Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
suka wankewa kwakwalwa haka yaji, kafin ya fahimci menene dan karamin abinda ke hannun shi mai dauke da sakon da yake da nauyin gaske "Zamu samu yaro ko yarinya?" Ya tambaya muryar shi na fitowa a shake, kai take daga masa, ya kuwa sake riketa kamar zai mayar da ita cikin shi, tun shekarar farko ta aurensu da sukaje asibiti aka tabbatar musu da lafiyarsu kalau, babu mai wata matsala suka dawo suka barwa Allah komai. Yana danne tashi damuwar ne saboda ya karfafa mata gwiwa, amman yasan abin yana damunta duk da bata cika yi masa zancen ba, amman indai suka tare, a dararen alhamis da juma'a, koma basa tare takan tuna masa daya tashi yayi sallar dare don neman biyan bukata, gashi kuma yau Allah ya amsa musu. Lubna sufyan Hausabook.com 665 Yaje Kano, a tsakanin samun cikin nata, laulayinta, kananun ciwuka da kuma taraddadin da ba'a raba mai ciki dashi, yaga Bukar, yaga Kaltume, ya gaisa dasu da wani yanayi a tare dashi da bai gama fahimta ba. Farin cikin da yake fuskar Daada na sanyaya wajaje da dama da baisan a zafafe suke ba tare dashi. Daga Bukar din kuma har Kaltume babu wanda yayi wani yunkurin karfafa alakar tasu, kamar sun matsa gefe suna jiranshi yaje musu da kanshi. Sai dai a daren da ciwon nakuda ya kama Murjanatu, ya dauketa a rude zuwa asibitin da take awo, ya kuma ki sakin hannunta duk yanda likitocin suka so, sai suka hakura suka barshi ya bisu dakin nakudar tunda ita kadaice a ciki, kuma kudine suke aiki balle a nuna musu fin karfi. Ba zaice baisan wacece uwa dan bai taso tare da ita ba, a ranar da ya kara fahimtar wacece ita, ya kuma ga dalilan da yasa aka daga darajarta a addini, a gabanshi kan da ya fito, ya kuma tokare saida aka kara Murjanatu, wani abu da ba zai manta ba har karshen rayuwar shi, dan Lubna sufyan Hausabook.com 666 baisan yana hawaye ba sai da wata cikin Nurses din tace masa "Haba dai oga, idan kana kuka ai zaka kashe mata jiki..." Lokacin da kukan yaron ya karade dakin, aka goge shi aka mika masa, sai komai ya tsaya masa, idan yace komai a lokacin, yana nufin komai, harda zuciyar shi da bugunta yayi wani irin kasa. Lokaci daya yaji baisan komai ba, baisan kowa ba sai halittar da aka saka masa a cikin hannun shi, abu na farko kuma daya fara dawo masa shine iyayen shi, iyayen shi da a yau ya fahimci duk wani dalili da zai nisanta yara da mahaifansu fa ba karami bane ba, musamman uwa da tasha wannan gwagwarmayar. Daya dago yaron yana yi masa kiran sallah cikin kunnen shi hadi dayi masa hudu ba da Khalid, sai wasu siraran hawaye suka zubo masa. Lokacin daya fito waje yayi waya ya fada ma Daada cewar Murjanatu ta haihu, da yammacin ranar baiyi tsammanin duka ahalin shi zasu taho ba, su dukansu suka yo mota uku suka Lubna sufyan Hausabook.com 667 taho. Wajen Kaltume ya fara nufa yana riko hannunta da fadin "Ummi, Ummi Na" Yana saka wasu hawaye kwace mata, saiya kwantar da kanshi a jikin kafadarta yana barinta ta rike shi, yaji duminta da zaluncin wasu mutane ya hana masa shi tsayin shekaru. Hannun shi na cikin nata suka shiga cikin gidan, suna bin bayan kowa saboda sun shige cikine suna basu wajen da suke tunanin suna bukata shi da Kaltume. Da Khalid yaji sunan yaron, saiya