Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
da rokon alfarma ya gifta a tsakaninta dashi zai kafa tarihi, saboda zai juyo mata da bukatarta ne ba zai karba ba, ta runtsa idanuwanta ganin ya bude baki yana shirin amsawa, kamar tana so tace masa yayi shiru, tana so ta roke shi ya bata wasu yan mintina ta shiryama amsar shi, ta shiryawa kin amincewar shi, ta kuma tabbatar duk fatanta kaddara ta rigata, yanda duk ta hango shi karkashin inuwa daya da Madina, hakan ba abu bane da zai taba yiwuwa ko a halin nan da suka tsinci kansu "Idan wannan ya zama dalilin da zan auri Madina, kamar ba ayi mata adalci ba..." Maganar ta fito daga bakin shi tana dukanta, numfashi taja ta baki tana kokarin fitar dashi ta hancinta taji an kira sunanta can nesa "Daada..." Yanayin yanda aka kirata din kamar da rashin tabbaci "Daada" Wannan karin Madina ta kira tana kai hannu ta kama hannun Daadar don ta tabbatar ba Lubna sufyan Hausabook.com 477 mafarki takeyi ba, zuciyarta nayo tsalle ta dawo makoshinta saboda murna, a hankali Daada ta bude nata idanuwan, tana fara karewa dakin kallo, saita mayar da hankalinta kan Madina da take kokarin tashi zaune. Tsakanin gidan Julde, daga inda take tsaye tana kallon komai kamar bata da wata alaka da abinda yake faruwa saboda jikinta da yaki bata hadin kai wajen yin wani yunkuri, ko da na motsawa ne taga abinda yake faruwa, ta kafe a wajen kamar anan tushenta yake. Kafafuwanta da takejin kamar sunyi sanyi na sanar da ita dadewar da tayi a tsaye. Sai dai tashin hankalin da take ciki ya girmi gajiya, ya girmi duk wani abu da kalmomi zasu iya misaltawa, shisa ta cigaba da binsu da idanuwa, tana nan likitan da Khalid ya fita ya kira ya dawo, ta gabanta suka kamo Julde suna wucewa dashi bangaren shi, bata motsa ba, duk kuwa da alamun da suke nuna kamar Julden baya numfashi. Sai dai akan yara wanne abune ya rage da bata gani ba? Kaddarar ma da bata taba hasashen faruwarta ba yau alamu suna Lubna sufyan Hausabook.com 478 nuna ta faru, idan mutuwa Julde yayi ba zatayi mamaki ba. Bayan yaran da ta haifa suna komawa, har bayan ta samu Bukar, baisa ta daina kallon Julde kamar zata iya rasa shi ba shima, Bukar da Yelwar ma da ta kwallafa rai akansu suna ina yanzun? Ji take ya kamata ace ma indai akan 'ya'ya ne ta jima da sallamawa, ta jima da mika wuya saboda ita sune kaddararta. Sai dai ya kaddarar zata juya mata haka? Ya zata zagayo ta soma yiwa jikokinta dauki dai-dai? Anya tana da zuciyar daukar wannan kuwa? Tana jin abinda yayi mata saura a cikin kirjinta yayi rauni, bashi da karfin daukar koma menene yake faruwa "Daada" Khalid ya fadi yana tabata, yanayin fuskar shi kuma data kalla na tabbatar mata ya dade yana kokarin rabota da inda tunani ya dauketa ya watsa "Daddy nata kiranki" Lubna sufyan Hausabook.com 479 Kallon shi tayi tana nuna masa alamar labbanshi kadai taga sun motsa, amman abinda ya fada bai karasa kunnuwanta ba "Daddy ya farka yana kiranki" Ya fada da fulatanci wannan karin, ganin dai kallon shi takeyi yasa shi kama hannunta yana juyawa, batayi musu ba, tayi mamakin yanda ta iya motsawa tana bin bayan Khalid din har dakin da Julde yake ta kokarin tashi zaune likitan da kuma Saratu nata hanashi "Naji muryar Daada, naji sallamarta, ku barni inje in