Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
akan batun mutuwar auren ta, babu kuma wanda ya sake mata zancen yaushe zatayi wani auren kamar yanda taji Baba na zargi a cikin tambayoyin shi. Dalilin ta ya sha bamban da duk wannan "Auren kisan wuta zakiyi Dije..." Baba ya jefeta da wani yanayi mai nauyi a muryar shi da yasa wani abu da tasan ba hanjinta bane amman yana da tsayi ya tsinke a cikin cikinta "Kinsan girman munin abinda zakiyi a addinin ki kuwa? Baki san haramcin shi ba ko?" Da sauri take girgiza ma Baba kai Lubna sufyan Hausabook.com 51 "Ba auren kisan wuta zanyi ba Baba..." Karya ta farko da ta gifta a tsakanin su tunda ta mallaki hankalin ta, ba'a sirri a gabanta ko laifi lokacin yarinta da yan matanci, don da Baba yace "Dije fadamun gaskiya kinji, me ya faru?" Take zayyane masa komai, ko da kuwa harda ita a cikin laifin. Shisa idan ta fadi magana yake yarda kai tsaye, amman yau yanayinta da muryarta duk sun nuna rashin gaskiyar ta "Karki sa yazo wajena in dai ba son auren shi kikeyi don ki zauna ba Dije, na rokeki karkiyi wannan kuskuren har ki raba zunubin shi dani..." Wani abune tsaye a makoshin ta da ta kasa hadiyewa, abin da kuma bai hanata sake furta wata karyar ba da ita ce matakin farko na canza abinda suka tsara ita da Datti "Zaman aure zanyi Baba" Karyar da zata bibiyeta a gaba Karyar da zatayi dana sanin ta Lubna sufyan Hausabook.com 52 ** Juma'atu babbar rana, juma'a hasken mako. Daren ta ma cike yake da albarka, abune da ko tsofaffi da aka haifa a musulunci suke kuma yin shi yanda suka taso suka ga anayi batare da neman ilimi ba sun san haka, kusan sune ma suka fara furta kalaman da basu san har a addinin da suke ikirarin bi ba kalaman su gaskiya ne, in da sun san darajar daren ranar da kuma ranar da ake so bawa ya raya da ibadun da zasu kara kusanta shi da Ubangiji, to da sun dage don ganin damar da suka samu ta kasancewa rayayyu kuma masu lafiya a darare da kuma ranakun juma'a mabanbanta bai wuce suna masu shagala ba. Juma'a ce ta uku a wajen Dije, don hatta da lissafin awannin da suke cikin ranaku basa bace mata, yanda duk ta hango kuntata a gidan Baabuga ta wuce hasashen ta, bata saba ba, suna da yawa a nasu gidan, amman ba irin wannan yawan ba, kuma bakai kadai ake bari da aiki ba, taimakawa kawai zakayi, a zamanta gidan Datti kuwa ba kullum take abinci sau uku ba, fiye da rabin lokuttan ma a gidan Hammadi sukeyi tare Lubna sufyan Hausabook.com 53 da Abu, sai ta dibo nasu ta taho da shi, ko Abun tace mata karta dora girkin rana, ta saka abinci da ita. Abu da tayi kewa fiye da tunani. Amman rashin son kazantar ta yasa sai ta share filin tsakar gidan na Baabuga sau biyu a rana duk da babu shafen sumunti, bandaki kuwa runtse ido kawai takeyi tana wanke iya inda zata tsugunna, tunda ta ina zaka fara wanke bandakin kasa? Wata irin jar kasa ce da lokaci yasa ta hade waje daya, ko kurar kirki bata tashi idan tana shara, amman ta bandakin batayi irin ta tsakar gidan ba. Bata kuma damuwa da zundenta da matan shi sukeyi, don ta kula kishi sukeyi da ita kamar babu gobe. Da sun san bata shigo domin ta zauna ba da sun sahirta mata, duka kwananta uku a gidan suka fara tashin hankalin sai ta karbi girki. Bata son hayaniyar shisa ta karba, kwana dai-dai sukeyi da take ganin kamar awa dai-dai ce, tuka tuwon gidan da kuma tarin wanke-wanke ba abu bane mai sauki. Satin ta biyu akayi dace Abu ta zo ranar girkinta, ta sameta da dora wannan tukunyar tuwon gayyar, tana kallo har