Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Gwaggo ta taba fada, ba'a so iyaye su tsinewa 'ya'yan su lalacewa sukeyi" Wannan karin dariya Julde yayi. In dai a cikin lalacewa akwai bin mata, ya rigada ya faru dashi tun kafin Datti ya tsine masa. Shaye-shayen da ake magana akai, wanda ya gani wasu sunayi bai taba burge shi ba, saboda bayason ya taba kusantar abinda zai rabashi da hankalinshi. To bayan wannan biyun akwai wata lalacewa ne? Sai ma ta tirsasa shi yayi auren da baya so, idan ya auri Saratu ba zai daina bin matan daya fara ba. Ba zai daina ba, shisa baiga amfanin auren ba. Hankalin Yelwa da bayason gani a tashe yasa shi nuna mata zaiyi kokarin ganin komai ya wuce masa, yayi hakuri da maganar. Amman kayanshi ya hada da nufin barin gidan da asuba kafin kowa ya fito. Saida yakai kofa ya fara tunanin inda zai nufa. Sai ya hango Daadar shi da halin da zata shiga, sai ya hasaso tashin hankalin da zai saka Yelwa. To ya gudu ma yaje ina? Saiya dawo, ya kuma ci karo da Datti a Lubna sufyan Hausabook.com 235 tsakar gidan, Datti daya kafe shi da ido ta cikin hasken alfijir daya fara ketowa "Gudu zakayi?" Ya tambaya cikin wata irin murya "Allah ya kwashe maka albarka idan ka fasa tafiya!" Ya fadi yana daukar buta ya nufi bayi kamar yanda yayi niyya. Kamar kuma bai fadi kalaman da suka saka jikin Julde mutuwa likis ba. Sai yaji kamar kalaman da suka dira a kunnuwan shi sun zagaya ko ina na jikin shi suna bin jijiyoyin shi sannan suka kwanta luf a wani wajen da suka fi karfin ganin idanuwa. Sai yake jin zaman nasu kamar wani iri ne na itaciyar da yake jira ya fara tsiro ya kafa rassa a tare da shi. Lokaci daya wani irin tsoro ya cika zuciyar shi, tsikar jikin shi ta mike kamar mai shirin zazzabi. Saiya koma daki, sallah ma sai da gari ya waye tangaran tukunna yayita. Daga ranar ne kuma bai sake daga maganar cewa baya son Saratu ba. Hidimar bikin duk da ake tayi da idanuwa yake binsu. Haka Datti ya Lubna sufyan Hausabook.com 236 fita daga lamarin shi gabaki daya, wani abu daya zame masa sabo. Bayan gaisuwa saiya rasa abinda zaice mishi, sabanin da, abincin dare ma kusan ko yaushe tare suke ci sai dai idan a gidan Hammadi yaci. Sai har Dije tayi bacci tana juyo hirar su. Komai ya canza duk akan Saratu, duk akan aurenta. Da Dattin yace masa yaje yaga gidan da zasu zauna, magana mai tsayi data hadasu a cikin wata daya da ake ta hidimar bikin shi "In dai yayi maka shikenan ba sai na gani ba" Bai kuma je din ba sai yanzun da aka rakoshi a matsayin ango. Har suka gama duk wani abu da yake al'ada a wajen su jin shi yake wani iri. Asalima yana jin amsa kuwwar amin din data daure kaddarar shi da ta Saratu waje daya. Kallonta yake da fararen kayan saki a jikinta da suka sha ado irin na amaren fulani. Mayafin kayan da aka ja aka rufe mata fuska da shi. Ya rasa abinda yake ji. Dakyar ya iya jan kafafuwan shi ya karasa inda take ya zauna a bakin gadon bonon da aka shimfide da sabon zanin gado. Iya dakin idan ka kalla zaka san Saratu 'yar gata ce, sannan gidan da ta fido kudi ba matsala bane ba. Lubna sufyan Hausabook.com 237 Sai da ya jishi a zaune tukunna wata irin gajiya ta jiki