Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
akai zata bi, kome ita ta hango a sama in dai shi bai ganshi ba bata da ikon sake hanya. Tayi kokarin magana, tama yi maganar, ita da Modibbo akan titin nan ba abu bane da take so, Lubna sufyan Hausabook.com 315 amman yaki bari duk maganarta ta wuce kunnuwan shi balle ya fahimceta harta canza kudirin da yake zuciyarshi Yaki fahimtarta kamar yanda yake tunanin taki fahimtar shi, taki gane duk wani zabinshi akanta gatane yake tunanin yayi mata. Mahaifin Modibbo da ma Modibbon a karkashin shi suke samun rufin asiri, shisa mahaifinshi baiki ba da yayi masa tayin fadada alakarsu. Ko bayan bashida rai Modibbo da ahalin shi basu isa su wulakantata ba, basu da wannan karsashin saboda zata gaji kaso mai girma a cikin abinda zai bari, kason da yasan Julde zai kular mata dashi har numfashin shi na karshe, tana da arzikin da tafi karfin wulakanci kowanne namiji a fadin marake. Gashi dadin dadawa shi Modibbon bafullatani ne gaba da baya. Me take so bayan wannan? Menene abinki a tare da Modibbo? "Daada shirunki na cutar damu, shirunki a abubuwa da yawa ya taimaka wajen kawomu inda muke yau, kiyi masa magana, dan Allah ki bude baki kiyi masa magana. Ki fada masa wani Lubna sufyan Hausabook.com 316 abu zai mutu a tare dani daga ranar da ya auramun Modibbo" Yelwa ta karasa maganar wasu irin hawaye masu zafi na zubo mata, shirun dai Dije ta sakeyi, shirun da ta fara koyan shi akan lamurransu daya hada da Datti bayan taga yanda maganarta batada amfani indai akansu ne. Tun suna kananansu kuwa, su suka kara taimaka masa wajen dishe muryarta a duk wasu lokutta da zata shata musu layin da take tunanin zai amfani gobensu, Datti ya goge musu shi su tsallaka. Idan kudi ya dauka ya basu take tunanin sunyi yawa ta kwace, zasu fita ko me zatayi kuwa, zasu same shi, zai dauki wanda suka ninkasu yawa. "Ubansu mai kudine, su yaran mai kudine Dije. Ki barmun yara suyi abinda suke so tunda ina da halin da zasuyi hakan..." Idan fada tayi musu, a gabansu zaiyi mata wanda sai ta shiga daki tayi kuka. Shima irin yau din ta dinga hango masa, da duk wata tsinuwa da zaibi yaran wasu dashi, da duk lokuttan da yake ganin shine ya isa akan tarbiyar su, dama Lubna sufyan Hausabook.com 317 lokuttan da yake ganin duk idan yaro yayi wani abu da bai kamata ba to laifin na iyayenshi ne, sune suka gaza a wani bigire na tarbiya, ikon canza kaddarar yaransu a hannun su take, sai Dije tayi kokarin fahimtar dashi. Yaran duk da suka kasance nagartattu, bayan kokarin iyayensu akwai addu'a, akwai addu'a da itace mataki da kuma jigon komai. Sosai taso ta fahimtar dashi tarbiya abune mai matukar wahala, bayan godiya lokacin da Allah yayi maka kyautar samun da, ya kamata tsoro ya cika zuciyarka, mutum ma ya baka amana kana taraddadin karka kasance cikin wanda zasu kasa sauke wannan amanar, ya kamata tsoro ya cika zuciyarka sanin Allah ne ya baka amana, amanar yaran da kai dasu zaku tsaya a gabanshi ya tambayeka akan wannan amanar. Idan kayi iya kokarinka wajen ganin ka sauke amanar nan, saika hada da addu'a, ka hada da sadaka don karesu daga abinda idanuwanka ba zasu taba hangowa ba. Idan kaga wani ya gaza a tashi