Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
fanke yayi dadi tunda kike tunanin yi" Dayan daya rage ta dauka tana ajiye robar "Fanken ne baya sona Daada duk son da nakeyi masa, kin manta na karshe da nayi" Dariya Daada takeyi, dan ba zata manta da wannan fanken da ya koma fankaso ba "Amman dai ba zan cika ruwa ba" Cewar Madina, Daada ta kasa daina dariya "Daada mana" Dakyar ta iya cewa "Ki dai kwaba kadan dan a takaita barna" Tare sukayi dariyar wannan karin, labari suke danyi, kusan ma Madina ce take bata labarin, Lubna sufyan Hausabook.com 559 wani littafi data karanta, itama Daadar rabin hankalinta ne yake kan Madina, saboda wata irin bugawa da zuciyarta takeyi a cikin kirjinta, kamar tana son sanar da ita wani abu data kasa fahimta, shisa ita kuma zuciyar taki natsuwa waje daya, take ta kai kawo cikin neman hanyar da zata isar da sakonta, tasan muryar Salim, amman yau da yayi sallama sai bugun zuciyarta ya kara tsananta "Hamma ne, yace zaije ya dawo ne daman" Madina ta furta, amman Daada jin maganar tayi can nesa da ita, haka da Salim ya shigo dakin, ya zabi ya fara sauke idanuwan shi akanta a maimakon Madina, Salim da yakeyi kamar bayason magana da kowa, Salim da zaiyi duk wani kokari na kaucewa hada idanuwa da ita bayan ya gaisheta dan karta samu halin sakeyi masa magana, yau nashi idanuwan ne suka fara laluben nata, labbanshi suka motsa ya furta "Daada..." Kafin ya matsa daga hanyar kofar kamar yana son bawa wani damar shigowa, sai idanuwanta suka bar na Salim suka koma kan kofar, inda Lubna sufyan Hausabook.com 560 duk wani mafarki, duk wani hasashe, duk wani tsammani a tsayin shekarun nan bai shirya zuciyarta tarbar abinda take gani yanzun ba. Kamar hudowar hasken rana ta tsakanin gizagizai, haka shigowar Yelwa dakin ta kasance mata, sai farin mayafin da yake yane saman kanta ya shiga idanuwan Daada, tare da wani hasken da bata da kalmomin misalta shi, batare data sani ba ta kai hannu saman cikinta, inda take jin wani abu yana yamutsa mata, a lokaci daya kuma abubuwa da yawa suka soma turereniya da juna wajen dawo mata A cikinta, Yelwa ta kwanta Watanni tara harda satika uku, lissafi ba zai taba kwace mata ba ko akan yaran da suka leko dan ta amsa sunan uwa, suka koma kafin ta taka wata rawar gani a wannan matsayin da suka bata Nakudar ta a tsakanin kai kawon Abu da kuma mahaifiyarta Kyawunta Lubna sufyan Hausabook.com 561 Kyawun Yelwa da ya zama abin magana wajen duk wanda yayi tozali da ita 'Yarta Tilon 'yarta Sai kauna irin wadda mahaifiya ce kawai zata taba fahimta ta danneta hartana kasa fitar da numfashi yanda ya kamata, wannan kaunar da babu wani laifi da yake disashe haskenta a zuciyar mahaifiya, kaunar yaranta, kaunar da ko mahaifansu ba zasu taba fahimta ba, saboda kashin bayansu bai karye ba, kugunsu bai amsa ba, ba suyi rayuwa a tsakanin duniya da lahira ba a cikin dakin nakuda, ba suja numfashi suna tsammanin shine na karshe ba, da suka fita suka nemo don su ciyar, a cikin shekaru biyu abincin daga aljihunsu ya fito ba daga jikinsu ba, ba zasu taba fahimtar wannan soyayyar ba. Hannu ta mika, saboda shine iya motsin da zata iya "Daada...Daada Am" Muryar Yelwa da take rawa ta ratsa kunnuwan Daada data lumshe idanuwanta tana