Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kudirinta ya girgiza. Idan ta shigo ta samu rabo ta kore ta, sanadi kawai zata zama, amman tasan akwai hakan a kundin kaddararta, akwai rabuwa da Hammadi, ko da matar da zai aura bata zama sanadi ba kuwa. Tun shi Hammadin da zai kara auren yana gujema maganar har nacin Abu yasa shi karbar hakan. Sai gashi ana masa tayin aure a cikin garin Marake kamar bashi da wani laluri na rashin haihuwa. Kwadayin su bayyane a kan fuskokin su tun kafin ma su furta masa bukatar su. Shisa duk yayi watsi da su, ya cigaba da dubawa Lubna sufyan Hausabook.com 102 "Bana so in auro wadda zata cutar damu Abu...ina addu'a kar muyi dana sanin auren nan" Amman yanayin ta na kara masa karfin gwiwa, sadaka tunda ya aminta da batun auren duk rana sai yayi tunda yaji wani Malami daya ziyarci kauyen nasu yana cewa tana kare masifu. Cikin ikon Allah ya sauke idanuwan shi akan Pendo, sai yaji zuciyar shi ta natsu, duk da yaje neman auren ta wajen Mahaifin ta da sanin cewa zai iya hana shi, bai hana ba. Daga baya yaji cewa mahaifiyar Pendo bata so auren ba saboda rashin haihuwar shi, amman Pendo ta kafe cewar ita Hammadi yayi mata. Ba'a wani bata lokaci ba tunda kudi ba matsala bane aka gama shirya komai. A cikin gidan shi ya kara gyara dakuna biyu da zasu kasance na Pendo. Abu bata san haka kishi yake ba, bata kuma san wata yaudara da cewar ta shirya ganin Hammadi da wata ba, sai da taga ana shigowa da kayan Pendo da jerin mutanen da suke rangada guda da wake-waken murna irin nasu na Fulani, har wata nama Pendo lakabi da Lubna sufyan Hausabook.com 103 "Amaryar Hammadi, uwar 'ya'yan shi" Zuciyarta ta tsinke kamar kunun kanwar daya sha sukari, ruwan ya zubo ta cikin idanuwan ta a matsayin hawaye. Hawayen da har bayan kawo Pendo bai tsaya ba, hawayen da ta kasa boyema Hammadi daya shigo dakin ya zauna gefen gadon ta kusa da ita "Dan Allah ki daina kukan nan Abu, kinga baki da isasshiyar lafiya, kiyi hakuri ki daina kukan nan kar ya saka miki wani ciwon" Habar zaninta ta kama tana goge idanuwanta da suka rine saboda kuka, wanne ciwo kuma? Har akwai wani ciwo da zata ji fiye da wanda take ciki a lokacin? Sai ace zafin rashin iyayi yasha bamban da kowanne, bata karyata ba, amman ba layin su daya da zafin kishi ba, sam ba wajen su daya ba. A gurin 'ya mace zafi na kishi kalar shi daban ne, har abada bashi da abokin kwatance. Duk tausasan kalaman Hammadi sun rushe lokacin da taga ya mike yayi mata bankwana, wani abu da bai taba faruwa ba tun farkon auren su, sai dai idan basa cikin gida daya. Lubna sufyan Hausabook.com 104 Wannan daren, wannan daren da ba zata taba mantawa ba, yanda taga ranar shi haka ya wuce yana zo mata da wayewar gari mai cike sa sabon lamari. Da fari zama suke da Pendo na lumana da girmama juna, kafin ma ta yunkura da sunan wani aiki Pendon ta rigata, idan ba Dije ta shigo ba, kusan komai tare sukeyi ranar girkinta da ranar girkin Pendon. Shima Dijen ce yanda duk Abu ta so ta sakema Pendo ta kasa, bata taba ganin Dije taki jinin wani babu dalili mai karfi ba sai akan Pendo. Itama Pendon ta kula, duk