sameta" Yanayin yanda yake maganar zai tabbatar maka da ba'a cikin hayyacin shi yake ba. Yana kuwa ganin Daada ta shigo dakin ya sake zabura yana kiran sunanta, waje ta samu tayi tsaye tana kallon shi "Daada banyi mata komai ba, bansan meya sameni ba, wallahi bansani ba, bansan meya sameni ba" Ya karasa maganar muryarshi na sauka kasa tare da kanshi daya saddar kamar wanda ya Lubna sufyan Hausabook.com 480 fada cikin zurfin tunani, dagowa yayi lokaci daya kuma yana kallon Daadar "Me yake damuna?" Yayi tambayar da nauyi cikin muryarshi, wani irin nauyi da Daada taji ya taba zuciyarta. Kallonshi takeyi ko zataji tsanarshi a ranta, amman babu komai banda tsanar halayen shi, shidin yana nan daram a zuciyarta, asalima duka laifukan shi take so ta dauka ta dora akan Datti, tayi amfani da kaunar da ya nuna musu, ta kuma fake a bayan bakin daya dinga bin Julde dashi, tayiwa danta uzuri, ta rage laifinshi a idanuwan duniya, ta roka masa gafara a wajen Allah kamar yanda takeyi a duk rana, dan nata bangaren babu wani abu da zaiyi ta kasa yafe masa, koya ranta ya baci dashi kuwa, ko da a cikin wannan laifukan akwai layin nan da yake tabbatar mata bai tsallaka ba yanzun. Da gaske babban kuskuren da al'umma sukeyi shine dora laifukan yara akan mahaifiyarsu, saboda a duniya duka babu wata uwa data ke so ace yau danta ba nagartacce bane, ko da kuwa ita akwai ayar tambaya a tata nagartar. Kowacce Lubna sufyan Hausabook.com 481 uwa fatanta ace idan an jera yaranta cikin sauran yara ya kasance shine yafi kowa, kyau, kyan hali da komai da komai. Dan tayi kokarin boye laifinshi baya nufin tana goyon bayan wannan hanyar lalacewar daya dauka, tana kokarin boyewar ne don zuciyarta ta rage mata nauyin da takeyi, tana kuma yi masa uzuri kome ya akaita saboda shine zabin karshe da take dashi, tana ganin yanda kowa yake aibata shi, kowa yake kyararshi, ya ake tsammanin itama tabi sahu bayan batasan komai ba daya wuce kare shi daga duk wani abinki? Ko bayan kwanaki a cikin satika, satika a cikin watanni, laulayi, kwanciya dakyar, tashi dakyar, rayuwa a cikin wata rayuwar da mai ciki ce kawai zata fahimta, awanni a dakin nakuda, duk wannan wahalar ana dora mata shi a hannunta abu na farko da yake zuwa ranta shine tabbatar da yana cikin koshin lafiya koda ita batajin wannan lafiyar a tare da ita, daga ranar komai na rayuwarta zai biyo bayan nashine, duk wata bukata da take da ita a kasan tashi take. Kuma sai ace tana so ta ga ya lalace? Ko da ta sake shi, ko da ta sangarta shi, ko da akwai nakasu a Lubna sufyan Hausabook.com 482 yanayin tarbiyar da ta bashi, a cikin zuciyarta tafi kowa son ganin ya kasance nagartacce. Wannan kaunar ta tsananin mahaifiya da yaranta babu wanda zai fahimta sai wata mahaifiyar. Ko yanzun da take tsaye so take ta karasa ta rike shi, gani takeyi kamar yayi zuru-zuru, duk ya rame, amman wani abu ya rike mata kafafuwa, kallon shi takeyi kamar yanda shima yake kallonta, hakan ya ba likita damar yin allurar baccin da Julde yaki tsayawa ayi a cikin karin ruwan da akeyi masa, cikin wasu dakika ta fara aiki, jikinshi ya fara yi masa nauyi, dole ya kwanta, kafin wani lokaci bacci ya dauke shi "Yana bukatar bacci don jininshi da ya hau ya sauka" Likitan ya fadi yana yi musu bayanin