Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Daada kawai ya kamata su ga raunin juna, ita kadai ta rage masa kamar yanda a halin yanzun shi kadai ya rage mata. Kafin azahar an fara fitowa da wake da shinkafa faranti faranti kamar ana biki ba zaman mutuwa ba. Lokacin hira ta barke, ana kwasa ana labarai iriiri, yana gefe yana jin kamar ya tarwatsa taron kowa ya kama gabanshi. Kasa-kasa ya fara jin zancen Yelwa, basuyi tunanin yanda suke maganar zai karasa kunnen shi ba, sai dai Allah ya hore masa ji, irin yanda yake zaton ya zarta na mutane da yawa, kamar iska na kara taimaka masa wajen kwaso masa maganganu zuwa kunnen shi "Da gaske da ciki ta dawo?" Lubna sufyan Hausabook.com 420 Ya jefi Daada da tambayar, saita dan juya masa goyon dake bayanta. Don kukan da yarinyar take tayine ma yasa wata a cikin yar uwarsu ta bada madarar shanu a bulunbotin tace a bata tunda taki kama maman duk wata mai shayarwa a cikin, don ita bata da wadatar ruwan mama, sai dashi take hadawa yaron da take goyo da basuyi sati biyu da rufe arba'in ba. Sai gashi ta sha kuwa. "Daada..." Julde ya kira da wani yanayi a muryar shi "Daada a waje naji ana maganar Yelwa ta dawo da ciki" Wani abu ya hautsina a cikin Daada, zufa na karyo mata "Ki hada kayanki da safe mu tafi tare" Yanda take kallon shi yasa shi fadin "Baki da wani dalilin zama... Baki ga Yelwa ba idan ta sake tafiya fa?" Kallon nashi takeyi tana juya kalaman shi, ma'anarsu da girmansu a wajenta. Bata amsa Lubna sufyan Hausabook.com 421 duk abinda yake fada ba ta juya ta koma daki, lokacin ne kuma 'yan uwanta da suka rage a cikin gidan suka zagayeta da tambayoyin inda ta samo jaririya da kuma abinda sukaji mutane na fada "Da gaske Yelwa cikin shege tayo tazo ta haife shi anan ta sake shiga duniya? Wanne irin bala'i ne wannan Dije?" Kallon su takeyi "Shege a zuri'ar Baba? Kamar abin kunyar da Julde yayi bai ishemu magana a garin nan ba? Ya zakiyi da wannan Dije?" Maganganu sukeyi tana jinsu, tana kuma fahimtar su, su da suka hada uba kenan, a kalamansu take tsinkayo yanda duk da basu fada kai tsaye ba suke dana sanin jinin da suka hada da ita, saboda ita da 'ya'yanta sun zame musu abin kunya, har a tsakanin maganganun taji kamar suna bada shawarar a shake jaririyar da babu wanda ya bata zabi ta inda zata fito, saboda komai zai fi zuwa da sauki idan bata numfashi. Wannan kalaman ne yasa Dije kallon Lubna sufyan Hausabook.com 422 su, zuciyarta tayi wani irin shiru a kirjinta lokacin da tace "Ku fitar mun daga gida" Ta sake maimaitawa, tana karawa a tsakanin zagin da suke mata, ta kafe akan basu amsa daya har saida sukai zuciya suka dauki mayafansu. Kamar fitarsu take jira ta dauki jaka tana fara harhada duk wani abu da hannunta zai iya kaiwa sama. Ta kuma shiga dakin Datti, nan ne ta ga ledar da ta gani a hannun Yelwa, ta dauko ta ta fito, sai ga Julde ya shigo "Ka tayani mu hada kayanmu Julde, da gaskene babu abinda ya ragemun a garin Marake" Da sabuwar jaririya, da iya abinda zata iya hadawa wanda motar Julde zata dauka, bayan kuma yayi mata alkawarin zai dawo ya kwaso mata sauran kayayyakinta, zai biya yabar sako a gidan Baabuga ko da Bukar ya dawo, zai bar sako inda zai riski Yelwa ko da