tarbiyar ka bishi da addu'a, ka godewa Allah da baisa ka gaza ba, idan ba zaka iya ba kayi shiru, ka kiyaye harshenka. Lubna sufyan Hausabook.com 318 Idan yarane ka gani suna abinda bai kamata ba, kayi musu nasiha idan zaka iya, ka bisu da addu'a bayan nasihar, ko ka tsaya da addu'ar kawai, kana da zabi kala-kala, a ciki harda mai sauki, kaja bakinka kayi shiru. Karka aibatasu, karka bisu da mugun baki, karkai tir da halayensu, karka dora laifin lalacewar su akan iyayensu, watakila sunyi iya kokarinsu, kaddara ce ta rinjayi wannan kokarin. Idan ma sun taimaka wajen wannan lalacewar baka da hurumin da zaka nuna musu yatsa. Allah daya zabeka, Allah daya baka ikon sauke amanar daya baka, shi ya basu amanar, a karkashin Ikon shi suka kasa saukewa. Babu wanda yafi karfin kaddara, kowacce iri ce. Amman Datti yaki fahimtar yaren duk da fulatanci tayi masa ba hausa ba. Sai hakanma ya dinga ja mata fadanshi da idan ya fara baisan yayi shiru ba. Suma da ta nuna musu makahon sone Datti yake musu, soyayyar da ta samo asali da samu da rashin sauran yaran da suka dingayi a baya. Ta nuna musu lokaci zai iya zuwa da Datti zai kasa basu duk wani abu da zasu bukata, zai kasa karesu daga abubuwan da suka Lubna sufyan Hausabook.com 319 fi karfin ikon shi, sai suka koma bayan Datti suka labe, suna nuna mata akwai rauni a tata soyayyar. "Kinfi son Bukar, Daada kinfi son Bukar damu" Julde ya taba fada mata kai tsaye, sai dai tana ganin a lokacin kamar shekarun shi basu kai ya fahimci tana sonsu duka ba, tana kaunarsu gabaki dayansu, wata irin kauna da bata da misali. Kawai akwai wani rauni a tare da Bukar da basu dashi, akwai wata kaunarta da Bukar din yake nunawa da a cikinsu babu mai nuna mata irinta, bawai tana kishi bane da yanda suka dinga zabar Datti akanta. Kawai shakuwar da take tsakaninta da Bukar, ko nisan da yayi mata ya kasa dishe haskenta. Kowacce uwa tana son yaranta, tana sonsu dai-dai da junansu, hanyoyin da take nuna wannan soyayyar ce take da bambanci. "Ban fi son Bukar ba, ku duka ina son ku" Kallonta yayi, kallonta yayi kamar bai yarda da ita ba, kamar kalamanta basuyi masa tasiri ba. Amman ya dora kanshi a jikinta, saboda Julde ne, ko fada tayi masa, ko fada yaja Datti yayi Lubna sufyan Hausabook.com 320 mata zai zo ya dora kanshi jikinta, kamar yana bata hakuri, kamar idan yayi hakan zuciyarshi na masa sanyi. "Kiyi masa magana Daada" Yelwa ta sake rokonta. Tace masa me? Tace karya aura mata Modibbo? Ta ina zata fara shiga wannan maganar? Shiru tayi, hakan yasa Yelwa ta sa bayan hannunta ta share fuskarta tana ficewa daga dakin. Idan Dije tace tayi niyyar magana to zatayi karya. Amman da Datti ya dawo, saita tsinci kanta da fadin "Ka kyaleta Datti, tunda tace bata son shi ka kyaleta. Ya kamata daga kai harsu ku fara saurarar juna ko zaku samu maslaha" Saiya kalleta, irin kallon da yasata ganin yanda a cikin yaran duka Bukar ne kadai yayi yanayi da ita, ko yanayin yanda Julde yake cin abinci irin na Datti ne, muryar shi ma haka. Akwai abubuwan da Yelwa zata furta duk da tana mace sai muryarta tayi mata iri daya da ta Dattin. "Babu wanda ya isa yasa a fasa auren nan, ko ita da kanta Yelwar" Lubna sufyan Hausabook.com 