dalilinshi nayin allurar baccin. Hannu Saratu da take zaune a gefen gadon ta kai tana dauke kwallar da take cikin idanuwanta. Juyawa Daada tayi, Khalid ya rufa mata baya, ganin tanayin hanyar waje ya sashi fadin "Bari in dauko Madina sai inzo in kaiku gida" Lubna sufyan Hausabook.com 483 Hakan kuwa akayi, idonta kur akan Khalid daya sabo Madina zuwa mota ya kwantar da ita a baya, itama bayan ta shiga tana daga kan Madina ta kwantar a jikinta, kamar bacci takeyi, tayi wani irin luf da ita, jikinta nade da zanin gado, kanta ne kawai a waje. Ko da tana yarinya bata da yawan rashin lafiya, hakora ma kanta ne kawai yake zafi, sai wasu ranakun idan ka taba jikinta zakaji akwai alamun zazzabi, amman wannan wahalar duka Madina batayi ba "Baki taso da uwa a kusa dake ba Madina, sai Allah ya dubaki komai yake zo miki cikin sauki" Daada ta tuna kalamanta bayan Madinar tayi wata kyanda da bata hada sati daya ba, ba kuma ta wani kwantar da ita yanda take yiwa sauran yara ba. Da ta fara girma, idan zatace kanta na ciwo ko cikinta, zai wahala ta tashi da safe ta sake maimaita wannan maganar, idan ta tambayeta ma zatace "Tun jiya ne Daada, da na sha magani nayi bacci yau ban tashi dashi ba" Shisa ganin yanda Khalid din ya sabota yakeyi mata wani iri, haka da suka karasa gidama. Lubna sufyan Hausabook.com 484 Mukullan gidan kowa yana dashi ita da Madina, nata kuma yana tare da ita, don dakyar ta bawa Nawfal riko lokacin tafiyarsu, suna kuma sauka Abuja ta tambaye shi "Daada kamar wanda zai gudu da mukullin nan? A asibiti ma fa wajen sau hudu kika tambaya" Dariya tayi "Mukulli na da tsautsayi, kai ka batar mana da guda daya, daga baka ko da zaka zo bama nan" Kai Nawfal ya dafe "Akan batan mukullin daya faru wajen shekara goma har yanzun banyi hankalin da za'a yarda zan iya ajiye wani ba, ai shikenan..." Ya karasa yana zuwa ya dauko mukullin ya danka mata, ta saka a yar jakar da take makale da ita. Wani irin takeji ganin yanda duk inda akayi da Madina take bi saboda alamu sun nuna batasan inda kanta yake ba, kan kujera ya shimfidar mata da ita yana fadin Lubna sufyan Hausabook.com 485 "Likita ya dubata itama, yace babu abinda yake damunta, bacci takeyi zata tashi zuwa wani lokaci" Kallon Khalid din tayi, sai taga kamar yana kokawa da wani abune, yana kokarin danne abinda yakeji don yaga kamar su duka suna bukatar wanda zai tallafe su a wannan yanayin da suka tsinci kawunansu "Bakomai kaje kayi hidimarka Khalid...Allah yayi maka albarka" Kai ya jinjina "Idan kuna bukatar wani abu sai ki kirani Daada, zan dawo ma zuwa anjima In shaa Allah" Wannan karin ita ta jinjina masa kai, saida ya fita take karewa falon kallo, ya kamata ace akwai kura tunda an kwana biyu bakowa, abinda bata sani ba shine duk kwana biyu sai Madina tace Salim ya kawota, ranar farkon ta dade, data dawo yake ce mata "Tun dazun, kin barni ni kadai tun dazun" Lubna sufyan Hausabook.com 486 Da ta sake dawowa kuwa tare suka shiga, daya fara shara kaman abin kirki ya ajiye mata tsintsiyar "Ni bana son shara Allah" Ya fada, dan dakin shima yana kokarin ganin kome yaci bai zube yanda zaiyi shara ba, idan abune ya shiga dashi, yana gamawa yake tattara ledojin ya fito dasu. Daya yi barin shinkafa kwanaki zama yayi ya mike kafa ya fara