jero duk wata godiya da zata iya tunawa wajen Ubangiji, Lubna sufyan Hausabook.com 562 da ya kadarta fitowar Yelwa daga cikinta, ya kadarta zatayi mata nisa, ya kuma kadarta rayuwa ba zata kare mata ba sai ta sake ganinta, idanuwan ta bude lokacin da dumin hannun Yelwa ya ratsa nata Shekaru goma sha bakwai ana neman hada ta sha takwas din, a cikin shekarun tayi numfashi da sanin adadin shi sai wanda ya bata ikon yi, sai dai a tsayin lokacin, a cikin kowanne shiga da fitar numfashinta akwai kewar ahalinta, wata irin kewa da zatace ta danne ruhinta dan idan tace zuciyarta kamar yayi kadan. Kewace mai cike da taraddadin ya lafiyar su take, duk da wautar tunani bata kawo mata rasa wani a cikinsu ba a tsayin shekarun nan. Ko a tunaninta abune da ba zata iya dauka ba. Musamman da idanuwanta suka sauka kan Daada, da taja numfashi ta fito dashi tana jin wani nauyi da yake danne da zuciyarta ya daga, ta runtsa idanuwanta ta bude su yafi a kirga a kasa da dakika, tana son maida hawayen da suka cika mata idanuwa suna hana mata ganin hoton Daada tar a cikinsu. Lubna sufyan Hausabook.com 563 Sai maganganu kala-kala suka dinga turereniya a cikin kanta, har tana rasa wanda ya kamata ta fara furtawa, shisa ta zabi "Daada...Daada Am" Suna fitowa daga wani lungu na zuciyarta, tazarar shekarun da tayi batare da Daadar ba na hadewa da ita waje daya. Da ta karasa cikin dakin sosai, saita durkusa a gaban Daada, kafafuwanta na gode mata saboda ko da bata taimaka musu ba gab suke da kasa daukar gangar jikinta duk kuwa da yanda take jinta sakayau, kamar fallen takarda. Sai dai har zuwa lokacin ta rasa abinda zata sake cewa,ta sauke kanta, hawayenta suna diga akan kafet din dake shimfide cikin dakin, data dago da kan ma hawayen ne suke zubo mata, tanajin karar hancinta da taja na komawa cikin kunnenta da wani irin yanayi saboda shirun da yake cikin dakin "Nayi kuskure" Ta furta cikin kanta "Ki yafemun?" Lubna sufyan Hausabook.com 564 Kalmomin suka biyo bayan wadancan duka a cikin kanta, kuskure ta sani, ta kuma fada a waccen haduwar da sukayi, daga lokacin da taji hannun Kabiru a cikin nata bayan auren da aka daura musu suna sauka garin Kano, ta kalli mutumin da yayi mata wakilci, ta juya ta kalli wanda yayiwa Kabiru wakilci sai Malamin daya daura musu aure da shine cikon mutum na uku, kuskuren da tayi ya danneta, amman ya zatayi da soyayyar Kabiru? Duk da a lokacin bata hango rabon da yake tsakaninsu ba, kuskuren kawai ta gani. Ta kuma sake ganin a daren da suka dorar da auren su zuwa wayewar gari, tayi wani irin kuka, ta wuni tanayi batare da ta samu saukin nauyin da zuciyarta tayi mata a rikon da Kabiru yayi mata cikin jikin shi yanayi mata rumfa ba "Inajin kamar ya kamata in baki hakuri Yelwa, kamar ya kamata inji ban kyauta ba dana raboki da ahalinki, na so kaina da yawa nasani. Amman zuciyata bata dana sani, haka girman soyayyarki ya rufemun ido, na kasa damuwa da laifin da nayiwa ahalinki na raboki dasu Yelwa, ina taso inji rashin kyautawar nan amman na kasa" Lubna sufyan Hausabook.com 565 Kanta kawai ta sake binnewa a cikin kirjinshi, hawayenta na cigaba da zuba, saboda in zata fadawa kanta gaskiya, a tsakanin nauyin zuciyarta da kuskuren da take jin tayi, akwai soyayyar