Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tayi tana fita daga kitchen din, wata kujerar Salim yaja ya zauna, saboda yasan Madina zatayi masa magana idan yaci kifin a tsaye. Kofi ta samu tana karasa ta bude fridge ta dauko ruwa ta zuba masa a ciki tana mika masa "Nagode" Ya furta a hankali bayan ya karba, itama taja kujera ta zauna, kamar hakan wayarta take jira ta fara ruri, tana dubawa taga Nawfal ne ya kirata video call. Dagawa tayi tana murmushi "Hamma..." Lubna sufyan Hausabook.com 449 Ta kira, lokaci daya Salim yaji dandanon kifin da yake bakinshi ya dauke gabaki daya. Zuciyar shi tayi nauyi a cikin kirjinshi, bayaso tana kiran kowa da wannan yanayin banda shi, wannan murmushin da yake fuskarta ya kamata ace bai kai haka girma ba tunda bashi take yiwa ba. Kishine yake damun shi, kishi da bai taba tunanin yanada irin shi ba, kishin da batama san yanayi ba "Kana ina haka? Ina Daada?" Ta tambaya "Jaan ta koroni, dole saina fito na sha iska wai, tana tare da Daada, bacci takeyi sanda na fito dai... Me kikeyi ke?" Juya camera din tayi tana haska masa kitchen din, kafin ta sake dawo da ita zuwa dubanta "Ina zaune a kitchen ni da Hamma Salim...ni ina girki, shi kuma yana cin kifi" Dariya Nawfal yayi Lubna sufyan Hausabook.com 450 "Aikin dare yayi ya dawo gida ya kwanta bacci maimakon ya nemi abinci ya tashi da yunwa ko?" Dariya Madina takeyi tana daga masa kai "Ina zaune a kitchen din Bajjo, ranka kuma zai baci" Dariya Nawfal ya sakeyi, Madina ta mikawa Salim din wayar, ya karba lokacin da ya sake kai wani kifin bakin shi, Nawfal kuma yana gaishe dashi, gira Salim ya hade masa a maimakon amsa gaisuwar yana sakashi sake yin dariya "Yaushe zaku dawo?" Salim ya tambaya bayan ya kara jin cewa Daadar ta samu sauki "Inajin nan da sati daya haka ko kwanaki goma idan Allah ya kaimu" Kai Salim ya jinjina "Ka kula da kanka..." Murmushi Nawfal yayi "Jaan na kula dani" Lubna sufyan Hausabook.com 451 Dakuwa Salim yayi masa yana yatsina fuska cikin yanayin da yasa Nawfal din yin dariya, yanke kiran yayi kafin ya mikawa Madina wayar. Karba tayi sai taji zuciyarta kamar batayi mata dadi da abinda Nawfal din ya fadi, duk da yayi maganar ne cikin sigar tsokana. Amman akwai gaskiya a kasan hakan, akwai kuma yanayin da yake nuna nishadin da fadin Murjanatu na kula dashi ya samar masa "Ki duba girkin nan koya totse" Salim ya fadi ganin tana jujjuya wayar a hannunta kamar tana jiran Nawfal din ya sake kiranta, ta kuwa yi masa murmushin nan nata tana sakashi sauke numfashi. Batayi masa musu ba ta tashi tana dubawa. Sai ta dauko lettuce din da ta wanke ta saka shi a kwando dan ruwan ya tsane ta fara yankawa. Ko da Salim ya gama cinye kifin shi bai bar kitchen din ba, komawa yayi ya zauna kan kujerar daya tashi yana sakata bashi labarin littafin da take karantawa, idan za'a karbi wukar hannunta a saka masa a wuya ba zai iya fadin me littafin ya kunsa ba. Hankalin shi yana kanta, amman kalaman da take fada basa karasawa kunnuwan shi, yanayin Lubna sufyan Hausabook.com 452 yanda labbanta ke motsawa, yanda takeyi da hannayenta idan tazo wajen da yayi mata dadi a labarin, da dariyarta sune abinda yake kallo. Baya ganin komai sai kyanta da ba kowa bane zai