in Dije ta shigo bayan gaisuwa bata sake bi takanta. Sai Abu ta hakura ta kyale Dije, musamman yanzun da itama take cikin tata matsalar ga daban akan Bukar. Canji ne dai Abu bata daina jin shi a tare da ita ba, wannan zazzabin na duk dare kamar anyi ruwan shi an dauke, sai kace bata tabayin ciwo ba, har jikinta ta fara mayarwa, fatarta ta murje ta kara haske, har Hammadi saida ya zolaye ta "Amarya ce ta goga mun kyallin ta" Lubna sufyan Hausabook.com 105 Tace masa tana dariya, tana jin dadin yanda ko na dakika daya bata taba ganin wani sauyi a tare da shi don ya kara auren nan ba. Har lokacin da Pendo ta cika watanni biyu da wasu yan kwanaki, lokacin da ta fara wani ciwo da duk alamun shi suka nuna cewa ciki ne da ita. Abu tayi mata murna, tayi ma Hammadi murna. Ta kuma shiga daki tayi kuka, kukan daya fito daga wani lungu na zuciyar ta da ya tabbatar mata da matsalar rashin haihuwar su ba daga Hammadi bane itace, tagani, kuma haka kowa zai gani. Cikin kasa da sati daya maganar ta gewaye garin tsaf, dangin Pendo kuma suka matsa ma Hammadi akan suna so ta koma gida ta reni cikinta har sai yayi kwari tukunna. Da yake ba mai son hayaniya bane saiya amince musu, ranar da suka zo daukarta haka sukaita yarda maganganu, Abu ko fitowa daga daki batayi ba gudun fitina, ta kuma hana Dije da jikinta ke ciri jin irin maganganun da sukeyi, har wata na cewa ai gara su dauketa kafin Abu ta kassara musu yarinya da abinda ke cikinta. Kamar duk garin basu san cewa inda Abu bata amince ba Lubna sufyan Hausabook.com 106 Hammadi ba zai taba kallon Pendo da zancen aure ba. Yanzun ma auren nata zai iya girgiza idan yaji gorin da suke yima Abu. Ai kam bayan sun tafi Dije mikewa tayi tana share hawayen takaici tabar Abu da ta kwanta kan gado wani abu na konewa a cikin kirjinta. Abinda ta danne bata bari Hammadi da yake ta binta da kallo ya gani ba, baice mata komai ba, amman zuciyar shi a bayyane take cikin idanuwan shi, tausayinta ya hana shi murnar cikin Pendo, sai taji soyayyar shi ta karu a zuciyar ta. Har tana sakata kokarin maida komai ba komai bane ta kuma cigaba da hakuri da kaddarar ta kamar yanda ta saba a tsayin shekarun nan. Sai dai me, Abu bata da tumbi, tana cikin siraran matan nan da cikin su yake hade da marar su, yanzun kuwa gani take yana kumburowa kamar ana hura mata shi, ba ita kadai ta kula ba. Har Hammadi saida yayi magana, sannan Dije, sannan duk wani da zata hadu da shi, kamar wasa har motsi-motsi taji wani dare, bata iya komawa bacci ba saboda firgici, gani take kamar Lubna sufyan Hausabook.com 107 wata cutar ce ta kamata. Ranar da taje gidan su ne, Inna ta kalle ta sosai tace "Abu cikine a jikin ki" Maganar da ta girgiza duniyar da take tsaye kai tana matukar kadata har tana rasa bakin musantawa, ciki, akwai ciki a jikinta tabbas, amman kamar cikin da Innar take nufi daban ne da wanda ta sani. A ranar zance yayi zance, lissafin da Abu ta dainayi na ganin al'adarta ya tashi yana bayyana watanni har biyar, yana kuma shafe mamakin rashin bayyanar cikin saboda na fari ne, idan da tana da jiki ma sai anyi da gaske za'a kula in dai ta