hawaye Abu ta dinga Lubna sufyan Hausabook.com 54 daukewa don karta gani, itama sai ta nuna mata bata gani din ba. Tayata tayi suka tuka suka kwasawa kowacce mace kason ta ita da bataliyar yaranta. Abun nata kallon ta, har kudi ta kwanto a habar zaninta tana ba Dijen da ta karba kawai tana ma Abu godiya. In ma ta tsaya gardama Abu baji zatayi ba, tunda bata san abinda suka shirya ba, haka bata san tana da kudin ta da Datti ya bata ba, masu yawan gaske kuwa. "Abinda duk kike so ki bayar a siyo miki Dije, ba iya cin abincin gidan nan zakiyi ba" Bata kuwa iya ci din, idan ranar girkinta ne da safe ta dama koko, takan fito da kofi ta diba ta shiga dakin ta inda take da tulin sikari da farar alawa, wata ran ta dauke ta tana gutsura tana kurbar kokon, yan kananan yaran kan bata tausayi, nasu kokon saita diba a wani bokiti ta zuba musu sukari, ko ba ranar girkin ta ba da yake ance kuruci dangin hauka, yaro kuma babu ruwan shi da mahaifiyar shi bata san ka in dai kana kyautata mishi, da sun faki idon iyayen nasu sai taga sun fado dakin ta wai ta saka musu sikari ko ta basu farar alawar ta, bata taba hana Lubna sufyan Hausabook.com 55 su ba, har kudi tana dauka ta basu su siyo yar alawa. Badon kowa takeyi ba sai dan kuruciyar yaran, da kuma yanda take jin ko kishi ya hadata da wata ba zata iyama yaranta mugunta ba, don shi da na kowane, watakila ma a cikin yaran kishiyar ne wani Allah zai nufa da samun arzikin da zatayi fatan ya ture yan ubanci gefe ya tallafi 'yan uwan shi. A wajen matan Baabuga ba haka abin yake ba, gani sukeyi kamar yaudara ce da kissa irin ta mata, don ta fisu samun fada a wajen miji. A dan zamanta matan duk sun canza, yan sutturun su da sukan siya da kudaden sana'o'in hannun da suke yi, can na kasan akwati suke fiddowa kowacce na caske gayun da basu sabayi ba. Matan Baabuga da halayen sune nishadin da takan samu a kuntataccen gidan shi duk idan wani uzuri ya fito da ita tsakar gida. Shikuwa duk daren duniya sai yayo mata kunshin tsire da rogo mai yawan gaske ya mika mata daki, shi take ci da dare ta rage har safe ta kara ci, wani lokaci da fura da tasha nono yake hado mata, tana kuma jin dadi, har rana ba zata wuni da Lubna sufyan Hausabook.com 56 yunwa ba tana jiran dawowar shi. Yawan hidimar yasa ta fahimci da kudaden Dattin ta akeyin su, shisa da wani irin nishadi take cin naman. A ranar kwananta kuwa in Baabuga ta shigo, kasa take sauka tabar mishi gadon karfen da aka kai mata. Wajen ma yayi mata kada don gadon da sauran tarkacen ta duk ya cike dan dakin da bashi da girma. In kuwa taji ya maida kofa ya rufe tare da bugun zuciyar ta yake yin haka, bai taba bi takanta ba, sai minsharinta da zai tayata hira har wayewar gari. Wannan juma'ar kuwa itace ta karshe da zatayi a gidan shi, ita ce kuma wadda tazo mata a baibai. Ita din bata da wani jiki, duk da tana da madaidaicin tsayi, amman siririya ce da in tayi wani aikin zaka iya mamaki saboda yanayinta bai nuna alamar karfi ba. Karfin da dagaske bata da shi lokacin da tun shigowar Baabuga dakin ya mayar da kofa ya rufe ya zauna akan gado madadin kwanciya kai tsaye kamar yanda ya saba ya fara kashe mata jiki. "Kwana uku ya rage miki da zama a gidan nan Dije, ina bukatar dukiyar da Datti yai mun Lubna sufyan Hausabook.com 57 alkawari dan ita kadai ce damar da nake da ita na tsayuwa akan nawa kafafun, tun tasowa ta a karkashin wasu nake..." Yake fadi kamar mai bata labarin da bata ga alakarta da shi ba, bata kuma son ji "Ko ban ciyar