Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ya karya wani bangare na zuciyar shi, saboda ta saka shi hasaso ace masa ya hakura da auren Mero, ko kuma a musanya masa auren nata da wata duk kyawunta da kyawun halayenta. Sai yaji ko Marake zata hade abune da ba zai taba yarda dashi ba "Kiyi hakuri..." Ya furta da sanyin murya wannan karin, sai tayi dariya, dariyar da yake juyowa har yanzun, saboda ta zama kamar itace dariyarta ta karshe da yaji "Kaunar da nake maka mai yawa ce Hamma, kai dai ka yafe mun kawai...sai yaushe zanga Meron ka?" Ta karasa tana canza akalar zancen. Da yasan ba za'a ganta kafin Mero ta shigo gidan shi ba, da yaja hannunta ya kaita sun gaisa, sai dai da yasan zasu nemeta su rasa din a washegari da idan ya jata ya kaita taga Mero ba zai taba bari Lubna sufyan Hausabook.com 342 ta bacewa ganin shi ba balle har suzo inda suke yanzun. Kanwar shi, tilon kanwar shi da yanzun yake kara fahimtar tarin kaunar da yakeyi mata "Ba'a ganta ba ko?" Saratu ta tambaye shi, idanuwanta cike taf da hawaye, kai ya girgiza mata, a karon farko tun da aka fara nemanta yanajin idanuwan shi sun ciko da hawaye, hakan Saratu ta gani ta riko hannun shi, fisgewa yayi yana sake girgiza mata kai, ta kara rikowa, wannan karin tana kamo duka hannuwan nashi "Ina Yelwa zataje Saratu? Ina zataje haka bata fadamun ba? Auren Mero ya dauke hankalina har haka ne? Ta nuna alamun da idona ya rufe bangani ba?" Kai Saratu take girgiza masa, ita kanta batan Yelwa ya maye mata gurbin duk wani tashin hankali da auren nashi ya haifar mata. Mutanen da take so a rayuwarta basu da yawa, zata iya kirgasu da yatsun hannunta, Yelwa na daya daga cikin mutanen nan. Ko ranar da ta kwanta, tunaninta bai kai na yanda Julde baya tare da ita akan gadon nasu ba, bai kai ga yana wajen Mero Lubna sufyan Hausabook.com 343 ba, balle tayi tunanin yanda ranar ne karon farko da zata rabashi a matsayin miji da wata. Gajiyar ranar da taji ta saukar mata gabaki daya bayan ta kwanta, laushin katifar na saka jikinta amsawa da wani yanayi mai dadi duk kuwa da zuciyarta da take a cunkushe. Sai tunanin Yelwa ya sake danneta, ina take? A wanne hali? Ta samu inda zata kwanta? A wanne irin yanayi? Sai hawaye suka cigaba da saukar mata, wani na bin wani. Me yasa ba tayi magana da Datti akan auren Modibbo da Yelwar ba taga ko ita zata iya sauya ra'ayin shi? Ko ita zai saurareta tunda yaki sauraren Yelwa. Babu kalar tunanin da baizo mata ba, kafin gajiyar dake nukurkusar jiki da ruhinta suyi galaba akanta bacci ya dauketa. "Da na saka ido akanta..." Muryar Julde ta sake kutsawa cikin tunaninta, kai ta girgiza masa, tana hade tazarar dake tsakanin su, duk da cikin jikinta ya sake saka musu wata tazarar, yana hana mata riko shi jikinta yanda zuciyarta take sonyi Lubna sufyan Hausabook.com 344 "Ka daina, dan Allah karka dora laifin nan akanka..." Hannuwan shi ya zame ya tsugunna, yanajin duka gwiwoyin shi sunyi masa sanyi, dakyar ta samu itama takai kasa tana zama. Tana kallon yanda yake kokawa da numfashin shi kafin ya mike. Batayi yunkurin masa magana ba balle ta hana shi, shiya shigo dakin da kanshi. Yana