kalli Nawfal "Nagode Hamma, da komai, nagode" Nawfal ya furta a hankali yanda Khalid din ne kawai zaiji, bai iya cewa komai ba, shiru yayi yana kara rike yaron a jikin shi, saboda bai yarda da kanshi ba "Wai Khalid kuka zakayi?" Cewar Adee, ya harareta da idanuwanshi da sukayi maikon hawayen da yake cike dasu, yana sa kowa yin dariya Lubna sufyan Hausabook.com 668 "To girma ya kamaka Khalid, sai kazo ka tsaida matar aure tunda ni dai nace banayi" Daada ta fadi, murmushi yayi, daman yana da niyya, tunda sun gama dai-daita kansu shi da Maryam da watannin su shidda da haduwa a lokacin, ya dai san akalla za'a saka musu wasu wata shiddan, tunda yana bukatar ya shirya sosai, in dai ya samu yanda yake so gidan nashi yana fatan ya zuba duka kayan amfani ya daukewa iyayenta tunda ya kula ba karfi gare su ba, wadatar zuci ce da kuma kokari irin na talatan da zuciyar shi bata mutu ba. "Yanzun fa mu da mu kara taruwa haka sai Bikin Khalid ko?" Murjanatu tayi maganar tana fisgo Nawfal daga duniyar tunanin daya fada "Ai Hamma na da matsala, biki wata takwas, mu an taba saka biki mai nisa haka a family dinmu?" Fadar Nawfal yana hararar Khalid dake zaune da takwaranshi da suke kira Junior a hannu Lubna sufyan Hausabook.com 669 yana ta kara gyara masa kwanciya, yaron dake ta sharar bacci "To abinka da bikin talaka, dole ina bukatar shiri, yanzun ba gashi saura wata shidda ba" Salim ne yayi tsaki wannan karin "Menene shirin a ciki?" Kai Khalid ya girgiza "Dan Allah idan ana maganar kudi, ka daina saka baki Hamma, albashinka da namu ba iri daya bane, ba zaka fahimta ba...kuma kai Hajiya Adee ta saka maka hannu" Da mamaki Salim yake kallon shi "Adee banda akwatuna, duk abinda aka saka a lefen nan ba kudina bane ba?" Dariya Adee takeyi "Na fa kara da takalmi da jaka Hamma" Tsakin ya kara ja yana girgiza kanshi kawai, yaga alama so suke su bata masa rai Lubna sufyan Hausabook.com 670 "Hamma kace duk abubuwan masu muhimmanci yi maka akayi, ai in ba wani auren zaka kara ba babu yanda za'ayi ka gane..." Bai karasa ba saboda hararar da Madina ta dago kai tana watsa masa batare da tasan ma tayi ba "Bajjo..." Khalid ya kira yana dariya, shima dariyar yakeyi yana daga hannuwan shi cikin sigar dake nuna saduda "Afuwan uwargida ran gida...subutar bakine" Ya karasa maganar da dariyar data fito daga kasan zuciyar shi, duk da kara tsuke fuska Madina tayi, yana kuma jin kaunarsu da bata da misali na cika zuciyar shi, a gefe daya godiya yake yiwa Allah yana karawa, godiyar da yake da tabbacin ba zata taba yankewa daga bakin shi ba har karshen numfashin shi. Epilogue 2 Mutuwa sunanta iri daya ne, sanadinta da sakonta ne yake bambanta, akwai mutuwar da Lubna sufyan Hausabook.com 671 zakaji labarinta kawai ta tabaka, akwai wadda zakaji labarinta ta baka mamaki badan wanda ta dauka yafi karfinta ba, akwai wadda zaka jita ta tuna maka taka mutuwar da kake zaman jira, akwai kuma wadda zata idan ka jita zata daga kafafuwanka ta sulmuyo da kai ta ka, ta hargitsa lissafi da duk wata natsuwa da kake tare da ita. Wannan mutuwar itace ta Yelwa a wajen Madina, mutuwar da ta basu notice tunda ta nuna alama ta hanyar rashin lafiyar Yelwar, sun kuma dauka a shirye suke da zuwanta sai da ta ratso