tsincewa, haka Khalid ya shiga ya same shi "Bari kayi?" Bai magana ba, irin wannan tambaye-tambayen ne na Khalid baya so, abu yana gabanshi, ya gani amman saiya sake maka tambaya akai "Shinkafar zaka bi ka tsince da dai-dai Hamma? Maimakon ka share?" Numfashi yaja yana fitarwa "Bana son shara, ka kyaleni Khalid, me ma kake nema ka shigo mun daki kayi tsaye kana damuna da magana?" Lubna sufyan Hausabook.com 487 Dariya Khalid din yayi, karshe shine ya share masa, sai yayi sati bai share daki ba, kome ya zuba zai tsince. Shisa Madina take bashi mamaki, ta tattara duka natsuwarta sai shara takeyi, waje ya samu ya dinga kallonta harta gama. Haka duk zuwan da zasuyi, tayi shararta, tayi goge-goge yana zaune, idan yaji kamar bashi da wani amfani ne ma zaice mata "Kawo in fasa miki omon" Ya kuwa bata dariya ranar, ko kuma yace "In kara dibo miki ruwa?" Idan ta gaji ne zatace "Hamma kayi zamanka, ai kayi babban aiki tunda ka kawoni, kuma zaka mayar dani, gashi kanata tayani da idanuwanka ma" Daman dan kar taga kamar bai tayata bane shisa yake magana. Ai kuwa gidan ko ina tas, dan da ta shiga tayi sallar azahar kamar bataje ko ina ba, sai dai sau daya Madina ta motsa. Khalid ya dawo kamar yanda yace, da ledojin da inda ya ajiyesu nan suke har zuwa yanzun. Anan falon tayi la'asar da alwalarta ta azahar da take rike Lubna sufyan Hausabook.com 488 da ita. Da Madina bata motsa ba zata kira wani ne yazo ya taimaka mata su kaita asibiti, ko a kira likita ya sake dubata. Tunani babu irin wanda Daada batayi ba, tasha babu wadda bata kama ba, sai dai inta kama din subuce mata takeyi. Wannan ciwon da tayi ta dauka karshen rayuwarta ne yazo, duk da Bukar da Yelwa suka cika tunaninta a lokacin, Madina saita danne su, saboda a wajen Madina itace komai, itace matsayin mahaifi da mahaifiya, bata taba tunanin zata roki Allah ya kara ara mata wasu shekaru a duniyar da ba dadin zamanta takeji ba sai saboda Madina, saboda tana son ganin wanda zai mayewa Madina gurbinta kafin tabarta. Tasha hango Nawfal ne zaiyi wannan aikin, sai yazo da maganar aure, sai kuma ta ganshi da Murjanatu a India, taga yanda yake kallonta kamar bashida sauran wajen da Madina zata zauna a rayuwar shi. Sai kuma ta ga yanda Murjanatun take kallon shi itama, yanda ko abinci ne saita fara ci kamar tana son dandana zafin shi a harshenta kafin ta mika masa, duk da haka idan akwai wani abu a Lubna sufyan Hausabook.com 489 kusa da ita da zaiyi fifita zaka ga ta dauka tana sake fifita masa abincin sanin bayason shi da zafi, tunda tazo ita take fita tayi abubuwa da yawa shi yana tare da ita. Idan kifine zaici, zata wanko hannunta ta zauna ta zare duk wata kaya da idanuwanta zasu iya gani kafin ta mika masa. Soyayya ba bakuwar Daada bace ba, bayan Hammadi da Abu, itama ta taba kalar tata soyayyar, yaranta kuma sun sake nuna mata indai soyayya ce suna cikin wanda Allah ya zaba ya kadartawa ita a filin duniya. Tun a asibitin saita cire rai, saboda Nawfal ya rigada ya gama samun abokiyar rayuwa, amman yau, tana so ta roke shi, tana so tayi masa magiya ya dan matsar da Murjanatu ya samarwa Madina wajen zama, saboda yanda bata taso kusa da iyaye ba, haka shima, sunfi kowa cancanta da su kula da junansu. Wannan zaren take ta sakawa tana warwarewa