321 Wani abu Dije taji ya tsirga mata, wani abu da bashi da kalma, saiya hado mata da tsoro, tsoro da firgici mai yawa. Yanda suka zo inda suke yanzun, yanda tarin kaunar da take tsakanin Datti da su Julde ta birkice tana juyewa zuwa haka cikin dan lokaci. Sai taji tana son magana da Abu, ta kudura a ranta washegari wajen Abu zataje, su tattauna akan yanda babu wani abu da yake da tabbas a cikin rayuwa. Yanda komai yake canzawa abin tsoro ne. Jikinta taji ya dauki dumi cikin wani yanayi da ta kasa fahimta, kamar zuciyarta na son sanar mata da komai na gab da birkice musu, kuma babu wanda ya isa ya hana hakan faruwa. Sai ace jiki daya gareka, ruhi daya, zuciya daya. Ba musanta hakan Yelwa take sonyi ba, tarin tambayoyi ne take dasu kawai, tun daga lokacin da ta hadu da Kabiru, ta dauka wani kasone mai girma daga zuciyarta ya mamaye, sai da rabuwarsu ta risketa cikin yanayin da ta hango, amman bai sa zafin rabuwar ya rage mata ba. Sai taji ba mamaye wannan kason mai girma na zuciyarta Kabiru yayi ba, saboda idan mamaye Lubna sufyan Hausabook.com 322 shi yayi zataji alamar shi da basa tare, zata rantse ko hannunta ta dora akan kirjinta, inda zuciyarta take tana iya jin fadin filin daya bari, kason yana tare dashi, da kason ya tafi yana bar mata filin daya taba zama. Sai kuma sauran abinda ya rage mata da yake wani irin ciwo, ciwo da ba zata misalta ba. Da kason daya tafi dashi, da kuma wanda ya rage mata, kenan ya hada zuciya kwara daya kenan a dunkule, meye takeji yana dokawa yan uwanta? Dame take son Julde? Julde da har yanzun idan aka raba yar duniyarta kashi uku, zai kwashe kaso biyu daga ciki, meye yake dokawa Daadarta? Baban fa? Me ya karya lokacin daya rabata da Kabiru? Meya karya a lokacin daya ja mata Allah ya isa yana kara kaurinta da wasu maganganun marassa dadin maimaitawa. Meye Baba ya karya lokacin da ya toshe kunnuwanshi daga duk rokon da take masa akan karya hadata aure da Modibbo? Ba zai yiwuwa ace zuciya daya ce take dauke da duk wannan bangarorin ba, zuciyarta da wani sashi ce a gabaki daya jikinta. Lubna sufyan Hausabook.com 323 Ruhin kuma fa? Sau nawa tana jin fitar shi daga jikinta ya koma gefe yana kallon abinda yake faruwa kamar basu da alaka, kuma a lokacin tana jin shige da ficen numfashinta, alamar akwai rai a tare da ita. Yanzun kuma fa? Yau kuma fa? Yau da ta tsallake komai, ta tsallake kowa, a karo na farko kuma ta saka kafarta a wajen Marake gabaki dayanta. Yau da tun da ta dauki mayafinta, tabi ta tsakanin mutane a taron bikinta, taji tabar wani abu daya girmi jikinta a cikin dakin nan, bayan kalaman Daada "Kowanne mai rai da zaki gani da tashi kaddarar Yelwa, ba ko yaushe bane abinda kake so yake alkhairi a tare da kai ba, ba kuma ko yaushe bane abinda kake ki yake sharri a wajenka, komai yana iya juyewa. Shisa ake so kaso kadan, ka kuma qi kadan. Kiyi hakuri tunda har anzo gabar nan. Datti na da taurin kai na sani, amman yana kaunarku, idan kika ture sabanin kankanin lokacin nan ke da kanki kinsan akaf duniyar shi babu kamar ku, yanayi miki abinda yake ganin shine iya gatan da zai iya baki..." Lubna sufyan Hausabook.com 324 Tana jin yanda Dije ta kara sauke murya tana cigaba da