dake ba, na baki makwanci, na kuma taimake ku, ki taimaka mun nima, ki taimaka mun Dije in dandana abinda nake ta hasashe tun shigowar ki gidan nan" Zuciyarta har cikin idanuwanta da suka ciko da hawayen tashin hankali take jin bugunta, musamman da Baabugan ya mike yana nufota. Takasance cikin mutanen da tashin hankali yake kwacewa sautin murya, hawaye ne dai ke zubar mata tana kuma matsawa baya, yanda ya riko damtsen hannun ta tasan bata da karfin da zata gwada da nashi. "Allah ya isa tsakani na da kai Baabuga, har abada ba zan yafe maka ba, Allah ya isa tsakani na da kai" Sune kalaman da ta furta cikin kuka da safe da zai bar dakin, amman ko bi takanta baiyi ba. Lubna sufyan Hausabook.com 58 Kuka tayi shi kamar ranta zai fita tun daren har wayewar gari, bokatan ruwa biyu ta ja a rijiyar da take can karshen gidan tana wanke jikinta, amman bata daina jin Baabuga a wajajen da bai kamata ba a jikinta, a wajajen da ba hurumin shi bane ba. Wuni tayi kuka, ta sake kwana tana yin shi, dan ledar daya shigo mata da ita ko kallon ta batayi ba har wani daren. Ta cine saboda tazo sallar ishayi ta dinga ganin wani duhu-duhu da bashi da alaka da dare, karta halaka kanta bayan wayewar garin zata zo mata da wani haske na daban. * Ta san fara'ar da ta kasa boyuwa a kan fuskarta ce abu na farko daya fara tona mata asiri a wajen yan gidan su "Bakiji maganata ba ko Dije? Allah ya kyauta, Allah ya kuma yafe mana gabaki daya" Baba ya fadi bayan ta zo mishi da takardar saki har uku da Baabuga yayi mata. Baban kuma yaga dalili kwanaki hudu bayan haka, yaga da sa hannun Baabuga akayi komai, gonar da ya siya ba Baba kadai ta sanarwa da Baabuga yayi Lubna sufyan Hausabook.com 59 auren yarjejeniya da Dijen Datti. Cikin kankanin lokaci zancen auren kisan wutar da Dije tayi ya karade kauyen Marake. Har mamaki ta dingayi, yanda mutane zasu dauki abinda bai shafe su ba suyi ta cece kuce akan shi. Ita yaki take da zuciyarta, kamar yanda suka tsara da Datti, sai ta gama iddar ta ne zai zo. Kewar shi ke nukurkusar ta, ko da ba suyi wata magana mai yawa ba suga juna. Amman a kasan zuciyarta tana jin zata iya daukar wannan dan takaitaccen lokacin, tayi kewar shi, tayi kewar Julde, dan Abu ita kadai tazo mata wannan karin "Fada ya kamata inyi miki idan da gaske na dauke ki yar uwa, amman banda wannan zuciyar, in da baki kaso auren nan ba ina gab da zuwa in kashe miki shi" Abu ta karasa tana rungume Dijen kafin ta saketa tana share hawayen, suna kuka yin dariya gabaki daya. Ko kowa yaji haushin abinda tayi Abu ta wanke mata komai tas, kafin ma kwanaki su karasa cika ta koma gidan Dattin ta. Ta koma kusa da mutanen da take ji fiye da Lubna sufyan Hausabook.com 60 wasu a cikin yan uwanta. Innar ta bamai yawan magana bace bayan "Allah ya kyauta" Bata sake furta komai ba, itama Dijen batayi wani yunkuri na kare kanta ba, sun sani, meye abin boye-boye. Auren kisan wuta tayi, zabinta ne, a cikin su babu wanda yasan soyayya balle tayi kokarin fahimtar da su, dul yayyaenta mata babu wadda ta auri kamar Datti. Takardar da Baabuga ya bata sai ta wanke mata abinda yayi saura na shi da take ji a jikinta, shisa ko tunaninta bai kara giftawa ta daren ba. Kwana take tana tashi da farin cikin yanda ranar take kara kusantata da cikar burinta na komawa gidan Datti. Hankalin ta ya dauke, bata bi takan jikinta balle ta kula da sauyin da yayi. Haka bata zaben abinci, wanda duk taci zama yake, sai dai ko gyada wani ya ambata sai taji kamar ranta zai