gani farat daya. Yana so rana daya, ya cire mata gilashin nan, ya rabata da kayan nan, ya ganta a cikin shigar atamfa, hannuwanta masu kyan nan da kunshi, ya ganta a cikakkiyar mace saboda a cikin kanshi daya hasaso tayi kyau, wani irin kyau mai sanyi. Ko da ta gama girkin ma sai dakyar ta samu ya bar kitchen din bayan ta zuba masa. Ta wanke yan kwanonin da ta bata, ta goge ko ina tana fitowa falon "Ke ba zaki ci ba?" Kai ta girgiza masa "Sai anjima, banajin yunwa ni kam" Da ya gama cin abincin ma ta kusan mintina sha biyar tana fama dashi kan yaje ya kwanta saboda yana bukatar baccin "Zan kwanta anan" Kai ta girgiza masa Lubna sufyan Hausabook.com 453 "Anayin kwakkwaran motsi tashi zakayi. Dan Allah ka kaje ka kwanta Hamma, nima baccin zanyi" A fuskar shi baiso ba, saboda ji yake kaman daga bangaren Saratun zuwa nasu yayi masa wani irin nisa, nisan da bayaso a tsakaninsu. Amman da gaskiyarta, ya gaji sosai, yana kuma bukatar baccin. Yana tafiya ta mike itama zuwa dakin daya zama nata yanzun a cikin gidan. Kai tsaye bandaki ta wuce ta watsa ruwa ta fito daure da towel, sai da ta shafa mai sannan ta saka kaya, sanin babu wanda zai shigo yasa tabar na jikinta, tunda lokutta da dama tana amfani dasune a matsayin na ciki, ta dora wasu akai, gara ta saka kaya hudu a jikinta komin zafin da akeyi in har ba zasu fito da wata alama ta halittarta ba. Sai dai abinda batayi tsammani bane ba ya faru, tana tsaye aka murda hannun kofar aka kuma bude duka cikin abinda bai shige dakika biyu ba, numfashinta ta dauke lokacin da idanuwanta suka sauka cikin na Julde. Shi ya fara sauke nashi yana kallonta, tun dawowarsu daga airport rakiyar Daada yake jin shi wani iri, yake Lubna sufyan Hausabook.com 454 jin shi kamar yana yawo a cikin wata kwalbane da baisan yanda zai fito daga cikinta ba. Baccin kirki baya samu, daya kwanta ya fara bacci sai yaji ya farka, idan za'a tambaye shi ba zai iya fadin dalilin farkawar tashi ba. "Ka kwantar da hankalinka Julde, ance ta samu sauki. Da yardar Allah babu abinda zai sameta" Saratu tace masa satin daya fita da ta farka tsakiyar dare ta ganshi a zaune. Kuma tanata kokari ya kula tun tafiyar Daadar wajen ganin ba suyi fada ba, watakila ta kula da yanda baya cikin hayyacin shi. Sai dai ya kalleta kawai, tunda baisan ya zai fada mata ba rashin lafiyar Daada bace kawai matsalar shi. Taya zai fara fada mata abinda shi da kanshi bai gama sanin menene ba? Yanajin kamar wani abu na sarke dashi, ko tuki yake yanajin abin gab dashi, idan ya sauka yana tafiya da kafarshi saiya waiga yafi a kirga saboda ji yake kamar abin na biye dashi. Ga wani irin tsoro da yake cike da zuciyarshi da baisan daga inda yake tasowa ba. Yanzun ma yana kasuwa yaji ya nemi yar nutsuwar da yake tare da ita ya rasa, yayi niyyar Lubna sufyan Hausabook.com 455 biyawa wani wajen kafin gida, inda zai samu wata nutsuwar ta daban, sai ya kasa. Saboda abinda yake nema yana da tabbacin ba zai samu a tare da kowacce irin mace bace zata fado masa. Kamar ya fasa ihu haka yake ji sanda ya shigo gidan, yaje dakin Saratu ya tura yaganta kwance tana bacci, sai ya karasa dakin Lukman ya tura yaji shi a kulle, hakan na tuna masa da kowacce rana ce, Lukman din yana da