Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kiran Innar ta cikin neman dauki ya dirar mata. Duka gidan babu wanda ya zaci zata kwana, Innar A'i kuka ta dinga yi don macece ita mai tsananin tausayi da raunin zuciya, harta Babba ya karaya da ciwon Dijen. Bata samu kanta ba sai washegari da wajen azahar, cikin daren sumanta biyu. Duk wani jike-jike an bata, amman takai kwanaki hudu bata warware gabaki daya ba. In ta faki idanuwan mutane takan share kwallar da take silalo mata, saboda alama ta digon jini ma bata gani ba balle tasa ran cikin jikinta ya fita. A watanni biyu magunguna babu kalar wanda Datti bai kawo mata ta gwada ba, amman ciki saima fitowa da yake yi. Sun hadu su duka sunyi kukan yanda Allah ya nuna musu iyakar su akan cikin jikinta, tashin hankalin ta yafi na Datti, saboda na shi tashin hankalin yana kara mata nata ne Lubna sufyan Hausabook.com 76 "Ina jin karshen duniya ta ne yazo Dije, shisa zan ga cikin wani na girma a jikin ki, shisa zanga kin haihu da wani..." Ya fada wani dare kamar wanda ya samu tabin hankali "Kuskure ne nayi, Hammadi yace in roki Allah ya yafe mun, watakila na makara wajen rokon, amman wannan hukuncin zan iya daukar shi kuwa? Cikin Baabuga ne a jikin ki, haihuwa zakiyi, ba dani ba da Baabuga" Idan yana irin wannan surutan sai dai taita kuka saboda bata da abinda zata fada mishi ta samu sauki. Ta tsani Baabuga da dukkan zuciyar ta, ta kuma tsani cikin da yake jikinta wanda ya zame mata karfen kafa, har tana jin tana haihuwar shi zata saka a zani ta aikama da Baabuga yasan yanda zaiyi da shi. Wannan ne kudirin da yake ranta duk sanda zata daga idanuwa ta dubi cikin jikinta. Haka yaci gaba da faruwa har sanyin safiyar Alhamis din da ta tashi da nakuda, wata irin nakuda da tazo mata da saukin da bata taba sanin akwai shi a tare da ciwon nakuda ba, cikin Lubna sufyan Hausabook.com 77 kankanin lokaci, kukan jaririn da Innar A'i ta karbi haihuwar shi ya karade dakin tare da kabbar da tayi da kuma hamdala. Dije na runtse idanuwanta, wasu hawaye masu zafi na gangaro mata, duk bidirin da sukeyi tana jin su, ta daiki bude idanuwanta "Ungo, rike shi kiga dan ki, rike shi yaji dumin ki" Cewar Innar A'i tana saka mata yaron a jikinta, cikin yanayin da bata ko bata wani zabi da ya wuce na dagowa ba, tana gyara rikon yaron a hannunta, sannan ta sauke idanuwanta akan shi, zuciyarta na wata irin dokawa, ta rike yaranta da yawa, ta rike Julde fiye da sau daya, amman bata san irin wannan yanayin ba, bako ne a wajen ta, ta kuma ji labarai da yawa akan soyayya wadda take tsakanin mahaifiya da abinda duk zata haifa, shisa ta dauka ta gama sanin wannan soyayyar, sai yanzun, sai yau da take rike da wannan yaron da take jin zata iya gifta rayuwarta ya tsallaka in har bukatar hakan ta taso. Lubna sufyan Hausabook.com 78 Hawayen ta na sauka kan fuskar shi, ya dan motsa, tana jin motsin ya faru tare da zuciyar ta. Kafin kwanaki bakwai su zagayo dakyar take iya kauda kai idan yana hannun wasu, da an dauke shi take jin kamar an dauke mata zuciyar ta har sai sun dawo mata da shi, ranar suna Baabuga ya kawo wani dan rago da yasa Baba sawa aka janyo daya daga inda yake kiwon dabbobi aka hada aka yanka. Yaro yaci sunan shi Abubakar, sunan wani dan Baabuga din da ya rasu. Ana kuma zuwa aka fadama Dije sunan da yaro yaci, wata mata na rangada guda tana dorawa da "Allah shi raya mana Bukar" Ta kalle shi ya sha askin suna yana bacci a hannun ta, wata irin kaunar shi ta soke ta, kauna