fita yabi ya nemo gyada duk inda take sannan ya dawo, bata samun nutsuwa, kudi ta cire ta aika gidan Asibi yayarta da yake tana siyarwa sai ta soyo mata kwano daya mai gishi ta zo ta adana tana diba kadan kadan, Lubna sufyan Hausabook.com 61 kamar nama haka takan ji gyadar. Bata kuma damu da rashin ganin al'adarta ba a watan farko, domin ta canza mata watanni biyu da suka gabata, ta kara kwanaki shidda kan lokacin ta, ta kuma kara kwanaki goma ana gaba. Wannan ma ta dauka hakan ne, kafin ya daidaita tunda batasan dalilin shi na hargitsewar ba. Har wani yammaci da Innar A'i kamar yanda suke kiran abokiyar zaman mahaifiyar su, duk da A'in ta rasu tana shekara uku. Kuma ba ita bace yarta ta farko, lakabin sunan yaki barinta ta kalli Dijen da take zaune tsakar gida tana tsintar wake, sosai take duban hasken da tayi, fatarta tayi wani luf ta jefeta da tambayar da ta razana duka ruhinta "Dije yaushe rabon ki da ganin al'adar ki?" A razanen ta dago da bayanannen tsoro a fuskarta, tana neman nutsuwar da zata rage gudun da zuciyarta takeyi cike da kai kawo a cikin kirjinta "Wancen watan da wanda ya gabata kafin shi duka nayi karin kwanaki, ta rikice mun" Lubna sufyan Hausabook.com 62 Dan murmushi Innar A'i tayi "To wannan rikicin kam mai motsi ne Dije" Ai batasan tasan ta mike ba sai da taji salatin Innar A'i, da kuma karar faduwar kwaryar waken da take kan jikinta tana fitar da me kyan tana zubawa a wata, ba'a kai da kwashewa ba aka sake yin ruwan sama irin na bazatar nan, duk sai wani yayi duhu cikin waken. "Ni jikar Takko da Allareeni..." Cewar Innar A'i tana dorawa da "Me yake damun ki Dije? Ciki ne fa, rabo mai girma amman kamar wani mugun abu?" Ganin hawayen da suka wanke fuskar Dije. A wajen ta ba ciki bane, a wajenta ba rabo bane, a wajenta mugun abune a jikinta da zai nisantata da Datti na tsayin watanni tara da doriya a maimakon uku rak kamar yanda suka tsara. "Baabuga ya cuceni" Maganar zuci ta subuce mata, wasu hawaye sababbi na zubo mata Lubna sufyan Hausabook.com 63 "Wallahi Dije zan kwade ki da mari idan baki nutsu da wannan haukan ba, ko dan kinga an sa miki ido? Babu wanda yai miki maganar wautar da kika aikata?" Nan tabar Innar A'in tana bambami da yake in dai wajen tarbiya ne a gidan kowa na da damar hukunta dan kowa kamar yanda zai ma nashi. Daki ta shige tana samun waje ta zauna dabas, yanayin ta zaisa kayi tunanin karshen duniyarta ne ya zo. Kuka take da yake fitowa daga zuciyarta, me zata ce ma Datti? Ta karya alkawarin da ta daukar mishi? Ta so binne daren su da Baabuga a matsayin tarihin da ba za'a taba tonowa ba, ba'aje ko ina ba asirinta yana son tonuwa kowa yagani. A yanda azabar son Datti ke nukurkusar ta ba zata iya fuskantar shi ba, kamar yanda ko ba tada niyyar komawa gidan shi ba zata taba hada iri da Baabuga ba Zabi daya take da shi Zabin da shine kuskuren ta na biyu. Kallon ta Abu takeyi, in da wani yace zata taba kallon Dije da irin wannan idanuwan zata karyata, saboda Dije ce, Dije da ko lokacin da Lubna sufyan Hausabook.com 64 Datti ya auro ta da kuruciya bata ga alamar hauka a tattare da ita ba. Ashe dai hauka bashi da alaka da shekaru? Ashe hauka na iya samun ka ako wanne bigire na rayuwa "Haukan da ya same ki kenan Dije?" Abu tayi maganar tashin hankalin da take ji na bayyana ta cikin muryar ta, hannu Dije ta kai tana dauke kwallar da ta taru a gefen idanuwan ta "Ba hauka nake ba Adda Abu, ke kadai ce zan iya tunkara da maganar nan..." Numfashi Abu taja, wata