fadin "Idan kinganshi yau, ki kalle shi, ki kalle shi sosai Yelwa kiga yanda yafi ki jin ciwon wannan abubuwan da suke faruwa. Dan Allah ki kwantar da hankalinki" Kai ta daga kamar ta ji, kamar kalaman sunyi tasiri a zuciyarta. Kamar bata gama yanke hukunci tsallake gabaki dayansu ba. Idan tace tun da aka rabata da Kabiru bata hakura dashi ba zatayi karya, bata son Modibbo, koma rana daya batajin zata taba son shi. Bata kara sanin daura aurenta da Modibbo dai-dai yake da yanke mata hukuncin kisa ba sai satika biyu kafin auren da ta fita, ta fita da sunan shiga wajen Saratu, ta mike hanya batare da tasan inda ta nufa ba. Iska take nema, so take tayi numfashi taji yakai mata inda ya kamata ya kai mata, tayi numfashi batare da taji kamar kanta zai rabe gida biyu da yanayin da ya cunkushe shi ba. A can kasan zuciyarta wata murya na fada mata Lubna sufyan Hausabook.com 325 "Idan kika cigaba da tafiya fa shikenan, zaki bar komai, zaki gujema auren Modibbo, kici gaba da tafiya karki juya, karki taba juyawa, akwai iska daban, komai zaiyi sauki in dai baki juya ba, ciwon da kike ji zai tsaya in dai kika cigaba da tafiya" Muryar kamar ta kara mata bugun zuciyarta, ta kuma karawa kafafuwanta saurin cikin tafiyar da takeyi, saurin daya sakata yin tuntube "Yelwa" Muryar nan ta daki kunnuwanta, muryar shi, muryar Kabiru. Bawai batajin ta a cikin kanta bane ba, yau dai sai taji kamar saida ta daki kunnuwanta ne sannan takaiwa kanta tana saukowa cikin zuciyarta, ta kada iska a cikin filin da rashin shi yabar mata "Yelwa..." Ya sake kira yana jan sunan cikin sigar da ta sakata juyawa, ta kuwa sauke idanuwanta cikin nashi, tana yawatawa dasu kan fuskar shi, zuciyarta ta dunkule waje daya, ta gangaro daga Lubna sufyan Hausabook.com 326 kirjinta tayo kasa tana karasawa inda yake tsaye kafin ta tarwatse "Yelwa" Wannan karin ya kira da wani irin yanayi mai nauyi, yanayin daya nuna har cikin idanuwanta, yanayin da yayi dai-dai da kamar ya kwashe bangarorin zuciyarta data tarwatse, ya riritasu cikin hannuwan shi ya mika dai-dai kirjinta, yana mayar mata da ita a mazauninta. Sai taja wani numfashi, ta sauke shi tare da abubuwa masu yawa Ashe karya tayiwa kanta. Da tace hango zata iya rayuwa babu shi Yaudarar kanta tayi. Da ta dauka akwai wata rayuwa mai sauki da basa karkashin inuwa daya a tare. "Na kasa Yelwa, nabi zabinsu, na aureta kamar yanda suka bukata. Ya zanyi? Kullum fuskarki nake nema a cikin tata, idan tayi kokarin kyautata mun dake nake son kasancewa ko da Lubna sufyan Hausabook.com 327 rashin kirki zakiyi mun... Sai na saketa, na saketa jiya, kowa ya juyamun baya yau" Ya karasa yana sauke numfashi hadi da sake saka idanuwan shi cikin nata "Ya zanyi? Wanne irin so ne wannan da lokaci yaki rage zafin shi?" Kafadu tadan daga masa, wasu hawaye masu zafi na zubo mata "Baba ba zai bani ke ba ko?" Kai ta daga masa, wani abu na tokare mata makoshi yana hana kalaman da suke cikin kanta su fito, shima hannuwan shi ya saka yana rufe fuskar shi dasu, kamar hawaye yake nema, nashi su zuba kamar yanda nata suke zuba ko zai samu sauki. Kafin ya dago da idanuwan shi da suka sake launi lokaci daya. A wannan ranar A wannan tsayuwar A tsakanin