Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
irin sama-sama, bai samu sauki Lubna sufyan Hausabook.com 639 ba sai da yaji hannun Murjanatu a cikin nashi, ta dumtsa kamar ta karanci wani abin yana damun shi, bata kuma sake shi ba har sai da suka koma falon, inda Julde, Saratu, Yelwa, Kabiru harma da Daada suke zaune. Yelwar tayi kyau cikin farin leshinta mai ratsin ruwan toka a jiki, fuskarta tayi wani irin fayau, idan baka sani ba, babu yanda za'ayi kasan tana dauke da ciwon dake neman rayuwarta. Idan kuma ka santa a baya, to tabbas zaka gane dalilin da yasa kaf Marake ake cewa ba'ayi matashiya mai kyawunta ba. Gefe da gefenta Salim da Madina suka zauna akayi musu hotuna wajen kala goma, kafin Salim ya mike yana bari a dauke su daga ita sai Madina da take ta kyafta idanuwa alamun tana kokarin maida hawayenta. Yelwa ba ta da karfin tashi, shisa duk wasu hotuna da akayi a zaunen tayi su,suka sallami mai hoton kafin su baje a tsakiyar falon inda kayan ciye ciye da tarin lemuka suke shirye cikin farantai masu kyau, kowa ya dauki kananun filet yana zuba abinda yake marmari, Salim ne ya zubawa Madina ganin tayi wani irin sanyi, karba tayi tana daukar samosa daya ta Lubna sufyan Hausabook.com 640 gutsira tana taunawa a hankali badon tana gane dandanon ba "Bani ruwa Madina..." Yelwa ta fadi, da sauri Madina ta dauki robar ruwa ta bude tana mika mata, ta karba hannunta na rawa, dakyar ta kai bakinta ta kurba, ta dawowa da Madina da take nazarin yanayinta robar, ta karba ta rufe ta ajiye, jingina bayanta Yelwa tayi da kujerar da take zaune ta lumshe idanuwanta, taja wani numfashi "Bansan me yasa ake saka cabbage a abin nan ba" Khalid ya fadi yana bata fuska ya hadiye spring rolls din dakyar, yana kuma saka Madina dauke idonta daga kan Yelwa ta kalle shi "Me kake so a saka a ciki to? Alayyahu?" Cewar Nawfal da ya sake kurbar lemon da yake hannun shi, don duka abubuwan da suke a baje a wajen, ba cimar shi bane ba "Malam ina magana ne da mutane 'yan uwana da zasu fahimci abinda nake cewa, ina nufin Lubna sufyan Hausabook.com 641 tunda ina magana ne kan abincin mu, mu mutane" Ruwa Nawfal ya zuba a hannu shi yana yarfawa Khalid daya kai masa duka yana kaucewa da sauri, ganin Khalid din na neman wani abu da zai buga masa yasa shi fadin "Hamma kayi masa magana..." Juya idanuwan shi kawai Salim yayi "Khalid karka dake shi, me yasa baka da hakuri ne wai?" Cewar Adee tana kwalawa Khalid din robar lemon da ta gama shanyewa tana dorawa da "Magana nake maka..." Baki a bude Khalid yake kallonta "Baki ga abinda yayi mun ba? Murjanatu" Khalid ya karasa yana kallon Murjanatu da tayi dariya "Kayi hakuri Hamma, bakina daure yake da igiyoyin aure" Lubna sufyan Hausabook.com 642 Kai Khalid ya jinjina "Bakin ki suka daure kawai, amman nasan basu hanaki ganin gaskiya ba, ki rabani da mijinki..." Dariya takeyi, don ko kafin tazo ta gansu, ta waya ma da video call shi da Khalid din ba gajiya sukeyi ba. Idan kagansu daban daban zaka ga matasan samari masu hankali da cikakkiyar nutsuwa. Amman idan kagansu tare to zaka ga yara ne da suke makale a jikin samari, shekarun da hankalin suke ajiyewa a gefe suna zuba yarintar da Lukman ma da