mai tsanani, kauna kamar bata dauki watanni tana son zubar da cikin shi ba, kamar bata dauki karan tsana ta dora mishi a watannin da yake kwance a cikin ta ba, daga randa ta sauke idanuwan ta akan shi ya shafe komai, komai banda kaunar shi Bukar Bukar dan ta Lubna sufyan Hausabook.com 79 Abinda bata sani ba shine wata kaddarar bata ma soma ba. In da wani yace kafafuwan shi zasu sake daukar shi zuwa kofar gidan su Dije zai karyata. Ya hakura da ita, shine abinda ya gayama zuciyar shi daga lokacin da Allah ya nuna musu cewar basu isa su cire cikin da yake jikinta ba. Tun tana mishi aiken yara a boye har itama ta hakura. A wajen Hammadi yaji maganar haihuwar ta "Dije ta sauka lafiya, ta samu da namiji" Kalaman suka bi ta cikin kunnen shi suna sokar wani abu a kirjin shi da yaji zafin shi ya gauraye ko ina na jikin shi, yawun daya hadiya mai daci ne, dacin da bashi da kalaman da zaiyi amfani da su wajen misalta hakan. Bai furta komai ba, Hammadi ma bai sake ce mishi wani abu ba. Ranar daya koma gida, sanda ya shiga ya dauko Julde a wajen Abu yayi bacci, kwantar da shi yayi yana kwanciya a gefe, yanda yaga rana haka yaga dare, tunani babu wanda baiyi ba. Lubna sufyan Hausabook.com 80 Alkawurra kala-kala na rabuwa da Dije babu wanda baiyi ma kan shi ba. Hanyar duk da yasan idan yabi zai ganta dainawa yayi, sau daya Abu tace masa "Da ka dawo da Dije dakin ta Datti..." Numfasawa yayi "Dan Allah Adda karki kara mun zancenta, na rigada na hakura, Allah ya hada kowa da rabon shi" Kuma Abu har kwanan yau da yake tsaye kofar gidan su Dije bata sake tayar masa da zancen ba. Kowa ya dauki idanuwa ya saka mishi, tunda shi yake azabtuwa da kadaici da kuma wata irin kewar Dije kamar zaiyi ihu, amman a gefe kishinta da yake ya danne komai, sanin ta hada shimfida da wani harda rabo ya shafe mishi komai, har safiyar yau daya dora idanuwan shi a kanta, ita bata ganshi ba, ta fito daga gidan Mamuda, amman shi ya ganta, ya kuma koma baya da sauri ya shiga kwanar daya fara cin karo da ita, zuciyar shi a cikin makoshin shi saboda tsallen da tayo. Lubna sufyan Hausabook.com 81 Ta kara kyau, tayi kyau kamar bata jin rashin shi a kusa da ita, ko da yaje gona bai iya wani abin kirki ba yace ma Hammadi kan shi na ciwo ya koma gida ya kwanta. Ana idar da sallar isha'i yasan cewa koya ake ciki saiya ga Dije, in bai ganta ba sam ba zai iya runtsawa ba, shisa yayo kofar gidan su, ya kuma aika aka kirawo ta, ta dauki wasu mintuna da yake jin su kamar awanni kafin fa fito, da alama bata san kowaye ba, yanayin da yake fuskarta ya nuna hakan "Dije..." Ya furta yana kuwa sa ta dube shi, duba na tsanaki, nan take hawaye suka cika mata ido. Yanda yayi ma kanshi alkawurra daban-daban a bangaren Dijen ma hakane, ko Autan maza ne shi ta hakura da shi, haka ta fadama kanta, haka kuma ta fadawa Abu randa tayi mata zancen shi, wacce wahala ce bata sha akan Dattin ba? Wanne aike ne batayi masa ba a tsayin watannin nan, kafin ta haihu duk kuwa da fadan da tasan zata iya sha idan Baba yaji ta tsaya da shi, bayan ta haihun ma haka, yayi biris da ita, amsar kirki ma bata samu ba daga wajen shi. Lubna sufyan Hausabook.com 82 Watanni goma sha daya kenan da haihuwar ta, idan aka hada da watannin baya, kafin haihuwar shekara daya da wasu watanni da lissafin su yake hango shekaru biyu. Rabon da ta saka shi a idanuwanta, rabon da taji muryar shi cikin kunnuwanta. Da bata da Bukar a kusa da ita fa? Bukar da murmushi kawai zaiyi sai taji duk