din a lokacin da hankulansu sukayi nisa da tunaninta. Tana da tambayoyin da ko a kasan ranta take tsoron furtasu saboda zasu iya saka ta fita daga addinin da shine rufin asirinta a duniya da lahira. Duk yanda ake mata gaisuwa, ake kallonta cike da tausayawa da ido kawai take binsu. Sai da Salim ya ratso taron matan dake cikin gidan bayan ya kirata tana kallon wayar ta kasa dagawa, ya kuma kama hannunta bayan ya gaishe da kowa, bai nuna ko a fuska ya damu da kallon da sukeyi masa ba, idanuwan shi na kan Madina da batayi masa gardamar mikewa ta Lubna sufyan Hausabook.com 672 bishi ba, akwai hijabin Daada a jikinta saboda sanyin da take ji. Bai tsaya da ita ko'ina ba sai bakin motar shi inda ya bude murfin yana sakata ciki. Ya zagaya ya zauna, jingina jikinta tayi a jikin kujerar motar tana lumshe idanuwa, bata bude su ba sai da taji ya tsayar da motar, ta daiyi mamakin ganinta a gidansu, ya kuma zagayo ya bude murfin motar yana mika mata hannun shi, batajin karfi ko kadan a jikinta, batayi musu ba ta kama ya taimaka mata ta fita daga motar, ko takalma babu a kafarta sai socks, janta yake har bangarensu, zuwa dakin shi, inda kamar hakan yake jira ya kama hijabinta ya zare bayan ya rufe kofar, ya cire gilashinta ya ajiye a gefen gado, ya kuma zagaya hannuwan shi yana riketa hadi dayi mata rumfa da jikin shi. Ba tasan menene ba a lokacin, dumin shi? Kamshin shi? Ko kuma kulawar shi ce, ko duka ne suka hadu sukayi tasiri akanta. Dan wani irin kuka da batayi ba a kwanakin nan ta tsinci kanta da rushewa dashi. Ya sake riketa, kuka takeyi tana karawa, kukan rashin mahaifiyar da bata jima da shigowa rayuwarta Lubna sufyan Hausabook.com 673 ba, kuka take a jikin Salim, Hammanta, kuma mijinta a yanzun. Kuka tayi har saida sauran karfinta ya kare, dan badan rikon da yayi mata bana wasa bane, kafafuwanta ba zasu iya daukarta ba. Dakyar da taimakon shi ya kaita bandakin shi ya rufo mata ya fita, fuskarta ta wanke ta kurkure baki ta fito, da bata ganshi ba sai ta kwanta akan gadon kawai, bata da karfin zama, bacci ne ya fara daukarta taji yana tashinta. Dakyar ta iya mikewa zaune "Kisa wani abu a cikinki" Ya furta yana mika mata robar yoghurt din da batayi masa musu ba ta karba, ta sha rabi, ya kuma sake bata dankalin turawa da wainar kwai, ta danci kadan, kafin ta girgiza masa kai "Ki kwanta ki huta, anjima sai in mayar dake" Komawa tayi ta kwanta, tana jinshi yana ta shige da fice kafin taji hawan shi gadon, haka kawai taji zuciyarta ta natsu, irin natsuwar da ta rasa a kwanakin bakwai, ya mika hannu ya jata zuwa jikin shi yanayi mata makwanci akan kirjin shi inda tayi luf da ita, zata iya rantsewa kamar an halitta mata shi dai-dai ita, dai-dai kwanciyarta, Lubna sufyan Hausabook.com 674 dan inda kanta yake a kafadarshi yayi dai-dai, tamkar an auna kafin a halitta masa. Yaune karo na farko da ta kwanta a jikin namiji, ya kamata taji daban, yakamata taji wannan rashin sabon da fargabar, amman babu komai a zuciyarta banda natsuwa, irin natsuwar da taji bayan labarin daura musu aure ya risketa. Shisa ta lumshe idanuwanta tana barin bacci ya dauketa. A bangaren Salim ne yanayin ya sha bambam, ba ita bace macen farko da ta hau jikin shi, ita daice ta farko da yake