ta dawo itama. Sannan ta kulle gidan ta bishi. Bata san me ta gane a hanya daya nuna mata alamun sun fita daga Marake ba, iska dai taji tayi mata kadan har bata iya numfashi yanda ya kamata Lubna sufyan Hausabook.com 423 "Ka tsayar da motar nan Julde..." Ta fadi a wahalce, bai musa ba ya gangara gefen titin yana tsayawa. Saita bude murfin ta fita tana tsugunnawa cikin neman iskar data rasa, tana jin Julde ya dafa kafadunta yana kiran sunanta. Komai ne yake danneta yana hanata numfashi, dakyar taja wani tana fito dashi hadi da wani gunjin kuka. Ta zauna a kasa a gefen titi, a gefen dajin da batasan na wanne kauye bane tana kukan abubuwan da ta rasa, kuka irin wanda bata tabayi ba, kuka a jikin Julde da hawayenta suka bude masa nashi. Kuka sukeyi da dukkan zuciyoyin su Kuka ne na kadaici Kuka ne na firgicin rashin sanin mai gobe tayi musu tanadi idan har yau ta kasance musu a haka Zuciyarta cike take da abubuwan da ta binne a wannan ranar, abubuwan da suka hadu suka kawo su inda suke yau, tabar Marake rike da hannun Julde, rike da hannun tilon dan da take jin shi kadai ya rage mata a wancen lokacin, yau Lubna sufyan Hausabook.com 424 kuma kasar ce gabaki daya zata bari, rike da hannun Nawfal Amanarta Amanar da Bukar yabar mata. *** ALHAMDULILLAH! Finally... Yau munga karshen dogon waiwayen da Daada tayi Any guesses? Me zai faru? Da idanuwa Khalid yake bin Salim da yana shigowa falon wajen tv ya nufa ya rage sautin gabaki daya tukunna ya wuce kitchen ya zubo abinci ya fito "Tashi ka koma waccen kujerar" Ya fadi yana sake hade girarshi da take a sama tun da ya shigo. In dai sunyi kallo a bangaren su to baya nan ne, ko a laptop dinsu ne sai dai su Lubna sufyan Hausabook.com 425 saka earpiece. Nawfal baya zama bangaren Nanna, sai da wani kwakkwaran dalili zaka ganshi a ciki. Shisa Khalid dinma ya hakura, tafiyar Nawfal karatu, a ranaku irin yau idan yazo cin abinci sai yai zaman shi ya danyi kallo, idan film dinma yaja hankalin shi sai yaje yayi sallah ya dawo ya cigaba da kallon abin shi. Ya nemi dalilin da zai sa Salim yawan zama bangaren Nanna a satikan nan ya rasa. "Ba magana nake maka ba" Salim din ya karasa yana kai masa duka a kafada "Ouchhh... Hamma" Cewar Khalid yana murza wajen hadi da mikewa dan yaji zafi sosai. Salim baya ganin girman shi dana sauran mutane ba daya bane ba, baya ganin laifin Lukman da yake kauce ma duk wani abu da zai hada shi da Salim din tun rannan daya mare shi. Ranar ne shi kanshi Khalid din ya ajiye shan kamshin da yake yiwa Salim din a gefe, bai san sanda ya tsinto muryar shi yana gaishe dashi a ladabce ba, gaisuwar da Salim din bai amsa ba, kallon shi kawai yayi yana wucewa. Lubna sufyan Hausabook.com 426 Kafin ma ya fito yabar falon, Salim ba zai taba duba shekarun shi ba balle kuma dan gemun daya fara tarawa. "Ka dauko mun ruwa" Salim ya fadi, kanshi ciwo yakeyi, ga zuciyar shi bata masa dadi ya kuma rasa dalilin hakan. Tun a hanyar dawowa daga wajen aiki yakejin son ganin Madina, ta zama abu na farko da zaici karo dashi daya shiga gidan. Amman tun dawowarta gidan sai yaga kamar yafi sakata a idanuwan shi lokacin da take gidan Daada. Yanzun tsakanin Magriba da Isha'i da yayi mata magana me