da zuciya ta saukar mishi tana kashe masa jiki, kafafuwa yaja kan gadon ya matsa can karshe ya kwanta. Duk da bata ganin shi taji kwanciya yayi. Wasu hawaye sirara suka silalo mata, ta cikin mayafin ta kai hannu ta goge su. Kafin ta zame mayafin ta ajiye gefe, tana fara cire tarkacen sarkokinsu dake wuyanta, goshinta, kunne da hannuwa. Don ita ko dankunne bata iya kwana dashi komin kankantar shi sai ta cire, idan ta tashi da safe ta mayar "Idan nice kullum saina batar da dankunne" Yelwa takan fada idan ta ga tana mayarwa da safe. A saman soyayyar da take yiwa Julde akwai wani kunci daya dinga kunsa mata tunda aka fara maganar aurensu da ta dinga shanyewa, sai ya dunkule ya zauna wani waje cikin kirjinta da yake mata ciwo "Har an daura, yanzun na hango su Baba suna dawowa" Yelwa ta fada mata cikin farin ciki, tayi murmushi, amman ba zatace ga daga inda ya fito Lubna sufyan Hausabook.com 238 mata ba. Saboda jikinta yai wani irin sanyi da bata zata ba "Zama dani ba zai taba miki dadi ba Saratu" Kalaman da Julde ya dinga jaddada mata suka dirar mata. Har aka kawota gidan jinta take kamar mai yawo a saman gajimare. Gashi nan tun bata kwana ba ya fara nuna mata gaskiyar kalaman shi. Kasa ta sauka tana shimfida mayafin da ta cire, ta dawo ta dauki daya daga cikin filon dake kan gadon ta kwanta. Sai dai hasken fitilar da take kunne taji cikin idonta fiye da misali. Jiki taja ta dauki fitilar da mai batira ce, ta kashe. Duhun da ya mamaye dakin na ba hawayenta damar sauka, su suka tayata hira har barawon bacci ya sace ta. ** Suna zaune cikin gida daya, amman tazarar dake tsakanin su zatayi daga Marake zuwa Dutsi. A tsayin satikan hudu ya koyi yin shiru ta fannin da bai taba hasasowa ba. Yaji dadin yanda Saratu ta bashi wannan tazarar da yaji yana bukata. Idan ta gaishe shi da safe bata sake ce mishi komai. Zatayi girki, zata ajiye masa. Lubna sufyan Hausabook.com 239 Idan ya dawo zai dauka ya ci saboda baida inda zaije yaci abincin. Kuma ba zai karya ba ta iya girki, a tsayin sati hudu yana tsintar kanshi da son komawa gida da cikin shi ya fara ruri saboda yasan zai sami abinci mai dadi yana jiran shi. Bayan wannan rayuwa suke a gida daya amman kowa harkar gabanshi yakeyi, idan dare yayi zatayi shimfida ta kwanta a kasa, ya kwanta akan gado. Ya kanji tana yawan motsi alamar rashin sabo da kwanciya daga ita sai zannuwan da take shimfidawa kafin yaji canzawar numfashinta alamar tayi bacci. Sai yaji kamar bai kyauta mata ba, amman kwana a kasan zabinta ne tunda bashi yace ta kwanta ba, gadon yana da girman da zai ishesu batare da wani ya takura wani a kai ba. "Na fita" Ya furta kamar kullum, addu'ar dawowa lafiya tayi masa cikin sanyin muryar da bayason ji a tare da ita. Saboda Saratu ce, sanyi-sanyi baya cikin halayyarta. Juma'a ce, yasan daga Hammadi har Datti basa fitowa da wuri, su Lubna sufyan Hausabook.com 240 kamar ranar juma'ar ce take zame musu ranar da sukeyin hutun karshen mako, dan wasu ranakun juma'ar ma cikinsu babu mai zuwa ko ina daya danganci kasuwancinsu, sai suyi amfani da ranar wajen ziyarar abokan arziki da kuma 'yan uwa. Shisa shima ya fara zabar ya wuce gidansu