wata damuwa da take zuciyarta ta kau, Bukar da tun da cikin shi ya kamata ace ta gane cewa ko da tana da rabon wasu yaran a gaba zai kasance daban a cikin su, zai zama wata fitila da zata haska rayuwarta a duk wani duhu da zata shiga. Hakorin nan da yara suke shan wahalar shi, hakorin da ta kusan fidda rai akan Julde lokacin da yayi shi, dariya Bukar yayi ta ganshi a bakin shi "Allah ya bashi sadaka" Cewar Innar A'i, sai dai menene ma Allah bai bawa Bukar dinta ba? A watanni goma sha daya, idan kofin ruwa ne Bukar yakai hannun shi a kai kokarin shi yaga ya bata ta fara sha, ko cikin gidan wani ya bashi yar alawa sai dai taji yana kokarin saka mata a bakinta Lubna sufyan Hausabook.com 83 "Allah ya aramun rayuwa mai tsayi tare da kai Bukar" Ta kan furta idan yayi wani abin daya girmi watannin shi, saboda haka kawai take ji a jikinta kamar ba zata samu wani lokaci mai tsayi tare da shi ba "Dije..." Datti ya sake kira yana katse mata tunanin da takeyi yana kuma ba hawayen ta damar zubowa, juyawa tayi duk da tasan yaudarar kanta takeyi, koya tsayar da ita, ko bai tsayar da ita ba ma ba zata iya kara wani taku akan wanda tayi ba "Dije dan Allah" Ya furta muryar shi cike da wani irin rauni da ya sake saka hawayenta zubowa "Na sake wani kuskuren ko?" Juyowa tayi, ta kasa magana, ko zata iya maganar ma bata san me zatace ba "Kishin ki yayi mun yawa, akwai dararen da nake jin kamar numfashina zai tsaya idan na tuna kina da wani yaron da ba nawa ba...ya Lubna sufyan Hausabook.com 84 zanyi? Ya zanyi ne Dije? Ya zan kalle ki ba zanga yaron da kika samu batare da ni ba" Kuka takeyi sosai zuwa yanzun "Idan zaki iya sake zama dani ina so in sami Baba" Ya karasa maganar zuciyar shi cike da tabbacin har yanzun idan ya rufe idanuwan shi ya yawata cikin tunanin shi ba ya hango shi tare da kowacce mace da ba ita ba, ta ina zai fara? Ita din dai, Dijen shi da duk wasu halayen shi ta sani, ta saba da su kamar yanda ya saba da hakurin ta "Idan kika ce a'a ban san ya zanyi ba" Kai ta daga mishi, ta kasa magana saboda kukan da takeyi, duk abinda ta fada yaudarar kanta takeyi, bata kara tabbatar wa ba sai yanzun da yake gabanta, take jin kamshin turaren nan da yakan siyo duk ranar kasuwa, turaren da bata taba jin shi tare da kowa ba sai shi, kewar shi take ji har cikin kasusuwan jikin ta. Tasan kowa ma ba zai kiya ba, zazzabin kwana biyu Bukar yayi yana da watanni goma cif, saiya yaye kan Lubna sufyan Hausabook.com 85 shi, juyin duniya yaki kama Mama, kowa sai yace ta kyale shi kawai tunda babu abinda baya ci, kamar ya hango mata dawowar Datti shisa ya saukaka mata komai. ** Dangin Dije, wanda suka dinga kwashe ma Datti albarka ana zayyane duk wani mugun halin shi da suka sakani bayan ya sake ta, saboda hango yankewar alherin da yake giftawa a tsakanin su da sukayi, yanzun kowa sai karyata kan shi yake da labarin sake daura musu aure ya riskini kunnuwan su, harma da tsaida mako guda bayan auren akan lokacin tarewar ta. Ikon Allah take kallo "Kinsan dan Adam ajizi ni Dije, amman ai ke da Datti auren ku har a aljanna..." Inji wata Gwaggon ta, abokiyar wasan Baba, da ita tafi kowa zakewa wajen kwashe ma Datti albarka, dan kuwa in taje gidan su, Dije kan bata dan hasafi, kuma Datti ya aika mata nashi ta siyi goro idan yaji zuwan nata, ga soyen sallah da ake aika mata nata kullin daban, kusan da kadan Dijen ta fita jin zafin sakin da Dattin yayi Lubna sufyan Hausabook.com 86 mata. Surutu kala-kala babu wanda bata ji