yasa bata fitowa falon sai tace masa "Azkar nakeyi Hamma...zuciyata bata da natsuwa saboda Daada, idan nayi addu'a ina samun sauki" Ba kalaman bane ba, yanayin yanda tayi maganar ne ya taba tashi zuciyar, saiya kasa ce mata komai, ya kasa fada mata abinda yake tashi zuciyar, a maimakon "Ni fa? Ni da bana ganin ki? Me yasa bana ganin ki kaman da yanzun kuma muna cikin gida Lubna sufyan Hausabook.com 427 daya? Lokacina da yake hade da naki fa? Bakya kewar mu?" Da tarin maganganu masu ma'ana da akasin haka da yake son yi mata, saiya gyada mata kai alamar ya fahimta. Saboda ita yake yawan zama bangaren Nanna yanzun, lokuttan daya kamata ace yana bacci sai yayi su a zaune yana jiran yaji fitowarta. Baya son yaje ya kwankwasa mata kofa ko tana bacci, ga waya tana kashewa "Wayarki a kashe Mug" Kai ta dan daga masa "Sai inta kallo ina jiran kiran Hamma Nawfal" Zuciyar shi ta sosu, sai da yayi dana sanin mata magana akan kashe wayar, zuciyar shi batayi masa dadine idan yaso jin muryarta bai samu hakan ba. Kalamanta sunsa zuciyar shi tayi wani irin zafi, kiran Nawfal take jira? Me yasa zata jira kiran Nawfal? Idan saboda Daada ne me yasa ba zatace masa tana jiran kiran Nawfal dan ya hadata da Daada bane ba? Me yasa ba zata hada da Daada a cikin maganar ba? Nawfal fa? Lubna sufyan Hausabook.com 428 Tunda Daada ta fara rashin lafiyar nan Madina take gwada shi akan Nawfal "Ga ruwan" Muryar Khalid ta kutsa cikin tunanin shi, kallon da yayi masa yasa shi ajiye robar yana komawa dan ya dauko kofi. Karar shigowar sakon waya yaji, haka kawai ya mika hannun shi bayan shi ya zaro wayar duk da yasan ba tashi bace ba, ya kuma saka hannu yana kasa da sakon ganin daga banki ne, idon shi ya kai zuwa kudin daya rage a gabaki daya asusun bankin. Wayar ya ajiye yana tsintar kanshi da kirga kwanakin wata a ranar, ko rabi watan baiyi ba. Abincin shi yake ci a nutse kamar taunawar na masa wahala "Account nawa kake amfani dashi?" Ya tambayi Khalid da ya kalle shi cikin rashin fahimta, bai maimaita tambayar ba, barin shi yayi ya sake juyata cikin kanshi har saida ya gane yana amsawa da "Guda daya..." Kamar Salim din ba zai sake magana ba, don saida ya karasa cinye abincin shi ya ajiye plate Lubna sufyan Hausabook.com 429 din, ya dauki robar ruwan ya kwance, ya kafa bakin shi yasa yana saka Khalid dan kankance idanuwa tunda baiga amfanin kofin da yasa shi komawa ya dauko ba tunda yasan ba amfani zaiyi dashi ba "Me ya samu motar ka?" Yana kula dashi baya daukar motar kwana biyu "Na kunna taki tashine fa" Khalid ya amsa a takaice, kai Salim ya jinjina, da kudin da yake asusun Khalid din ko shine ba zai kira bakanike ba tunda baisan nawa motar zata ballo masa ba. Yasan tunda suka fara tsayawa da kafafuwan su, Julde kuma ya zabi ya kyalesu don su koyi rayuwa dai-dai da samun su, yanayin kashe kudinsu da Khalid ya bambanta, tunda samun su ba daya bane ba. Har ranshi, lokutta da dama yakan so ya dauki kudi ya ba Khalid saboda bayason ganin yanda sai yayi tunani fiye da sau daya kafin ya siyi wasu abubuwan. Amman bayason ya sa Khalid din yaji kamar ya raina masa abinda yake samu ne. Lubna sufyan Hausabook.com 430 Idan wani ya kalle su sai yayi tunanin basu da matsalar