yake kanin su bayayi. Wani lokacin sai Salim ya raba musu waje "Kai Bajjo koma can kujerar" Amman ba za'ayi minti goma ba zakaji wani a ciki yana kai kara da cewar dayan yana kallon shi, karshe sai Salim din ya hada da zagi sannan zasu natsu. Wani irin shiru ne ya gifta cikin dakin na dakika, dan kowa a cikinsu zai iya rantsewa har iskar dake yawo a dakin sai dai ta tsaya tare da shirun, kafin zuciyar Madina tayi wata irin dokawa da ta sakata juyawa ta kalli Yelwa, tayi luf a cikin kujerar, idanuwanta a lumshe, kallonta Madina takeyi sosai tana so Lubna sufyan Hausabook.com 643 taga tayi motsi ko yaya ne. Ganin bata motsa ba ya sakata tabata tana rasa a cikin jerin sunayen da ake kiran uwa dasu wanne yafi dacewa ta kirata dashi kafin harshenta ya iya hada jimlolin "Ummi..." Yanayin da ta kira sunan yana saka hankalin kowa a dakin komawa kan Yelwa, Julde ne ya taso daga inda yake yana ture har Madina ya riko hannun Yelwa da kamar hakan take jira ta sulale akan kujerar, ya kuwa rikota gabaki daya yana dagota hadi da kallon su Salim cikin neman taimakon daya kasa furtawa. Salim ne ya tashi yana kokarin kama hannunta amman Julde ya hana shi, girgiza masa kai kawai yakeyi "Daddy dubata zanyi, likita ne ni ka manta" Sannan Julden ya barshi ya rike hannun Yelwa da yaji yayi sanyi a cikin nashi. Baisan me yasa ya fara kallon Daada ba, ya kuma yi dana sanin hakan, murmushi tayi masa, wani irin murmushi mai ciwo kafin hawaye su silalo mata, ta kai hannu ta goge su "Ta rasu ko? Allah ya karbi ajiyar shi" Lubna sufyan Hausabook.com 644 Ta karasa muryarta na karyewa, sai ta kalli Julde, tana jin yanda shi kadai ya rage mata "Bukar" Wani sashi na zuciyarta ya kira mata sunan shi, amman yana ina? Julde kadai take dashi, haka tata kaddarar take, haka Allah ya tsara mata, ta amsa sunan uwa, a tare da sunan ta fuskanci kalubale kala-kala, tun daga yaran da suka fito daga jikinta dan ta amsa sunan uwa kawai, har kan wanda suka fito suka rayu da ita ta amsa sunan a aikace, a lokaci daya suka nuna mata yanda ta gaza a matsayin uwa, shima Julden wanne tabbaci take dashi na cewar shi zai zuba mata kasa? Ba ita zata ga fita da gawar shi ba? "Karka ce mun ta rasu Salim...karka fadamun ta rasu" Julde yake fadi yana jin duniyar na jujjuya mishi "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Madina ta furta, a zaune take, amman sai taji kamar ta sake komawa ta zauna, kamar kuma wani abu ya daki duka ilahirin jikinta Lubna sufyan Hausabook.com 645 "Daddy..." Salim ya kira a tausashe, duk wata alama ta mai rai tabar jikin Yelwa, sai dai in fuskarta ka kalla, da siririn murmushin da yake kai, zaka iya rantsewa bata rasu ba. Sai dakin da yayi shiru baka jin komai sai sautin kukan Saratu, Adee da Murjanatu da suke ganin abin kamar almara. Nawfal kuwa ji yayi kamar an zare masa lakkar jikin shi, zai iya tuna sau nawa yaje makabarta, kuma shima tun yana yaro ne, ya kasa dauke idanuwanshi daga kan Yelwa da yanzun suka gama hotuna da ita "Bajjo..." Ta kira shi kamar ta sanshi, tun ranar daya fara ganinta taji suna kiranshi haka, itama ta kira shi, tana kallon shi kamar akwai tarin abinda take son fada masa, da ta samu dama kalamanta basu