jin ba a jikin shi kawai take kwance ba har a zuciyar shi, yau kuma sai yake jin control din da yake yiwa kansa a lokuttan da yake tare da ita yana neman kwace masa. Wata wutar sonta nayin rassa a duk gabban jikin shi. Ya gyara mata kwanciya yafi a kirga ko zai samawa kanshi sauki, amman hakan ya gagara. Tayi bacci, amman shi ko idanuwan shi bai rufe ba, har azahar, shiya tasheta bayan ya zameta daga jikin shi ya shiga bandaki ya dan watsa ruwa yayo alwala. Bai mayar da ita gida ba sai la'asar, sai kuma lokacin wata irin kunya tayi mata rumfa, tasan kowa dake dakin zaisan cewa Salim mijinta ne, Lubna sufyan Hausabook.com 675 bama su ba, yanda zata shiga gidan ta hada ido da Daada shine babbar damuwarta. Taji dadi da bata ga Daada a falon ba, saita wuce dakinta kai tsaye. Ta kwanta akan gadon tana jin saukin nauyin da kirjinta yayi mata. Musamman data cigaba da jero "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Tana kara maimaitawa. Kamar ko da yaushe, a dan tsakanin Salim saiya sake zame mata bangon da take jingina dashi ta samu saukin tsayuwar da take neman gagararta. A gefe daya kuma Kabir ne, mahaifinta da ta kira da "Abba..." Karo na farko bayan rasuwar Yelwa da suka hadu, sai ya durkushe a wajen, kuka marar sauti na kwace masa, itama kukan takeyi, kuka sukayi a falon Daada batare da wani ya lallashi wani ba, kuka Madina takeyi na mahaifiyar data rasa, kuka take na mahaifin da yake gabanta, kuka takeyi na godiyar Allah daya sa tana da rabon ganinsu ta san su. Shi kuma kuka yakeyi na matar shi daya rasa, matar data tsallake kowa da komai nata ta zabe shi, matar da tayi Lubna sufyan Hausabook.com 676 gararamba a titi tsayin shekaru ta sanadin shi, matar da ciwon da basu taba tsammani ba ya dirar mata, kafin mutuwa ta risketa tana yi musu tsakani na har abada. Mutuwar da ta saka shi kokarin neman sauran yan uwan shi saboda yanda yake jin shima bashi da wani sauran lokaci mai tsayi. Yan uwan da suka karbe shi kamar basu taba korar shi ba, suka yi nadama kamar sun jima da gane kuskuren su. Ya kuma yi kokarin daukar Madina ya hadata dasu da jagorar Salim daya rakasu. Taga 'yan uwan mahaifinta, taga ahalin da idan ta juya a garin Kano zata kira da nata. Yanda duk in anyi wani motsi mai girma Kabiru zaice musu "Babu ni idan ba Yelwa, inaji a jikina tazarar mu ba mai nisa bace ba" Jinshi kawai sukeyi, suna kuma tausaya masa, ko Daada sai da tayi maganar shi, tasan Yelwa batayi zabi me kyau ba lokacin data tsallake su, amman alamu sun nuna ko su suka laluba zai wahala su zabo mata mijin da zai mata soyayyar da take gani a idanuwan Kabiru. Sai suka fara Lubna sufyan Hausabook.com 677 saka shi a addu'o'insu, da fatan Allah ya saukaka masa radadin rashinta ya takaita masa kewa. Sai dai jikin shi bai masa karya ba, kalaman shi duka akan gaskiya suke, a lokacin da ya bi Yelwa kwanaki arba'in da shidda cif a tsakanin su bayan zazzabin kwanaki biyu rak. Wata mutuwar da ta sake taba su dukansu. Saboda Kabiru ba irin mutanen da zasu rabeka ka kasa kaunarsu bane ba, ko murmushin shi kawai da kyallin shi yake kaiwa har cikin idanuwanshi zai tsaya maka, balle kuma kirkin shi, komai a tare da Kabiru mai tsayawa a zuciya ne. "Hamma daman sun dawo ne dan mutuwa