batun girman cikine. Ko a mafarki bata hango ba balle kuma faruwar shi a gaske. Shikenan? Rana daya Allah ya wanke mata gorin juya. Da fari taki yarda, ta mike, ta koma ta zauna tana tuna yanda babu wani abu da yafi karfin Allah. Kuka kuwa na murna babu wani makusanci na Abu da bai tayata da shi ba. Hammadi kuwa hannuwa ya dora kan cikin nata yana kasa cewa komai, a durkushe yake amman ya kasa dagowa, sai da ta dora nata hannayen kan nashi tukunna, Lubna sufyan Hausabook.com 108 hawaye yake, hawayen da bai san yanda akayi suka fara fitowa ba ballantana ya iya tsayar da su, hawayen shi da suka bude mata kofar nata "Abu kinga ikon Allah ko? Kinga munyi garaje? Munyi gaggawa, da mun hakura..." Kai take girgiza masa, ba suyi garaje ba, har kasan ranta take jin auren Pendo da Hammadi babu garaje a cikin shi, ba kuma kuskure bane ba. Kallon shi tayi da wani yanayi cikin idanuwanta "Ka godema Allah kawai Hammadi Am, mu godewa Allah da tarin ni'imomin da yayi mana... Kar muce komai banda godiya" Kai kuwa ya daga mata, murnar da tayi ba zata misaltu ba, godiyar ta ga mahaliccinta zata cigaba dayi tana karawa har tsayawar numfashin ta, sai dai akwai wani sanyi da zuciyarta tayi, sanyin da take ji har cikin kasusuwan ta. Shisa murnar da kowa yake tayata da murmushi take amsawa. Da yake labari baya boyuwa, sati bata cika ba aka dawo da Pendo, dariya ma suka bata, maganganu dai basu gaji ba, ta kula a jinin dangin Pendon yake. Lubna sufyan Hausabook.com 109 "Dan Allah kiyi hakuri da abubuwan da yan uwana suke ta fada...nayi miki murna har raina... Allah ya sauke ki lafiya" Pendo tace mata bayan kowa ya watse ta shiga tayi mata barka da dawowa. Murmushinta ta fadada "Babu komai Pendo, Allah ya sauke mu lafiya zakici" Murmushi Pendo tayi a kunyace tana kasa amsawa, babu komai a tsakanin ta da Abu sai alkhairi, karamcin matar daban ne. Zama suka cigaba dayi na aminci har cikin Abu ya cika wata bakwai, tana zaune tana tukin tuwon da Pendo take tsaye a kanta saboda taki tashi tabari ta tuka, taji bayanta ya amsa, amsawa da zata rantse kashin daya fara daga wuyanta zuwa kugunta ne ya karye, kafin ta kira sunan Allah ya sake karyewa a karo na biyu a waje daya, wannan karin yana hadawa da wasu kasusuwa cikin mararta da batasan akwai su ba, suma karyewar taji sunayi. Pendo ta taimaka mata ta mike tana kiran duk wani sunan Allah da yazo bakinta ko zata samu Lubna sufyan Hausabook.com 110 sauki, har suka karasa daki Pendo na mata sannu, amman can nesa take jiyo muryar Pendo kamar basa daki daya saboda ciwo. A daddafe Pendo ta karasa tukin tana sake leka ta, amman ciwo kamar gaba yakeyi, ta katangar ta kwala ma Dije kira ta zagayo. Abu kamar wasa, nakuda ce ta taho ma Dije gabaki daya, Pendo ce ta saka mayafinta tana ficewa, dan aike ta samu aka aikama Hammadi da harda gudu ya hada yana ganin nisan da gidan shi yayi da gonar. Zuciyar shi a cikin tafukan kafafun shi lokacin daya shiga gidan, ya samu cikin yan uwan Abu mutum biyu sun zo, kasa ce musu komai yayi, gaisuwar su ma bayajin ya amsa, wani gunjin ciwo ya juyo daga cikin dakin da yasan daga Abun shine, gunjin