tsawaita ba "Kayi kama da Hamma Bukar, sai dai baka da sanyin shi, wannan sanyin da shi kadai yake dashi...idan kayi dariya kamanninku sunfi fitowa" Lubna sufyan Hausabook.com 646 Murmushi kawai ya iya yi mata zai tuna, saboda baisan meya kamata yace ba, Bukar din ya bace a tunanin shi, baisan kamannin shi ba balle ya hadasu da kalamanta ya auna yaga gaskiyar su. Yau ma kuma tana ganin shi ta kirashi "Ina wuni, ya jikinki?" Ya tambaya, tayi masa murmushi "Alhamdulillah...gani a zaune" Sai ya tsinci kanshi da yin dariya "Allah ya baki lafiya" Bai tuna ta amsa ko bata amsa ba, Allah dai ya amsa addu'ar tashi, ga lafiya nan ta samu, ciwon yazo karshe. Khalid ma ya kasa dauke idanuwan shi daga kanta. Ashe duk wani labari na mutuwa da yake ji, duk wani kai gawa da akeyi da shi, duk tunanin mutuwar shi da yakeyi a kullum, duk yanda yake fadawa kanshi ba wai sanin mutuwa kawai yayi ba, har zuciyar shi tasan da zamanta karyane, bata zo kansu bane shisa yake ganin haka. Wannan zantukane da yaudarar da kowanne dan adam yakeyiwa kan shi, daman haka mutuwar take? Lokaci daya? Ba zaice bata Lubna sufyan Hausabook.com 647 nuna alama ba tunda tana ciwo, amman haka kawai? Yau? Duka suna zagaye da ita suna labari, suna dariya har ta ratso ta cika umarni ta fita suna nan zaune basu ji alamunta ba. Wanne irin zumunci ne wannan? Ba ma ance ko mutuwa na kunyar idon iyaye ba, ga Daada a zaune, amman mutuwar bata ki dauke mata yarinyar da bata jima da dawowa rayuwarta ba. Kallon komai Khalid yakeyi kamar shirin fim, musamman yanda Salim yake fama da Julde daya kamo gawar Yelwa ya kwantar da kanta a jikinshi yana dan bubbuga fuskarta cikin son ta bude idanuwan da ta riga da tayi musu rufewar karshe. A tsakanin kukan su Saratu, hawayen Mami, da wahalar Julde ta karbar mutuwar tilon yar uwar shi, haka suka tattara suka fita daga dakin dan a suturta, haka kuma kukan da sukeyi bai hana Adee da taimakon Saratu suka shirya Yelwa suna saka mata kayanta na karshe, ankon da yake jiran kowanne musulmi. Haka su kuma da tarin mutanen unguwar su da suka zo sukayi mata sallah, suka dauki gawar suka nufi makabarta, a hanya Khalid yake jinjina Ikon Allah ganin tarin al'ummar da suke Lubna sufyan Hausabook.com 648 biye, ganin kuma Yelwar duka yaushe tazo Kano, waya santa da zaizo dominta? Wanda suka sansu suka zo donsu din mutanen unguwa ne, wannan al'ummar kuwa ta wuce mutanen unguwa, harda masu adaidaita sahu kasancewar makabartar tsallaken titi, haka suka dinga parking suna fitowa, can ya tsinkayi muryar wani yana tambayar "Wai waya rasu?" Wani kuma na amsa mishi da "Bansani ba wallahi, kamar wani yace wata babbar malama ce, shine nace bari ayi rakiyar dani, Allah ya yafe mana ya datar damu da kyakkyawan karshe" Murmushi Khalid ya tsinci kanshi dayi, Allah kenan, mai son bayinshi da Rahma, a cikin alamomi na dacewa dai wannan dimbin jama'ar da suke raka Yelwa ya nuna cewa tana daga cikin mutanen da sukayi dacen karshe me kyau. Ya dauka abinda zaisa Salim hawaye ba karami bane ba, amman yanda aka gama binne Yelwa, Kabiru ya mike ya koma ya fadi a gefen kabarin Lubna sufyan Hausabook.com 649 suka kamo shi yana hawaye babu wanda bai karyawa zuciya