dariya mai sauti da bata da alaka da nishadi tana subuce mata "Saboda ni kadai ce ban taba ko batan wata ba balle in san zafin haihuwa...shisa ko?" Kai Dije take girgizawa tunda Abu ta fara magana, har ga Allah ba haka bane nufin ta, kamar yanda tace ne, babu wanda zata fara tunkara da maganar tana son zubar da cikin da yake jikinta Lubna sufyan Hausabook.com 65 "Me yasa to? Me yasa zaki tunkare ni da wannan maganar? Na dauka zaki fi kowa sanin nice karshen wadda ya kamata ki tunkara da cewa kin samu rabon da ya isheki a duniya har kike neman zubar da wani" Wannan karin barin hawayenta tayi suka zubo, saboda idanuwan Abun ma cike yake taf da hawaye da wani kwantaccen bakin ciki da Allah kadai yasan shekarun da tayi tana dauke da shi "Karki ce haka Adda...Julde kadai gare ni, kin san shi kadai ne..." Numfashi Abu ta shaka ta bakinta saboda hancinta ya toshe da wani abu da ba zata iya fada ba "Da alama ya isheki, shi kadai din" Da zata iya da ta ciro abinda yake cikin Dije ta mayar a nata, a lokacin da wani yake nema ido rufe, yake nema da dukkan zuciyar shi a gefe daya, a dai-dai irin wannan lokacin wani yake samu yana kuma neman maraba da shi. Idan ba Allah ba waye zaiyi haka? Duka bangarorin biyu Lubna sufyan Hausabook.com 66 Yana sane da su, bai kuma manta da su ba, saboda dukkan su a cikin jarabawar Shi suke. "Ba haka bane ba, ba haka bane ba.. Ba zan iya hada jini da Baabuga ba, ba zan iya ba... Ba zan iya ba Adda..." Ta karasa maganar muryarta na sarkewa saboda dacin da take ji "Jini ne ba zaki iya hadawa da Baabuga ba ko kuma cikin da zai hanaki komawa gidan Datti ne bakya so? Ki fadama kanki gaskiya...ki bude zuciyarki ki duba gaskiya..." Ba sai ta bude zuciyarta ba, amsarta a bayyane take, dula dalilan biyu ne, mikewa Abu tayi tana saka gefen mayafinta ta dauke kwallar da take shirin zubo mata "Dije kar wannan ya kara zama kuskuren ki...in dai cikine zaki zubar to ba da hannu na ba, ba kuma da goyon baya na ba" Bata ma bata wata dama ba ta fice daga dakin, da akace ga Abu nan, ta jiyo muryarta har wani sauki-sauki taji, ya Abu zata juya mata baya a wannan bigiren da tafi bukatar ta? Babu yanda Lubna sufyan Hausabook.com 67 za'ayi ta fita, ko meye ya faru tasan ba za'a taba bari ta fita batare da ta cika kwanakin iddarta ba, amman lokacin da zata cika kwanakin iddar lokaci ne da komai zai iya sake cakude mata. Ga idanuwa da Innar A'i ta saka ma duk wani motsi da zatayi, ko abinci sai ya zamana sai Innar ta duba ake bata shi, ko aike tayi sai tace a miko mata ledar ta duba taga meye a ciki. Kuka ne abokin hirarta duk dare kafin baccin wahala yayi awon gaba da ita, tayi ciki ba daya ba, ba biyu ba, amman wannan bata laulayi, ciwo ko na girar ido, gyada ce da ta dauko tun washegarin ranar da ta gane akwai cikin ta rabarma yaran gidan ita tas, kilan wannan ta zama sanadin da zai fita, sai dai me, kamar mahaukaciya kwana biyu a tsakani dole ta sake fitar da wasu kudin ta bada aka nemo mata gyadar, shine ma tana gama ci tayi amai kamar zata amayar da kayan cikinta. Tun daga lokacin saiya zamana ko ambaton gyadar bata so ayi. Zuwa kuma yanzun kowa da yake gidan yasan tana dauke da juna biyu, babu dai wanda yayi mata maganar. Lubna sufyan Hausabook.com 68 Kamar wasa haka kwanaki suka dinga wucewa da ita batare da ta samu tsayayyar mafita ba har ranakun iddarta suka cika. A ranar kuma Datti ya aiko kiranta, daman jiran shi takeyi, Allah kadai yasan jigatar da tayi da kewar shi a tsayin watannin