da yasa shi zabura kamar zaiyi cikin dakin ya rabata da abinda yake azabtar da ita haka. Dole ya fita daga gidan kar suga hawayen shi, tsaye yayi a kofar gida, anan Datti yazo ya same shi, suka tsaya suna jiran ikon Allah. Har akayo Magriba aka dawo babu wani canji, gabannin isha'i ta haifo danta da ya fado babu rai. Lubna sufyan Hausabook.com 111 Tun kafin su fada mata taji a jikinta, sanyin da zuciyarta yayi randa tasan da cikin yasa ta fara shirya ma zuciyarta karbar kowacce kaddara tazo mata, saiya zamana dacin da taji takaitacce ne, tana maye gurbin shi da hamdala, ko yau mata suke zancen nakuda tana da labarin bayarwa, ko yau ake zancen haihuwa babu wanda zai kalleta ya wareta. Idan kyautar iya haka ta tsaya ta gode, ta kara godewa. Da ta rike yaron ma addu'a tayi masa, tana kara godema Allah kafin ta mika musu shi. Aka taimaka mata ta mike don ta gyara jikinta. Hammadi ne ya kasa tsaida hawayen shi, a karo na farko ya dandani abinda Datti yaji, tausayin Abu na cika zuciyar shi fal, kima ta 'ya mace da darajar ta na daguwa a idanuwan shi. Haka aka suturta ta gawar akaje aka binne ta. Ko Pendo sai da tayi kuka har ya zamana Abu ce take lallashin ta. Gani take itama abinda yake cikinta kamar ba rayayye bane ba. Danginta nata hauka da yarda maganganu, idan kuma dakon gawa takeyi fa? Kowa mamakin karfin hali irin na Abu sukeyi, ita kuma mamakin yanda suka karkata Lubna sufyan Hausabook.com 112 hankulan su kaf akan rashin da tayi, suka kasa ganin girman kyautar da Allah yayi mata. "Bansan me zance miki ba... Na rasa me zance Abu" Hammadi ya fadi bayan sun samu kebewa da juna, murmushi tayi "Ba sai kace komai ba, ka kara tayani godewa Allah, hakan kawai ya wadatar" Numfashi Hammadi ya sauke, kallon ta kawai yake yana jinjina ma karfin zuciya irin tata. Har zancen sai da Pendo tayi masa "Anya akwai irin Adda Abu kuwa? Gaskiya kaf Marake ban taba ko jin labarin irin ta ba" Dariyar alfahari yayi, Abu, Abun shi kenan. * Duk wata kulawa Pendo na samu daga wajen Abu har cikinta ya shiga watan haihuwa, inda aka sake daukarta zuwa gidan da zata haihu kuma tayi wanka acan. Yanda Abu taji gidan yayi mata shiru duk sai kewar Pendon ta addabe ta, kaji motsin mutum ma wani abu ne, musamman Lubna sufyan Hausabook.com 113 yanda suke zaman lafiya. Da hakane har a wajen yan uwan Pendo da taje gida duba ta, to Dije ta fara mata maganar "Dan Allah Adda karki ce zakije gidan su Pendo, kin san ba mutunci gare su ba...suna iya yaba miki bakaken maganganu" Ko da Dijen batayi magana bama ba zataje ba, takan dai tambayi Hammadi, kuma tana cewa ta gaishe da ita, duk da shi da bakin shi bai taba ce mata yaje wajen Pendo ko kuma zaije ba. Ta san ba zai rasa zuwa ya duba su ta ba. Ranar talata labari yazo ma Abu cewar Pendo na nakuda, kamar tayi tsuntsuwa taje haka ta dinga ji, sai dai bata wani dauki lokaci ba, tunda duka gabannin azahar ne, kafin la'asar ta haifi yarta mace, Hammadi da kanshi yazo yana fada mata, saida ta rungume shi don murna. Su duka biyun sun kasa daina fara'a. Tare suka koma gidan su Pendo, bata damu da kallon da aketa mata da