ta lallabo ta dauke mun su daya bayan daya? Wacce irin kaddara ce wannan? Anya ina da zuciyar dauka?" Madina ta tambaye shi hawaye na silalo mata, ya riko hannunta "Kowanne rai da tashi kaddarar Madina, amman Allah baya dorawa bawa wadda ba zai iya dauka ba, ki godewa Allah da kika samu lokaci tare dasu, duk da bai tsawaita ba kin samu, akwai Lubna sufyan Hausabook.com 678 yara da yawa da har abada ba zasu san iyayen su ba, tasu kaddarar kenan...wasu ma kafin haihuwar su suke rasa iyaye mazan, a wajen haihuwa kuma su rasa matan...kiyi hakuri, dan Allah kiyi hakuri, Allah zai sanyaya zuciyar ki" Kauda kai kawai tayi wasu hawayen na zubo mata, saboda kowa sai dai yayi kokarin fahimtar halin da take ciki, amman ba zasu taba ganewa ba, wanda ya taba shiga cikin irin shine kawai zai fahimta. Kwanaki bakwai bayan rasuwar aka tsayar da ranar da zata tare gidanta, aka saka sati biyu. Da na farko ya cika aka kawo mata lefen da batayi tsammani ba, saitin akwati masu shidda guda biyu. Haka ta dinga kallon akwatinan tana hasaso kudin da Salim ya kashe wajen cika su. An sanarwa yan uwansu, na mahaifinta, dan tarewar har Marake sai da su Khalid sukaje da motoci uku ran daren suka kwaso dangin Daada, suka kuma bata mamaki da suka hado harda Abu. Abu data fito daga motar tana sharar kwalla, sababbi na zubowa bayan tayi tozali da Daada Lubna sufyan Hausabook.com 679 "Dije wanne dalili na baki na watsar dani haka? Kika sa naji zumunci dake tsakanin mu bai kai inda nake tsammani ba" Itama Daadar tana kuka take girgiza mata kai "Na taho ne a halin kidima, ki yafe mun, kina daya daga cikin mutanen da tunaninsu bai taba barina ba...saboda kece kadai nasan kin soni, zaki kuma soni batare da kin juyamun baya ba a duk wani juyi da kaddara zatayi mun..." Anyi koke-koke, anyi alhini, an kuma yi hirar yaushe rabo, kaunar da jini kadai kan samar ta nuna a fuskokin kowa. Kafin Madina tayi nata kukan lokacin da aka rakata dakin miji, tayi kuka kashi-kashi, amman fiye da rabin kukanta na farin cikin da taji ya dirar mata ne, ganin tarin mutanen da sukayi mata rakiya gidanta, kuma kusan kowa a ciki ta duba alaka ta jini ta hadasu, kowa kuma yana riketa kamar yana son tabbatar mata rashin Kabiru da Yelwa ba zaisa ta taba yin maraici ba. Kafin su tafi su barta da Salim da tun bayan sallar godiya da sukayi suka ci abinci dan yanata mata koken yunwar da yake ji, suka kwanta ya riketa a jikin shi yana fadin Lubna sufyan Hausabook.com 680 "Nagode Madina, da kika zabeni, duk da ina da dalilai da yawa da nasan cewa ban cancanta ba. Daga ranar da aure ya hade mu waje daya, daga yau, zanyi kokarin ganin na kare miki mutuncinki, zanyi kokarin ganin nayi miki rikon da ba zakiyi dana sanin zaben da kikayi mun ba..." Cikin sanyi yake maganar, a hankali, da wani taushi da ita kadai take gani a tare dashi "Nice da godiya Hamma, kai da ka zabeni tun da ayar tambaya akan asalina, kai da ka zame mun bangon jingina a lokutta mabanbanta, Hamma nice zan gode maka daka zabeni, daka soni" Wani abu yakeji yana tsirga masa, shekarunta da yaketa nanatawa kanshi da karantarta na bace masa, baisan komai ba a lokacin sai soyayyarta, kwakwalwar shi ta hade waje daya da zuciyar shi kamar yanda yake son hade