ba "Ka sakeni Khalid, dan Allah ku bani yan mintina, zan tashi, nima ba dadewa zanyi ba, inaji a jikina ba wani tsayin lokaci zamu dauka a tsakanin mu ba, ku barni in kara bankwana da ita kafin in tarar da ita dan Allah..." Sakin shi sukayi, suka tsaya, ya kusan mintina biyar kafin ya iya mikewa, su juya suna barin Yelwa da halayenta duk kuwa tarin soyayyar da sukeyi mata. Haka suka koma suka shimfida tabarmi aka kafa rumfa ana karbar gaisuwar mutuwar da ciwo baisa sun hangota kurkusa haka ba. Kamar yanda kwanakin suka shiga wucewa kamar kiftawar idanuwa, daga asabar din rasuwar har wata asabar din ta zagayo da ta cika kwanaki bakwai dai-dai, ranar da tayi daidai da ranar da za'a share zaman makokin, suna zaune da tsirarun mutanen unguwa da kan tayasu zaman, da kuma Julde da yake a tsakiyar Khalid da Nawfal, yayi duhu a cikin kwanakin yayi zuru-zuru dashi, alamar mutuwar ta dake shi ba kadan ba. Lubna sufyan Hausabook.com 650 Kamar daga sama ya tsinkayo wata murya da lokaci ya fara dishe masa tasirinta na fadin "Hamma wa na rasa? Na zo a makare ko? Kace mun ba Daada bace ba, dan Allah kace mun ban rasa Daada ba?" Ya kara maganar kafafuwan shi dake masa barazana na saka shi durkushewa akan tabarmar kan dole, wata irin iska na kadawa a lokacin da Julde ya dago idanuwanshi, ya sauke su akan Bukar, akan fuskar Bukar da take cike da kasumba, akan fuskar Bukar da yayi wata irin rama kamar wanda ya tashi daga jinya, akan fuskar Bukar da hawayen da suke saukar masa, sai yaji jikinshi ya mutu, yaji kamar bashi da sauran kalamai, kamar idan yayi kwakkwaran motsi zai farka yaga mafarki yakeyi, abinda bai tabayi ba a tsayin shekarun nan, har shakkun kaunar da yakewa Bukar saida ya darsar masa, ganin bai taba ko da mafarki dashi ba. "Daada ce ko Hamma? Na rasata? Kaddarar haduwar mu ta kare tun a wancen lokacin..." Kai Julde ya tsinci kanshi da girgizawa Lubna sufyan Hausabook.com 651 "Yelwa ce...Daada na cikin gida" Kai Bukar yake jinjinawa, wasu hawayen na sake sauko masa da jin mutuwar Yelwar, kafin ya maida dubanshi kan Nawfal da ya kura masa ido ko kyaftawa ba yayi. Ya bude baki da nufin magana Nawfal ya mike, ko takalma bai saka ba yabar wajen, baiga alamar lafiya a tare da Bukar ba, Yelwa ta fara dawowa, suka saka rai akanta gabaki dayansu, sai ta koma, ta tafi inda hakuri ya zame musu dole tunda ba dawowa zatayi ba, kwana nawa a tsakani, shikuma zaizo? Duk shekarun nan? Sai yanzun? Sai yau kamar sun hada baki da Yelwa. Duka hayaniyar falon yake jin ta zuqe mishi, babu wani abu da yake karasawa kunnuwan shi, kallon su yakeyi daya bayan daya da wani abu mai kama da alfahari, wani abu da ya girmi so, ya kuma wuce kauna, yanayi ne da akansu kawai yasan akwai shi, yake kuma jinshi. Anya akwai abinda yafi dangi dadi? Akwai abinda yafi 'yan uwa? Sai ya kalli Bukar da ga Kaltume a zaune a falon amman yana kusa da Daada, yana Lubna sufyan Hausabook.com 652 zaune a kasa kan kafet din dakin a gefenta na dama, Madina tana gefenta na haggu, Salim kuma yana gefen Madinar, kallo daya zakayiwa fuskar shi kagane inda yana da wani zabi bayan zaman wajen zai dauka. Nawfal ya rufe idanuwan shi, ya sake budesu akan su Bukar, shekara