ya fara gaisawa da Daada, su zauna suyi hira da Yelwa. Hirar tasu da Yelwa bata rasa abinda zata fada da zai rike shi na tsayin kowacce rana da yakejin shi kamar a cikin keji. Yau ma da wannan yanayin ya tashi, ya fara tashi dashi ne tun safiyar shi ta farko da ya bude ido da auren Saratu akan shi. Ance idan wani babban abu zai sameka kana ji a jikinka, ko ka tashi da rashin kuzari, sanyin zuciya ko wani yanayi da bai zai misaltu ba. Julde ya yarda da wannan fadar a baya, ya yarda har lokacin daya karya kwanar gidansu ya hango cincirin mutane, saboda yanayin daya tashi da shi ba bako bane ba. Ya fara sabawa dashi, baisan kafafuwanshi sun kara sauri ba saida ya ganshi a kofar gidan "Rayuwa kenan..." Lubna sufyan Hausabook.com 241 Muryar da baigane mammalakinta ba ta kutsa a kanshi, amman son shiga cikin gidan Hammadi da shine farko daga inda ya bullo kafin nasu, don yaga abinda yake faruwa yasa duk wasu surutai da akeyi bace masa, Dije ya gani a tsaye, kafafuwanta babu ko takalma, asalima kallo daya zakayi mata kaga tashin hankalin da yake tare da ita. Wajenta ya karasa yana fadin "Daada me ya faru? Lafiya? Me yasa naga mutane?" Ya jera mata tambayoyin zuciyar shi a kan harshen shi. Yanda ta kalle shi yana sa tsikar jikinshi tashi saboda ya tabbatar wani abu mai girma ya fara dasu, girman da zai musu wahalar dauka. Julde ne a gabanta, kuma da alama magana yake mata, amman batajin komai sai muryar Abu "Lafiya kalau ya dawo sallah Dije, yace mun jikin shi a mace yake, ni nace masa ya kwanta watakila daren da muka raba ne muna hira, bacci ne bai wadace shi ba... Na tashe shi yaki tashi. Nayi nayi ya tashi yaki tashi... Ina Datti? Ku zo ko ku zaku tashe shi ya tashi" Lubna sufyan Hausabook.com 242 Har yanzun tanajin hannun Abu data saka cikin nata tana janta zuwa gidan da Datti da yake biye dasu cikin rudani. Sai dai yanda Datti ya dago shi taga ya koma ta kalli Abu, ta kalleta da zuciyarta a karye saboda tasan baccin da Hammadi yayi bana tashi bane ba. Ba Abu bace ta kasa yarda, Datti ne, Datti daya fita ya dinga zuwa da mutane kala-kala. Tun liman daya ce musu "Allah ya karbi abin shi" Abu ta zame tana zama, ta kuma ja kafafuwanta ta hade su da jikinta bata sake cewa wani abu ba. Datti ya kira mutane sunfi ashirin, kana cewa ya rasu zai sake fita ya kira wani. Yanzun haka da suke tsaye tashin hankalin da ake ciki kenan, ya kama Hammadi ya rike a jikinshi "Hamma ko zaka tafi zaka nuna mun alama, zakayi rashin lafiya, zaka kwanta jinya. Ba zaka tafi haka ba, ka tashi ka fada musu ba zaka barni ba saboda kai kadai ka rage mun" Ya karasa yana mayar da shi ya kwantar, ya sake dago shi a karo na biyu Lubna sufyan Hausabook.com 243 "Hamma wa zaimun fada? Wa zai gayamun banyi dai-dai ba? Dan Allah ka tashi..." Ya karasa cikin wata irin murya da ta shiga kunnen Julde da wani irin yanayi, saboda hanyar dakin Hammadi kawai Dije ta iya nuna masa "Julde zo kaga Kawunka.. Kayi masa magana ko zai tashi kai..." Cikin dakin ya shiga ya kama gawar Hammadi yana kwantar dashi, ya kuma kamo hannun Datti da yake kokarin kwacewa "Karka cemun ka yarda da zancen su, karka cemun ya rasu" Yake fadi