maganganu kasa-kasa ba, kishine suke taya Pendo, bai kuma dameta ba. Musamman yanda Pendo ta wanke mata Lubna sufyan Hausabook.com 114 zuciya da murmushin daya nuna najin dadin ganinta ne "Adda Abu nayi kewarki, baki zo kin ganni ba, yau dinma bani kika zo gani ba" Dariya Abu tayi, yarinya ce basu bata ba, tana goye bayan wata kakar Pendo akace wanka akayi mata tana bacci, ba'a so ana yawan sauke jinjira haka. Murmushi tayi tana amsawa da "Allah ya raya mana cikin aminci" Tayi musu sallama tare da yima Pendo alkawarin zata dawo ta sake duba su, har takai kofa ta juyo muryar Pendo "Adda Abu..." Juyawa tayi, murmushi Pendo tayi mata "Nagode da dukkan karamcin ki, nagode" Kai kawai ta daga mata, da ta san cewar wannan ce rana ta karshe da zata saka Pendo a idanuwanta da ta tsaya sun kara hira, da ta tsaya ko ba zasuyi hira ba tayi ta kallon ta, ta kara daukar wasu hotuna na Pendon da zata adana tana dawo dasu tamkar tarihin da Pendo Lubna sufyan Hausabook.com 115 ta zama a safiyar sunan 'yarta da ta tashi da wani irin ciwon ciki. 'Yar da dangin Pendo sun san cewa kulawar ta zata koma karkashin Abu ne gabaki daya da basu hanata daukarta a ranar da aka haifeta ba. Sai dai wasu kaddarorin sun fi gaban hasashe Wannan shine tunanin Abu lokacin da take rike da yarinyar da taci suna Saratu, hawaye fal a idanuwanta Kaddara Kowanne rai da irin tashi *** Dalilan da suka hanata yi ma maza kudin goro akan cewa basu da adalci, zuciyoyin da suke kirjin su bangaren tausayi na wasu da yawa a mace yake kadan ne, mahaifinta baya cikin wannan dalilan, saboda shima ya kalle ta yace "Ki dauki Bukar ki mayar da shi gidan mahaifin shi Dije, shine kwanciyar hankalin ki, shine kuma rufin asirin shi" Lubna sufyan Hausabook.com 116 Kasa cewa komai tayi, ta dai daga ido, ta kuma kalli Baba, ta kalle shi da idanuwan da bata taba kallon shi da su ba, ta kalle shi a ranar ba'a matsayin mahaifinta ba, zuciya ta uwa tasa ta kalle shi ta kuma saka shi a jerin mutane marassa tausayi, mutanen da suka kasa duba halin tagayyarar da rayuwar Bukar zata shiga idan ta dauke shi ta mayar gidan Baabuga. Kowa ya manta yanda da wahala ka fita baka ci karo da daya a cikin yaran Baabuga sun gantali akan hanya ba, yar makarantar allon da ake kokarin saka yara a kauyen ma su basa cikin wannan tsarin. A cikin dalilan ta nakin yiwa maza kudin goro Hammadi yana cikin su, Hammadi daya fita daban da sauran mazan da rayuwa ta hada hanyarta da su. Saboda har cikin zuciyarta tana da yakinin Hammadi ba zaiki rikema Abu dan da ta samu batare da shi ba, ko da yafi daya kuwa. "Ba zan rike dan Baabuga ba, ba zan rike ba wallahi. Karki fara kawo mun shi cikin gidana, idan ba zaki mayar masa da shi ba kisan inda zaki ajiye shi, amman ba cikin gidana ba..." Lubna sufyan Hausabook.com 117 Sune kalaman Datti, kalaman da baiyi kokarin tausasawa ba, iya gaskiyar shi ce ya fada mata tasani, amman kai tsaye haka? Ba ana sakaya wata gaskiyar ba? Ana mata lullubi da bargo mai taushi yanda in aka jefa dukanta zai isa da sauki "Dan Allah... Kar ka duba Baabuga, karka duba Bukar din ma, ka dubani, ka duba halin da