hawayenta da bushewar idanuwan shi Lubna sufyan Hausabook.com 328 Suka yanke hukuncin daya kawosu inda sukw yau Su gudu Su ka gudu Ya saka hannunshi cikin nata bayan sun zauna a motar da Yelwa bata cikin nutsuwar da zataji inda suka nufa. Ya dai biya kudi sun kuma shiga, tana jin dumin hannun shi da zufa na ratsawa ta jijiyoyin nata hannun har zuwa zuciyarta da take cike da wani irin hargitsi. Karo na farko da ta rike hannun wani namiji da ba muharraminta ba, dumin sai yayi mata daban, a lokaci daya kuma yayi mata kama da wani abu, wani abu kamar zunubi, wani abu kamar kuskuren da zata iyayin dana sanin shi a gaba, wani abu kamar kuskuren da lokacin gyara shi ya kure mata. * "Zan kara aure Saratu" Ya fada mata, saboda ko babu soyayya a zamansu ta haifa mishi Salim, akwai tsohon cikin shi a yanzun, tana shirin sake haifo masa Lubna sufyan Hausabook.com 329 na biyu. Tana shirin sake shafe wani daren, ko wasu kwanakin a dakin da ba zaka juyo komai banda nishinta ba. A wahalar da tasha, a irin tashin hankalin daya shiga shi kanshi sai da zuciyar shi tayo tsalle zuwa makoshin shi ranar daya ga tana amai. Daga inda yake tsaye cikin firgici ya kasa karasawa wajenta balle ma yayi mata sannu yake mata ihu cikin kanshi "Wani cikin Saratu? Bakya tausayin jikin ki? Ina kika samo karfin zuciyar sake shafe wasu awanni cikin ciwo na nakuda?" Kamar cikin ita ta bawa kanta shi, ita kadai ta yanke hukuncin samun shi, bashi da wata rawa daya taka. Sai dai iya laulayin da tayi na wannan cikin ya daga darajar mace a idanuwan shi ta wani fanni da sai yanzun zuciyar shi ta bude ya fahimta. Karfin hali da Allah yayi wa mace mai girma ne. Ya tabbata inda shi ya sha wahalar da tasha lokacin haihuwar Salim, da ba shimfida kawai zasu rababa harda gida. "Ke na fara fadawa..." Ya dora kamar hakan ya isa ya wanke mata ciwon daya dirar mata, wani irin ciwo daya soki Lubna sufyan Hausabook.com 330 kahon zuciyarta har abinda yake cikinta ya amsa. Kishi na ban mamaki nasa har duhu-duhu take gani. Tasani, duk fitar da zaiyi sai zuciyarta tayi ciwo, sai tunani daban-daban ya ziyarceta, dawa yake raba mata kanshi? Wacece shimfida daya dashi yana nuna mata abinda take dauka soyayyar shi ce mai tsayawa a zuciya. Waya rike a jikin shi? Balle kuma taji kamshin shi ya bambanta, tasan wata ta kwanta a kirjin daya kamata ya zama wajenta ne ita kadai, hannuwan shi ita kadai suke yiwa rumfa sai yaran su idan ya dauke shi, sai sauran da zata haifo masa saboda ita kadai Hammadi ya haifa, ita kadai tana da burin cika gidanta da zuri'ar da take fatan a nade duniyar da wani daga jinin Hammadi a cikinta. Yau kuma abinda take takama zata nunawa sauran matan da yake bi, tayi tinkaho dashi. Idan hanya ta hadasu ta daga Salim ta nuna musu, yanda take da wani bangare na Julde da a cikinsu babu wanda zai taba samu. Yanda jininta da jininshi suke yawo a jikin Salim din. Ta ajiye shi a gefe ta fada musu yanda duka Marake kowa ya shaida auren su, kowa ta wuce zai Lubna sufyan Hausabook.com 331 kirata da matar shi, wani abu da babu macen da zata taba samu. Shine yake fada mata zata raba da wata? Gidanta, gidansu, wata zai kawo ya saka a ciki? "Wacece?" Ta tambaya a tsakanin