cikin fitar hayyaci, so yake ya kwace rikon da Julde yayi masa ya koma jikin Hammadi "Baba don Allah" Julde ya fadi saboda duniyar duka yake jin ta tashi daga kasan shi ta koma sama kanshi tayi baya ta fado ta danne shi "Baba..." Lubna sufyan Hausabook.com 244 Ya sake kira yana saka idanuwan shi cikin na Datti da sukayi wani irin fayau "Ya rasu" Ya fadi, maganar na komawa cikin kunnen shi, girmanta na zauna masa. A karo na farko yana dandanar menene zafin mutuwa, yanayin da yake bako a wajen shi. Sanyin da hannun Datti yayi a cikin nashi ne yasa ya sake shi. Sake gyara zama yayi kafin yakai jikin shi kasa gabaki daya ya dago yana neman numfashin da yai masa tsaye, dakyar ya fito dashi tare da wani gunjin kuka daya da hawayen Julde saukowa. Zama yayi yana kamo Datti daya fada jikin shi yana kuka kamar karamin yaro, su duka dakyar aka fito dasu daga dakin. Dije na kamo Abu da babu digon hawaye ko daya fuskarta suka fito don bada damar a hada shi. Zuwa lokacin gidan ya fara cika da mutane, saida aka fito da gawar, Abu ta hango su sannan ta zabura ta mike. Dije ta rikota, amman karfin da take ji ba zai kwatantu ba. Matan duk da suke gabanta ta dinga tsallakewa saida takai tsakar gida inda aka shimfide Hammadi cikin sutturar Lubna sufyan Hausabook.com 245 da itace zata zamo ta karshe a duniyar kowa. Ana kokarin shigowa da munkarar da za'a saka shi ciki "Hammadi Am" Ta kira shi a karo na farko sunan na fitowa da zuciyarta da take da yakinin za'a binne tare da shi "Da kace mun hirar jiya bankwana ne, da ka fadamun sanyin jikinka tabin mutuwa ne. Dana zauna tare da kai, dana kwanta a gefenka ko bata dauke mu tare ba inji fitar numfashin ka..." Ta karasa can kasan makoshi "Allah ya amsa addu'arka, ban tafi nabarka ba. Kai kabarni...kai ka fara barina Hammadi..." Hawayenta suka rike sauran kalaman, a wajen ta durkusa tanajin karshen duniyarta yazo tare dana Hammadi. Bata san hannayen suwa ke kokarin dagata ba "Kubarni... Dan Allah kubarni" Lubna sufyan Hausabook.com 246 Ta roke su, sai suka saketa, amman tanajin su a gefenta. Har aka saka Hammadi a munkara aka fita dashi, ihun kukan mata na cika kunnenta "Allah ya yafe maka Hammadi Am... Allah ya hadamu a aljannar da kake hango mana tare da rabon da bamu samu ba anan" Idan tace bata ji barinta zaiyi a yan kwanakin nan ba zatayi karya, akwai bankwana a cikin duk wani abu da sukeyi, sai dai bata hango yau bane. Da suka sake kamata batayi musu ba, mikewa tayi suna janta zuwa dakin da ta fito. Yawan mutanen basu hanata jin wani irin fili da gidan yayi, har kirjinta take jin wannan filin, kamar Hammadi ya tafi da komai, a jikin Dije ta dora kanta tana jin yanda ta lalubi hannunta ta dumtse kamar tana son fada mata tana nan gefenta, babu inda zataje. Yanayi ne da bai hana mata jin kadaicin da zai kasance tare da ita har karshen rayuwarta ba. Sai dai mutuwar Hammadi cikar lokaci ce Akan kowa mutuwa cikar lokaci take jira Kaddarar su yanzun ne zata fara. Lubna sufyan Hausabook.com 247 Daga nesa suke jin labarin mutuwa, a wautar tunani irin nasa bata hango zumuncin mutuwa zai biyo takan wanda suka sani nan kusa ba. Sai dai kamar yanda ake