shi, akwai kaunar da takeyi masa da bata san yawanta ba. Ko yanzun da take son juyawa ta koma gida, zai wahala yafiya ce abinda zata fara rokansu, idan ta saka gwiwoyinta a kasa a gaban Datti tana da yakinin abinda zai fara fitowa daga bakinta ba zai wuce "Dan Allah Baba karka rabani da Kabiru..." Da kalamai kwatankwacin wannan, sannan ta roke shi ya yafe mata ta kara daya taimaka ya fahimci girman son da take yiwa Kabirun da yasa ta tsallake su ta bishi. Ko yanzun ma da take durkushe a gaban Daada, dana saninta baya jingine da auren Kabiru, kewar su da tayi tafi komai yawa. Hannu ta dago ta share kwallar da ta riga ta gangaro mata, ta dan juyar da kanta ta kalli Kabiru da yake tsaye, idanuwan shi akanta, kamar zubar hawayenta yake jira yagani su bashi izinin karasowa yayi irin zaman da tayi a gefenta, cikin son nuna mata yanda ba zai taba barinta ita kadai ba. Lubna sufyan Hausabook.com 566 A tsayin zamansu, tun tana jiran ranar da Kabiru zai nuna mata halinsu na maza da akafi yi musu tambari dashi harta daina, tun tana jiran alhakin bijirewa iyaye ya kamata ta wannan fanni saida ta daina, ba zatace basu taba fada ba, za dai tace a kowanne lokaci laifin nata ne, zata kuma ce na rana daya Kabiru bai taba biye mata ba, karshen abinda zaiyi ya nuna mata ranshi ya baci shine ya saka takalman shi ya bar mata gidan, da zuciyar shi tayi sanyi idan ya dawo bayan sallama, lokutta da dama yakan dora da "Kin huce in shigo? Ko in har yanzun bakya son ganina?" Wasu ranakun kuma "Yunwa nakeji Yelwa, in shigo ki taimaka ki bani abinci ko fushin bai bari kin girka mana ba?" Mazan da ta sani a rayuwarta basu da yawa, a tsakanin kawaici irin ma Hammadi da sanyin hali na Bukar, zatace Kabiru ya hada duka ya kara da wasu halayen nagartattu. Zai wahala kaga fuskar shi babu wannan murmushin da kyallin shi yake haskawa har cikin kananun Lubna sufyan Hausabook.com 567 idanuwan shi. Shisa a hankali ya koya mata kwantar da hankalinta, natsuwar da yake tare da ita kullum tayi mata inuwa harta mike kafafuwanta, saboda ta dauka kalubalen su daga bangarenta ne kawai kuma sunyo masa nisa. Tunda da sana'arshi ta fitar da dabbobi suka dogara, tafiye-tafiyen shi basu taba damunta ba. Ta hadu da nagartattun makotan da ko a barin da tayi na farko da Kabiru baya nan bataji rashin yan uwa a kusa da ita ba, sunyi mata taimakon da sai da yasa ta hawaye saboda batayi tsammanin a zaman su tayi musu wani abu da ta cancanci wannan karamcin ba. Sai dai mutanen arziki ba sunayi maka kirki bane dan kayi musu, karamcin ne cike da zuciyar su shisa rarrabashi baya taba yi musu wahala. A kowacce tafiya idan zaiyi tana ganin damuwar nisan da zaiyi mata cike da idanuwan shi "Ina ta duba garin da masu irin sana'ata basu yawaita ba mu koma, bana son yanda nake barinki ke kadai" Ya fadi kamar a lokacin yasan wannan tafiyar tashi zata zama sanadi na farko na jirkicewar Lubna sufyan Hausabook.com 568 lamurran su. Murmushin da tayi masa cike yake da kokarinta na karfafar shi. Bata hango tsakanin wannan murmushin nata da wani akwai wata tazara mai nisa ba, sai dai satika hudun da yakanyi duk idan yayi tafiya suka shige babu amon shi balle kuma labari, sai ta daina lissafi da kwanaki lokacin daya hada watanni