fita wajen dakin Mero ya nufa, ya sameta a kwance, tana shirin mikewa ya bita kan gadon ya kwanta a gefenta "Nagaji sosai" Ya furta cikin karamar murya, saita kai hannunta tana dorawa akan fuskar shi, lallashin shi take so tayi, wani nata bai taba bacewa ba, ba zatayi karyar hasaso yanda yakeji ba. Kamar jira yake ta tabashi, wasu siraran hawaye suka zubo masa, kirjin shi yayi nauyi fiye da yanda ya tabayi lokacin rasuwar Hammadi. Akwai bambanci a wancen rashin da wannan, tunda dashi aka zuba ma Hammadi kasa har aka rufe shi ruf, yasan inda yake, ko yanzun yaso zaije makabartar, har gaban kabarin yayi masa Lubna sufyan Hausabook.com 345 addu'a. Amman Yelwa fa? Ba zai ce ga halin da take ciki ba ko inda take balle ya fara nemanta. "Idan ba'a ganta ba fa?" Ya tambaya "Za'a ganta, zata dawo..." Mero tace masa, bai yarda ba, amman kalamanta sun dan nutsar dashi. Kamar yanda ya nemi samun nutsuwa a tare da ita. Sai ya waye garin, kamar sauran dararen da ya raya tare da ita. Wata irin nutsuwa ce da bai taba tunanin ana samu tare da mace ba. Da farko ya dauka mantar dashi tashin hankalin da yake cikine na kankanin lokaci da yayi. Sai dai kamar komai, batan Yelwa ba ciwo ya daina musu ba, sabawa sukayi da ciwon. Meron ce daban, ita din da kanta ce yake jin ta bambanta da duka sauran matan da ya taba mu'alama da su. Sai dai me, ya dauka ta ishe shi, a zuciyar shi Mero ta ishe shi, bashida wani waje da zai sake saka wata mace kuma da sunan aure. Inda ba'a hada shi da Saratu ba, Mero ta ishe shi a matsayin mata, kawai wata murya ce a cikin Lubna sufyan Hausabook.com 346 kanshi take saka masa alamar tambayar ko akwai mata kamar Mero? Ko akwai wanda suka fita? Duk idan zaiga wata macen ta wuce sai tambayoyin su cigaba da yi masa yawo. Kuma su suka sake janshi ya koma bin mata watanni shidda bayan auren su da Mero. Bai san tana da kishi ba sai daren daya dawo taga sawun labba da jambaki a bayan wuyan shi. "Saika nuna mun abinda kowa yake gujemun da aurenka Julde? Saika shigomun da tambarinta cikin daki? Ba zaka iya wanke jikinka daga daudar daka kwaso ba zaka hawomun gado kana neman hada jikina da naka?!" Ta karasa tana hankado shi daga kan gadon cikin karfin da bai taba sanin tana dashi ba, kokarin tambayarta yakeyi abinda tagani a jikin shi tunda baisan da jambakin ba, kamar ya tunzurata, ta cigaba da hauka kamar wadda jinnu suka shafa, dakyar ya iya riketa ganin kamar tana neman abinda zata illata shi dashi, saida yasa karfi sosai tukunna ya iya riketa, saita fara wani irin kuka daya rikita masa lissafi Lubna sufyan Hausabook.com 347 "Na daina, kiyi hakuri dan Allah, ba zan sake ba Mero, ki kalle ni...ba za sake ba" Yake fadi yana rike fuskarta da tasa hannuwanta akan nashi tana kokarin kwacewa "Ba zan sake ba..." Yake fadi yana maimaitawa, yana so ya yarda da kalaman shi fiye da yanda yake so ta yarda dashi. Tana son Julde, tana masa wani irin so da kafin ta shigo gidan shi taga wanda Saratu takeyi masa ta dauka ba zai misaltu ba. Sai yanzun da take hadiyar abinda tasan Saratun ta shanye a shekarun zamanta dashi takejin ba zata iya ba, mutuwa zatayi, zuciyarta