fadine, rai bakon duniya. Musamman Yelwa da idan gari ya waye ta tashi, sai ta fito ta taka kafarta gidan sai taji wani abu a cikin kirjinta ya fadi, saita tuna shikenan, ba zata ga Hammadi ba, ba zai jata da hirar nan tashi mai cike da raha ba. Sai taji komai ya tsaya mata, a tare da kowa tana ganin yanda rashin Hammadi duk ya taba su, musamman Datti da yayi wata irin ramewa. Tashin hankalin su duka ya karu lokacin da Abu ta gama takaba tace ba zata iya zama a gidan ba, duk kuwa Julde da Saratu da akasa suka dawo don kar kadaici ya dameta "Gidan yayi mun fili Dije, kinsan darare nawa na rufe idona da fadan kar in bude su? Ko zan tarar da Hammadi? Banda abinda zan cike ramin da Hammadi yabar mun. Idan ina cikin gidan nan babu ranar da mutuwar shi zatayi mun sauki. Ina bukatar shakar iska daban da wadda ta Lubna sufyan Hausabook.com 248 cudanyu da ta shi ko kirjina zai rage ciwon da yake mun" Watakila yanayin yanda tayi maganar ne, ko kasancewar ranar karo na farko da tayi wata magana data nuna halin da take ciki. Babu wanda ya iya hanata komawa gidan dan uwanta da suka karbeta suna kuma bata daki. Sai akabar Saratu da Julde a gidan kawai. Julde da yake jin kamar an dibi wasu shekaru an kara masa da rasuwar Hammadi saboda yanda abubuwa da yawa suka koma karkashin kulawar shi. Saiya zamana duk wani abu da Hammadi ke kula dashi na daga dukiyar su ya koma hannun shi, ciki harda gadon Saratu, tunda Abu an fitar da ita, komai ya koma karkashin kulawar dan uwanta da ta koma gidan shi. Ya dauka girma a hankali yake zuwar ma mutum, tare da shekaru. Sai nashi ya dira batare da sallama ba, tare da auren Saratu da zuciyar shi ta karba a matsayin daya daga cikin kaddarorin shi duk da ya rasa yanda zaiji soyayyarta. Rasuwar Hammadi ta canza tsarin zamansu, batare da sanin dalili ba, ana fitowa da Lubna sufyan Hausabook.com 249 gawar sai ta fado mishi a rai, yanda ya kafafuwan shi suka dauke shi zuwa gidan ba zai tuna ba. Ya dai dauki mayafinta ya saka mata bayan ya kama hannunta ya mikar da ita "Lafiya? Me ya faru?" Da duka sauran tambayoyin da take jera mishi muryarta cike da firgici na wucewa ta cikin kunnuwan shi da wani irin yanayi. Bai tuna ya rufe gidan ba, ya dai riko hannunta sun taho. Har yau idan ya kalleta sai yaga rashin tabbacin da ya bayyana akan fuskarta, kafin wani yanayi da ba zai taba mantawa ba ya maye mata gurbinshi hadi da gunjin kukan da zaka san ya fitone daga lungun zuciyarta. Bai sake sakata a idanuwanshi ba sai ranar bakwai din Hammadi "Kaje ka dauki matarka ku koma gida" Dije ta fada masa, bai musa ba, inda ya saka kafafuwan shi nan take mayar da nata a duhun daren da babu hasken komai saina farin wata da taurari. Sun koma gida, ya tuna hawayen da suke cike taf da idanuwanta lokacin daya kunna musu fitila Lubna sufyan Hausabook.com 250 "Hakuri zamuyi Saratu" Ya fada yana ba hawayenta damar zubowa, ya kama hannunta, ya jata zuwa jikinshi yana riketa cike da tausayin daya bude masa hanyar shigar wani yanayin da ya canza akalar daren nasu. Ta amsa masa tambayoyi da yawa, ta kuma sake tabbatar masa da abu daya, aurenta kuskure ne, kuskurene badan bata cika mace