batasan bacci ya dauketa ba, a cikin baccin harda mafarkin ta roki Nawfal din kuma yaki amincewa, in ba mafarkin ba, ita da take hasaso su karashe rayuwarsu da juna, me yasa zata roke shi shekaru biyu? Lubna sufyan Hausabook.com 490 "Daada" Madina ta sake kira, tana murza idanuwanta wannan karin, gilashinta da yake gefe da Khalid ya bawa Daadar ta dauka tana mika mata, sakawa tayi ta kalli Daada, idanuwanta cike da tarin tambayoyi wannan karin, tana kuma saka bugun zuciyar Daada karuwa saboda bata san me zatace mata ba "Jikina yayi mun nauyi kamar nayi kwanaki ina bacci..." Ta karasa maganar tana zaro jikinta daga bargon da take ciki, sai dai jikin nata ta kalla, ta rage kayanta kafin ta kwanta, tana da wannan yakinin, amman ba zata taba fitowa haka ba, kanta yayi nauyi na gaske, girgiza shi tayi a hankali tana dafa kujerar ta mike, duk wasu tambayoyi zasu iya jira ta watso ruwa ko zata dawo dai-dai. Harta taka saita dawo ta rankwafa tana riko Daada jikinta "Daada nayi kewarki sosai, kamar in biyoku wallahi" Lubna sufyan Hausabook.com 491 Yanda ta sauke wallahin muryarta na karyewa da alamun kuka zatayi yasa Daada saurin fadin "To ba gani na dawo ba, kije ki watso ruwan ki fito, kinga abinci Khalid ya kawo mana tun dazun nake jira ki tashi muci" Raba jikinta tayi dana Daada dakyar, tana kai hannu ta kasan gilashinta ta goge kwallar da taji ta tarar mata "Yanzun zan fito" Cewar Madina tana nufar dakinta cikin hanzari, Daada ta bita da kallo, wani abu na hadewa a cikin kirjinta Kamar lokaci yayi Lokacin da zata amsa tambayoyin da Madina bata taba bude baki ta furta mata su ba... Ba zaice ga asalin abinda ya faru da Baban shi ba, tun idan ya rufe idanuwanshi yana hada kadan daga cikin alamomin fuskar Bukar har ta bace masa, muryarshi da yake tunawa ma gani Lubna sufyan Hausabook.com 492 yake kamar hasashen zuciyarshi ne. Sauran abubuwan a bakin Saratu yaji "Babanka ma tsallakewa yayi ya barka, me yasa ni za'a tilasta mun zama da kai?" Ranaku babu adadi, ya sha numfasawa da nufin tambayar Daada, saiya kasa, saboda yanda take kallon shi, saboda abinda yake gani a cikin idanuwanta, shine yake tsayar dashi kowanne lokaci, saboda tasha furta "Bukar..." A kasan numfashinta idan yayi sallama, ko kuma taga giccin shi, sai yaga ta runtsa idanuwanta ta sake budewa ta girgiza kanta a hankali, yanayin saiya taba zuciyar shi. Taya zai tambayeta, me zaice mata? "Daada me ya faru? Ina Babana? Me yasa ya tafi bai sake waiwayen mu ba?" Bayan yana ganin yanda take da tambayoyi iri daya da nashi, yana kuma ganin yanda rashin dawowar Bukar din yake nukurkusarta fiye dashi. Duka sanin shekara nawa yayi masa? Daada tasan shi tun yana cikin jikinta, ta so shi Lubna sufyan Hausabook.com 493 tun kafin ta dora idanuwanta akan shi. Da wacce zuciyar zai tambayi uwa labarin batan danta? Ya taba tambayar Julde sau daya "Kome zan fada maka zanyi karya Bajjo, Bukar ya tafi neman karatu Maiduguri, da farko baya hada shekara yake zuwa ganin gida, daga baya saiya dade baizo ba, sai mu dade bamu saka shi a idanuwanmu ba. Bansan dawowar shi ta karshe ba, saboda ina nan Kano, na koma na samu ya dawo ya barka..." Shirun da yayi bayan amsar Julde yasa Julden kiran sunan shi a hankali "Ba kai kadai yabari ba, mu duka ya