makaranta. Wani abune ya tuna masa Madina na gidan, kawai so yakeyi yayi magana da wani, wani wanda yake ji a zuciyar shi watakila ya samu nutsuwa. Ko idanuwanshi ya rufe da wahala ya lalubo hotunan Madina guda uku a cikin kanshi da ta saka wasu kaya na mata, tunda ta fara hankali kuma duk ganin da zaiyi mata banda hannuwanta da fuskarta baya iya tuna yaga wani abu. Sai yau da baisan yanda zai fara hana idanuwanshi yawatawa akanta ba. Ganin da yake mata gajera saiya dauka kamar Adee take itama, bambancin nasu yana tare da shigarsu da ta bambanta. Tunanin shine da bai taba yi mata kallo na biyu ba ko idanuwan shine bai sani ba, Lubna sufyan Hausabook.com 456 amman akwai abinda ya kange shi daga hasaso cewa abinda Madina take boyewa a karkashin shigarta kenan. "Daddy..." Muryarta dake rawa ta kutsa cikin tunaninshi tana saka shi dakyar ya dago da idanuwan shi ya kalleta "Ka dawo? Sannu da zuwa... Inzo in zuba maka abinci?" Rashin sanin abinda zai fada yasa shi daga mata kai "Barin saka kaya in fito" Ta furta tana murmushi, haka kawai taji zuciyarta na mata rawa, taji wani tsoro ya ratsata irin wanda bata taba tunanin zata jishi idan Julde yana tsaye a wajen ba. Yanda saida idanuwan shi suka sake yawatawa a jikinta kafin ya ja kafafuwanshi ya fita ya saka tsikar jikinta mikewa cikin yanayi marar dadi, sai taji kamar wata dauda ta manne mata. Kallo ne da baiyi mata dadi ba, kallo ne daya sake ninka tsoron da yake zuciyarta ya kuma raunana Lubna sufyan Hausabook.com 457 kallon da take yiwa Julde batare da ta sani bama. Yana fita jikinta har rawa yakeyi ta karasa ta kulle kofar tana murza mukulli, zuciyarta a makoshinta lokacin data gama saka kaya ta fito tana nufar kitchen. Abincin ta hada masa tana kai masa dining table, daga nan inda take tsaye tace masa "Daddy ga abincin naka" Tayi nufin komawa dakine sanda taji muryar shi na fadin "Ki bani ruwa" Ta manta da ruwa, kitchen din ta sake komawa ta dauko kofi da robar ruwa, ta ajiye robar tana shirin ajiye kofin taga ya mika mata hannu, batayi tunanin komai ba ta mika masa kofin, yanda hannunsu ya hadu kadan ya rage kofin ya subuce mata da Julde bai rike ba, zuciyarta taji ta sake yin wani tsalle kamar tana kokarin rabuwa da kirjinta. Da sauri ta juya tana barin wajen Lubna sufyan Hausabook.com 458 "Yanda ka kunyata ni Julde... Allah ya kunyata ka a idanuwan mutanen da suka fi komai muhimmanci a wajenka..." Julde yaji kalaman sun dawo masa lokacin daya bi bayan Madina da kallo kafin ta bacewa ganin shi, idanuwan shi ya runtsa ya sake bude su yanajin jikin shi ya dauki wani irin dumi Sai dai wata kaddarar yanzun ne shafinta zai bude...! Duk labarun tashin hankalin da yake ji basu taya shi shiryawa zuciyar shi wannan da yake so wani ya girgiza shi yace masa mummunar mafarki ne yakeyi ba, ko a tarihi ba zai tuna kunnuwan shi sun tsinkayo mishi wani yana bada labari kwatankwacin abinda yake gani yanzun ba. A tsaye yake akan kafafuwan shi, har yanzun yana da tabbacin akan kafafuwan shi yake tsaye saboda yana jin sunyi sanyi. Duniyar da yake tsaye akanta ne ta birkice dashi tana nuna masa iyakarsa. Kamar awanni ba kasa da dakika ba haka yaji tsakanin rufe idanuwan shi da yayi ya sake bude su kamar yana