kudi, tunda basu da nauyin iyali, amman motocin dake hannuwansu ma kadai iyali ce, sau nawa yaji abokan aikin shi na cewa idan mota ta ballo maka wani gyaran ko matarka ba zataci kudin a wata daya ba. Kamar kowa suna da kananun bukatu, suna da hidindimu, kuma duk da Julde na da wadata, su suna neman albarka, zakayi siyayya ka kawo gida, lokaci zuwa lokaci zaka shigo da cefane, shi ko takalman yaga sun masa kyau yakan siyowa Saratu. Iya farin cikin da take nunawa a fuskarta yakan rage masa duhun da yake ji a kirjin shi. Yana da kashe kudi ya sani, yakan alakanta hakan da wadatarsu da yake da ita. Amman yanda Khalid bashi da kashe kudi "Ba'a biyanku da kyau a wajen aikinku ne Khalid?" Ya karasa tambayar yana daga kai ya kalli fuskar Khalid din da yayi wani murmushi da Salim yaji baya so, saboda hade yake da wani Lubna sufyan Hausabook.com 431 yanayi na kamar duk bayanin da Khalid din zai masa ba zai fahimta ba "Ana biya" Ya amsa, bayason wannan takaitattun amsoshin da Khalid yake bashi "Nawa?" Ya sake tambaya yana tsare shi da idanuwa. "Dari da goma" Sosai yake kallon Khalid din kamar yana son ya gano amsoshin da suke masa yawo batare da ya fito da tambayoyin su a fili ba. Albashine me kyau, a hidimar shi kawai bai kamata ace sun kare haka ba. Me yakeyi da kudi? "Sako ya shigo wayarka, na duba. Magana mai yawa ba dabi'ata bace Khalid, shisa zan tambayeka kai tsaye...me kake da kudi?" Gyara zaman shi Khalid ya sakeyi, kallon Salim din yakeyi sosai shima "Na sake ganinka" Lubna sufyan Hausabook.com 432 Ya furta muryar shi na fitowa a dishe, da zuciyar Salim da abincin daya gama ci suna yo masa wani irin tsalle, ko da yana da abin da za fada shiru zai zaba, dan yanajin maganar shi dai-dai take da dawowar abincin da yake cikin shi "Na sani, nace ba sai kamun bayani ba, amman ina son sanin dalili, me yasa?" Ya karasa maganar yana kallon idanuwan Salim din daya sauke daga cikin nashi. Ba'a taba masa tambaya mai nauyin wannan da Khalid yayi masa ba. Ba kuma amsa bace bata da ita, ta inda zai fara furta amsar ne bai sani ba. Mutuncin Daddy zai zubar a idanuwan Khalid? In ba haka ba ta ina zai fara fada masa saboda Daddy ya fara neman mata? Abinda yake tattare da matan da yasa bai duba lahirar shi ba, bai duba Nanna ba, balle kuma ya duba su ya so yaji shima, yaji din, ya kuma rasa ta inda zai fara dainawa yanzun. Saboda tun kafin a ajiye masa wasu dalilai yake jin Khalid kadai ya isa ya zama dalilin da zai daina in har yasan ta inda zai fara. "Daddy?" Lubna sufyan Hausabook.com 433 Khalid ya fadi cikin wata irin murya, yana dorawa da "Saboda Daddy ko?" Yana ruguza wani abu a kirjin Salim da baisan yana wajen ba. Numfashi Khalid yaja yana fitarwa cike da kunar rai. Ya sani, ya dade da sanin abinda Julde yakeyi, saboda shi mutum ne mai kula da al'amuran mutanen da yake so. Har Lukman kuwa da ake tunanin rayuwar shi ta bambanta data kowa a gidan, Khalid zai iya fadar karfe nawa yake zuwa makaranta ya dawo, ranakun da yake zuwa islamiyya da wanda baya zuwa yanzun, wanne abinci ya fiso da wanda baya so, saboda yana kula. Fiye da yanda suke tunani, idanuwan shi nakan duk wani motsi nasu. Shisa ya dinga jin kamar ya dauke ido da yawa daga