take kallon titi, take ganin bishiyoyin da suketa wucewa suna kara tazarar da take tsakaninta da Marake. Shikenan? Da gaske tabar tsatson ta? Dalilai fiye da daya sun hade waje daya, a cikin wannan dalilan harda jinjirar da take rike a hannunta tana bacci kamar a duniya kaf bata da wata matsala. Sai take jin tsakanin juma'a da asabar kamar wata rayuwar ce zuwa wata saboda nisan da tazo mata dashi. Amman jiya ne, jiya ne komai ya faru, a daren shekaranjiya daya kasance na juma'a ne baccin da zata kira dana asara yayi nasarar dauketa. Saboda ji tayi kamar bata jima da rufe idanuwanta ba ta budesu da saukar kalaman Yelwa Lubna sufyan Hausabook.com 407 "Na kashe shi Daada... Na kashe Baba... Inalillahi wa ina ilaihi raji'un... Na kashe Baba Na!" Tabbas ta mike zaune, ta kuma kama Yelwa da take wani irin fitar da numfashi kamar tana tsakanin rayuwa da wata duniya ta daban, akwai hasken fitilar da ta fara dishewa alamun batirinta yayi sanyi a cikin dakin, wani numfashin da Yelwa ta sake fitarwa da damkar da tayiwa Dije na tabbatar da ciwon nakuda ne ya kama Yelwar. "Babaa... Na kashe shi Daada... Na kashe Baaba" Yelwa take fadi a tsakanin ciwon nakudar da take yi, sai Dije ta saketa tana mikewa tsaye gabaki daya zuwa kan gadon Datti, tun kafin ta tabashi tasan babu rai a tare dashi. Abinda ya saukar mata wannan karin yayi dai-dai da ruwan daya sauko. Ya kuma yi dai-dai da wani irin nishi da Yelwa tayi tare da dirowar 'yar da bata dauki lokaci wajen sanar da dirowarta duniya ba ta hanyar karade dakin da kuka. Idan Dije tace ga inda ta samu karfin halin raba idonta da gawar Datti ta dawo kan Yelwa da bata taimakon da take bukata tayi karya. Kafin Lubna sufyan Hausabook.com 408 ta gama gyara wajen bayan ta samu ta yanke cibi, ta kuma ajiye yarinyar kan shimfidar da ta tashi. Ruwan ya fara tsagaitawa, cikin nuna alamun asuba tayi. Dije kuma ta sami tabbacin hakan da rangada kiran sallar farko da akayi. Saita fita daga dakin zuwa dakin girkinsu, jinta takeyi kamar ba ita ba, da yayyafin da akeyi ya sauka jikinta ma sai ta dago hannayenta karkashin duhun asuba, bata gane komai, bata gane abinda yake faruwa da ita. Komai dai ya kara canzawa, ciki harda bugun zuciyarta da bata juyo alamar shi. Dakin girki ta shiga ta hada wuta ta dora ruwa a tukunya ta dawo. Saitayi tsaye, kuka jinjirar takeyi har lokacin, amman Yelwa bata motsa daga inda ta haihu ba, kamar ma bata motsi itama. Saita rasa wa zata fara nufa. Yelwar dai ta sake tsintar kanta da tunkara. Ta kamata ta dago da ita tana jijjigata "Yelwa.... Yelwa" Ta kira cikin wata irin murya, amman bata motsa ba, sakinta tayi tana fita ta dibo ruwa ta dawo tana sake dagota hadi da shafa mata ruwan a fuska, sai da tayi hakan wajen sau Lubna sufyan Hausabook.com 409 hudu, tukunna Yelwar taja wani dogon numfashi ta bude idanuwanta, ta kalli Dije, saita mayar ta rufe tana mirginawa ta sauka daga jikin Daada taja jikinta ta dunkule waje daya hadi da sakin wani kuka da alamu suka nuna daga wani sashi na zuciyarta yake fitowa, kamar bataso farkawa ba, kuka takeyi kamar babu abinda ya rage mata a duniya. "Ki tashi Yelwa, ki karbeta