son wani Lubna sufyan Hausabook.com 459 sashi na zuciya ko kwakwalwar shi su karyata masa abinda yake gani. Mintina nawa ne daga bangaren su zuwa nan din, duka anyi awa da fitar shi? Ya za'ayi ace gabaki daya duniyar ce tayi juyin waina dashi haka? Yaune fa, dazun nan, ya dawo daga wajen aiki a gajiye, ya wuce bangarensu kai tsaye yayi wanka ya sake kaya, maimakon ya kwanta yayi bacci, da cajar wayarshi da ya dauko danya makalata sannan ya kwanta ya baro bangaren su zuwa na Saratu, saboda yana son ganin Madina, sai dai guga takeyi daya kira wayarta. Takawa yayi daga falon yana karasawa har dakinta ya kwankwasa, sai da ta bashi izinin shiga sannan ya tura kofar. Dakin Adee ne ada, banda litattafan Madina da suke ajiye kan durowar gefen gado, kusan dakin yana nan yanda ya san shi. Haka kawai sai kewar Adee din ta saukar masa kamar basa waya kullum. Kusan rabin rayuwarta ita da Nawfal a makaranta sukayi ta, saboda itama har sakandire dinta makarantar kwana ce. Amman dan lokacin da take gida, yayi kewar wannan lokacin, fadansu saboda bata san Lubna sufyan Hausabook.com 460 yanda zatayi abu a hankali ba, ko zaune yake a falon saiya sani idan itace take wanke wanke, zai iya rantsewa cokali take dauka tana kwalawa a jikin kwanoni saboda ta saka shi magana, ko tafiya zatayi saita dinga jan kafafuwanta. Idan bai kai mata duka koya zageta ba batajin dadin. Adee ce duk a cikin kannen shi zata zauna kan kujerar da yake kai, ko mai zaman mutum dayace saita zauna a hannunta. Har tambayar Saratu yakeyi "Nanna anya baki haifo Adee bane don kawai ta takuramun?" Ko ita Adee din gab da bikinta da ya kai mata wata masga sai da tace "Na kusa bar maka gidan Hamma, sai kayi kewata" Gani yake kewarta na me zaiyi? Gashi kuwa yanzun, dakinta kawai ya gani amman zuciyar shi tayi wata irin matsewa a cikin kirjinshi. Kewarta yakeyi sosai. A bayan zuciyarshi ya adana cewar ya kamata ya biya yau ko zuwa Lubna sufyan Hausabook.com 461 gobe ya ganta. Tunda kwana biyu bata zo gidan ba "Na kusa gamawa... Saura guda biyar" Madina ta fadi tana masa murmushi, zaune take bakin gado tana gugar a kai, kofar Salim ya sake budewa sosai, wannan dokar Saratu ce tuntuni, in dai wani a cikinsu zai shiga dakin Adee to kofar a bude za'a barta, sannan kamar yanda tun suna hade waje daya, ba'a ware musu bangarensu ba, akwai kujeru a nasu dakunan, dakin Adee ma akwai. Babu mai hawar mata gado in dai sun shiga. Da aka ware musu bangarensu kuma, da hankalin shi dai zai kirga lokuttan da Adee ta taka bangaren su, sai dai su suzo na Saratun. Har yanzun kuma akwai kujerun guda biyu, daya daga ciki yaja yana zama. Yanajin yanda zuciyar shi ta nutsu da kusancin da yake da shi da Madinar "Bacci ya kamata ace kanayi Hamma" Kafadarshi daya ya makale mata saboda bayason yin magana, bayason cewa komai. Da Lubna sufyan Hausabook.com 462 zai samu, baccin zaiyi, daki daya da ita. Baccin da yafi kowanne yi masa dadi da nutsar dashi shine lokuttan da yayi su a kofar gidan Daada, a cikin motar shi, sanin tana gefen shi a zaune tana kallon shi, ko tana danna wayarta, ko tana karatu. Tana dai gefen shi, koma me ta zabi tayi kafin ya tashi, awa dayane, wasu ranakun awa biyu. Amman idan ya tashi sai yaji duk