ba, musamman babin halayen kirkin Datti, wasu ma bakine a wajen ta, ita da ta kwana ta tashi dashi a karkashin inuwa daya na tsayin shekaru, sam bata san yana da wannan nagartattun halayen da danginta suke ta yabawa ba. Harda yayyenta da ya ba kyautar zannuwa na binni da ya bayar aka taho mishi dasu daga birnin ikko, kudi yake kashewa kamar wanda zai dauki budurwa. Har Inna da bata da yawan magana sai da tace "Ki yawaita addu'a Dije, Allah ya sa zaman ku mai dorewa ne wannan karin, Allah kuma ya kauda mugun baki akan ku" Duk kunya irin tata sai da ta amsa da "Amin" Can kasan makoshi, sai take jin kamar kwanakin sunki sauri, kamar sunki matsowa. Kirgawa takeyi, amman tamkar sunfi karfin yatsun hannun ta. Sai dai me, ana ce mata tabar Bukar nan sai an kwana biyu an bita da shi taji zuciyarta ta fada, wani hadari mai rugugi na Lubna sufyan Hausabook.com 87 haduwa a cikin kanta, don wauta irin tata komawarta gidan Datti kadai ta hango, bata hango barin Bukar ba, bata kuma hasaso wani zaice ta ajiye shi ba. Tayi yaya to? Ta fara kwana bata gan shi ba ta saka zuciyar ta a ina taji sanyi? In an kwana biyu fa taji suna cewa, kwana biyun bahaushe da bata da tsayayyun ranaku. Kamar suna cewa taje ne zata wayi gari ta wuni ta sake kwana bata rike Bukar a jikin ta ba, bai kira sunata da har yanzun shi kadai ya iya furtawa ba taji muryar shi mai sanyi, ina suke so ta saka ranta? Bayanannen tsoron da yake kan fuskarta yasa Innar A'i murmusawa "Lallai Dije..." Ta fadi saboda ta hango wauta shimfide cikin idanuwan Dijen "Da shi kike tunanin tafiya? Kin dai san da ya kara wayau gidan uban shi zaki mayar da shi ko?" Wannan karin zuciyar da tayi tunani saita nemo ta daga inda ta fada ce ta bazamo tana dawowa mazauninta kafin ta cigaba da dokawa da wani Lubna sufyan Hausabook.com 88 sabon tashin hankali, gidan uban shi? Gidan Baabuga? Mutumin da ko sau daya bai taba zuwa da nufin duba lafiyar yaron ko me yake ci ba? Baabugan da take mantawa daga jikin shi Bukar ya fito? Baabugan da yaran da suke da iyaye ma a cikin gidan shi bai iya basu kulawar da ta dace ba shine ake cewa ta dauki Bukar ta kai, tabbas wasa suke mata, ko kuma rayuwar ce basa kaunar ganin ta a ciki shisa suke son rabata da Bukar da zaiyi barazana da hakan. "Gara ki sama ranki salama akan yaron nan... Ki kuma yi hakuri don bana tunanin Datti zai rike miki shi" Yayarta Kulu ta dora akan zancen Innar A'i, suna karasa hade mata dan wajen shan iskar da ya rage a cikin kirjinta, tana jin komai ya tsaya mata. Bayan nan yanda duk sukayi da ita haka take binsu dan bata da wani kuzarin kirki, doki da murnar da takeyi na komawa dakinta duk ya dishe, hasken fitulun daya gauraye gidan nata lokacin da aka kaita bai taimaka wajen haska duhun daya lullube mata zuciya ba. Wata nasiha da fatan alkhairi da ake ta mata take jiyowa can nesa, sai kace ba cikin daki daya suke da masu Lubna sufyan Hausabook.com 89 maganar ba, da wannan yanayin Datti ya same ta, fuskar shi dauke da haske kamar sabuwar auduga, bakin shi yaki rufuwa saboda farin cikin da yake ciki. "Sai nake jin yau din kamar mafarki" Ya furta yana zama kusa da ita, shi yana jin shi kamar a mafarki ita tana jinta kamar ta farka daga mafarki, in tace ga inda ta tattaro karfin halin biye masa suka raya daren ba zata iya fada ba, surutan shi da alkawurran shi duka basuyi tasiri akan ta ba. Har washegari bata wani jin dadin jikin ta, shima ya kula da haka, dan kafin ya fita saida yace mata "Dan Allah ki saki