daya, ya kamata ace ya saba, zuciyar shi ta aminta ta yarda da ba mafarki yake ba, su dinne suka dawo, iyayen shi, kuma duk wani alamu sun nuna zamansu ba mai karewa bane nan kusa. Tunda Bukar din tare suke zuwa kasuwa da Julde, bayan ya bashi gida mai daki biyu (two bedroom) daya siya da sunan Lukman, yake kuma shirin zuba yan haya, sai dai kafin yayi hakan ne Bukar ya dawo. Zaice ya shafe kwanaki bakwai bayan dawowar shi yana kaucewa haduwa dashi, asalima kayanshi ya hada da kuma matar shi suna tafiya Kaduna saboda ya fuskanci abubuwan da suke gaban shi na kasuwancin da ya kafa a garin na Kaduna. Duk wani sauran kuzari da ya rage masa ya tattara yana mayarwa akan aikin da fatan ya dauke masa hankali daga dawowar Bukar, sai Lubna sufyan Hausabook.com 653 dai kamar duk wata sa'a da zata wuce da yanda amon muryar da yake fada masa idan kuma da gasken Bukar ta leko ta koma zaiyi masa kamar yanda Yelwa tayiwa Madina fa, yake karuwa. Ko da ta leko ta koma dinne kamar ya kamata ace ya tsaya ya samu wani lokacin da zai adana a zuciyarshi ko dan gaba. Yaji dadin da Murjanatu bata tayar mishi da maganar ba, duk yanda yake ganin tana son yin hakan a lokutta mabanbanta, sai dai idan yaje jikinta zata kara rike shi, zata sumbace shi a kunshi ko duk inda labbanta zasu iya kaiwa tana son fada masa tana tare dashi duk runtsi, idan kuma yana da bukatar abokiyar tattauna damuwar shi tana nan, tana nan a kowanne irin yanayi da hargitsi da zai tsinci kanshi. Ya godewa Allah, ya godewa Murjanatu, ya godewa duk wani dalili, karami da babba daya hadu waje daya ya samar mishi da ita a matsayin matar aure, saboda yasan ba dabarar shi bace balle wayon shi. Sai dai kwanakin suka fara yi masa tsayi, aikin daya ke fatan binne komai a cikin shi ya daina bashi kariya daga tunanin da yake ta turewa. Lubna sufyan Hausabook.com 654 A idanuwan shi zaka ga ramar daya fara a tsaye, idan kuma kasan shi yanda ya zama shiru-shiru zaka san wani abu yana damun shi, wani abu mai girma. A ranar wata laraba, ya yanke shawarar komawa gida wajen sha biyu na rana, gara yaje ya rabi jikin matar shi ko zai samu salama a ranshi, ya shigar da motar shi cikin gidan nasu da Murjanatu ke korafin har yanzun bai gama yi mata yanda take so ba, ya fito ya ga maigadin su yana bude gate din da alamun wata motarce zata shigo, zuciyar shi ta buga, ta kara bugawa ganin motar Khalid ce, wajen sati kenan yana gujema duk wani kira da Khalid din yayi masa a waya saboda yayi masa maganar Bukar. Bai san dalilin da tunanin awannin dake tsakanin Kano da Kaduna ba wasu masu yawa bane balle suyiwa Khalid katanga a tsakanin su, zuciyar shi ta kara bugawa ganin Bukar ya fara fitowa daga motar, kafin Khalid ya fito, sai dai shi bai fara takowa ba, a jikin motar ya tsaya yana kallon Nawfal kamar yana son gaya mishi "Ga abinda kake gudu nan na biyoka dashi" Kamar kuma yana son ce mishi Lubna sufyan Hausabook.com 655 "Wannan baya cikin abinda zaka iya gujewa fuskanta Bajjo" Ya hadiye wani abu da yaji ya tsaya masa a wuya, lokaci daya kuma jikin shi ya dauki dumin da bashi da alaka da zazzabi, kafin numfashin shi ya fara yi masa barazana ganin Bukar tsaye a gaban shi. Yadi ne a