gajiyar da ya kwaso ya nemeta ya rasa. Madina na da wannan tasirin a rayuwar shi. "Ka ci abinci?" Kai ya daga mata, meatpie ne daya siya da daddare, guda biyu ya rage, shine ya ci da safen kafin ya baro asibiti, kuma bayajin yunwa. Kai ta daga masa, dankali da kwaine da shayi sukayi da safen, Khalid ma da nashi ya tafi don yace ya makara, Lukman kuwa a kitchen din ya tsaya yana ci da sauri-sauri, shima saida tace ta zuba masa ya tafi dashi ya girgiza mata kai. Ta zauna kenan a dining table zata karya Julde ya fito, haka kawai ta tsinci kanta da mikewa bayan ta fito, ta dauki plate din. Bayan sunanta daya kira ba zatace ga abinda yake fada ba, saboda yanzun idan ta ganshi sai taji zuciyarta na mata rawa. Ya Lubna sufyan Hausabook.com 463 dai miko mata wani lemo da ta amsa tana shigowa daki dashi. Yanzun ne ma ta hango shi ta mika hannu ta dauko, robar tayi mata kyau sosai, lemon na mangwaro ne, ta saka karfinta wajen kwance murfin, sai taga ya bude kamar a kwance yake daman, ko dan wasu robobin ba'a datse su da karfin nan. Kurba tayi "Wanne irin lemo ne?" Salim ya tambayeta, sai da ta hadiye ta kara saboda dandanon yayi mata dadi sannan ta amsa shi "Na mangwaro ne, Daddy ya bani dazun... Zaka sha?" Kai ya girgiza mata, yana dai kallo harta shanye duka robar a gefe suna cigaba da hira jefi-jefi "Bacci kake ji Hamma, kamata yayi ace ka kwanta" Ta furta ganin yayi hamma a tsakanin maganar da sukeyi tafi a kirga, bai amsa ba, kallonta kawai yayi. Itama kanta take ji kamar an dora Lubna sufyan Hausabook.com 464 mata dutse, ga wani lumshewar rashin dalili da idanuwanta sukeyi mata, ko bashin bacci taci baya mata haka, balle ta samu wadataccen bacci "Ke ma baccin kike ji, karatu kika tsaya jiya ko?" Kai ta girgiza masa, badon bata so ta tsaya karatun ba, sunyi waya dashi yana asibiti yace mata ta kwanta tayi bacci saboda tayo masa korafin kanta yayi mata nauyi. Kuma sai tayi abinda yace din "Kai kace in kwanta Hamma" Tayi maganar kamar bata da wani zabi daya wuce bin umarnin shi, hakan ya sanyaya wani bangare a cikin zuciyar shi "Kawai dai wani baccin ne ya kamani yanzun" Ta dora da fadi tana kara gyara zamanta. Saiya mike "Ki kwanta, nima bari inje in dan samu baccin... Mu fita yawo anjima?" Ya karasa maganar da alamun yana jiran amsarta, kai kawai ta iya daga masa. Shi yaja mata kofar daya fita daga dakin. Kuma kai tsaye Lubna sufyan Hausabook.com 465 bangaren su ya wuce ya kwanta a falo kan doguwar kujera, bayajin yayi baccin awa daya yaji ya bude idanuwan shi, dan ya dauki wasu mintina yana neman dalilin yankewar baccin nashi ya rasa. Wayar shi daya laluba don ya duba lokaci yaji bata gefen shi yasa shi tashi zaune yana tunanin inda ya ajiyeta. Saiya tuna ya barta dakin Madina, abinda yaso yayi, ya tura kofar a hankali, ya mika hannu ya dauko wayar shi, ya rufo mata a hankali, dan duka fatan shi yana kan ta samu baccin. Shisa har yanzun yake tuhumar kanshi ko mafarki yakeyi. Yake addu'a da yakinin da bai taba yi ba tunda yake a rayuwar shi, abinda yake gani a gabanshi ya kasance mafarki ne "Akwai macen da zata gifta ta gabanka baka bita ba Julde? Kana da wani layi in dai akan mace ne da ba zaka iya ketarewa ba?" Maganganun Saratu a wani dare