jikin ki dani Dije, ba zan sake maimaita wannan kuskuren ba" Murmushin karfin hali tayi masa, duk da haka dakyar ta samu ya fita don ya dan bata sararin da zatayi tunani me kyau ko zata samu mafita. Ta rasa, mafita dayace shine ta roki Datti daya barta ta rike Bukar a wajenta, tunda yana da halin da zai iya kula da su gabaki daya. Idan kuma yaki zata roki Inna da ta rike shi a wajen ta, amman ba zata taba mayar da shi gidan Lubna sufyan Hausabook.com 90 Baabuga ba, kome zai faru ba zata kai danta wannan gidan ba, sai dai in bata numfashi. Da wannan tunanin ta dan samu sassaucin kuncin da take ji, duk da kewar Bukar din da take nukurkusar ta. Ta dan samu sauki da shigowar da Abu tayi, saboda sunyi hira suna ta raha, taso ta bita gidanta tace "Ki rufa mun asiri, ke fa yanzun sabuwar amarya ce, kafin wani ya ganni ace nayi girman banza nazo na fito da yar kanwar tawa" Dariya tayi tana sunne kanta "Kai Adda..." Itama Abun dariya tayi tana mata sallama ta fita dan ta dora girkin rana. Bata kuma ba Julde ya shigo "Daada kin dade baki dawo ba" Hannun shi ta kama tana riko shi "Yanzun ai gashi na dawo" Lubna sufyan Hausabook.com 91 Ta karasa maganar tana saka dayan hannunta ta shafi sumar shi da take a nannade irin ta Baban shi. Tana godema Datti da ya sake bata damar kasancewa da gudan jininta a karkashin inuwa daya, jikinta Julde yahau ta kuwa rungume shi, tana jin shi yayi luf kamar yana son fada mata yayi kewar ta amman bashi da wata hanya da ta wuce wannan, a jikinta yayi bacci tana kallon girman da yayi, tana kuma kallon yanda kyawun shi yake kara fitowa kamar ba danta ba, jikin shi a murje alamar hutu da cima mai kyau da kuma kulawar da yake samu, kulawar da take ma Bukar dinta mafarkin samun ta. Ta katanga Abu tayi mata maganar abinci, nufinta ta tura Julde, sai kiran ya bata sanadin fitar da take son yi, ta kuwa saba Julde da ta kai daki ta kwantar saboda baccin da yake yi sanda zatayi sallar azahar, ta dauki mayafi ta ja kofar gidan ta shiga "Oh ni Abu...fitowar dai kikayi" Dariya tayi "Ai shima yasan zan shigo dole" Lubna sufyan Hausabook.com 92 Tsakar gida kan tabarma ta shimfidar da Julde, tare Abu ta zubo musu abincin da suna ci suna ta hira kamar sun shekara basu ga juna ba, hannu da Abu ta cire daga cikin abinci na saka Dije cewa "Ba dai har kin koshi ba" Kai Abu ta gyada mata "Ina jin cikina ne fa yayi datti, kinga dana fara cin abinci sai inji duk ya dagamun hankali, na jika magungunan da Hammadi ya kawo kamar ma ba sha nake ba, zan sake masa magana harna shawara a samo mun..." Kallon ta Dije take tana ganin yanda tayi yar fuska duk da itama ba jikin ne da ita ba, abinka da farar fata duk sai Dije taga ta dashe mata sai kace mai karancin jini "Kinsan yanzun idan na dora tukunya bana tashi daga wajen, dan koya na kishingida sai bacci ya kwashe ni, satin daya gabata sai da aka aiko karbar abinci na farka, ruwan zafi kawai na dora, wutar taci ta cinye..." Lubna sufyan Hausabook.com 93 Dariya Dije tayi wannan karin tare da Abun, su duka basu kawo komai a ran su ba har suka rabu. Ko da wasa Abu bata saka ma ranta komai ba, bata taba batan wata ba, wannan karin da taga kwanaki nata wucewa batare da taga al'adarta ba, saita danganta hakan da canjin yanayin da wasu matan kanyi magana a kai, amman ita bai taba faruwa da ita ba, tana karawa da yawan rashin lafiyar da takeyi da ba Hammadu ba, har ita da kanta yanzun ta fara damuwa da shi "Anya ba zamu shirya muje binni a duba mun ke ba