fashewa zatayi ta mutu. Saratu bata shiga harkarta, idan ita ta gaishe da ita zata amsa, amman idan batayi mata magana ba, ko inda take bata taba kallo. Idan kuma tace bata kishin Saratu zatayi karya, ga yaranta masu kyau, tana gidan ta haifi Fadila. Ranar farko tana tsakar gida a bakin kofar dakinta, Saratu takai ruwan wanka, amman Fadila ta ki barinta ta shiga wanka saboda kukan da takeyi "Ko ki kawo in rike miki ita?" Lubna sufyan Hausabook.com 348 Ta fadi, yanda Saratu ta kalleta sai taji tsoro, sai dai ga mamakinta, kwanto Fadila tayi daga bayanta tana karasawa ta mika mata ita, ta juya abinta. Ta dauka Salim da baya zuwa wajenta ko ta masa magana, Saratu ce ta hana shi, abinda bata sani ba shine, Saratu bata sonta don so, inda za'a bata zabi zata zabi tabar mata gidanta da mijinta. Amman bata da wannan zabin, yarane kona rana daya bata saka a ranta Mero zata cutar mata dasu ba. Abu ta wanke mata wannan shakkun daga ranta. Labarai takeji akan kishiyar uwa, inda za'a bawa wani labarin yanda Abu ta riketa zai iya karyatawa, yace ba gaskiya bane ba, shisa itama ta zabi ta shure duk wani mugun labari. Tun daga ranar kuma in dai zata bukaci daukar Fadila, Saratu bata hanata, saita je har kitso tabar mata Fadilan, ba dai ta shiga harkarta ko kadan. "Yar uwata ce Mero, ko ban auri Saratu ba 'yar uwata ce...zan rokeki, ki zauna lafiya da ita gwargwadon yanda zaki iya..." Lubna sufyan Hausabook.com 349 Shine rokon da Julde yayi mata. Koshi yayi mamakin da a cikinsu babu wanda ya taba kai masa karar dan uwan shi, Saratu ta bashi mamaki. Sai wata kimarta da bai taba tunanin zai gani ba ta ginu a zuciyar shi duk da soyayyarta har lokacin ta kasa samun waje. "Na daina, ba zan sake ba" Sune kalaman shi, ta haddace su, amman ta dade da daina yarda dasu. Da ta auri Julde ta aure shi da halin shi, amman a kasan zuciyarta ta aure shi da nufin soyayyar da taga yana mata ta canza shi, ita zata canza shi, zatayi abinda matar shi ta gida ta kasa. Sai yanzun ta gane babu yanda zaka canza wanda baya so ya canza, babu wata soyayya da ta isa ta canza halayya in har babu niyya, idan da niyya soyayyar ko yanayin saiya zama tsani na canjin, taimako kawai zaiyi bashi bane jigo. Jigon canji na kowanne irin hali shine niyya, niyyar nan itace komai. Idan ta kalle shi taji wani ciwo da yake taso mata tun daga dan yatsan kafanta har kasan zuciyarta sai ta dinga hasaso barin shi, ko ta tafiyarta ta huta, tabarshi da matan da ya zaba Lubna sufyan Hausabook.com 350 akanta, akan su iyalin shi. Amman abubuwa da yawa sai su riketa, kalaman shi, nadamar shi kowanne lokaci ta sake kamashi kamar ba zai kara ba, soyayyar da take masa da take sakata jin kamar ta yafe mishi, kamar zata cigaba da yafe mishi a kullum. Musamman da ta samu ciki, sai kulawa da soyayyar da yake nuna mata suka karu, kamar bashi da wasu yaran, kamar a tare da ita zai fara samu. Tana son abinda yake cikinta tun kafin tasan jinsin shi, amman kalar soyayyar da Julde yake nuna ma abinda ke cikin sai ya sake ninka mata kaunar da takeyi masa. Gajeriyar nakuda tayi, kuma mai sauki, cikin kasa da awa biyu har tayi