kan fadan da suka saba ita da Julde suka dawo masa. A lokacin bai gane abinda take nufi ba, asalima kalaman sun tsaya masane saboda kamar basuyi masa dadi ba, kamar tunda yasa Lubna sufyan Hausabook.com 466 kafafuwan shi cikin takalmin Julden yake kokarin fahimtar shi, ya dauka zai tsaya kan mace dayane, duk sanda zai bi wata zai raya a zuciyarshi itace ta karshe, sai wani abu ya sake jan shi, wani abu mai wahalar fassarawa, wani abu da wanda ya tsinci kanshi cikin yanayin bukata irin tashi ce kawai zai fahimta. A lokacin sai yake ganin inda itama Saratun zata saka kafafuwanta a cikin takalman Julde data yi masa uzuri ko kadan ne, data gane abinda yakeyi abune mai wahalar bari, da ta gane akwai darare mabanbanta daya kudurci cewa shine daren shi na karshe tare da wata mace da bata halatta a wajen shi ba, amman saiya kasa. Sai wani abu ya sake mayar dashi, wani abu mai girman gaske. Wannan ne layin da take magana a kai daman? Layin da komin lalacewar da kayi bai kamata ace ka tsallaka ba? Ashe haram kala-kala ne? Girman wani ya kamata ace baka gwada dauka ba saboda ba danne ka kawai zaiyi ba, harda makusanta zai hada idan ya tashi. "Banyi mata komai ba" Lubna sufyan Hausabook.com 467 Julde ya sake fadi yana kallon Salim, a gefe daya kuma yana dawo da Salim din cikin hayyacin shi yana kuma tabbatar masa da ba mafarki bane ba, abinda yake gani gaskiya ne. Idanuwan shi Julde ya raba daga kan Salim yana mayarwa akan Madina da take kwance da alama batama san duniyar da take ba. Ya sake mayarwa kan Salim, jikinshi bari yakeyi, ba kuma waje ba, har cikin tsokar shi yakejin hakan, zuciyarshi na wani irin bugu da tun halittarta wannan ne karo na farko data taba yi masa haka. Ya dade yanajin shi kamar wanda wani abu yake bibiya, kamar bacci yake yana mugun mafarki, yanzun kuma da yaji ya farka saiya taradda mafarkin ya biyoshi har wannan duniyar ma. A karo na farko a tsayin lokaci da yaji ya furta "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" A cikin kanshi, yana shirin sake karantowa sallamar da ta karade falon har suna ji daga inda suke ta hana shi "Madina!" Lubna sufyan Hausabook.com 468 Khalid ya kira da alamun murmushi a muryar shi, tun jiya Nawfal yace masa ya zauna cikin shirin zuwa dauko su daga airport don zasu kamo hanya a jiyan, zasu tsaya Abuja su kwana saboda Murjanatu, yau din zasu biyo jirgin Kano, amman karya fadawa kowa saboda suna son ba Madina mamaki. Saurin da yakeyi kenan da safe, ya karasa wajen aiki, akwai takardun da suke bukatar kulawar shi, ya kuwa gama akan gaba, dan yana fita daga office, kiran Nawfal din na shigowa wayar shi, ya kuma ga lambar shice ta Najeriya, alamar sun karaso. "Daada kamar dai kinje yawon shakatawa ba jinya ba, irin wannan karo haske da kiba haka? Gaskiya da na sani na biku" Ya furta cikin sigar tsokana, har ranshi yana jin dadin ganin saukin data samu, dariya kawai takeyi, da alama murnar dawowa da kuma ganin shi ta hana tsokanar tashi tasiri, ko da ya sake cewa "Bakinki yaki rufuwa Daada, nifa auren nan bawai inayi bane ba, duk kyan nan da kika kara" Lubna sufyan Hausabook.com 469 Hannu takai tana kamo kunnen shi hadi dayin dariya, shima dariyar yakeyi yana fadin zata cire masa kunne dan