uku, cikin jikinta kuma ya shiga watan da lissafi ya nuna cewa yana gab da fitowa duniya. Sauran lissafin da take tare dashi ya karasa kwacewa ne ranar da ta fito daga bayi tana kokarin zama dan daura alwala wata mata ta shigo mata gida babu ko sallama tana kallonta da fadin "Yelwa ko?" Tana da yakinin mamakinta ya bayyana akan fuskarta "Baki sanni ba nasani, matar Kabiru ce" Abinda yayi saura na zuciyarta da baya tare da Kabiru taji yana barazanar fitowa daga kirjinta Lubna sufyan Hausabook.com 569 "Kin dauka kinyi nasarar rabamu zakiyi rayuwa dashi ke kadai ne? Ke kin isa yayi mun saki uku ke ki rayu dashi? Waye ubanki?" Kafafuwanta Yelwa taji suna rawa wannan karin "Ki nemarwa cikin jikinki uba idan rabon shine ya hada hanyarku, amman in dai Kabiru ne, ni kuma ina da sauran numfashi yanda nabar shi ya barki kenan. Na so in barki ki cigaba da duban hanya, amman ina son kallon idanuwanki ne kamar yanda nake son kiga fuskata" Ko da ta fita bayan "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Da ta furta wani zazzabine ya danneta, kafin tashin hankali ya fara barazana da rayuwarta. Ba kirga kwanaki takeyi ba ballantana a lokacin tasan kwana nawa ta hada kafin tunanin komawa Marake ya dirar mata, ta dai san in tayi numfashi sai abinda yake cikinta ya motsa mata kamar yana tuna mata da yanda take wata rayuwa a tsakanin duniya da lahira. Sai wani sabon firgici ya sake danneta akan wanda take ciki. A wajen Kabiru ta koyi rubutu da karatun Lubna sufyan Hausabook.com 570 hausa tunda gatan da Datti ya nuna musu bai barsu sunyi karatun ba duk kuwa yanda Dije taso su dashi, haka kawai safiyar data tashi da nufin tafiya Marake wani abu yake fada mata ba zata rayu da abinda yake cikinta ba, wannan abin na sake tabbatar mata da macece, a lokaci daya kuma yana sakata rubuta wasikar da bata da yakinin zata isa inda take son isar da ita. Sai dai ganin Datti a kwance ya kara birkita mata komai, daren nan da ta kasa mantawa har yau na dawo mata, muryar shi bayan ta roke shi daya yafe mata, raunin da yake cikin muryar lokacin daya furta "Soyayyar da nayi muku laifi ce Yelwa? Me yasa kuka kasa gane kune gabaki daya duniyata? Ko dan nima ban kara tabbatar da hakan ba sai da kuka zabi kuyi mun nisa naga fadinta? Na jini ni kadai? Komai ya tsayamun yana sakani tunanin inda na kuskure a tawa soyayyar..." Ya karasa muryarshi na karyewa tare da wani abu a zuciyarta "Na yafe miki..." Lubna sufyan Hausabook.com 571 Hawayenta suka zubo "Zuciyata na ciwo, sosai..." Kai ta daga hawayenta na zubowa, tasan itace silar komai, saita dauka tunda ta tafine ya kwanta ciwo, ta bude bakinta da nufin sake rokon shi ya yafe mata sai yaja wani irin numfashi da bataji ya fitar dashi ba, kafin zuciyarta ta buga tare da bayanta daya amsa "Kin kashe shi" Wata murya ta fada mata a cikin kanta. Kuma ko da ta fadawa Daada ta kashe shi a lokacin batayi kokarin musa mata ba. Ta san ta haihu, saboda ko mahaukaciya ta san da, balle kuma ita da ta haihu cikin hayyacinta. Zata tuna wankan da Daada tayi mata, kayan da ta saka mata, yarinyar da ta damka mata a hannunta don ta shayar da ita. A cikin wannan firgicin ne wani irin abu ya tsirga mata daya sakata ajiye yarinyar tana mikewa tsaye. Wannan abin