ta gama. Da taimakon Dije da kuma matan Baabuga guda biyu da suka zo, da aka saka mata yaronta a hannu sai da ta faki idon mutane ta share kwallar farin cikin da ta silalo mata don kar ace tayi rashin kunya. Amman murmushin dake fuskarta yaki bacewa, ta kuma kasa daina kallon shi. Addu'arta ta amsu akan yaron da yaci suna Aliyu, take kuma kiran shi da Haidar. Yayi kama da Julde, yayi kama da sauran yan uwan shi Lubna sufyan Hausabook.com 351 Salim da Fadila. Ta kuma ci albarkacin Haidar, Salim na zuwa wajenta saboda yaron, duk da sai tayi masa magana hamsin sai taci sa'a zai amsata sau biyu, zai daga kai ya kalleta sai ya dakuna fuska, a yan shekarun shi yana nuna alamar kamar bayason hayaniya, kamar sautinta yayi masa yawa a cikin kunne, tunda wani lokacin zata ga idan baki tayi, yan uwanta daga gidan Baabuga, yana zaune a dakin, zai takai dan yatsa kunnen shi kamar mai son toshe hayaniyar su, karshe zai riko gefen zaninta yana nuna mata Haidar, in ta dauke shi zai tashi ya fice daga dakin. Tana son yaron, yanda yake komai nashi kamar ya girmi shekarun shi, komai ma a tare dashi, tsayin shi, nutsuwar da zaka gani a fuskar shi da rashin son hayaniyar shi. Har ranta taji dadin yanda Saratu batayi mata katanga da yaran nata ba, bata kuma yi musu katanga da nata yaron ba. Zata so zumuncin su ya dore Sam bata hango inda lokaci ya saka ma alakar su aya ba Lubna sufyan Hausabook.com 352 Kamar yanda batayi tunanin zamanta da Julde ba mai dorewa bane ba Shisa ta kara mike kafafuwanta, ta sake bude zuciyarta tana karbar sabuwar soyayyar da Julde yake nuna mata sanadin Haidar, kulawar shi kamar ba zai kara bata mata rai ba, kamar sabani ba zai sake shiga tsakanin su ba. A dan lokacin, idan ma ya koma halin shi, to yana iya bakin kokarin shi wajen boye mata. Hakan yayi mata, kar taji, karta gani kuma. Bata son duk wani abu da zaizo ya birkita mata kwanciyar hankali da ta samu. Larabarta a nutse tazo mata, shisa bata hango juma'arta zata zo da wani abu akasin abinda larabar ta wanzar mata ba. Tana zaune a kofar dakinta tana kallon Haidar da take jin kamar a cikin zuciyarta yake rarrafen da yakeyi, kaunar shi na cika mata zuciya. "Kiyi mun addu'a, akwai abinda nake shiryawa, idan harya tabbata zamu bar Marake, Mero zamu koma Kano ko don su Haidar, ina so su samu ilimin da ban samu ba, ina jin kamar ba zasu mori tarin dukiyar da nake da ita a kauyen nan ba..." Lubna sufyan Hausabook.com 353 Saita tsinci kanta da hasaso mafarkin shi, itama ko basu bar Marake ba, tayi ma kanta alkawarin Haidar saiya samu ilimin addini dana boko, saiya cika mata burinta data watsar saboda soyayyar Julde "Assalamu alaikum..." Taji muryar da ta roka mata aminci amman babu amincin a tare da ita kwata-kwata. Zuciyarta ta dunkule tana gangarawa ta tsaya a dai-dai kafafuwan Talatu, kafin ta daga kai ta kalleta, ta cogalo daurin dankwalinta gaban goshi, mayafinta akan kafada, fuskarta tasha kwalliyar da ko cikin dare ka farka saika ganta a furkar Talatu. Da cingam abakinta da take taunawa cike da duniyanci. Talatu, itace Autar su Musa da rikonta ya koma hannun shi tun farkon auren shi, shekaru