kan Salim shisa bai gane halin da yake ciki da wuri ba, amman Salim ne, yaushe ma ya bude bakin shi yayi magana da matan balle har ya bisu? A cikin halaye marassa kyau wannan ne karshen abinda za'a jingina Salim dashi saboda ya sha bamban da dabi'un shi. Sai dai kaddara Lubna sufyan Hausabook.com 434 bata zabe, babu kuma wanda yazo duniya da rubutun yanda halayen shi zasu kasance a goshin shi. Idan duniya ta tashi miko maka farantin dabi'u sai ta cakude maka mai kyau da marar kyau a waje daya, waresu hankalin ka da karfin yaki da zuciyarka ne kawai zaiyi maka hakan. Shirun Salim din ya tabbatar masa da komai, numfashi ya sake ja yana fitarwa "Akwai Angry Ustaz a manhajar twitter, yanayin wani aiki build a well, suna bin garuruwa su duka kauyukan dake karkashin garin inda suke wahalar ruwa sai mutane su tara kudi a gina rijiya a garin...da dan tsada idan mutum daya zai biya duka kudin, inayin biya uku ko hudu, saboda Daddy, saboda bansan ya zanyi ba, duk idan naga ya fita ya dawo ina kallon shi da nauyin da yake kafadun shi, yanzun gaka..." Har lokacin Salim bai dago kanshi ba, cikin wata irin murya yace "Rijiya kayi a madadina Khalid?" Lubna sufyan Hausabook.com 435 Dan daga kafadu Khalid yayi, kirjin shi yayi nauyi. Wanne zabi suka bar masa? Yana kaunar su, wannan rayuwar ta duniya yana da yakinin mutuwa ce kawai zata raba tsakanin su, yana musu kaunar da yake fatan kasancewa tare dasu a aljanna,hakan ba zai faru ba idan suna wasa da lahirarsu haka. "Ya zanyi Hamma?" Mikewa Salim yayi, baice komai ba ya fice daga dakin zuwa bangaren su. Ya rasa dalilin da yasa baya ganin hanya sosai har saida ya shiga dakin shi ya mayar da kofar ya kulle tukunna ya gane hawaye ne cike da idanuwan shi, kirjin shi yayi wani irin nauyi cikin yanayin da bai taba sanin akwai shi ba tunda yake a duniya. Iska yake ja yana fitarwa hadi da kokarin mayar da hawayen dake ta yi masa barazana "Pull yourself together Salim" Ya furta cikin wata irin murya, amman ya rasa ta inda zai fara tattara abinda Khalid ya wargaza masa, babu wasu kalamai da zasu fassara asalin abinda yake ji, bacin rai? Farin ciki? Karyewar zuciya? Rauni? Mamaki? Kowanne a cikin Lubna sufyan Hausabook.com 436 abubuwan ne da wasu da baisan sunayensu ba suka hade masa waje daya. Dakyar ya iya jan kafafuwan shi zuwa bandaki, ya watso ruwa ya fito, babu abinda ya bashi tsoro sai wata irin bukatar mace data taso masa saboda yanajin duminta ne kawai abinda zai kauda masa wannan hargitsin da Khalid ya jefa shi ciki. Rurin wayarshi yaji, yana mamakin lokacin daya cireta daga silent, karasawa yayi kan gadon ya dauka. Ganin Nawfal ne ya sakashi saurin dagawa ya kara a kunne "Bajjo..." Ya kira, sai dai Nawfal din bai amsa ba "Bajjo..." Ya sake kira, banda numfashin Nawfal din da yake juyowa ta cikin wayar da zai dauka ko kiran ya yanke ne "Meya faru? Kamun magana" Cewar Salim yana zama gefen gadon "Ina Hamma?" Lubna sufyan Hausabook.com 437 Nawfal ya bukata ta dayan bangaren yana dorawa da "Na kira shi bai daga ba" Dan dafe kai Salim yayi "Dole sai Khalid? Ba zaka iya magana dani ba?" Jin yayi shiru yasa Salim din sauke numfashi "Ina Daada? Ya jikinta? Yau za'ayi mata aikin ko?" A takaice