daya tsirga mata shine yake tunkudar zuciyarta da wani irin karfi daya shallake ikonta. Ko yarinyar da kukanta ya isa kunnenta da wani yanayi batayi tunani ba balle takalmi da mayafi, saboda Lubna sufyan Hausabook.com 572 abinda yake fisgarta yana gaya mata ta bi hanya kawai. Hanyar kuwa tabi, hanyoyin da ba zata iya gane su ba, saboda ba'a cikin hankalinta take tafiyar ba. Bata kuma san ko wani yayi nufin taimakonta da abinci inta karba sai dai taci shi tana tafiya saboda inta zauna sai taji wannan abin yana fisgarta komin zugin da kafafuwanta sukeyi mata na alamun gajiya. Kamar yanda bata san ta shafe shekaru biyar a wata irin duniya da ko makiyinta bata fatan ya shiga ciki. Kafin wata safiyar juma'a data canza mata komai, tana tafiya kawai ta tsinci kanta a gefen titi kamar wadda take yawo a mafarki saboda karshen abinda zata tuna shine ta haihu, shine tana cikin dakin Datti, sai kuma rasuwar shi, sai ta ganta a gefen titi a tsaye, kafafuwanta babu ko takalmi cikin wani yanayi daya nuna gararambar da ta sha. Haka kuma bata san cewa a wannan juma'ar ake taron suna a wani gida, a daya daga cikin sababbin unguwanni masu tasowa a lokacin a garin Kano, sanadin wannan sunan da za'ayi sun kira me majalisi don shagali a kofar gida, katon Lubna sufyan Hausabook.com 573 dutsen da tunda suka siyi filin, har akayi gini yana nan gefe, samari suka taru suka saka karfi wajen mirgina shi don a kara samun wajen da mutane zasu tsaya su kalli majalisin da za'ayi, a kasan dutsen kuma suka ga katuwar layar da basu tsaya dogon tunani ba suka warwareta, daya a ciki ya bada shawarar a kone zaren da layar duka, suna jinjina neman duniya irin na mutane, da kuma tunanin wa akayiwa wannan mugun abin aka danne da wannan dutsen da Allah kadai yasan shekarun da yayi a wajen. Da yake Allah ya yanke mata wahala, sai sanadin samun saukinta ya biyo ta hannun mutanen da ko a titi zai wahala kaddara ta hadasu balle tayi tunanin gode musu. Da taimakon mutanen kauyen da take gararamba aka dorata a motar Kano, da tambaya da komai ta gabo Bachirawa, unguwar da gidansu yake, unguwar da taga ta canza mata gabaki daya saboda gine-ginen da akayi, da wata tambayar da taimakon Malam Malami mai almajirai da suke layi daya a wancen lokacin ta gano gidanta, gidansu ita da Kabiru. Harta karasa ta kwankwasa kofar gidan Lubna sufyan Hausabook.com 574 batayi tunanin za'a bude ba, har yau kuma ba zata manta yanayin fuskar Kabiru ba. Ba zata manta yanda bai iya ce mata komai ba sai hannunta daya kama yana janta zuwa jikinshi yayi mata wani riko tamkar an mishi alkawari karuwar kwanakin shi a duniya idan ya riketa. Haka ba zata manta dumin hawayen shi da suka sauka akan kafadarta ba. Sun kwana a gidan, shi yana da labarin bayarwa, ya fada mata yana son dawowa gida amman saiya kasa, da yayi yunkuri sai yaga wani duhu da tunanin shi na dawowa gida yake bacewa a ciki, abokin cinikayyar shine ya kula da hakan, ya kuma tsaya kai da fata wajen karbo mishi taimako wajen wani Malami har abin ya karye, sai dai daya dawo ya nemeta bai ganta ba saiya koma, ya nemi abokin shi inda cikin rashin sa'a suka tarar Allah ya amshi rayuwar Malamin, zargin abinda ya same shi shiya sameta yasa shi bin duk wani Malami da zaici