Abu? Duk kin fita hayyacin ka, bana son wannan zazzabin da kike kwana da shi" Murmushin karfin hali tayi mishi "Daga dan zazzabi?" Kuma ita a cikin jikinta tana jin ya wuce dan zazzabi, yanayi ne da bata taba jin shi ba tunda take a rayuwar ta, kai kawai Hammad ya jinjina, raunin da ke zuciyar shi na nunawa har cikin idanuwan shi da basa iya boye sirrin da ke cikin zuciyar tashi Lubna sufyan Hausabook.com 94 Basu hango rabo ba Basu hango samu da rashin da ya tunkaro su ba "Hammadi Am" Ta kira tana kara gyara kwanciyar ta a kusa da shi, muryarta na fitowa daga can kasan makoshi, kuma a raunane, da ba kusa da ita yake ba, da ba dukkan hankalin shi yana kanta ba, da baiji ta kira shi ba, da sunan shi da yake jin kamar an rada masa shine don harshenta, hannu ya kai yana sake taba jikinta a karo na babu adadi tun kwanciyar su, akwai zazzabin har lokacin "Hammadi" Ta sake kira muryarta na sauka fiye da kiran farko, har tsikar jikin shi sai da ta mike. Duk wani labari na soyayya da ya taba ji bai kai matsayin a dora shi mizani daya da abinda zuciyar shi take ji akan Abu ba. "Na'am..." Lubna sufyan Hausabook.com 95 Ya amsa sanin halin ta, duk da tasan ba bacci yake ba, tana iya cigaba da kiran sunan shi batare da ta fadi abinda take so ba har saiya amsa ta, wasu lokuttan dan kawai ta ga ya daga ido ya kalle ta "Kinsan fa ina jinki Abu, ko ban amsa ba ina jin ki" Sai tayi dariya, dariyarta da yake so "Bafa wani abin zan fada ba, kawai dai ina son in kira sunan ka" Girma na shekaru dai ba zai taba canza wasu abubuwan a tare da ita ba, kuruciyar ta dashi kadai yake gani tana nan daram "Alfarma nake roko Hammadi, ba zan so takura ba, amman a lokaci daya kuma ba zan so kace a'a ba, dan Allah ba kunnuwan ka kadai nake so ka bude kaji ni ba, harda zuciyar ka" Numfashi ya sauke da taji hucin shi saman fuskarta saboda kusancin da suke dashi da juna. Tana son Hammadi, wani irin so da ba zai misaltu ba, amman a kwanakin nan sai take jin kamar zatayi mishi nisa, kamar jikinta na nuna Lubna sufyan Hausabook.com 96 mata alamar zata bar shi, zata barshi taje inda zata jira zuwan shi, bata son yayi kadaici kafin ya tarar da ita "Ka kara aure..." Maganar ta dake shi fiye da zaton ta, kafin ya samu damar cewa wani abu ta dora da "Dan Allah ka kara aure, nasan duk alkawurran da muka daukar ma kan mu a baya... Ina so ka kara aure, inajin kamar rabon inga jinin ka a duniya na tare da hakan" Shiru ne ya biyo bayan maganar ta, shirun da kan zo da duhun dare, shiru irin wanda yakan biyo bayan magana mai nauyi da bukatar nazari. "Abu..." Hammadi ya kira sunanta, kirjin shi yayi masa nauyi, kalamanta sun danne shi, idan yace baya son ganin jinin shi a duniya yayi karya. Ko giccin Julde ya gani sai wani abu ya matse a cikin kirjin shi "Baffa..." Lubna sufyan Hausabook.com 97 Haka Julde yake kiran shi, ko da na dakika daya idan ya rike shi ya so ya manta cewa ba daga jikin shi ya fito ba, ya so ya yaudari kan shi, na dakika daya kawai, sai kalmar ta fizgo shi ta dawo da shi, sai ta tuna mishi cewa Julde dan Datti ne. Tun kafin ma azo kan shi Dattin ma da baisan kara ba, Datti da baya gajiya da fada masa cewar Julden dan shine, ya sani, amman Datti baya gajiya da tunasar da shi. Bai fada ba, amman abin yana masa zafi har kasan zuciyar shi. Rashin da akwai ciwo, rashin haihuwa jarabtace da wanda yake cikinta kawai ya san zafin hakan. Ba zaka taba sanin ka damu da haihuwa ba sai kaga alamun ba zaka same ta ba, sai kaga hakan