jikin Bukar din bula mai haske, sai hula data hau da yadin. Ramar da take fuskar shi a wancen lokacin babu ita yanzun, sannan yayi gyaran fuska, farin gashin da ya fara nuna shekarun shi ya kara masa wani irin kwarjini na ban mamaki, sanyin halin shi da kowa yake yawan magana akai shimfide a fuskar shi "Na so in baka duk lokacin da kake bukata, sai dai lokaci abune da yake karanci a ahalin mu Nawfal, ka yanke mun duk hukuncin da kake so, amman kayi hakan bayan ka saurare ni, dan Allah, ba uzuri zan baka ba, bayani zanyi maka, dalili na kawai zan fada maka..." Ba zai iya tuna mintina nawa yayi a tsaye inda yake suna kallon-kallo shi da Bukar din, zai dai iya tuna Khalid ya karaso, yayi masa maganar da Lubna sufyan Hausabook.com 656 ba zai iya tunawa ba, a cikin wannan rudanin kuma suka shiga falon gidan shi, yanajin shi kamar bashi ba har lokacin da Murjanatu ta kawo musu ruwa, lemuka, kayan marmari sai snacks din da ba'a rabasu dashi saboda tana so, ta kuma yi wata magana da yasan ba zata wuce gaisuwa da kuma abincin da zata dora musu ba tunda basu sanar da zuwan nasu ba. Ruwa ma Khalid ne ya bude robar ya mika masa, baiyi musu ba ya karba ya sha yana ajiye robar hadi da kallon Bukar daya bude bakin shi ya fara bashi wani labari mai kama da shirin film din Hausa. Yace masa sauran kwana daya ranar da suka shirya barin garin shi da Kaltume ta cika, hasashenta na faruwar wani babban abu da rayuwar su ya tabbata, ya dauki Nawfal din sun fita masallaci sallar Isha'i, aka kuma yi dace an gayyato wani bakon Malami da ya tsaya yin wa'azi akan matsalar da ake ta fuskanta ta yawan mace-macen aure da muhimmanci sauke hakkin iyali, hakikanin gaskiya zuciyar shi a wannan lokacin tana gida, tana ga Kaltume, amman babu wanda yayi kokarin barin Lubna sufyan Hausabook.com 657 masallacin, shisa shima baiyi wani yunkuri ba ya zauna kawai. Har aka gama wajen tara da rabi, dan Nawfal yayi bacci a jikin shi, sai sabar shi yayi suka nufi gida, zuciyar shi na tsananta duka, wani irin yanayi na ziyartar shi, musamman daya ga gate din gidan a bude, kuma yasan sun sallami maigadin su tun satin daya wuce. Zuciyar shi ta mirgino ta fado kasa inda ta tarwatse bayan ya shiga gidan ya ganshi anyi masa dai-dai, kamar ana neman wani abu, kuma babu Kaltume babu dalilinta. Wani irin firgici da tsoro suka daki ruhinshi, duka tunanin shi ya tsaya akan dangin mahaifinta da basu daina bibiyarsu ba, basu dauke idanuwansu daga dukiyar da aka bar mata ba, kadarorin da ta dinga siyarwa tana siyen zinari tana ajiyewa, wasu kudin kuma ta barsu a cikin asusun bankin data bude dan hakan kawai. "Idan zabi ya gifta tsakanin ni da Nawfal ka zabi yarona, dan Allah kayi nisa dashi yanda dangin Abba ba zasu cutar mun dashi ba saboda abin duniya..." Lubna sufyan Hausabook.com 658 Duk wani abu mai muhimmanci yana cikin mota, sun gama tattara kayan da zasu dauka sun saka a ciki tunda safe, daya karasa motar cikin rashin hayyaci, jakar da tafi kowacce muhimmanci kawai ya iya dauka, daga shi sai kayan jikin shi da silipas, a kafa ya karasa tasha, acan suka kwana da safe ya kama hanya. Sai dai bayan yaje Marake ya ajiyewa Daada Nawfal batare da bayanin komai ba, juyawa