inya tashi kara aure ace ba za'a bashi ba "Batare da ita kuke ba?" Khalid yayi tambayar yana kallon Nawfal "Ita wa?" Nawfal ya bukata duk da ya gane cewa Murjanatu yake tambaya "Anty na" Dariya Nawfal yayi "Tare muke, zata karaso gobe ko jibi In shaa Allah, kasan ta dade rabonta da nan, to ta tsaya wajen yan uwanta a Abuja..." Daada taso su wuce da ita gidanta ne kai tsaye, Khalid yace "Daada so kike Madina ta dauki gaba damu? Ai mu biya mu dauketa kawai sai mu tafi mu sauke ku tare, bata fa walwala tunda kika tafin nan, sai kince a cikin bare kika barta ba 'yan uwa ba" Lubna sufyan Hausabook.com 470 Murmushi Daada tayi, itama kewar Madinar na danneta, dan kwanakin nan kullum sai tayi mafarkinta, ko safiyar yau dan baccin daya dauketa a cikin jirgi, mafarkin Madina ne ya farkar da ita, zuciyarta kuma sai tayi mata nauyi, lokacin daya rage a tsakaninsu take jin kamar yayi mata nisa fiye da kullum, kamar ba'a hanyar gida suke ba. Shisa suna shiga cikin gidan, Khalid ya kwala mata kira Daada taji kiran har cikin zuciyarta, ganin inda Khalid ya nufa, Nawfal na rufa masa baya yasa Daada dinma taji tana so ta karasa don ji tayi ba zata iya jira har Madina ta fito ba. "Madi..." Khalid ya soma, ganin Salim a tsaye yasa maganar koma masa "Hamma..." Ya kira da alamar tambayar me yakeyi a tsaye haka a wajen a cikin idanuwan shi, fuskar Salim din Khalid ya kalla yana ganin wani abu a shimfide akai da yasa karawa bugun zuciyar shi gudu, haka kawai kafafuwan shi suka soma yi Lubna sufyan Hausabook.com 471 masa barazanar kasa daukar shi ta hanyar yin wani irin sanyi "Me ya faru? Menene?" Nawfal yake tambaya yana wuce Khalid ya karasa inda Salim yake, sai lokacin Salim ya motsa tun bude dakin da yayi, sai dai ya motsa a makare dan har Nawfal din ya karasa, ya kuma ture hannun Salim da yake kokarin hana masa ganin meye a cikin dakin. Idanuwan shi ya fara runtsawa yana yo baya kamar an watsa masa ruwan zafi, yanda zuciyar shi take dokawa na saka shi neman taimakon bangon wajen don dai-daita tsayuwar da take neman gagarar shi "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ya tsinci kanshi da furtawa, yana sake runtse idanuwan shi gam, yana maimaitawa cikin sallamawa ga Ubangiji da neman taimakon Shi wajen bacewar abinda yagani daga duniyar shi na har abada "Hamma" Khalid ya kira, tsoron da yake cike da zuciyarshi na bayyana a muryar shi, kai Salim yake girgiza Lubna sufyan Hausabook.com 472 masa, ba saiya karaso ba, ba sai yaga abinda zai canza duniyar shi na har abada ba, amman ya kasa kin karasawar, cikin dakin ya shiga gabaki daya, yana kuma yin abinda su duka suka kasa, karasawa har inda Madina take kwance yaja mayafin da yake kan gadon ya rufa mata a jikinta "Ban mata komai ba..." Julde ya furta yana kallon Khalid, rigar shi da take ajiye a gefe Khalid ya dauka ya mika masa, ganin bai karba ba yasa Khalid kallon shi, wani abune a cikin idanuwan Julden da ba zai fassaru ba, kamar shima neman wanda zai tambaya abinda yakeyi a tsaye a dakin yakeyi, kamar kuma neman wanda zai jijjiga shi yace masa mafarki yakeyi yake nema "Kasa rigarka..." Khalid ya fadi muryar shi na fitowa a raunane, karba Julde yayi yana mayarwa, sai yakejin nauyin rigar tare