zuciyata take ciki...karkayi saurin yanke hukunci haka, Bukar ba mai rikici bane ba, zai zauna cikin gidan nan kamar baya nan" Tayi maganar cike da roko, zuciyarta a cunkushe, idanuwanta a cike da hawayen da tun ranar da aka fara mata magana kan ta mayar da Bukar gidan mahaifin shi suka soma zuba, ba su kuma yanke mata ba "Sai dai zan gan shi...idan na shigo gidana zan gan shi, zai tuna mun daren da kikace mun shi kadaine daren da kika rabamun kanki da Baabuga... Daren dana tsana, Baabuga dana tsana Dije, abinda daren ya haifar da bana son ko ji balle in tashi in gani a duk rana... Dan Allah... Dan Allah karki sake mun maganar nan..." Lubna sufyan Hausabook.com 118 Yanda ya karasa maganar cikin roko yasa ta mike tabar masa wajen a wancen lokacin. Ta kuma turo kofar dakinta harta saka sakata abinda bata tabayi ba. Babu kalar abinda bata saka a cikin ranta ba, warwarewar dai ce ta gagara. Musamman da taga da gaske Datti yake ba zai rike mata Bukar din ta ba "Zanma Hamma magana in za'a kai masa dabbobi a hadamun da guda daya, ya bani kudin in rike yarona da su" Lomar tuwon da Datti yakai bakin shi ya tauna, yanajin ta wuce ta cikin makoshin shi, zafin na ratsawa ta duk lokon da tuwon ya wuce kafin ya saukar masa a ciki da wani irin nauyi, kallon ta yayi, babu alamar wasa a fuskarta, asalima yanda ta hade girar sama da ta kasa ya nuna cewa ba shawara tazo suyi ba, gaya masa takeyi, kawo mata wani zancen kuma zaiyi dai-dai da neman sabuwar rigimar da bai shirya ma ba. Bai taba sanin Dije ta iya rigima ba, ko zata iya kallen idanuwan shi ta mayar masa da magana haka sai akan Bukar din nan. Lubna sufyan Hausabook.com 119 Bukar da ya tsana har kasan ran shi, Bukar da ko sama da kasa zata hade waje daya ba zai zauna masa a gida ba. "Madalla..." Ya amsa yana cigaba da cin tuwon shi, ta kasan idanuwa yaga ta mike sannan ya daga kai ya bita da kallo. Daki ta shige ta turo tana saka sakata. Murmushi ya tsinci kan shi dayi, in dai akan maganar Bukar ne ba zai taba biye mata ba, duk da fushin da ta dauka bashi kadai ya shafa ba, ya kula harda Julde, hanya daya da tasan tana da ita da zata iya bakanta masa rai, yanda duk taso ba zai bari hakan ya faru ba. Shisa idan ya dawo saiya biya ta gidan Hammadi ya ganshi ya dawo, can yake barin shi yanzun, saiya dauko shi ya dawo da shine zatayi abinda zaisa dole ya biye mata. Da safe ma saida ya gama shiri zai fita, ya shiga dakinta don yayi mata sallamar da bata ko daga kai ta kalle shi ba, ya juya ya tsinkayo muryarta "Zanje gida" Lubna sufyan Hausabook.com 120 Labulen ya saki bai amsata ba, yasan me yaji lokacin daya rabu da ita, kuskure ne da yayi sau daya, kuskure ne da zai karasa sauran rayuwar shi yana kokarin ganin bai maimaita ba, shisa ya fice batare da yace mata komai ba kafin wata zuciyar tace masa ya nuna mata yana da iko a kanta, ya hanata yaga abinda zai faru. "Sai mutane su dauka ni da Abu bama fada, babu wani zama da za'ace ba'a samun sabani Datti, yau da gobe tafi karfin wasa. A zaman aure sai ana kauda kai, sai kuma ana hakuri, idan kaga yayi karqo to dole akwai wanda akafi cutama, dole