numfashi "Julde wacece? Wa zaka aura?" Ta karasa tana kallon shi, tana so taji, da wa zai rabata mata abu daya da ta dauka mallakinta ne har abada "Mero...yar uwar Bukar ce" Batasan dariya ta kubce mata ba, ba kuma zatace ga daga inda ta fito ba. Daman mana, ta saba raba abubuwa da Bukar, ciki harda Hammadi, harda mahaifinta da ta taso ta ga yana nuna ma Bukar kalar kaunar da bai taba nuna mata ba, yana cire hannunshi daga kan abinda yake ci ya tura a gaban Bukar din bayan tana zaune a gefen shi. Taji yanda uwar rikonta, yanda Abu bata da sunan da take ambata sai Bukar. Kamar shine abu mafi kyawu da bashida wani gurbataccen yanayi a tare dashi da suka Lubna sufyan Hausabook.com 332 fara gani a rayuwar su, kamar a idanuwansu babu yaron da nagartar shi zata isa idanuwan su balle har su aunata da ta Bukar. Tunda taga Datti ya tsane shi ta fara tayashi saboda a wajenta, tsanar da Datti yayi masa kawai ta isheta, sai ya hada da wani irin kishin shi da takeyi. Saboda ta tsani raba abubuwan da take tunanin natane da wasu, ta tsani hakan fiye da komai a duniya. Da ya yanke hukuncin tafiya tafi kowa murna, tafi kowa addu'ar idan ya tafi karya dawo, ya zauna can har abada, ya fita daga rayuwar su. Sai gashi lokaci zuwa lokaci saiya dawo, saiya kara tuna mata da yanda ta tsane shi, ta tsani murmushin shi da kamar baisan wata damuwa a duniya ba. Son da Julde yake masa bai isa ba? Bai isa ba sai Julden ya auro mata yar uwar Bukar? Me yasa babu wani abu na alkhairi da yake tare da Bukar ne? Tsanar shi ce ta ninku a zuciyarta kamar shi zai dauki auren Mero ya bawa Julde. "Ka fita Julde, ka fita karka dawo na wasu kwanaki bana son ganinka wallahi" Ta karasa muryarta na karyewa Lubna sufyan Hausabook.com 333 "Saratu..." Ya kira muryar shi cike da wani irin taushi "Haukana kake son gani? Kalar haukan da ko a labarai baka taba cin karo dashi ba? Ka cigaba da tsaya mun a cikin dakin bayan na baka zabin da bani dashi!" Ta karasa cikin wani irin karaji daya saka shi fita daga dakin, badan yana tsoronta ba, sai don abu biyu, cikin dake jikinta, da kuma matsayin daya san tana dashi a wajen Datti, Datti da yake so ya tsaya masa a wajen neman auren Mero, ba zaiso ganin haukan da take ikirari ba, wannan karin babu riba a cikin biye mata. Shisa ya fita yana bata lokacin data nuna masa tana bukata. Har zuwa lokacin da Datti yaje nema masa auren Mero, da ga mamakin su dukansu ba'a hana masa ba. Abinda basu sani ba su duka shine babu yanda Musa baiyi da Mero ba. Har karatun da yasan tana so yayi amfani dashi "Na hakura da karatun Kawu" Lubna sufyan Hausabook.com 334 Tace cikin wata karamar murya, saiya sake komawa fadan daya bari yana daukar lallashin daya dauka zaiyi tasiri a kanta. "Ba zaki sake zuwa Maraken nan ba tunda baki da hankali Mero" A daren da yayi wannan furucin, safiyar Mero ta sulale tabar masa gidan, tana daga masa hankali tana kuma tuna masa girman amanarta da take a hannun shi. Saiya biyota har Maraken, saboda ta tabbatar masa zata zabi Julde ne akansu, kowanne hukunci zasu dauka akanta ba zaiyi wani tasiri ba. "Yaran yanzun tsoro suke bani Musa, rayuwar mu da tasu ta bambanta, idan suna son abu babu wanda ya isa ya