duk wata tazara da take tsakaninsu shi da Madinar da batayi mamaki ba, a littafin hausa ne kawai zai tsaya rainonta, za'ace ya jirata saboda tayi kankanta, amman a irin litattafan da take karantawa shekarun nata ne kadai abinda zai Lubna sufyan Hausabook.com 681 jira, a wasu kasashen ta kai sha bakwai, a wasu ta kai sha takwas. Sai dai babu wani littafi, babu kuma wani hasashe da ya shirya mata wannan daren da ba zai gogu ba. Daren da tausaya, kauna da kuma lallamin Salim basu hana kwallarta zuba ba. Sai dai ta samu sauki da tabbaci a rikon da yayi mata kamar zai mayar da ita cikin shi. A hankali Salim ya bi duk wani lungu da sako da soyayyarsa ta samu zama a tare da ita batare data sani ba ya taso da son nan, tun tana mamakin yiwuwar kaso mutum da duk wani abu da zaka iya, amman duk rana sai yayi wani abu da zaisa kaji wannan son ya karu. Alkawarin da yayi mata kan karatu yayi kokarin cikawa duk kuwa da kishin da yanzun take sanin Salim din yana dashi. Ya kaita ta rubuta jamb da kanshi, ya jirata ta gama ta fito suka tafi gida. Karfi da yaji ya koya mata saka dogayen hijabi, ya kuma koya mata mota dan bayason ta shiga ta haya, kafin ya gama tara kudin motar da zai sai mata, tashi yake bar mata idan tace masa zata fita lokacin da yaci karo dana aikin shi. Shi ya hau ta haya. Lubna sufyan Hausabook.com 682 A haka ta samu gurbin karatu a jami'ar Bayero. Bayan roko da tarin nasihar kula da kanta da Salim yake fada yana kara jaddada mata, duk idan zata fita haka zaiyi kici-kicin da fuska, kamar inda yana da zabi, inda baiyi mata alkawari ba, da ya hana karatun. In tana masa dariya wasu lokuttan kai kawai yake jinjinawa. Saboda ba zata gane ba, ba zata taba fahimtar baiwar halittar da Allah yayi mata a kasan kayan da take boye su ba, baiwar da yayi mata da sirrine a zuciyar Salim din. Taya zai san duk wannan ya kasa kishi da fargabar kar wani ya ko hango masa duk wannan? Sai dai a cikin abubuwan da Madina ta kasa fahimta game da Salim, yanda baya bari taje gidan iyayen shi ita kadai, ko me akeyi kuwa zaice ta bari suje tare, idan sunje din kuma tare suke komawa gida. Ko kowa yana nan, ko ta roke shi ya barta zata ga ya hade fuska cikin yanayin da yake nuna mata ba zai tankwaru ba, dole ta tashi ta bishi su tafi. A ahalinsu kaf kuma babu wanda ya fahimci hakan sai Julde da Saratu, babu wanda abin yake damu a zuciya irin Julde, da zuwa yanzun yasan aura masa Lubna sufyan Hausabook.com 683 Saratu da Datti yayi gatane da son da baya mata ya hana shi gani. Har zuwa yanzun kuma mace daya ya so, Mero, kuma tazo a daya daga cikin kaddarorin da zasu horashi, ya sameta, halin shi ya nisanta shi da ita, nisa na har abada tunda tana gidan wani a matsayin matar shi. Sai dai ko baiso Saratu ba, yanzun tilas ya girmamata, saboda ko Meron, duk son da yayi mata, duk ikirarin son da takeyi masa da tayi bai hanata tsallakewa ta barshi ba, bai kuka hanata fadawa kowa dalilinta ba. Wani tonon asiri da Saratu bata tabayi masa ba a tsayin zaman su, sirrin neman matan shi da duk wani wulakanci da ya taba yi mata a tsakanin su yake tsayawa. Abinda ya fahimta a kurarren lokaci, abinda kuma yake jin ciwon rashin fahimtar shi tare da ciwon yanda koya yaran nashi suke zaune a gidan, in