karo dashi wajen neman ya taimaka masa da addu'a akanta, amman karshen abin baizo ba. Ya koma Marake kuma, labari ya samu na taje can, harta haihu, sai dai babu wanda yasan inda Lubna sufyan Hausabook.com 575 take daga nan, haka ma su Daada, a 'yan uwanta yaji labarin Yelwa data haihu ta gudu ne saboda abin kunya, Daadar ma saita kasa zama, anman anfi kyautata zaton Kano ta gudu inda Julde yake da zama. Wani zance daya daki zuciyar shi, bakinshi yayi masa nauyi wajen fada musu abinda Yelwa ta haifa ba ta hanyar da suke tunani bane ba, saboda idan ya fada wacce shaida zaiyi amfani da ita wajen gamsar dasu gaskiyar shi? Daya dawo Kano saiya rasa gabas zaiyi ko arewa, garin Kano da girma, ta ina zai fara neman su Daada? Idan ya gansu kuma bai samu Yelwa a tare dasu ba ya zaice? Wanne labari zai basu? Ya gudo musu da yarinya ta kuma bace a karkashin kulawar shi? A cikin labaran shi duka da ido Yelwa ta dinga binshi, saboda ita bata da labarin bashi, yasan ta haihu, yasan mace ta haifa, yasan mahaifinta ya rasu. Ina taje? Me yasa ta tafi? Me takeyi a wannan shekaru biyar din duka bata sani ba, mahaukaci koya warke bashi da labarin bayarwa tunda hankalin da zai rike faruwar abubuwan ne gabaki daya ya kubce masa. Ta dai fada masa tsohuwar matarshi tazo, ta kuma fada Lubna sufyan Hausabook.com 576 masa maganganun da tayi mata wanda har yau suke mata yawo "Sahura?" Ya tambaya da mamaki shimfide a fuskar shi, ranar taji sunanta, sunan da bata so ta sakeji ko a mafarki. Sun sake kwana a garin Kano, sai dai Kabiru ya tsorata, shisa suka bar Kano "Fadan nan ya wuce ayi cacar baki, ko a ware aji karfin juna Yelwa, fadan da Sahura ta dauka damu fadane da in ba imaninmu zamuyi nisa dashi ba Allah yana iya sake bata nasara akanmu dan ya sake jaraba mu, gara muyiwa Kano nisa, muyi nisan da sai dai a buga kasa a bata labarin mu wanda zai iya zama gaibu za'a gaya mata, idan wani abin ya sake samun ki ba zan iya yafewa kaina ba" Yanda ya karasa maganar, ramar da tagani a tare dashi da yanayin da yake cikin idanuwan shine abinda yayi galaba akanta ta bishi, bayan tarin alkawurran da yayi mata na cigaba da neman ahalinta da kuma alkawarin yanda ya rabota dasu zai sake sadata dasu cikin hukuncin Ubangiji. Sai gashi ya cika mata wannan Lubna sufyan Hausabook.com 577 alkawarin a lokacin data cire rai da samuwar hakan. Dan har suka hawo mota jinta takeyi kamar a cikin mafarki take yawo, mafarkin da bata farka ba sai yanzun da ta ganta a gaban Daada, sai yanzun da taji hannun Daada rike da nata. Sai ta dan karkata kai tana kallon Madina da ta zuba mata ido ta cikin gilashin da yake makale da fuskarta. Yarinyarta Yarinyar da rabonta yasa ta tsallake komai a karo na farko Yarinyar da ta haifa kaddara ta sata tsallaketa tare da komai a karo na biyu Sai wani abu ya tsirga mata, ta sake kallon Daada da tambayar da bata iya furtawa ba, Daada ta daga mata kai kamar ta karanci tambayar "Madina..." Daada ta furta muryarta a sarke saboda kukan da yake son kwace mata, sai Yelwa ta rigata, saboda bayan hawaye sun zubo mata, da taja Lubna sufyan Hausabook.com 578 numfashi tazo saukewa saiya taho da wata irin shessheka da ta kasa dannewa Tunda yake bai taba tunanin shan wani abu ba sai a sati