yasa ka fita daban a cikin sauran ma'aurata, sai ka gansu rike da nasu yaran zakaji kamar suna nuna maka yanda ba zaka taba samun naka bane "Dana yayi kaza" Sai kaji kamar sun goga maka gishiri akan ciwon ka "Yar waje na ce" Lubna sufyan Hausabook.com 98 Kamar suna maka habaici ne a fakaice, suna nuna maka sun samu baka samu ba, suna da su kai baka da su, zasu iya, kai ka gaza. Sosai akwai ciwo, hakurin bana lokaci daya bane ba, musamman idan addu'ar kowa bayan ka kyautata mishi bata wuce "Allah ya saka da alkhairi, Allah ya kawo rabo mai albarka kaima ka samu mai maka addu'a" Da zai iya, da yace musu subar sauran addu'ar, suyi masa ita iya zuciyar su ba sai sun furta yaji ba, ba sai yaga wannan tausayin a cikin idanuwan su ba, suna kallon shi kamar rashin haihuwa wata bayananniyar nakasa ce da yake tare da ita "Bana sha'awar kara aure" Hannun shi da yake jikinta ta kamo tana hade yatsun su waje daya, tana jin alamun aikin karfi na yau da kullum a duk lokacin da ta rike hannun shi, inda da haske ma tasan in zata duba ba zata rasa sabon ciwo a jiki ba. "Na sani, shisa nace ka bude zuciyar ka" Numfashi yaja yana saukewa a hankali Lubna sufyan Hausabook.com 99 "Ko na bude babu wanda zai bani 'yar shi bayan a bayyane yake bana haihuwa" Dumtsa hannun shi da yake cikin nata tayi "Inji wa? Kaf garin marake ko 'yar wa ka nema za'a baka... Dan Allah ka duba bukatata" Baice komai ba, matsawa ya sakeyi yana hade sauran wajen da yake tsakanin su, itama bata ce komai ba, barin kusancin su tayi ya karasa musu sauran zancen. * "Bangane kince ya karo aure ba? Adda idan ta zo ta haihu fa?" Murmushi tayi ganin tashin hankalin da yake shimfide a fuskar Dije "To ai abinda muke nema kenan daman" Kai Dije take girgizawa, maganar ta kasa zauna mata, bata kasance cikin mata masu zafin kishi ba, ta duba, ta hango Datti da wata, akwai ciwo a hasashen da tayi, amman ciwo ne da zata iya rayuwa da shi batare daya cutar da ita ba. Sai dai da ta saka kafafuwanta a takalman Abu, ta Lubna sufyan Hausabook.com 100 haska, ta hango rashin haihuwa, ta hango Datti da karo wata, ta hango rabo a tsakanin su sai taji numfashinta ya fara neman tsayawa, kirjinta yayi wani irin nauyi. Idan tayi mata gori fa? Idan ta hanata daukar dan ko yar? Miji ne ta rigada ta kwace shi daman, idan ta kore ta daga gidan gabaki daya fa? Shikenan? Babu haihuwa kuma mijin ma babu shi "Kayya... Adda maganar nan abar ta, karki fara abinda ba zai bulle damu ba gabaki daya" Dariya kawai tayi, ba zata ce bata jin kishi ba, soyayyar Hammadi duk kauyen sun shaida kalarta daban ce, balle kuma ita da akalar soyayyar ta karkata akan ta. Kishin raba shi da wata, ba kishin ta shigo ta samu rabo da shi ba. Tana ma Hammadu son da take addu'a da dukkan zuciyar ta rashin haihuwar su ya fito daga bangaren ta. Shi din ya zame mata komai a lokuttan mabanbanta, a wajen haihuwarta ta rasa mahaifiyar ta, kowa zai shaida wuya bata kisa, da Abu bata rayu ba saboda wahalar da ta sha a wajen kishiyar mahaifiyar ta. Lubna sufyan Hausabook.com 101 Tana dakin Hammadi ta sake rasa mahaifinta, sai ya zame mata wani bango da take jingine da shi, bangon da har yan uwan da suka nuna mata tsangwama a baya sun rabota suna morar wannan bangon. Da zuciya daya take son Hammadi ya kara aure "Zata iya shigowa ta samu rabo ke kuma ta rabaki da gidan" Daya daga cikin maganganun da tayi ta ji kenan daga yan uwa da abokan arziki, kowa da kalar tashi, basu sa ta tsorata ba balle

Chapter 4 of 27