bari" Shisa ya kasa tambayar Daada, da gaskene su duka ya bari, ko a kalaman Julde yana jin ciwon da yake zuciyarshi na tafiyar Bukar din da rashin sanin abinda ya faru dashi. Sai dai a lokacin ya dauka tafiyar Bukar ta karya wani abu a zuciyarshi, tana kuma karyawa duk ranar da zai wayi gari tunanin ya fado masa. Yanda Julde ya rike shi, yana da yakinin ko a hannun Bukar ya tashi, soyayya ta mahaifi iya wadda zai samu kenan. Duk da tunasarwar da Saratu take Lubna sufyan Hausabook.com 494 yawan yi masa, na cewa Julde ba mahaifinshi bane ba, ya kuma sani, tunda ko a makaranta ba da sunan yake amfani ba, Nawfal Bukar yake sakawa. A zuciyar shi, Julde kawunshi ne daya dauki matsayin mahaifin daya tsallake shi. Baisan matsayin da yake dashi ya wuce duk wani tunanin shi ba sai jiya, saida yaga abinda a labaran duk da suka taba isa kunnuwanshi bai taba cin karo da kwatankwacin su ba. Ba kamar Khalid da Salim ba, halayen Julde masu kyan kadai ya sani, shisa da yaga wannan bangaren ya girgiza, abinda kuma ya karye a zuciyar shi ba irin wanda ya karye da tafiyar Bukar bane ba, da kuma rashin dawowar shi, ko tunanin Bukar ya mutu bai jefashi kunci irin wanda yake ciki ba. Ko ganin kirki bayayi sanda ya karasa cikin dakinsu. A kasa ya zauna, sai yaji kamar bashi da karfin zaman shisa ya kwanta, da takalma da komai a kafarshi, yaja jikinshi ya dunkule waje daya. Zuciyarshi ciwo takeyi da yake amsawa a ko ina na jikinshi, da zai iya daya cirota ya ajiyeta a gefe ya dan sarara. Baisan kuka yakeyi ba saida yaja numfashi yaji wata shesheka ta kwace masa Lubna sufyan Hausabook.com 495 kamar karamin yaro, kuka yakeyi da yaji dadi babu kowa a kusa dashi balle ace za'a bashi hakuri ko a lallashe shi. Kuka yakeyi da yake neman zuciyarshi ta samu saukin ciwon da takeyi ko kadanne. Anan kasan wani wahalallen bacci ya dauke shi. Sanda ya tashi yanayin duhun dakin ya sanar dashi Magriba tayi ko kuma tana gab, tunda yake bai taba baccin rana irin wannan ba. Mikewa yayi dakyar, ko ina na jikinshi ciwo yake masa kamar mota ta taka shi. Karasawa yayi wajen makunni ya kunna kwan dakin, mamaki ya fara cika masa zuciya ganin Khalid kwance akan gadon. Alamu sun nuna ya dawo, ya ganshi kwance a kasa, ya zagaye shi ya hau gado ya kwanta. Bai kuma tashe shi yayi sallah ba, yanda yaga Khalid din kwance luf sai yaji zuciyarshi ta doka, wani tunani da yasa kafafuwan shi motsawa na gifta masa "Hamma..." Ya kira da sauri yana bubbuga shi, a hankali ya motsa yana juyo da jikinshi "Yamma tayi sosai, kayi sallah? Ni ko azahar banyi ba" Lubna sufyan Hausabook.com 496 Kai Khalid ya daga masa, yayi azahar da la'asar duka, baima dade da shigowa dakin ya kwanta ba "To ka tashi ko ba'a kira Magrib ba yanzun za'a kira" Ya karasa fadi yana wucewa bandakin, fuskarshi ya fara wankewa sannan ya dauro alwala ya fito, azahar da la'asar ya gabatar, yana idarwa yaji ana kiran Magriba, saiya mike, a hanyarshi ta zuwa masallacin yake neman gafarar Ubangiji ta sallolin da baiyi akan lokaci ba, saboda hade sallah ba sabonshi bane ba, wani iri yakeji. Da aka idar saida ya duba Khalid bai ganshi ba, nan ya zauna cikin masallacin saboda zuciyarshi ta dan samu sarari, sanyin masallacin ya sanyaya masa wajajen da suke masa zafi, yasan yana