dayan nan, idan yana cikin yanayi irin wannan Madina ce kawai yake gani yaji komai ya dan lafa masa, to yanzun abinda yake ji yana da alaka da ita. Ashe da yayi tunanin ya san girman son da yakeyi mata karya yayiwa kanshi, ko da yaga ya kusan rasata bai shiga rudani irin na kwanakin nan ba, idanuwanta ne abu na karshe da yake gani cikin kanshi kafin ya samu bacci, haka daya bude ido dasu yake fara sallama, ba dan bai taba ganinsu cike da abubuwa da yawa ba, tunda tana da idanuwan da zasu iya baka labarai kala-kala akanta idan ka natsu cikin kallon su, ba tare data bude bakinta ba, amman ranar ta dago ta kalle shi, tayi masa kallon da bata taba yi masa irin shi ba, ta kalle shi da wani kyalli da shine karo na farko daya fara ganinshi cikin idanuwan nata. Ta kalle shi kamar duka fatanta yana karkashin kafafuwan shi, sai yaji wani abu daya girmi ace Lubna sufyan Hausabook.com 579 tsikar jikinshi ce tana tashi, ko yayi musu sallama ba zai tuna ba, ya dai bar dakin, ya saka takalman shi yaja kafafuwanshi zuwa motar shi, inda yana zama ruwane abinda ya fara nema ya jika makoshin da yakejin ya bushe masa "Yarinya ce Salim, ko shekaru sha takwas bata karasa ba, yarinya ce, get a grip" Yake fada yana sake maimaitawa kanshi, a lokaci daya kuma yana so ya tuna ma kanshi bai kamata ace yarinya kamarta bace take neman susuta shi haka. Shisa ya dauke kafarshi, ya bata tazara ta gama karbar dawowar itayenta, tayi musu duk wata tambaya data jima tana adanawa a cikin zuciyarta. Yanda ta kalle shi kamar babu wani abu da zai tambayeta da zata kasa yi masa ya bashi tsoro, ya girgiza wajajen da baisan da zaman su ba a cikin zuciyar shi. Ko zata karbi soyayyar shi daya mika mata bayaso tazo ta haka, bayaso ta karbeshi saboda ya zama sanadin dawowar iyayenta, idan zata karbeshi yana so ta karbeshi saboda shine zabinta. Amman sai tazarar take taba shi fiye da yanda yayi zato. Sai ya zamana kamar komai na Lubna sufyan Hausabook.com 580 rayuwarshi ya yanke shawarar tuna masa ita, ko a asibiti duk wasu marassa lafiya da suke karkashin kulawar shi a satin, suna dauke ne da cututttukan da suka tattauna akai shi da Madina, yana duba su komai na hirarrakin na dawo masa, kewarta da son ganinta na kara nukurkusar shi. Kwanan shi na hudu kenan a asibiti, anan yake wuni kuma. Abinci ma sai dai yayi order a kawo masa har cikin asibitin, turawa yakanyi saboda, abincin kanshi yana kara tuna masa da cewar alkawarin da yayi mata na ba zai dinga zama da yunwa ba, ko da bayaji ma idan har yasan jikinshi na bukatar abinci ko kadanne zaiyi kokarin ganin yaci. Sai gashi ta fara kutsowa har cikin baccin shi tana sakashi farkawa babu adadi a duk wani bacci da zaiyi na dare ko na rana. Ranar kwana na takwas dinne kiran Nawfal ya shigo wayarshi ya daga batare da yace komai ba "Zaka dawo gida da kanka ko in kwaso kowa muzo asibitin su tayani dauko ka?" Lubna sufyan Hausabook.com 581 Hannu yakai yana murza goshin shi, ta inda yakejin alamun ciwon kan dake neman wajen zama "Bajjo" Ya kira, muryarshi na fitowa da gajiyar da baiso ba "Mu taho din kenan" Halayenshi basu taba hana duka kannen shi tsokanar shi ba, amman a cikinsu babu wanda yake iya sakashi yin abinda bai niyya ba kamar Nawfal, saboda ko me zaiyi