tankwara su... Yana sonta, da kaina nayi masa magana yace aurenta zaiyi. Ni da mai mu godewa Allah da ya ajiye halayen da muke ganin katanga ne da bashi aurenta a gefe, ya nemi mallakarta ta hanyar da duka ba zamuyi dana sani ba..." A fuskar Musa zakaga ba haka yaso ba, akwai yaron amintaccen abokin shi da yake ta nuna alamar yana son Mero, yaro dan boko, Baban ma Lubna sufyan Hausabook.com 335 ya fadawa Musa ya samu aikin koyarwa a garin Kaduna. Wanda ya taso a kauye ya samu cigaba na barin kauyen zuwa rayuwar da tafi ta cikin shi inganci abin ayi masa murna ne. Sai ita? Da ta tashi a birni zata jajibawa kanta zaman kauye? Kauyenma da yaron da bincike ya nuna ko ilimin muhammadiya ma bashida wadatar shi balle kuma na zamanin. Ta kowacce fuska a ganin Musa, Mero ba sa'ar auren Julde bace ba. Kasancewar shi dan kauye ma bashi bane abu mafi girma, halayen shi da basu da kyau sunfi komai tashin hankali "Idan bai riketa bafa? Baabuga idan ya sakkota?" Musa ya tambaya, jinjina kai Baabuga yayi "Nayi wannan tunanin, amman ya zamuyi? Sai mu dauki hakan shima a cikin kaddararta kamar haduwa dashi, gara komai ya faru karkashin inuwar aure, idan bai riketa ba, babu wanda zaiki aurenta, illar da take cikin kin aura mata shi tafi ta aura mata shi tashin hankali" Lubna sufyan Hausabook.com 336 Zabine sukayi mai wahala, daga Baabuga har Musa, zabin da yake wa iyaye da yawa wahala. Saboda suna hango abinda yaran basa hangowa, suna hango musu zaman aure da mutanen da tsarin rayuwar su gabaki daya basu dorashi a nagartacciyar hanya ba, a cikin wannan hangen nesa sai su kasa ganin abinda yake kusa dasu, yake gab da fuskar su, amman idanuwan su sunyi nisan kiwo. Zabin na yaran ne, a wannan matakin nasiha, kokarin fahimtarwa shine na iyayen, idan har yaran suka cigaba da toshe kunnuwan su da rufe idanuwan su daga hasken da ake ta nuna musa. Sai abar su da duhun, sai abarsu su dandana duk wani firgici da tashin hankali da yake cikin duhun, da kansu zasu miko hannuwa suna neman taimakon iyayen da suka ture daga farko. Zabi ne da Datti ya kasa, ya kasa akan Yelwa da Kabiru, ya kasa barinta tayi kuskuren da yake tunani, ko babu komai kuskuren natane, a wasu matakai na rayuwa, duk yanda iyaye zasu so, duk kumajin su, duk shige da ficensu ba zasu iya kare yaransu daga wani kuskuren ba, sai dai su tsaya tare dasu bayan aikata kuskuren, su Lubna sufyan Hausabook.com 337 tayasu gyara shi idan mai gyaruwa ne, su tayasu tabbatar da basu sake maimaita irin shi a karo na biyu ba, ko kuma su tayasu daukar nauyin kuskuren da suka aikata. Saiya nemi hada lokacin auren Julden da sauran kwanakin da suka rage ma na Yelwa. Sai daren auren yazo ma gabaki dayansu a birkice. Cike kuma da taraddadin inda Yelwa ta tafi saboda bayan kayan jikinta da kuma mayafinta bata dauki ko da allura ba. Daga yammacin zuwa daren babu inda ba'a duba ba a cikin kauyen Marake, wanda ma yaganta ba'a samu ba. Haka suka waye gari cikin wannan tashin hankalin da bai hana daura auren Julde da Mero ba, saboda Datti yace a daura, wani abu ko guda dayane ya tafi akan yanda suka tsara ranar. Amman yininta ma anyi shine wajen karade makotan kauyen nasu cikin nema da kuma cigiyarta. Babu