Nawfal ya amsa da "Alhamdulillah. Eh..." Shiru ya sake gifta musu "Sai anjima Hamma..." Nawfal ya fadi, kafin Salim din yace wani abu ya kashe wayar ta dayan bangaren. Karamin tsaki Salim yaja, kamar su duka sun hada baki yau, babu abinda suke so sai su dagula masa lissafi. Kaya ya sake ya dauki turaruka ya feshe jikin shi, saiya tuna baiyi ko sallar la'asar ba, da fitar zaiyi inya dawo saiya hada duka yayi Lubna sufyan Hausabook.com 438 "Ya zanyi Hamma?" Maganar Khalid da yanayin muryar shi suka dawo masa suna hana masa fita, tsaki ya kara ja ya koma bandaki ya dauro alwala, sanda ya idar har anyi isha'i, don haka ya gabatar da ita. Ya sake mikewa ya fice daga dakin. Bayason haduwa da Khalid, da ya sani yayi musanyar aikin shi na yau dana dare, tunda da yawa bason aikin daren sukeyi ba. Yana son ganin Madina, da dukkan zuciyar shi yana so ya ganta. Wayar shi da yasa aljihu ya ciro ya kirata, yayi sa'a bugun farko ta daga "Hamma..." Muryarta ta daki kunnenshi, wata irin nutsuwa daya manta rabon daya sameta ta ratsa "Ki fito in ganki" Ya fada yana kasa gane muryarshi saboda yanda tayi kasa. Bata amsa ba, ta dai kashe wayar daga dayan bangaren. Sai yaga kamar ya kusa awa yana jira kafin ta fito, wandone na jeans a jikinta, sai ta saka wani takalmi mai gashi da ita kadai yake gani dashi, rigarta fara, ita dashi Lubna sufyan Hausabook.com 439 zasu shiga ciki saboda girmanta, ta saka farar hula akanta, sai hannunta da take kaiwa tana gyara zaman gilashinta kamar tana tsoron idan batayin hakan lokaci lokaci zai iya fadowa. Tayi masa kyau, Madina tana yi masa kyau ko me zata saka. Murmushi take masa da yake haska wajaje da dama a cikin kirjin shi. Sai da ta karaso gab dashi yaga fuskarta ta kumbura, idanuwanta sun sake kankancewa ta cikin gilashinta. "Kuka kikayi ko?" Murmushin ta sake fadadawa "Tun dazun ne fa... Kuma na wanke fuskata" Murmushi ya tsinci kanshi dayi, in dai tana kusa, fara'a bata masa wahala, zata fadi wani abu da ko bai tanka ba zai saka shi murmushi. Yanayin da yake ciki da yanda take tsaye a gabanshi, sai ya daga hannu, nufin shi ya taba kuncinta, koya ne yaji duminta a jikin hannun shi. Saiya kare da sake tura mata gilashinta yanda takanyi "Ba kayi bacci ba ko Hamma?" Lubna sufyan Hausabook.com 440 Dan daga mata gira yayi yana sa tayi dariyarta da yake so "Ya nuna a fuskarka... Girarka ta karayin sama fiye da kullum" Kai ya girgiza da murmushi a fuskarshi "Mu fita yawo" Dan yatsina fuska tayi "Mu zauna muyi hira, kaje ka kwanta... Kana da aiki gobe da safe... Kayi bacci" Yanda yake hade fuska yasa Madina dorawa da "Dan Allah Hamma kayi bacci..." Sosai yake hade mata fuska "Bana ganinki yanzun" Ya furta da wani yanayi a muryarshi "Kayi bacci, zaka ganni gobe In shaa Allah... Ina nan daka dawo aiki, sai muje yawon" Kallonta yake tana ganin musun da yake son yi shimfide cikin idanuwan shi Lubna sufyan Hausabook.com 441 "Ba gobe kawai ba, kullum idan ka dawo zaka ganni" Hannun shi ya mika mata, batayi musu ba ta saka nata a ciki, tana ganin kankantar nata hannun. Numfashi ya sauke mai nauyin gaske, ganinta, magana da ita, da hannunta daya rike ya samar mishi nutsuwar da yake bukata, kallon ta yake Kallon da ba zai