ki shayar da ita ko zatayi shiru" Dije ta fadi, muryarta na komawa cikin kunnuwanta da wani sauti da ta kasa fahimta. Amman Yelwa bata ko nuna alamun motsawa ba, sai da ta sake kamota, ko ina na jikinta bari yakeyi "Na kashe shi Daada... Na kashe shi.... Na kashe shi" Take fadi tana kara maimaitawa kamar karatu. Kai kawai Dije ta iya dagawa tana taimaka mata ta tashi zaune, ta saka mata yarinyar a hannunta, sai tayi shiru, kamar ta gane inda aka sakata, kamar tasan a jikin wadda ta kwanta cikintane tsayin watanni. Sai dai daga yanda ta Lubna sufyan Hausabook.com 410 riketa take bin muryar Dije akan ta shayar da ita zaka gane duk tanayin hakan ne cikin fitar hayyaci. Kamar rabi da rabi take cikin duniyar. Sake fita Daada tayi tana zama dakin girkin, kamar zazzabi takeji da kuma sanyi da ma wani abu da bashi da suna duk a waje daya. Ta kwashe ruwan ta dauka takai bayi ta dawo ta kara zuba wani. Har taje ta karbi yarinyar daga hannun Yelwa ta goyata ta kama Yelwar ta fito da ita bata daina kuka tana maimaita "Na kashe shi" Ba, sai dai wannan karin kamar kanta take fadawa maganar ba Daada ba. Tunda babu itace da zani Daada tayi amfani taiwa Yelwa wanka, tana tuna mata lokacin da tayi mata hakan fiye da yanda za'a iya kirgawa a kuruciyarta, a jinyar da tayi. Sai dai na yau ya sha bamban da sauran. Kayanta ne ta daukowa Yelwa ta bata ta saka, ganin kamar hankalinta yayi nisa da ita yasa Dijen saka mata kayan da kanta. Jaririyar ta yiwa wanka itama, tana tunanin abinda zata saka mata a jikinta. Saita tuna ragowar kayan Haidar da suke gidanta. Ta bayar da wasu da Lubna sufyan Hausabook.com 411 yawa, amman akwai sababbi wajen kala hudu da tun na lokacin yana jariri ne da basuyi amfani dasu ba. Watakila Mero ta adana ne, sai kuma kaddara bata barta da zabin tsayawa daukar su ba. Su ta lalubo ta saka mata. Ta mika ma Yelwa da take zaune ita tana daukar mayafinta ta lulluba taje ta bude gidan tana fita tayi tsaye a bakin kofar gidan tana rasa inda zata nufa kowa zata fadawa, sai Abu ta fado mata a rai, safiyar data shigo musu bayan rasuwar Hammadi. Mutuwar ta kadata, sai dai yau ta gane babu abinda taji, ba kuma ta fahimci komai ba, maraicin da take ciki na sake danneta. Hakama rashin Abu a kusa da ita, tana nan tsaye, yayyafin da akeyi na rage karfi har maza suka fara dawowa daga masallaci "Dije?" Makocinsu ya kira cikin son tabbatar da ita din ce "Dije lafiya kuwa? Me yake faruwa ne? Ba dai jikin Dattin bane ba ko?" Lubna sufyan Hausabook.com 412 Da yake yasan bashi da lafiya, bai ganshi ba kwana biyu yayi sallama, ya kuma shigo bayan Datti ya bada izinin hakan. Sai taji harshenta yayi nauyi, dakyar ta iya furta "Ya rasu... Ya rasu ne" Inalillahi wa ina ilaihi raji'un din daya furta na dira kunnuwan ta, wani gashi da batasan da zaman shi ba a wajaje mabanbanta a jikinta yana mikewa "Bari in fadama Audi sai aje a sanar da liman mu taho tare" Kai ta iya daga masa. Tana nan tsaye har suka dawo suka sameta, sannan ta iya motsa kafafuwanta tana binsu cikin gidan, ta kuma nuna musu dakin da Datti yake a ciki. Tana kallo suka shiga don su tabbatar da cewa ya rasun. Ita