akwai wanda akafi tauyewa, dole daya na hakuri da daya fiye da yanda dayan yakeyi, bansan me yasa tsarin ya kasance haka ba, amman hakanne, kuma muma haka za mu cigaba da gudanar da zamantakewar...gata nan, zama ya sake hadaku a karo na biyu, a naku zaman ko ba'a fada ba ansan wa yafi hakuri da wani, kaima saika kai zuciyarka nesa a lokuttan da ka kure hakurin ta" Zantukan Hammadi ya dauka anan inda yayi masa su yabar su kamar ko da yaushe idan ya samu sabani da wani, Hammadi ya tsaya yana Lubna sufyan Hausabook.com 121 masa nasiha akan zamantakewa da mutane da kuma amfanin hakuri harma da yawan kauda kai. Saboda yasan baida wannan zuciyar, hakuri ba halin shi bane ba. Sai a yan kwanakin nan da Dije take saka kara tana zungurin duk wani abu da tasan zai hassala zuciyar shi amman ya kauda kai, duk da yana saukewa akan duk wanda ya gifta masa a waje. Hakan ne ma yasa Hammadi yi masa magana "Da bacin ranka kake zuwa Datti, idan zaka dinga hucewa akan wanda basu san hawa ba basu san sauka ba, ka daina zuwa har saika warware matsalar ka da matar ka" Numfasawa yayi "Saina rike mata yaro, akan naki rike mata yaro ne take ta tashin hankali" Ya fadama Hammadi din tunda boyewar bata da amfani "Bukar?" Hammadi ya tambaya, kai ya daga masa Lubna sufyan Hausabook.com 122 "To menene dan ka rike shi? Taimaka mata zakayi, kuma shima yaron inka duba gidan Baabuga zaka taimaka masa" Kai yake girgizawa tunda Hammadi ya fara magana "Wallahi ba zan rike wannan dan iskan yaron ba" Kallon shi Hammadi yayi yana kada kai kawai hadi da fadin "Allah ya rufa asiri" Tunda yasan hali, abinda duk zai dora bayan wannan kamar zai kara tunzura Dattin ne. Akwai lokuttan da shiru shine mafi alkhairi, komin yanda kake ganin kusancin ka da mutum kuwa. Hidimar shi ta ranar Hammadi ya cigaba da gudanarwa, yana jin masifa da tijarar da Datti yake yiwa mutane. A gefe daya Dije shiryawa tayi, ko ta gidan Abu bata biya ba, saboda itama ta kara mata takaicin da take ciki da kafewar da tayi akan Hammadi ya karo aure. Tana zaune da mijinta lafiya, bai daga hankalin Lubna sufyan Hausabook.com 123 shi akan halin rashin haihuwar su ba, ita ta daga nata. Ko tsoron wata tazo ta haihu da Hammadi ta koreta daga gidan batayi. Idan akayi magana sai tayi murmushi, murmushin nan da Dije take jin zafin shi har ranta, kamar Abu tana son fada musu tasan wani abu da su basu sani ba, tana hangen abinda kome zasu taka ba zasu taba ganin shi ba. Har ta shiga gidan su zuciyarta a cunkushe take, ta daiji dadin ganin Baba bai fita ba, a cewar Innarta yayi ciwon ciki da dare, saiya tashi bayajin karfin jikin shi, shisa da ta same shi bayan sun gaisa ya jiki ta fara yi masa ya amsa sannan ta dora da "Akan Bukar ne daman Baba...ni ba zan mayar da shi gidan Baabuga ba, zanma Hamma magana yau akama Dabbata a siyar sai in kawo kudin nan a ajiye a dinga masa hidima a cikin su kafin muga abinda Allah zaiyi" Numfashin da Baba ya sauke na korar shirun daya biyo bayan maganar da tayi Lubna sufyan Hausabook.com 124 "Dije kina tunanin ba nida abinda zan rike Bukar dashi ne? Shisa nace ki mayar da shi gidan mahaifin