iya hango abinda gobe ta tanadar musu ba a cikin so Tun tasowarta, koya ta juya zata ga Daada a kusa da ita. A wautar tunani irin nata ko a mafarki bata taba hasaso nisa da Daada irin haka ba. Ace ba unguwa bace a tsakaninsu, ba gari bane ba, kasa ce kacokan a tsakaninsu. Awanni ne masu yawan gaske idan akace lissafasu za'ayi. Komai ba tajin dadin shi. Duniyarta tayi tsaye waje daya, tana zaune kawai sai taji hawaye na cika mata idanuwa. Duk da taji muryar Daada yafi a kirga yanzun, ta ganta a video calls din da Nawfal ya kirata yana hadasu. Ta tabbatar mata da cewar tana samun Lubna sufyan Hausabook.com 442 sauki, har anma kusan saka lokacin dawowar su. Ta wani bangaren hankalinta ya kwanta, amman kewar Daada fa? Abinda duk take so a gidan shi takeyi, banda Salim kowa na bata wajen da suke tunanin tana bukata, tunda Saratu tayi duk wani kokari na ganin ta saki jikinta da ita amman ta kasa. Tasan babu jituwar kirki tsakanin Saratu da Daada, a iya tunaninta da fahimtarta kuma akan Nawfal ne hakan ya faru. Duk yanda Saratu take faran faran da ita sai ta tsinci kanta da kasa sakewa da matar. Tana shiga kitchen ta tayata aiki sosai, haka su sharar gidan da mopping ma, wasu ranakun ita take dafa musu abincin gidan gabaki daya. Tunda Saratu ta kula ta iya girkin sosai, idan tace tabar mata bata musawa. Yau ma daya daga cikin irin ranakun ne, sai ta zabi ta dafa wake da shinkafa tunda miyar kifi ce tayi. Sabonta ne zama kitchen idan tana girki duk fadan da Daada zatayi, musamman yanzun da Khalid ya nuna mata wani waje da zata iya sauke litattafai a cikin wayarta, da kuma manhajar da ta dauko don bude litattafan, ta dai fi son taji littafi a hannunta, wannan yanayi ne Lubna sufyan Hausabook.com 443 da ba zai misaltu ba, ko kamshin takarda daban yake a wajenta. Nutsuwar da kamshin yake samar mata abune da ba zata iya amfani da kalamai wajen fassara shi ba. Sai dai ya saukaka mata ba saita dauki littafi zuwa ko ina ba, yanzun a kitchen da ta shiga a wayarta sai ta cigaba da karatunta tana zaune a kujerar robar da take cikin kitchen din. Hankalinta gabaki daya yana kan littafin da take karantawa mai suna Obsidian na Jennifer L. Armentrout. Tun daga shafin farko jiya littafin ya riketa, so takeyi kawai taji ya za'a kare. Shisa bataji shigowar Salim ba saida yasa hannun shi yana rufe mata screen din wayar da ta tattara nutsuwa a kai "Hamma..." Ta kira cikin kasalalliyar muryar da yaji kaman ya fito wanka an kunna masa fanka, yanda ta sauke idanuwanta a fuskar shi tana sauke numfashi a hankali yasa har gwiwoyin shi yaji sunyi masa sanyi. Mata da yawa, mata kala-kala da ya gani, ya taba, suka bishi. Babu wadda take da tasirin nan da Madina take dashi a rayuwar Lubna sufyan Hausabook.com 444 shi, yarinyar da ko shekara ashirin bata hadaba a duniya ce take sanyaya masa jiki har haka. Dan yatsa yasa yana tura mata gilashinta yana sa tayin dariyar nan tata da sautinta yake sa kaji kana son kasancewa cikin irin nishadin da take ciki. "Yunwa nake ji, me kike dafawa?" Ya furta yana jingina da kantar kitchen din ya harde hannayen shi a kirjin shi. Sai taga duk ya cika kitchen din "Wake da shinkafa da miyar kifi. Nanna tace za'ayi salad, amman wake