nan, bata damu da fadan da Baba zai iya yi ba, batama jira wani yace komai ba, ko mayafin da ta dauka sa da takai soron gidan ta yafa shi, tana fita tagan shi tsaye, jikin shi sanye da rigar saki da farin wando na hadi, hasken farin wata na haske mata fuskar shi tar, murmushi ne ya kwace mata, kafin hawaye su cika mata idanuwa, shima murmushin yayi mata. Jikin shi na bari da son riko ko da hannun tane, tun kafin Hammadi ya fada mishi ya rame yaji fuskar shi ta fada "Nayi kewar ki, sosai nayi kewar ki" Ya fadi muryar shi na fitowa a raunane, itama tayi kewar shi, siraran hawayen da suka zubo matane ta bari suka sanar da shi haka don ta kasa magana, wasu yanayoyi ne take ji da bai kamata ace sun hade mata a lokaci daya ba Lubna sufyan Hausabook.com 69 "Gobe zan samu Baba da maganar auren mu, ya mayar mun dake, ya dawo mun dake Dije ko zan samu nutsuwa" Wannan karin wani irin gunjin kuka ne ya kwace mata da ya fito daga lungun zuciyar ta, cikin tashin hankali Datti yake kallon ta, musamman da yaga ta durkushe tana zama kan dakalin da yake gefen gidan nasu saboda kafafuwan ta da suke barazar kin daukarta, shima zama yayi a gefe, sai dai maganar duniya da yayi mata baisa ta dago ba, saima sautin kukan ta da yake karuwa, wani irin kuka da bai taba ganin tana yin irin shi ba duk zaman su, ko da kuwa yayi mata fadan nan nashi da yake daga mata hankali, yau nashi hankalin ne a tashe. Babu kalar tunanin da baiyi ba, har mamakin sauri irin na kwakwalwar shi yayi, saboda gudun aikin da takeyi mishi a cikin dan kankanin lokaci haka, kafin kalaman Dije su tsayar mishi da komai, idan yace komai yana nufin har da bugun zuciyar shi na dakika kafin tayi wani tsalle tana neman hanyar fita daga kirjin shi gabaki daya Lubna sufyan Hausabook.com 70 "Ina dauke da juna biyu..." Kalaman suka sake dawo mishi kamar saukar aradun da bai taba yarda yana faruwa ba tunda bai taba cin karo da hakan ba, kafin wani duhun kishi ya lullube shi, duhu fiye da na dararen da kan samu saukin nasu da hasken farin wata ko na taurari, baisan ya tashi daga kusa da ita ba, sai da ta dago jajayen idanuwan ta tana saukewa cikin nashi yana ganin nisan da sukayi ma juna lokaci daya "Me yasa? Abu daya na roke ki Dije...me yasa zaki hadamun jikin ki da na shi?" Mikewa tayi, saiya matsa taku biyu baya, yana sa bugun zuciyar ta yana karuwa "Dan Allah Datti" Kai yake girgizawa, kwakwalwar shi na hasko mishi hotunan Dije da Baabuga batare da ta tausaya ma halin da zuciyar shi take ciki ba, idanuwan shi ya runtsa yana bude su. Ya sake runtsa su saboda wani hawayen bakin ciki da yake jin yajin su cikin idanuwan shi, ashe akwai sauran abinda zai iya bayyana hawayen shi Lubna sufyan Hausabook.com 71 haka? Wannan karin shine ya tsugunna, yana jin kamar ana zarar wani abu tare da shi, da farin ciki ya wuni, zuciyar shi cike taf da shi, ya daren shi zai juye haka? Ya zaiji zuciyar shi ta fada wani waje da yake jin ganota zaiyi masa wahala. Hawaye ne wani nabin wani yake zubo ma Dije, ganin yanda Datti yake kokawa da numfashin shi, sai ace zuciya bata da kashi, sai ace tsoka ce zalla, abinda take ji yana karyewa cikin kirjinta yanzun fa? Meye shi? Abinda take gani yana karyewa yanzun a tare da Datti menene shi? "Ina so in zubar... In zubar da cikin, tun da nasan da shi nake so in cire shi... Bansan ya zanyi ba...kuskure ne...wallahi ba yanda zanyi" Sai da Datti ya dafa kasa sannan ya iya mikewa, a sarari yake, fili ne gaban shi da bayan shi, sai dai yana kallon