ma Nawfal din sai dai yayi, amman abinda yace zaiyi ba zai fasa ba. Kowa din ba zai wuce Khalid ba, in kuma za'a hada Nawfal da irin Khalid biyar ba zasu iya daukar shi ba. Sai dai bayason kure Nawfal din, bayason yaga shi da Khalid dinne kawai zasu zo ko kuwa harda wasu zai gayyato suyi masa hayaniyar da bashida wajen daukarta. "Ba zaka iya numfashi a hankali bane?" Salim ya fadi yana janye wayar daga kunnen shi, shisa yake amsa waya a speaker, saboda ya tsani yanajin wannan numfarfashin cikin kunnen shi Lubna sufyan Hausabook.com 582 "Ya zanyi numfashi a hankali Hamma?" Kara hade girarshi Salim yayi kamar Nawfal din yana ganin shi sannan yace "Ban sani ba, karar numfashin yana shigarmun kunne" Ya karasa yana saka kiran a speaker ya ajiye wayar kan teburin da yake gabanshi "Karar numfashi? Kasan me? Ba kira nayi muyi maganar nan ba, mu zo?" Wannan karin numfashi Salim ya sauke "Zan dawo gida anjima" Ko da baya ganin Nawfal yasan kai yake jinjinawa "Idan baka dawo ba zamu zo" Bai amsa ba ya kashe wayar. Bai fita daga asibitin ba sai bayan la'asar, daya fito daga masallacin saiya nufi motar shi, duk da hargitsin da yake ciki akwai wata natsuwa ta daban da koya taba saninta toya manta haka take, duk lokacin da zai shiga masallaci ayi sallah dashi a Lubna sufyan Hausabook.com 583 jam'i akan lokacinta sai yaji kamar an diga masa haske a duhun da bai taba sanin yana tare da zuciyarshi ba. Ba kamar lokacin da inya hada salloli ya idar zaiji wani irin nauyi ya danne masa zuciyar ba, yanzun sakat yake jinta ta wannan fannin, sai tarin zunuban da yake rokon yafiyar Allah akansu cike da wata kunya marar misaltuwa. Kunya hadi da tsoro saboda yaga maikon da zina take dashi, yaga yanda take da karfin ruguza abubuwa da yawa, a duniya kenan, ko anan din bashida kafafuwan tsayawa a gaban makusantan shi idan daudar zunuban shi ta bayyana, sai yanzun tsoro ko yace firgici yake shigarshi, nauyin zunubanshi nayi masa rumfa "Astagfirullah..." Ya furta a kasan numfashin shi yana murza mukullin motar ya tasheta, a kasan duk wannan firgicin baya manta Allah Mai yawan Gafara ne, Mai yawan Rahma. Yana fita titi wayarshi nayin kara alamar shigowar kira, harya shirya zagin da zai watsawa Nawfal idan ya daga sai zuciyarshi tayo wani zullo kamar tana son Lubna sufyan Hausabook.com 584 fitowa ta daga kiran da kanta ganin Madina ce, yana karawa a kunnen shi kafin yace wani abu ta rigashi da fadin "Hamma..." Kuma baisan ko zuciyarshi bace take kitsa mishi abinda su duka suke sonji, kamar akwai kewarshi a muryarta, a yanayin yanda ta kirashin "Kina ina?" Ya tambaya saboda ba zai iya sake kwana bai sakata a idanuwan shi ba "Ina gida" Ta amsa a takaice, kai ya jinjina kamar tana ganin shi ya sauke wayar daga kunnenshi yana katse kiran daga bangarenshi, kafin ya mike yana shan U-turn ya koma hanyar da zata hadashi da gidan Daada. Yana parking din motar shi yana jinta tana kwankwasa gilashin motar kamar tana kofar gida tana jiranshi, daga inda yake ya fara kallonta. Rigace mai hula a jikinta, ta saka hannunta daya a cikin aljihun rigar, dayan tana kwankwasa masa kofa, akwai wata Lubna sufyan Hausabook.com 585 hular ta sanyi fara kal a saman kanta, sai kuma taja ta rigar

Chapter 22 of 27