ta mika musu ruwan da zasuyu amfani dashi wajen yiwa Datti wankan shi na karshe. Tana tsaye bakin kofar, sai dai kafin a gama hadashi har mata na nan makota sun fara shigowa, su suka kama Dije da batayi musu ba suka shiga daki da ita. Idan da mamaki a fuskokin su ganin Lubna sufyan Hausabook.com 413 jaririya sabuwar haihuwa da take ta tsallara kuka basu nuna ba. Ba kuma suyi yunkurin hana Dije da ta dauketa ta goya ba, tana samun waje ta zauna. Tun yarinyar na kuka har tayi luf alamar tayi shiru ko kuma bacci ya dauketa "Ki fito kiyi masa addu'a..." Za'a taimaka mata taji ta mike da kanta, har dakin ta shiga, ta ganshi shimfide an hada shi. Tsayin shi na kara fitowa kamar an jashi. Tana tsinkayo muryar mutane, harda wanda zata iya kira da abokan Datti na fadin "A'a matar shi zatayi sallama da shi sai a fito da gawar" Tana kuma sake jin wasu sunata kiran "Gawa". Sunan shi harya bace, wani abu da ya girmi tsoro ya tsirga mata. Tsugunnawa tayi, kirjinta kamar zai fado "Kace zakayi son kai idan ka rokeni gafara Datti. A iya zaman mu idan ka batamun na yafe maka, Allah nake roko daya shafe kuskurenka ya yafe Lubna sufyan Hausabook.com 414 maka...nagode nima... Nagode da tarin kaunar ka..." Sauran kalaman sai suka makale mata, kallon shi takeyi kamar takai hannu ta yaye likkafanin ta sake ganin fuskar shi, sai dai ko da bata yaye ba, zata rantse da Allah idanuwanta sun yaye mata farin mayafin, fuskar shi take ganin tarau kamar yana bacci. Sai ta mike, tana jin zaren dake rike da sauran hankalinta na tare da yanda zata ja numfashi ta fitar da sanin kowanne a ciki yana kusantata da tarar da Datti. Basu kawo yau da sauki ba, sun fuskanci kalubale mai tarin yawa, akan auren su, a yaran da sukaita binnewa, a yaran da suka rayu kaddararsu tazo da nauyi. Sai dai zata zabi Datti, idan aka bata dama zata sake zabar shi a matsayin mijinta. Ko da kowa zai mata tambari da mahaukaciya, zata sake zabar Datti iya adadin da dama zata bata. Saida ta fito ta kalli liman da yake tsaya yana ce mata "Sai hakuri, kowanne mai rai mamaci ne, muma duk lokaci muke jira... Allah ya jikan shi ya yafe masa" Lubna sufyan Hausabook.com 415 Tana amsa shi da "Julde na hanya, inda duk yake yana hanya. Don Allah ku jira shi, da sassafe yake isowa. Yana hanya duk inda yake" Abinda duk suke fada baya karasawa kunnuwanta, rokon su tayi da su jira Julde. Kamar kuwa ta san yana hanyar. Duka alhamis din tazo masa da wani irin yanayi, haka ya koma gida daga kasuwa. Shisa ya biyewa Saratu sukai tashin hankalin da ta kwana biyu tana nema akan Nawfal. Yaran da baiga me ya tsare mata ta dauki karan tsana ta dora masa ba. Sai dai daya kwanta wasu mafarkai ya dingayi da suka kara hargitsa shi. Yelwa ya gani a tsugunne tana kallon filin wajen kamar tana jiran wani abu, ya bude bakin shi ya kirata amman babu sautin da yake fitowa. Bai san ya akayi yaga Datti ba, a tsaye yake shi, idanuwan shi na kan Julden, a maimakon Yelwa da yaga kamar tana jiran wani abu, Datti na kallon shine kamar yana jiran shi. Farkawar da yayi bai iya komawa bacci ba, zuciyar shi bugawa takeyi kamar wani abu na shirin faruwa dashi. Shisa