fita daga ciki komai zai sake danne shi. Sai yai zamanshi har akayi isha'i sannan, shima dakyar ya tafi, don ji yake kamar ya kwana cikin masallacin, dole gidanshi ko bai gina masallaci ba, zai ware wani waje da sallah kawai za'a dingayi, watalila yayi sanyi da albarka irin wadda masallacine kawai yake da ita, don ya Lubna sufyan Hausabook.com 497 samu wajen kwanciya idan yana cikin damuwa. Zuciyarshi matse a cikin kirjinshi da yaga Khalid a zaune kan darduma, a gida yayi sallah kenan, abinda zaisa shi sallah a gida ba karami bane ba. Baiyi masa magana ba "Ina mukullin motarka?" Ya tambaya, hannu yasa a aljihu ya ciro ya mika masa, nashi aljihun ya duba yaga yana da dubu shidda. Sai ya fita, baiyi wani nisa ba yayo musu takeaway badan yana jin yunwa ko yana cikin yanayin son cin komai ba, jikinshi na bukatar abinci ya sani, haka Khalid, yafi bukatar ganin yaci wani abu ma. Yana komawa ya samu Khalid harya kwanta, a kasa ya ajiye komai "Hamma ka taso mu ci abinci" Cikin sanyin murya Khalid ya amsa shi da "Banajin yunwa Bajjo, ka kyaleni dan Allah" Mikewa Nawfal yayi ya shiga bandaki ya watsa ruwa ya fito ya sake kaya ya kwanta shima "Ka tashi kaci wani abu, ka kashe mana kwan dakin kuma" Lubna sufyan Hausabook.com 498 Khalid ya fadi, don yana kallon Nawfal din, ko amsa bai bashi ba "Da kai nake magana kana jina kuma" Bargo Nawfal yaja ya rufe jikinshi har kai "Ka girmi wannan yarintar, har mata kake da Bajjo" Baiyi magana ba, yanajin Khalid din sarai, idan ba haka yayi masa ba, ba zaici abincin ba, bashi bane yaro, Khalid ne yarinta bata saki ba, yi masa dabara bashida wahala, yanajin shi yaja tsaki a jere yafi sau hudu kafin ya sauka "Saika sauko muci dan ubanka" Duk yanayin da yakeji bai hana murmushi kwace masa ba "Magana fa nake maka" Bude bargon yayi ya fito yana kokarin danne dariyar da take neman subuce masa. Abincin sukaci, shinkafa da dankali ne ya siyowa Khalid, shikuma ya siyowa kanshi kifi da dankali, yayi mamakin yanda sukaci abincin sosai, shiya kwashe kwanonin ya dawo, suka zauna suna Lubna sufyan Hausabook.com 499 dan hirar da ba zasuce ga asalin abinda suke fada ba, hirace da kowa abinda yake son magana akai daban da abinda yake fitowa daga bakin shi. Wani numfashi mai nauyi Khalid yaja yana fitarwa, idanuwanshi kafe jikin bangon wajen kamar mai son gano duka amsoshin tambayoyin da yake dasu akan bangon yace "Idan abin nan ya taba har yaranmu fa?" Wani irin shiru ya ratsa dakin kafin Nawfal ya iya bude bakin shi da yakejin yayi masa nauyi "Babu abinda ya faru, kaji Daddy ai, yace babu abinda ya faru" Kai Khalid ya jinjina, Julde nada halaye da yawa, amman karya bata cikinsu "Bai faru ba yau..." Khalid ya fada yana rasa ta inda zai fara gayawa Nawfal halayen Julde daya sani, da kuma yanda Salim yaga babu halin daya kamaci ya dauka irin wannan, da gaskene kowa yana da labarin bayarwa, kowanne mutum da zaka hadu dashi a hanya yana da labarin da zai baka inda zaka tambaye shi, amman wasu labaran duk da Lubna sufyan Hausabook.com 500 akwaisu ba zasu taba baduwa ba, wasu labarin kokarin binne su akeyi yanda ko kurarsu wani ba zai tarar ba balle kuma yaji su. A cikin wannan labaran akwai wannan, saboda ba labarinshi bane ba, masu labarin idan suna so ya sani zasu bashi