takwas ta baiwa Mero, lalacewar da Musa yaga zatayi yasa shi yi mata auren da ta kaso a watanni hudu kacal da yin shi, bayan nan aurenta hudu, harda na farkon biyar. Na karshen ne Mero tana da cikin Haidar taji labarin Talatu ta kaso shi shima. Lubna sufyan Hausabook.com 354 Ko da tana gidan Musa, idan Talatu ta kaso aurenta tafi kowa shan wahala, haka kawai ta dauki karan tsana ta dora mata, kamar kishi takeyi da ita, duk wani abu da zata gani a wajenta in bata rabata dasho ba sai ta samo irin shi sak, ko dinki Mero tayi sai Talatu tayi irin shi. Sai daya suka hadu tunda Meron tayi aure, tunda sau daya taje ganin gida da tayi arba'in din Haidar "Ke kuma duk bokon sai kikaci baya? Kika bar binni kika tafi kauye aure?" Yanda Talatu tayi maganar zaka rantse ba kauye bane asalinta, Mero murmushi kawai tayi bata tanka ba, ta dai kula da yanda Talatu take ta kallon Haidar, tunda kayane masu kyau da tsada, irin na binni Julde yake bayarwa a siyo musu, daga ita har shi da suke a kauye sunfi Talatun kyawun gani "Yau dai gani a gidan ki" Cewar Talatu, tana tsugunnawa ta dauki Haidar, sai Mero ta kasa amsa mata sallamar da tayi mata, ta kasa ko da yi mata murmushi, saboda zuciyarta na gaya mata zuwan Talatu ba alkhairi Lubna sufyan Hausabook.com 355 bane a wajenta, saboda Talatu bata da wani dalili da zata kawo mata ziyara tun daga Kano har Marake. Hasashenta gaskiya ne Hasashenta baiyi mata karya ba Zuwan Talatu dai-dai yake da hargitsewar gidan aurenta... Duk yanda ake fada mata rashin tabbaci na rayuwa bata taba yarda ba, idan misali akayi mata da mutuwa sai wasu tambayoyin su cunkushe mata, ko idan mai lafiya ya shiga halin rashinta, mai dukiya ya rasa dukiyarsa, sai a dinga fadin rayuwa kenan, bata da tabbas. A cikin wannan abubuwan bata ga dalilin da za'a kira rashin tabbaci ba, rai ne dai kowa yasan bakone a duniya, iya lokacin da aka dibar masa na bakunta yake jira, haka dukiyar, itama aro ce aka baiwa wasu zababbun mutane, lafiyar ma haka. Babu abin mamaki don an rasa daya a ciki, daman tun farko ansan da rashin tabbacin su. Lubna sufyan Hausabook.com 356 A cikin jerin abubuwan da Mero bata dorawa rashin tabbaci ba shine auren Julde, duk yanda kowa yake da shakku akai, duk irin maganganun da aka dinga fada mata tana saka kafafuwa tana turewa, duk irin yanda halayen shi basu sauya ba kamar yanda tayi tsammani. Da hannuwan shi akan fuskarta, idanuwan shi a cikin nata yace "Ina son ki Mero, halayena nawa ne, kar rashin canza su ya sa ki dauka son ki bai kai bane ba, ina son ki, ko na miki laifi karki manta ina son ki, ko da ban fada miki kullum ba, ko da wasu ranakun ban nuna miki a aikace ba, ina son ki, a kowanne yanayi zamu tsinci kanmu Mero, sonki na daga cikin abinda nake ji zai kasance tare dani har karshen rayuwata ko da komai ya barni" Kalaman shi suka zauna mata, kamar yanda bata manta da amsar da ta bashi ba "Halayenka ne karshen abinda zan duba a zamantakewar mu, zuciyata taka ce, kasani. Kowa da ya isa dani ya sani, saboda akan soyayyar ka na fara nuna musu basu isa dani ba, Lubna sufyan Hausabook.com 357 halayenka ba zasu sa in barka