yayi a ranar ya sake shiga mota dan ya bi bayan Kaltume, ya kuma sauka cikin rashin sa'ar samun dangin mahaifinta sun baza neman shi, Kawunta ya kai rahota ofishin 'yan sanda cewar Bukar din ya batar da ita, ya gudu da tarin dukiya, yana komawa ana kama shi. Bashida wata shaida, Kaltumen da zata zame mishi shaida baisan inda take ba, yaci wahala a hannun 'yan sanda a nufinsu na tambayar shi inda dukiyar Kaltume take, case din daya dauki wata daya, da Kawunanta suka ga ba zaiyi magana ba suka maka shi kotu, inda yake da yakinin cin hanci akayi amfani dashi wajen garkama shi a gidan yari, laifin shi daya, da kaddara ta hada shi hanya da Baban Kaltume, ta Lubna sufyan Hausabook.com 659 kuma hadashi aure da ita. Bashi da wata hanya da 'yan uwanshi zasu san halin da yake ciki. Sai dai a lokacin da suka garkama shi gidan yari, Kaltume gidan mahaukata suka kaita suka lakaba mata ciwon haukan da bata dashi, yanda take kiran mijinta da danta, suka kuma cewa likitocin tayi aure, amman mijin da dan duk sun mutu sakamakon hatsarin da suke tunani shine ya taba mata kwakwalwa take ta sambatu taki amsar mutuwar. Ko da bata hauka, ciwon damuwa da kuma fargabar halin da mijinta da danta suke ciki ya taba kwakwalwarta, tun tana yunkurin yakice zuciyarta harta bar damuwar tayi nasara akanta, dalilin da yasa asibiti riketa kenan. Da shekaru suka fara tafiya sai ta amince, ta kuma fara yarda da cewar watakila da gaske haukan takeyi. A cikin yaran Kawunanta, yar shi ta hudu, Hamida ce tayi nasarar jin abinda ya faru lokacin da ta tsinkaye shi suna tattauna maganar da dan uwan shi, suna kuma tunanin inda Bukar da Kaltume suka kai dukiyar da har a lokacin suka kasa cire ransu daga kanta. Basu kuma bar zuciya da tunanin ba, saboda su kuma Lubna sufyan Hausabook.com 660 ta zabi fannin shari'a, har bayan tayi aure, shekaru sunja basu bar ranta ba, tana kuma kallon mahaifinta da zaluncin da bashi da nufin yin nadama akan shi balle kuma ya tuba. Ita ta fara nemo Bukar bayan mahaifinta ya kwanta wata irin cuta da likitoci suka kasa gane kanta, Allah kuma ya matse shi da ta tayar masa da zancen su Bukar bai musa ba wajen warware mata komai, saboda a lokacin babu abinda yake bukata sai samun salama daga azabar ciwon da yake fama dashi, duk da mahaifin nata ya shirya tsaf dan bada shaidar da zata wanke Bukar a gaban alkalai, shari'ar bata zo da sauki ba, musamman data hada da ahalin da suka ki bawa Hamida goyon baya saboda tonon asirin su gabaki daya. Sai dai bai wani daga burin shi akan samun nasara ba, ya rigada ya sallamawa kaddarar da ta fado masa, a zuciyar shi kuma yayi sallama da kowa nashi, ya dai san duk inda suke fatan su da addu'o'in su na tare dashi, musamman Daadar shi. Sai gashi sunyi nasara, sai gashi ya shaqi iskar 'yanci da ya fitar da rai da ita, sai a lokacin kuma ya iya tambayar Kaltume, sai lokacin ya bari Lubna sufyan Hausabook.com 661 zuciyar shi ta tambayeta, ya kuma yi karo da labari mai dadi, an fito da ita, asalima ita suka fara fitowa da ita, tana dai karbar kulawa ne bisa turbar da ta dace a hannun likitoci saboda damuwar data taba kwakwalwarta, kuma ana samun cigaba. Kamar ganin shine babban maganin da tafi