da kansu, idan yana da rabon ya sani zai sani kamar yanda shima ya sani. Numfashi ya sake ja, kirjinshi na tafasa, daya runtsa idanuwa, fuskar Daada ta dawo masa dazun, yanda tayi masa murmushi kamar babu ciwo a kirjinta, kokarin yakice zuciyarshi yakeyi dan karta hasaso masa abinda Daadar take ji amman ya kasa. Ya Daddy zai musu haka? Jin wani abu na toshe masa makoshi, tafukan hannunshi yasa ya tallabi fuskarshi dasu yana sauke numfashi hadi dajin dumin hawayen shi na zubowa, wanne irin abin kunya ne wannan? Ya zai iya sake hada idanuwa da Madina yanzun? Ta sani? Idan bata sani ba ta sani din ya zataji? Rayuwarta zatayi canzawar da ba zata taba komawa dai-dai ba. Saboda Julde ya tabasu ta fannin da warkewarshi zaiyi wahala, tabon da zai bari kuma zai dauke su har karshen rayuwarsu bai Lubna sufyan Hausabook.com 501 daina ciwo ba, ko motsin kirki Nawfal baiyi ba, numfashin shima bayaso yayi karar da zata katsewa Khalid yanayin da yake ciki. Kuka ne yau anyi musu abinda dole zasuyi shi, zai karya idan yace baiji sauki-sauki ba, hade kanshi da gwiwa Khalid yayi, ya dauki lokaci a haka kafin ya dago, sai Nawfal ya kauda kanshi kawai, ya bashi tazarar da yasan yana bukata harya mike ya shiga bandaki, saiya tashi ya hau gadon ya kwanta. Daya fito shi ya kashe musu fitilar dakin, sannan shima ya kwanta, ko saida safe ba suyiwa juna ba, kowa ya juya kwanciya, zuciyoyinsu cunkushe da tunanin da yayi kamanceceniya a lokaci daya kuma yasha bamban. * Da safe har wajen karfe goma suna daki, Nawfal yaji Khalid yayi waya wajen aiki yace musu ba zaije ba bashida lafiya. Shikuma yayi waya da Murjanatu tace masa ta gama shiryawa, za'a sauketa filin jirgi, yasan duk inda take tana gab da sauka, shisa yayi wanka ya shirya ya koma ya zauna. Khalid yake so yaga ya tashi sai su shiga bangaren Saratu tare, amman saiya koma ya Lubna sufyan Hausabook.com 502 kwanta, yana so yace masa ya tashi suje amman bayason fama masa ciwon da duka suke ta lallabawa. Dakyar ya tattaro karfin gwiwa ya mike yana fita, ya kai wasu mintina a bakin kofar dakin kafin ya shiga da sallama, a kitchen ya samu Saratu "Ina kwana Nanna" Ya fadi muryarshi na rawa, juyowa tayi, sai yaga fuskarta kamar a kumbure "Bajjo...kun tashi lafiya" Mamaki yasa shi ya bude bakin shi, amman sauti ko daya yaki fitowa, ya rufe yayi gyaran murya kadan kafin ya iya amsawa da "Alhamdulillah, ya jikin Daddy?" Dan juyawa tayi kafin ta amsa "Da sauki, bacci yakeyi" Kai ya jinjina yana kokarin juyawa saboda baisan me zai sake fada ba "Ka tsaya ka wuce muku da abin kari" Lubna sufyan Hausabook.com 503 Wani mamakin ya sake dukanshi tare da maganganunta, tunani yakeyi, idan akwai ranar da ta taba yi masa tayin abinci, koma ta damu da yaci ko baici ba, asalima rashin cin nashi yafi muhimmanci a wajenta tunda yanda duk zata dafa saita tabbatar ya haramta a wajen shi. "Sai dai in kaiwa Hamma, zan fita ne ni" Juyowa Saratu tayi "Haka zaka fita baka ci wani abu ba? Ka tsaya ka tafar muku dashi ku duka, kaima karka fita bakaci wani abu ba" Ko yaso yayi magana ba zai iya ba, wani abu ya tokare masa makoshi, iya wannan maganar, iya wannan kulawar ya tuna masa dararen da ya shafe cikin kewar kulawar uwa, tasa zuciyarshi ta motsa da wani irin

Chapter 19 of 27