ba, sai dan ita kadai ta masa kadan kamar yanda ya hanga, irinta guda hudu sun masa kadan. Sai dai in duk bayan wani lokaci zai sake su ya sake auren wasu. Bai san ta inda zai fara kauda idanuwan shi da zuciyar shi daga kan wasu matan ba. Kamar akwai wani abu a cikin jikinshi da yake saka shi jin son kasancewa da duk macen da zata gifta ta burgeshi. Ranar farko da ya labe a bayan ganin komai ya tafi dai-dai ya koma Kano, ya hada shimfida da wata ya tashi sai yaji kamar an dora masa wani dutse mai nauyi a saman kai, igiyoyin auren dake kanshi na masa wani irin dauri da harya dawo Marake bai sake shi ba. Musamman daya taka cikin gidan daya zama nasu yanzun, saiya ga kamar Hammadi na Lubna sufyan Hausabook.com 251 kallon shi, kamar bai rike amanar daya kamata ace yana rike da ita ba. Sai dai akwai abinda yake fisgar shi da nauyin shi yafi na dutsen da yake ji ya danne shi, daurin shi ya girmi igiyar auren Saratu "Yan duniya na binni, kayi harkarka hankali a kwance baka da tunanin komai" Ya tuna zancen wani direban babbar mota a irin hirarrakin su. Shima haka ya dauka, sai da tura ta kai bango, matsi yayi matsi yanajin yanda Saratu tayi ma bukatar shi kadan. Lokacin ya fara abotar sirri da yaran da yake jin Datti na kwashewa albarka yana kira da 'yan iska. Saiya fahimci ita lalacewa bata da wani layi a tsakanin binni da kauye, zabi kawai take bukata, na kaddarar da tafi karfin iko, ko na kaddarar da take zuwa da son zuciya. Saboda a cikin Marake da yake tunanin kowa ya san kowa, sababbin abokan shi suka tayashi binciko rayuwar da bai taba tunanin akwaita a kauye ba. Kowacce rana a cikin tana kara busar masa da zuciya tana nisanta shi da tsoron kar wani ya binciko sirrikan da yake boyewa. Ya fara Lubna sufyan Hausabook.com 252 ninkayar da baya tsoron nutsewa sam, saboda a idanuwan Julde bashi kadai bane ba, mutane da yawa sunayi, wanda aka sani da wanda ma ba'a sani ba. A cikin wanda aka sani din surutun wani lokaci ne, musamman shi namiji. Maza nawane a kauyen aka kama da haura gidaje kuma maganar ta shude a cikin tarihi? Wasu sababbin labaran na binneta? Matan da sukayi cikine ake rabawa da kauyen ba mazan da sukayi musu cikin ba. Daya daga cikin dokokin da al'ada ta shimfida da Julde yake ganin ba zai taba fahimta ba. Dokar tayi masa, saboda ta fifita zunubin da yake tunanin girma daya ne, a wani yanayin ma za'a iya kwashe kusan duka kason a mayar kacokan akan macen. Laifin da suka aikata da amincewar junan su zai juya ya koma kamar ita kadai tayi. "Kudin shi ta gani ba komai ba" Wasu zasu ce "Julde fa dan gidan Datti, ko babu kudi tabi kyau" Lubna sufyan Hausabook.com 253 Ta kowacce fuska idan asirin shi ya tonu yana da yakinin mutane da yawa zasu nema mishi uzururrukan da zasu rage girman laifin shi. Lokaci kuma zai dishe musu hasken laifin har saiya zamana kamar bai faru ba. Kamar yanda lokaci ya fara saka shi daina jin nauyin laifukan shi. Shisa zuwa yanzun bai damu ba, lamurran shi yakeyi hankali a kwance, a gefe daya yana gudanar da harkar dukiyar su cikin basirar da ta dauke hankalin Datti daga sauran lamurran shi saboda ganin da yakeyi nutsuwar da yake masa hasashen