bukata, zaren da zata kama ya fisgota daga duniyar damuwar da take ciki. Sai ta samu wani sauki daya ba likitocin mamaki, ya kuma yiwa Bukar dadi saboda bayason su kara wasu kwanaki a garin na Borno batare da sun fice ba, duk wata neman yafiya daga Kawunanta, da nuna nadama bai taba zuciyar Kaltume ba, garama Bukar ya bude bakin shi ya furta ya yafe musu, ko dan darajar Hamida, amman Kaltume shiru tayi, tunda ko addini ya bata zabin yafewa ko akasin hakan. Sunyi mata babbar cutar da ba zata yafu ba a wajenta. Wata shari'ar sai a lahira. Haka suka tarkata dan abinda ba'a rasa ba, bayan tarin godiya da fatan alkhairi suka nufi Marake. Komai ya kara zuwa masa da sauki bayan ya nufi gidansu yaga yanda yanda daga na Datti har na Hammadi suka zama kango saboda Lubna sufyan Hausabook.com 662 rashin mutane. Sai yaja Kaltume suka nufi gidan Baabuga, inda yayi murna da ganinsu, harda hawayen shi, anan kuma suka samu labari mai dadi, na zuwan su Nawfal, na ziyarar da suka sake kawowa a karo na biyu, suka kuma samu lambar wayar da Khalid ya rubuta yana bawa Baabuga da nufin ko da wani abin zai taso. Harda cikakken adireshin inda suke da zama a jiki, shisa Bukar din bai kira Khalid ba, suka kwana, washegari suka samu motar Kano, da kudin hannun shi yayi amfani ya kamawa Kaltume daki saboda yanda ta nuna alamar galabaita, ya barta acan da nufin komawa ya dauketa idan ya gano gidan. Kallon shi Nawfal yakeyi, tunda ya fara magana, har wani jiri-jiri yake ji saboda yanda yake so ya nannade kanshi cikin duk bayanin Bukar da yake kama da almara ko zai fahimta. Daga yanda suke kallon shi yasan jira suke yace wani abu, amman ya kasa ko kwakkwaran motsi balle ya iya furta wani abu. Kiran sallar azahar shiya tashe su, tare sukaje masallaci, suka dawo, inda Murjanatu ta kawo musu shinkafa da sauce din kifi da tayi da tumatir da albasa, dan ba tattasai Lubna sufyan Hausabook.com 663 garesu a gidan ba balle attaruhu, ko nama basu dashi, idan tayi sha'awa zata fita ta siya ko tayi order, to a hankalima, saboda Nawfal din kaunar da takeyiwa nama ta kula kara nisa takeyi. Sai salad da tayi musu, da kuma lemuka, ta bar musu wajen, Khalid ne ya zuba ma Nawfal din da ya dinga wasa da cokalin shi a cikin abincin har suka kammala. Suka yi masa sallama suka juya, ya dai rakasu bakin mota, ya koma ya samu Murjanatu harta kwashe komai. Kamar kuma ko da yaushe bata yi masa magana ba, bata tambaye shi wani abu ba. Shine ma a daren ranar ya dinga jaddada mata irin son da yakeyi mata da kuma godiyar da yake yiwa Allah da ta kasance cikin rayuwar shi. Haka kwanakin suka dinga zuwa suna wucewa har sati biyu bayan zuwan su Bukar, yana kwance Murjanatu tazo ta tsaya akan shi tana girgiza shi cikin wani yanayi daya saka shi tashi zaune babu shiri. Kallonta yayi, hawaye ne cike taf da idanuwanta, ta kasa magana, sai wani abu da bai gama fahimtar menene ba ta mika masa, baiyi musu ba ya karba ya duba, sai dai so yake ya tuna inda Lubna sufyan Hausabook.com 664 ya taba ganin abinda yake rike dashi, kafin ya fahimci amfanin shi, zama tayi kusa dashi sosai tana zagaya hannuwanta ta riko shi jikinta "Allah ya dubemu..." Kamar wanda kalamanta

Chapter 25 of 27