tuki ne abu na farko Lubna sufyan Hausabook.com 416 daya koya bayan sun koma Kano, sannan mallakar mota tashi ta kanshi. Ya godewa Allah ya sake gode masa da wannan ni'imar lokacin da bai saurari Saratu ba, ko wanka baiyi ba karfe hudu na safe ya fita daga gida yana kamo hanyar Marake. Ana ta yayyafi a wasu kauyukan. Baiyi karfin da zai kasa ganin hanya ba, ji yake tamkar Maraken ta kara masa wani irin nisa. Da ya shiga cikin garin sai yaji bugun zuciyar shi ya karu. Sai ma daya doshi gidansu yaga mutane a kofar gidan, daga nesa ya ajiye motar ya kasheta ya fito yana takowa da kafafuwan shi cikin hanzari. "Sannu Julde... Sannu kaji" Wani a cikin taron mutanen ya fadi "Datti lokaci yayi" Kalamai uku, kalaman da ba zai taba mantawa dasu ba, lokacin da zuciyar shi tayo kundunbala daga cikin kirjin shi tana gangarawa cikin gidan, ya kuwa bita, bata tsaya ko ina ba sai a bakin gawar Datti da aka fito da ita tsakar gidan. Ya ji gwiwoyin shi a kasa, bai dai fahimci ko rarrafe yayi ya karasa ba. Ya kuma dora kanshi a jikin Lubna sufyan Hausabook.com 417 gawar Datti yana jin wani abu na rushewa a tare dashi "Yanda ka kunyata ni Julde... Allah ya kunyata ka a idanuwan mutanen da suka fi komai muhimmanci a wajenka..." Kalaman Datti da sune na karshe a tsakanin su suka dawo masa, suna jijjiga zuciyar shi daga inda take tana komawa kirjin shi ta zauna da wani irin karfi. Mikewa yayi yana ratsa duk matan nan harya tarar da Dije ya kamota yana fito da ita daga dakin "Daada bai yafe mun ba, Baba bai janye kalaman shi a kaina ba... Ya tafi bai yafe mun ba" Kallon shi Dije takeyi, sai take jin wani abu na bude mata, kamar ganin Julden na fisgota daga duniyar fitar hayyacin da ta shiga ne, kamar yanzun zata dawo ta fuskanci komai "Ka taho a kama, gawa bata jira fa" Wani ya fadi, da sabon firgici a fuskar Julde yake kallon Dije "Kaje... Kaje ka dawo" Lubna sufyan Hausabook.com 418 Ta iya fadi, idanuwanta sun kankance duk da babu digon hawaye ko daya a cikinsu. Juyawar kuwa yayi, tana kallo suka daga munkarar da Datti yake ciki suka fita dashi daga gidan, suna tafiya tare da wani sashi mai girma na zuciyarta. Ta lumshe idanuwanta, kirjinta kamar an hura wuta a ciki. Bata sake saka Julde a idanuwanta ba sai dare, bayan mutane duk sun tafi, sai yan uwanta da suke uba daya, saboda wanda suke uwa daya matan ba'a cikin marake suke aure ba, da alama kuma labarin rasuwar bai karasa musu ba. "Daada..." Taji muryar shi, sai ta fita ta same shi yana tsaye. Kallon shi takeyi "Daada da gaske Yelwa ta dawo?" Kai ta daga masa, kiran Yelwa da yayi na bude wani sashi daya toshe a cikin kanta "Banganta ba, tun da dafe banganta ba, sai yarinyar" Numfashi Julde yaja ya fitar, abinda yaji ana fada a waje da gaske ne kenan. Anga Yelwa ta shigo Lubna sufyan Hausabook.com 419 garin da tsohon ciki, ance ma ta haihu, jinjirar ko jinjirin ne goye a bayan Dije. A wajen zaman makokin da Julde baiga amfanin shi ba, saboda ana dawowa aka fara fito da kokon da baisan wake da karfin halin sheka shi a yanayin da suke ciki ba. Hawayen dake ta masa barazana yake dannewa, saboda yanajin shi da

Chapter 16 of 27