wani labari, haka Datti ya shigo cikin gidan yana kallon Dije da ta dago kanta ta kalle shi. Su duka kaman an ninka musu shekarunsu saboda tashin hankali, kafafuwan shi na rawa ya karasa wajenta, ya riko hannunta, hawayen shi Lubna sufyan Hausabook.com 338 na rigan nata zubowa. A karo na farko yana dora ayar tambaya akan abinda yayi mai zafi haka "Wanne zunubi na aikata Dije? Me nayi haka? Soyayyar da nake musu laifi ce?" Yake fadi numfashin shi na wani irin fita kamar mai cutar numfashi. Kaf Marake babu wanda zai taba fahimtar tashin hankalin da suke a lokacin sai wanda ya taba shiga kwatancin halin da suke ciki, wanda ya taba rasa yaro ta hanyar mutuwa ya kuma duba gabas da yamma, kudu da arewa yana rasa wani yaron, wannan karin ta hanya mafi wahala. Saboda a tare da mutuwa babu taraddadi, a tare da mutuwa idan ka kalli kofa sai dai a wautar tunani, kasan ka fita da gawa, ka saka a kabari kabi da kasa, ba kuma zata fito ta dawo ba. Hakuri ba zabi bane ba, dole ne. Yanzun fa? Ta ina zasu fara? Hakuri ba zabi bane ba yanzun, babu shima a cikin abinda yake faruwa dasu. Yelwa ce, ina zataje? Yelwa da a cikin Marake ma ba ko ina ta taba takawa ba. Ina zasu fara nemanta? Sai dai wannan kaddarar da tafiyarta ta fara Lubna sufyan Hausabook.com 339 Wadda dawowarta zata dasa tafi wannan. Gani yake kamar idanuwan shi ya rufe ranar da Mero ta tako cikin gidan shi a matsayin mata, ya bude su ya ganta rike da rabon da suka samu, ya ganta rike da dansu Haidar. Ba akan shi aka fara masa haihuwa ba, tun da ga Salim, ga kuma Fadila, ga kuma wani cikin a jikin Saratu, dan haihuwar gab da gab takeyi. Abubuwa da yawa sun faru daga ran daren aurensu zuwa yanzun. A cikin wannan abubuwan akwai batan Yelwa da har yanzun suke cikin duban hanya don ganin ta inda zata bullo. Mutum, ba dabba ba, a wayi gari ace an nema sama ko kasa an rasa? Kwanaki bakwai bayan bacewarta, bai san abinda Dije take ji ba, hakama Datti, ya shiga gidan ya same su zaune duka suna kuka, babu wanda yake yunkurin bawa wani hakuri a cikinsu, sai ya juya kawai batare da yace musu komai ba, shima idan ya fita da safe hanyoyi kawai ya kebi, inda duk kafarshi ta dauke shi sai duhu ya farayi tukunna ya dawo. Yayi tunanin duniya ko a cikin Lubna sufyan Hausabook.com 340 hirarrakinsu Yelwa tayi wata magana da zata saka shi fahimtar inda take, amman ya rasa. Rabi da kwatar hankalin shi yana kan dokin ganin Mero ta zama mallakin shine, gata a cikin gidan shi, su kwana su tashi daki daya, amman bashida nutsuwar nuna mata tarin kaunar da yakeyi mata "Akwai abinda zan maka ka kasa yafe mun Hamma?" Ta tambaye shi kwanaki biyu kafin daurin auren su, cike da mamakin tambayar ya girgiza mata kai "Abinda nayi maka wanda ka sani da wanda baka sani ba, da ma wanda zanyi maka a gaba duk ka yafe mun?" Murmushi yayi, yasan bata son Modibbo, amman a cikin idanuwanta yake ganin wani yanayi na mika kai, da kuma sallamawa da cewar bata da wani zabin daya wuce hakuri da auren "Auren nan bashi bane karshen duniyar ki Yelwa, ki kwantar da hankalin ki, nima nayi Lubna sufyan Hausabook.com 341 nawa binciken, Modibbo bashida wani hali marar kyau" Murmushin da ta mayar masa

Chapter 13 of 27