da wani abu daban na ratsa shi, tsikar jikinshi ta shiga mikewa, da fankar dakin ta kada, sai yaji saukar iskar a jikin shi da wani irin yanayi, kamar tun shigowarshi dakin Lubna sufyan Hausabook.com 473 wannan ne karon farko daya san da zaman fankar, sanyi yakeji, sanyi yakeji har baisan hakoran shi na haduwa da juna ba balle jikin shi da yake bari "Daddy" Khalid ya kira yana kai hannu ya rike damtsen hannun Julde dashi, amman yanayin da Julde yake ji na sanar dashi karshen komai yazo, ga numfashin shi ya daina kaiwa inda ya kamata, iskar fanka na kadawa tunda yanajin sanyinta na kara masa wanda yakeji, amman bata kaiwa hancin shi balle idan ya shaka ta wadace shi, rufe idanuwan shi yayi da niyar ya budesu, amman sai wani duhu na ban mamaki ya lullube masa komai. Khalid na rike da hannun shi yayi kasa yanajan har Khalid din da yake kiran sunan shi a wahalce. Salim na kallon su, yana kallon Khalid na jijjiga Julden amman ya kasa motsawa balle ya kai musu wani taimako. Daada data yi tsaye inda take ma batayi wani yunkuri ba, jikinta ya bata koma menene ba abinda zata so bane ba, zuciyarta tayi raunin da bakowanne tashin hankali zata iya dauka ba Lubna sufyan Hausabook.com 474 yanzun, tana kuma da tabbacin wannan tashin hankali ne da zai iya karasa abinda yayi saura a cikin kirjinta. Duk da wasu zasuce wanne dare ne jemage bai gani ba? Amman ita tasan baiga daren mutuwar shi ba, wannan kuma dai-dai yake da hakan a wajenta "Me yake faruwa ne Daada?" Saratu da ta shigo gidan take ta sallama harta karaso babu wanda ya nuna alamar yasan tanayi ma balle ya amsa ta tambaya, kallonta kawai Daada tayi da idanuwanta da batama san sun cika da hawaye ba taji wani tashin hankali na tasowa tun daga dan yatsan kafarta har tsakiyar kanta kafin ya tattaro ya samu wajen zama a cikin kirjinta, sai dai data karasa cikin dakin bata tsammaci zata ga Julde kwance kamar gawa ba, bata kuma sake tabbatar da shi din kacokan ne duniyarta ba sai yanzun da ta ganshi kwance haka, ba zatace a tsaye ko a zaune ta rarrafa inda yake ba, ta dai ganta a kasa, ta kuma ga kanshi a jikinta, hannuwanta na bin fuskar shi tana son tabbatar da karshen duniyar ta baizo tare da nashi ba. Lubna sufyan Hausabook.com 475 Da gaske ne wani tashin hankalin ya fi gaban kwatance... Kallon shi takeyi, sai take ganin kamar ta kalli mudubi, saboda tana da tabbacin tashin hankali da ciwon zuciyar da yake tattare da ita ne a tare dashi, irin abinda take ji ne shimfide a cikin idanuwan shi, kuma tana da yakinin idan akwai wanda yasan ciwon Madina bayan ita, to Nawfal ne, idan akwai wanda yake son Madina kamar yanda take son ta, Nawfal ne. Wannan tunanin ne ya bata kwarin gwiwar numfasawa tace masa "A karo na farko zan roke ka alfarma Bajjo, shekaru biyu na rayuwar ka zaka aramun duk da nasan ba'a hannun ka suke ba, ba gabaki dayansu ba, dan lokaci kadan a cikin kowacce rana ta shekara biyun, ba asirin Julde zaka taimaka mun mu rufe ba, ahalina, sauran ahalina zaka tayani karewa, kar abinda ya rabo mu da tushen mu ya sake nasara akan mu a karo na biyu..." Wani abu ya gilma ta cikin idanuwan Nawfal din kamar walkiya, yana tabbatar mata da karo na Lubna sufyan Hausabook.com 476 farko

Chapter 18 of 27