samu tare da cikar kamalar da a ganin Dattin inuwar aure kan samar, ta tabbata. * Yelwa zata kira sake haduwarta da Kabiru daya daga cikin abubuwan da suka fi karfinta, irin barin makauniyar da kaddara take yiwa mutane batare data duba ta ina takai dukan ba. Idan tace tunda ta hadu dashi daga farko bai dinga ziyartar tunaninta ba zatayi karya. Tana kwance, tana zaune, tana hidimar yau da kullum. Sai taji shi yana fitowa daga inda yake cikin dumbin tunaninta yana yo sama, yana sakata tunanin abinda yake dashi a fuskar shi Lubna sufyan Hausabook.com 254 da bata taba gani tare da kowa ba. Yanayin dake cikin kananun idanuwan shi da bata taba tunani ba. Sai mutuwar Hammadi ta binne mata shi har sai lokacin da ta sake ganin shi, ranar tana hanyar komawa gida daga aiken da Dije tayi mata "Yelwa..." Ya kira sunanta da murmushin shi, yana tuna mata da lobawar data kula bari daya na kuncin shine yakeyi duk idan yayi murmushi, kananan idanuwan shi na sake shigewa ciki. Bakine don baki, amman daga inda take tsaye zata iya kula da murjewar fatar shi da kyallin da yakeyi na alamar bai tashi cikin wahalar rayuwa ba ko da ba masu kudi bane, ba zasu rasa rufin asiri ba. A kasan yanda ya kira sunanta kamar ya santa, tare da murmushin shi kamar akwai wata alaka a tsakanin su "Daga ina haka?" Ya jefeta da tambayar da tasata ganin karfin halin shi, har lokacin da murmushi a fuskarshi "Aikena akayi" Lubna sufyan Hausabook.com 255 Ta amsa tana tsintar kanta da dorawa da "Zan koma gida..." Kai ya jinjina "Zan iya rakaki?" Kafin ya gama rufe bakin shi ta girgiza masa kai, kirjinta na wata irin dokawa. Murmushin shi cike yake da fahimta "Ki gaida gida. Nagode" Ya fadi yana juyawa, tabi shi da kallo, kamar haduwar zata tsaya iya nan. Kamar ba zai samu wajen zama a zuciyarta ba. Kamar ba zata dinga neman duk wani uzuri da zaisa ta fita don kawai ta ganshi ba. Kwanakine suka dinga hadewa cikin satika har ta bude ido da soyayyar Kabiru da sanyin halin shi ya dasa mata. Mazan da suke cikin rayuwarta basu da yawa tun tasowarta. Datti ta fara dubawa a matsayin mudubi, sai dai tun kafin tayi hankali Hammadi yasa ta fara dora ayar tambaya akan halaye da yawa na mahaifinta, a cikinsu harda rashin hakurin shi. Lubna sufyan Hausabook.com 256 Sai Julde da ya dauki taurin kai irin na Datti, amman idan ba ka kure hakurin shi ba, zaka dade baka ga bacin ran shi ba, sannan abinda duk yaso yi hanashi kan zama rikicin da rayuka da yawa sai sun baci. Sai Bukar, Bukar bawan Allah, Bukar da nisa bai sauya komai daga halayen shi ba. Ziyarar duk da yake kawo musu sai taga kamar yana kara yin sanyi ne, ko ta dan tsukun bayan rasuwar Hammadi sai da yanayin shi ya dawowa da kowa mutuwar sabuwa, saboda kuka yayi, kuka irin na maraici, kukan da zakayi zaton daga jikin Hammadi ya fito. Harya koma duk idan ta ganshi sai taji kwalla ta cika mata idanuwa, saboda yanda yakeyin komai da sanyi-sanyi, yanda harya tafi mutuwar Hammadi bata gama sakin shi ba. Amman a cikinsu bata ga mai kama da Kabiru ba, bata san ta inda zata fara ba idan akace ta zayyana halayen shi. Watakila haka So yake, baka jin komai, baka ganin komai sai shaukin