shi?" Kanta ta sake saddawa kasa saboda bata so yaga hawayen da suke cike da idanuwanta "Nace ki mayar dashi ne badan ba zan iya rike shi ba, sai dan shine abinda ya kamata. Iya gatan da za'ayi ma rayuwar shi kenan" Mikewa tayi, hawayenta na zuba, Baba bai hanata ba, ko da ya hanata bata jin zata iya tsayawa saboda ko ganin hanya batayi sosai, hawaye sun mata duhu bayan wanda ya lullube zuciyarta. Bata bi takan Innar A'i dake mata magana ba ta sa kai tana ficewa daga gidan gabaki daya, bata ganin komai sai Bukar da ta baro kwance dakin Innarta yana bacci, yanzun sai taga kamar yana baccin ne a nutse sanin ba zata taba barin komai ya same shi ba. Amman ina, duk wani kokari da takeyi na ganin ta kare shin nema yake ya subuce mata. Gidan Hammadi ta shiga, kuka na kwace mata tana hada ido da Abu Lubna sufyan Hausabook.com 125 "Adda ba zan iya gani sun maida shi gidan nan ba, wallahi zuciyata ba zata dauka ba...baki ganshi yau yana kwance ba, kamar duka basu duba kankantar Bukar, mutuwa zaiyi a gidan Baabuga, mutuwa zaiyi a irin wannan rayuwar da sukeyi" Riketa Abu tayi tana jin zuciyarta na karyewa, maza akwai ikirarin soyayyar 'ya'ya, a baki zaka dinga jin ikon su, a wajen jama'a zakaji alfaharin da sukeyi, musamman idan wannan yaron ya taka wani mataki ne na nasara "Dana" Haka zaka ji su "Yata ce, yar waje na ce" Bata dandani zafi na haihuwa ba, amman a tsakanin laulayi, a cikin fitowar rana da faduwarta, tana tare da Dije, lokutta mabanbanta, hannunta yana rike dana Dije a yayin nakuda, yaran da basu ma zauna ba, a haihuwar Dije ta uku, a irin wannan wahalar da taga ta sha saida wani sashi na zuciyar ta ya numfasa cikin jin dadin yanda jikinta bai taba Lubna sufyan Hausabook.com 126 dandana irin wannan wahalar ba. Sai lokaci daya namiji ya kalli mace yace mata ba zai rike mata danta ba saboda ba nashi bane ba, ba zai rike ba saboda baiga wani dalili da zaisa ya rike ba. Tunda suka fara wannan maganar Abu take jin kamar ta kama Datti ta girgiza shi. "Laulayin da ta sha kadai dalili ne, nakudar da tayi kadai dalili ce" Haka take so ta fada masa, idan bashida halin rikewa Bukar zata iya fahimta, duk da har abada ba zata fahimci kowanne irin dalili da zai raba uwa da yaranta ba, idan tace kowanne dalili tana nufin kowanne iri. Me yasa namiji zai auro mace kuma ta rike masa nashi yaran? Me yasa? Sai ace shi ba zai rike mata nata ba saboda basu fito daga jikin shi ba, amman shi ta rike nashi da basu fito daga nata jikin ba. "Nayi magana da Inna, tace ko da za'a maida Bukar din ba yanzun ba, yayi kankanta tunda ko shekaru biyu bai cika ba, a barshi ya kara ko da shekara ce nan gaba... Kafin nan mun samu mafita da yardar Allah" Lubna sufyan Hausabook.com 127 Abu ta fadi a tausashe, amman kukan da Dije takeyi yaki tsayawa, saboda jikinta ya fara sanyi, zuciyarta ta fara karaya, ji takeyi kamar an dauki Bukar an mikawa Baabuga ne, abinda zaiyi dai-dai da tagayyararsu gabaki daya. Tayi kuka har zazzabi ya rufeta, dakyar Abu ta samu tayi shiru, anan gidan tayi azahar, sukaci abinci tare da Abun ta kuma kwanta ana. Abu tace mata

Chapter 5 of 27