ba, yanda basu sakani kin fara rayuwa da kai ba" Ashe bashi kadai ta yaudara ba harda kanta, harda zuciyarta da bata taba hango mata halayen shi zasuyi muni ba, basu taba hango mata bakar ranar da zata kafa mata tarihin da bata fatan ya maimaita kanshi ko da a mafarkinta ne "Kanwar mahaifiyata Julde..." Muryarta ta koma cikin kunnenta da wani irin yanayi, kamar ruhinta ya bar jikinta ya koma gefe yana son gangar jikinta kadai ta tabbatar da abinda ta gani. Tunda Talatu tazo gidan kwanaki biyu da suka wuce bata da sukuni, ta daina zama tsakar gida saboda haka kawai take son takaita ganin da Talatu zatayiwa Julden. Sai dai yau din girki ya zagayo kanta, bata da wani zabi, tare da Talatu suka fito da safe duk kuwa yanda tayi fama da ita akan zatayi aikinta ita kadai, duk kwana biyun da tayi ai ita kadai take musu girkin da zasu ci, bata ga dalilin da yau din zata tsiri son tayata ba. Lubna sufyan Hausabook.com 358 Yanda ta sake kasa da murya da suka gaisa da Julde ya mata wani iri, ta daga kai ta kalli Julde, sai dai idanuwan shi akanta suke, ya hade girarshi waje daya cikin wani yanayi da take yawan gani a fuskar Salim idan tayi masa magana, kamar a takure yake, kamar yana so ya roketa da ta ganshi taki ganin shi, ta ganshi karta kula shi. Abinda bata sani ba shine ba'a gidanta Julde ya fara ganin Talatu ba, yana da rike fuskokin mutane, shisa yana shigowa ya ganta yasan bashi bane karon shi na farko. Duk da akwai sauyi a tare da ita, wannan Talatun ta kara wayewa. Kwana yayi yana tunanin inda ya taba ganinta, sai washegari da yazo fita ta tare shi tana dubedube kar Mero ta fito, cikin hanzari tace mishi "Ba bafullatanin J-town bane? Ko bakai bane na taba gani a dakinta?" Rabata yayi ya wuce, kwakwalwar shi nayi masa tariyar dararen shi a sabon gari, a tsakanin dakunan matan da yayi mu'amala dasu, yana tuna J-town, wata yarinya yar garin Jos da akewa laqabi da sunan garin da ta fito din. Ya Lubna sufyan Hausabook.com 359 tuna inda ya santa yanzun, don ta matsa daf da inda yake zaune a dakin J-town ta dora kanta a kafadarshi tana riko hannun shi, ta sauke murya tana fada masa kalaman da yake tsammanin dasu take amfani wajen karkatar da hankulan maza akanta, su sake mata jikinsu da bakin aljihunsu tayi yanda ta ga dama dasu. Ba zaice batayi masa ba, itama macece, kuma kamar ko da yaushe yana so yaji ta inda ta bambanta da sauran, shisa ya biye mata. A ranar ya sake sanin kishi irin na matan bariki, yanda sukayi baram-baram da J-town har ana rirrike su zasu gwabza su gwada karfi. Ya dauke mata kaine saboda a karo na biyu da muryar nan da take manne dashi ta rada masa son sake kasancewa da Talatu, ya manta yanda take, yanzun da yake neman mace irin Mero, kowama bi yakeyi batare da dogon tunani ba. Amman Talatu na da alaka da Mero, duk da har yanzun bata fayyace masa ya alakar tasu take ba. "Ina bakuwar ki?" Ya gwada tambayarta, yanda ta amsa masa kamar bataso bakinshi ya sake furta wata Lubna sufyan Hausabook.com 360 magana data danganci Talatu yasa shi fasa tambayar yanda suke da ita. Tunda kusan kowa da yake gidan Kawunta ya sansu a bakinta, ya kuma ga