da kake ciki. A yanzun idan laifi Kabiru yayi zai wahala ta gani. A fuskar shi da mutane da yawa zasu kalla ba adadi kafin su ga abu daya me kyau taga tarin abubuwan da suka burgeta. Soyayyar da Lubna sufyan Hausabook.com 257 take masa ta kara haska mata abubuwa da yawa tare da shi. "So banzan abu ne Yelwa" Saratu ta taba ce mata, kalaman sun bata dariya a lokacin, bata jin ta fahimce su, a cikin kanta basu da wata ma'ana. Amman yanzun sai ta kirga su, banda sunanta, kalmomi hudune suka tashi jimlar, kalmomi hudun da zata fassara a cikin shafuka masu yawan gaske "Nagaji da haduwa dake a wajajen da nake raba hankalin ki da duban hanya ko wanda kika sani zai ganmu. Nagaji da boyewa kamar abinda muke bashi da kyau Yelwa...ina son taka kofar gidanku..." Ya fadi yana hargitsa zaman lafiyar da suke ciki, yana kusanto mata tshin hankalin da take hangowa daga nesa "Baba na...Baba na ba zai baka aure na ba" Ta fadi, kalaman na komawa cikin kunnuwanta suna sake hargitsa duk wani lissafi da yake tare da ita. Sai numfashinta ya soma yi mata barazana, idan ta shaki iskar sai taji bata kaiwa Lubna sufyan Hausabook.com 258 har cikinta balle ta karasa ta rarrabu a jikinta. Duk yanda tasan cewa Datti ba zai bar auren su da Kabiru ba, bata bar kanta ta hango meye makomar hakan ba. "Kibar ni in gwada, ya zaka karaya da yaki tun bakasan su waye abokan karawarka ba?" Ya karasa da nufin bata dariya. Sai dai ita da nishadi sunyi hannun riga a wannan lokacin. Jininta akan farce yake har juma'ar da Kabiru yace zai shigo Marake da dan uwan mahaifin shi kasancewar shi maraya, sai suyi masa jagorar tambayar aurenta a wajen Datti. Daren juma'ar na zama na farko data kwatanta sallar daren da taji ana yawan fadar anayi don neman biyan bukata, bata san raka'a nawa ya kamata tayi ba, goma ta fara, sai taga kamar tayi kadan, da ta fara jerowa saida gwiwoyinta sukayi sanyi. Akan dardumar ta kwanta, a karo na farko hawaye na silalo mata. Tana son Kabiru, wani irin so da bata da kalaman misalta shi. Da safiyar ranar komai ta kasa ci "Kinyi zururu, baki da lafiya ne?" Lubna sufyan Hausabook.com 259 Dije ta tambayeta, sai ta matsa jikinta tana kwanciya akan cinyarta "Kirjina ciwo yake Daada, kuma kamar zazzabi na son kamani" Da yawa zasu iya kiran shakuwar da tayi da yaranta a matsayin sangarta su, wasu ma suna ganin bata da kunya. Musamman yanda bata boye soyayyar da take musu ko a gaban waye. Har Julde da auren shi zai iya shigowa ya zauna a tabarma ya zame jikinshi ya dora kanshi a cinyarta "Daada nagaji" Yakan fadi, wasu ranakun zaiyi har bacci. A cikin su ukun, Bukar ne mai kunya, ko da kunyar shi bata hana masa kwanciya a jikinta ba, raunin zuciyar shi zai hana, zaiga kamar yayi mata nauyi. Tunda tsintsiyar shara bata dagawa idan har yana cikin gidan. Bukar dinta da kewar shi take cika zuciyarta lokutta mabanbanta, tafiyar shi bata taba tsaya mata irin wannan karin ba, ba don yanda mutuwar Hammadi ta tabashi ba, wannan yanayine da suma sun shige shi, ta kuma son a hankali ciwon zai ragu. Sai dai Lubna sufyan Hausabook.com 260 kewar tana nan daram, tunda kaunar da take tsakanin su mai

Chapter 10 of 27