da shinkafar bai dahu ba tukunna, yanzun ma na zuba shinkafar" Dan hade girar shi ya sakeyi yana sakata yin dariya "Ina miyar kifin?" Sai da ta kalli tukunyar, sannan ta kalle shi, ta bude baki, kafin tayi magana ya raba jikinshi da inda yake tsaye ya karasa ya bude, cokali ya dauka ya tsamo kifi guda daya "Hamma me kakeyi?" Lubna sufyan Hausabook.com 445 Inda zai saka kifin yake nema, wani kwano ya gani ya dauka ya saka kifin a ciki yana kara tsamo guda biyu "Inalillahi... Hamma kifin zaka tsame mana? Ka tsaya a kirga aga kowa nawa zai samu" Makale mata kafada yayi yana kara yanka daya sannan ya rufe tukunyar "Guda nawa ka dauka?" Madina ta fadi tana mikewa tsaye itama, sama yayi da kwanon hannun shi "Ni ki kyaleni yunwa nakeji" Dariya takeyi har lokacin "Ka kawo to inga guda nawa ka dauka" Yana sake sama da hannun shi Saratu ta shigo kitchen din "Me kake mun a kitchen Salim?" Tayi masa tambayar cikin harshen fulatanci "Yunwa nake ji" Lubna sufyan Hausabook.com 446 Ya amsa Madina na karbewa da "Shine ya kwashe mana kifi Nanna" Kallon shi Saratu tayi, sai ya sauko da kwanon yana nuna mata tare da turo labbanshi "Ba da yawa na diba ba Nanna... Yunwa nakeji" Lukman ne karami a cikin yaranta, amman babu mai nuna har yanzun shi yarone a wajenta kamar Salim din, duk da maganarshi bata cika tsawaita ba, dan ya shagwabe mata ko a gaban waye baya masa wahala. Yanda zai kalleta ya shagwabe fuska, ya juya ya canza fuska wa kannen shi yana basu umarni har mamaki da dariya yake bata. Sai dai ta kula da abu daya, dariyarshi ta karu tun dawowar Madina gidan, kamar akwai wata shakuwa a tsakaninsu da yanzun ne take sanin akwaita. Sannan ko baiyi magana ba idan yaga Madinar yanayin fuskar shi saiya canza, girarshi da bayason saukewa ko yaushe da kanta take sauka kafin karamin murmushi ya bayyana kan fuskarshi da tazo waje. Lubna sufyan Hausabook.com 447 Surutun kowa har da na Saratun kuwa yana nuna ya dame shi, amman banda na Madina, da kanshi zai fara janta da kananun hira. Kacokan ya dawo da zama a falonta duk saboda Madina din, shisa ita ta rage zaman falon dan suyi hirar su cikin kwanciyar hankali tunda ta kula Madinar bata sakewa yanda take so idan tana waje. Da tasan matsayin Yelwa a wajenta da ta sake da ita, da tasan yanda itace wadda taso a kusa da ita ba Nawfal na da ta bata dama fiye da wadda ta bata a filin rayuwarta. Ayar tambayar da yake zagaye da asalinta bai damu Saratu ba. Saboda tana jin abinda zata iya yiwa Yelwa shine kulawa da Madinar, fatanta shine hasashenta tsakanin Madina da Salim ya zama gaskiya. Saboda sirrinsu zaifi lullubuwa idan hakan ta faru, daga ita har Julde babu wanda zai bukaci wani tone-tone, sune dangin Madina, sune kuma iyayen Salim. Sai dai wani fatan zai iya kasancewa a hasashe kawai zai tsaya Kamar yanda wasu sirrikan da kansu suke bayyana kansu ba sai sun jira an tono su ba Lubna sufyan Hausabook.com 448 "Baka karya ba?" Wannan karin Madina ce ta amsa mata da "Yau laraba, aikin kwana yake da duka satin nan" Kai Saratu ta jinjina "Ka nemi wani abin kaci kafin a gama abinci" Kwanon ya ajiye yana karasawa wajen fanfo ya wanke hannun shi kamar ba dashi suke magana ba. Murmushi Saratu

Chapter 17 of 27