Dije yaji kamar tayi masa katanga da samun wadatacciyar iska. Juyawa kawai yayi yana jin yanda take kiran shi amman ko juyawa baiyi ba. Tafiya yake da Dije take jin takun ta kamar a cikin kirjinta da yake kara daukar dumi. Dakyar ta iya komawa cikin gida tana wucewa daki kai tsaye, maganar da Innarta Lubna sufyan Hausabook.com 72 take mata ma bata tsaya ta saurara ba, tana shiga ta samu wajen lungun gadon Innar ta zauna tana jan kafafuwanta ta hade su da jikinta hadi da sakin wani irin kuka mai cin rai. Ba zata gaji da aika ma Baabuga Allah ya isa na yanda ya canza musu komai a dare daya ba. Ta tashe ni, ta tsani abinda yake cikinta. Haka Inna ta shigo ta sameta tana kuka kamar an labarta mata mutuwar Innar ko ta Baba "Kinga ki sahirta ma kanki wannan damuwar Dije, lamari na duniya a hankali ake bin shi, musamman abinda baka isa ka sauya ba...kiyi hakuri kibi komai a sannu" Maganar ta kunnen haggunta ta shiga tana bi ta dama ta fice batare da ta samu wajen zama ba, wacce duniya ce zata bi a hankali? Duniyar da batayi mata adalci ba? Me zata bi a hankali, daga sakin ta zuwa yau, babu wani abu guda daya da yazo mata da sauki, sai ita ce zata bi komai a hankali? Wannan magana ce da bata da hankalin daukarta a yanzun. Runtse dai bata runtsa ba, dan sai cikin dare ta samu tayi sallar isha'i, da alwalar ta mayar da asuba tana Lubna sufyan Hausabook.com 73 kwanciya dakyar. Koko da kosan da aka kawo mata haka akazo aka dauke da rana da aka kawo mata wake da shinkafa da ya sha man gyada, ko yunwar ma bata ji, dakyar ta iya mikewa ta dauro alwala tazo tayi azahar. Tashin hankalin da take ciki bai bari ta tuna da wani wani wanka ba, da la'asar ta idar da Sallah kenan Innar A'i ta shigo tana jingina bayanta da bangon dakin "Kinki cin komai duk yau Dije, in baki duba kanki ba, ki tausaya ma abinda yake cikin ki kici wani abu dan Allah" Ta san Innar ta ce ta turo Innar A'in, wasu hawaye masu zafi suka zubo mata, takai hannu tana dauke su "Kiyi hakuri, watannin zaki ga sun wuce kamar kiftawar ido in dai Allah ya bamu aron rayuwar, kiga kin koma dakin mijin ki kamar komai bai faru ba, amman in kika rasa lafiyar ki fa?" Haka Innar A'i ta dinga bata baki, a cikin maganganun babu wanda suka fi mata tasiri irin jin zancen komawarta gidan Datti, shisa ma Lubna sufyan Hausabook.com 74 harta dauki kwanon abincin, aikuwa tas ta cinye shi, tana dorawa da furar da Innar A'in tasa aka kai mata, sai taji wani karfi na daban yana shigarta, da kuwa shafal take jinta. Bata sake samun wani karfin ba sai da aka aiko kiranta bayan isha'i, har tuntube tayi garin sauri, innar ta zatayi magana Innar A'i ta girgiza mata kai tana dorawa da "Ki rabu da ita, in ta ganshi ta samu nutsuwa, yaran yanzun na da bambanci da mu, in aka matsa mata mu duka lamarin ba zai mana dadi ba" Bayan Dijen ta fita ta samu Datti tsaye kamar jiya, sai dai fuskar shi ta kumbura kamar wanda yaci kuka. Wata yar leda ce ya zaro daga cikin aljihun shi yana bata. "Kulli daya zaki juye duka a ruwa ki sha yau, ki kara juye dayan ki sha gobe" Karba tayi da sauri, sai dai bai jira amsarta ba ya juya. Tsaye tayi bata koma gida ba saida ya bace ma ganin ta. Jikinta bari yake sanda ta koma cikin gida, sai take ganin kamar wani zai ganta, kasa samun nutsuwa tayi har sai da dare ya Lubna sufyan Hausabook.com 75 raba, tukunna ta iya shan maganin, washegari ma bata samu wani sarari ba sai Magriba. Aikuwa wajen karfe daya wani irin ciwon mara da yasa ta

Chapter 3 of 27