dai Salim na nan da Madina ya shigo zaiga yanda nutsuwa ta kwacewa Salim, zai kuma ga yanda yake gyara zama yana duk wani kokarin kare Madina daga ganin shi, kamar yana tsoro, zai sake kallonta da idanuwan da suka wuce na mahaifi. Lubna sufyan Hausabook.com 684 Abinda ya kasa sabawa da ciwon shi, abinda yake shiga daki ya zubar da hawaye duk idan ya kadaice. Tabbas ko dashi kadai aka barshi ya ishe shi horo, kuma ya ishe shi karin ganin girman Allah, da zaka yiwa laifi, ka maimaita, ka tuba ya yafe maka, ka sake maimaitawa, kaje da kokon tuba kuma ya sake duba ka da Rahmar Shi ya yafe maka. Shisa Julde a yanzun yake kokarin ganin ya gyara tsakanin shi da Allah, tunda ya gane, yana kuma da yakinin Allah ne kadai zai gyara tsakanin shi da sauran mutane, wata rana ya wanke shi a idanuwan Salim, ya yarda da kaddara ce da take tare da kowanne rai, ita ta fisge shi ya dubi Madina da wani ido na daban, kaddarar da ya san ba zata sake faruwa ba. Salim din bawai nadamar Julde bace bai yarda da ita ba, zuciyar shi ce baisan yanda zata wanke masa shi ba, baisan ya zai goge hoton data adana masa ba, watakila a gaba, watakila hoton na daya daga cikin abinda lokaci zai tafi dashi, ko kuma akasin hakan. A kowanne yanayi dai, shi din mai godiya ne, musamman a ranakun daya dawo daga aiki a gajiye, ko a ranakun daya Lubna sufyan Hausabook.com 685 ranshi yake a bace, saiya dawo gida, ya samu Madina da murmushinta, Madina da sanyinta, Madina da duk wani halaye daya hade ya samar da ita tana jiran shi, hannuwanta a bude a matsayin tashi, matar da Allah ya bashi duk da yanajin bai cancanci samunta ba. Sai ya godewa Allah, musamman da bincike ya nuna akwai karamar ajiyar shi a tare da ita. Saiya rikota a jikin shi "Ina son ki" Ya furta yana dora goshin shi akan nata, ta lumshe idanuwanta kawai, bata gajiya da yanda yake yawan fada mata yana sonta, sai dai ita son da takeyi masa a yanzun tana jin kalmomin ukku sunyi kadan su misalta shi, tare da cikin da yake jikinta dai take fatan ya fahimci kadan daga ciki, tunda ta shirya tara iyali dashi, ta shiryama kaddarar data hada rayukan su karkashin inuwa daya, ta shirya ma zama dashi a kowanne yanayi zasu tsinci kansu. Tunda har abada din da kowa yake musu fata ana karawa da gaban abadan ma duka tafiya ce mai nisa. Sai dai zatayi ta, zasu cigaba da yinta cikin godewa Lubna sufyan Hausabook.com 686 Allah da kuma fatan kowacce kaddara, mai sauki da marar sauki idan ta riske su, ya basu mafita, ya basu karfin zuciyar daukarta. Ta sauke numfashi tana zagaya hannuwanta ta rike Salim din, Hammanta, mijinta. Nima kuma na sauke alkalamina anan, cike da godiya ga Allah da naga farko da karshen tafiyar nan duk nisan da tazo da ita. Godiya ga daukacin mutanen da addu'o'in su suka sama mun kwarin gwiwa a duk lokacin da naso tsayar da tafiyar nan. Nagode da goyon bayan da kuke bani a ko da yaushe Nagode da yanda kuke supporting dina da kalaman ku, wasu a ciki da katin waya, data harma da wanda sukayi mun kyautukan da suka bani mamaki Nagode Nagode Nagode Lubna sufyan Hausabook.com 687 Ku sani, batare da goyon bayanku ba, ni din a matsayin marubuciya ba kowa bace ba. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

Chapter 26 of 27