wasu. Amman bai tabajin ta ambaci Talatu ba, watakila halayen Talatun ne dalili. Ya kudiri niyyar kaucewa duk wata hanya da zata hadashi da Talatu har lokacin da zata bar gidan tunda yasan bashida iko da halinshi, sanda zaiyi wani abin da zai iya ja masa matsala ba zai sani ba sai bayan ya aikata. Sai dai lokacin da kake kaucewa abu, lokacin yake kokarin kusantoka. Wannan tsautsayin ne yake bibiyar shi tun safe, da nauyin jiki ya tashi kamar ba zai fita ba. Saratu ta tambaye shi unguwa, ya dauki kudi ya bata, tun sanda zai fita da safe yaga tana ta shiri abinta. Bata cika shisshige mishi kamar da ba, auren shi da Mero ya canza abubuwa da yawa a tsakaninsu, kamar ta rage fada, ta rage magana, ta rage kula dashi, ta rage abubuwa da yawa da bai san ya saba dasu ba sai bayan ta janye masa haka. Idan ya kalleta kamar yau sai yayi kewar wadannan abubuwan. Lubna sufyan Hausabook.com 361 Sabo abune mai wahala, ko itace da girki tana iya kawo masa abinci tace masa zata duba yara, sai ya bita wasu ranakun sannan zata dawo masa, yana iyajin tana kokarin tashi ta koma dakinta, sai idan ya riketa ya hanata fitane "Kamar bakyason kasancewa dani yanzun Saratu..." Ya taba fada a wani dare da ya kasa hakuri da rashin kulawarta "Mu biyu gareka Julde. Kuma yaushe ka fara damuwa a abinda nake so ko bana so? Ba kayi auren soyayya ba? Karka damu dani, mu cigaba da zamanmu yanda muka saba" Bayajin surutu daya fada mata ba haka suka saba zamansu ba, bata saba share shi ba, komin yawo ko fadan da sukayi, ko da ba'a jikinshi ba, a gado daya suke kwana. "Yaushe zaki dawo?" Ya tambaya, kallon shi takeyi da mamaki a fuskarta, kamar ba zata amsa ba tace "Sai da yamma, zan biya inyi kitso" Lubna sufyan Hausabook.com 362 Kai ya jinjina yana mata sallama, da Talatu bata nan, yanda yakejin jikinshi yayi masa nauyi haka. Haidar zai dauka ya kaishi wajen Daada, ya dawo ya wuni manne da Meron shi. To itama tace masa zata danje gidan Baabuga, ba jimawa zatayi ba, dubiya zatayi ta dawo. Shisa kanshi tsaye yayo gida wajen sha biyu na rana da nufin ya kwanta ya danyi bacci ko zaiji dadin jikin shi. Da yaga gidan a bude ya dauka ta fita harta dawo, da sallama ya shiga, yaga tsakar gidan babu kowa, kuma ba'a amsa mishi ba, saiya bude dakin shi ya shiga. Kayan jikin shi ya rage ya karasa kan gado ya kwanta yana maida numfashi hadi da lumshe idanuwan Da yaji an tura dakin ma, bai bude idanuwan shi ba, a tunanin shi Mero ce, wani numfashi ya sauke yana mika hannun shi "Yau banajin dadin jikina Mero" Ya furta, yana bude idanuwan shi babu shiri lokacin da ta saka hannunta cikin nashi, saboda yaji ba Mero bace ba, ba yatsunta bane ba, zai gane su a cikin dubban mata ko da idanuwan shi a rufe suke. Yanda idan ta sakala su cikin nashi Lubna sufyan Hausabook.com 363 yakan jisu cif-cif, kamar an auna ne kafin a halitta mata su, dai-dai rikon shi, tsayinsu yanda zasu kwanta a cikin nashi ya rike yana wasa dasu, yana kallon fararen kumbuarta da baka rabawa da jan lalle. Kokarin fisge hannun shi yake, saita zauna kan gadon, jikinta yana taba nashi da yaji ya mutu murus "Meye haka Talatu? Me yake damunki?" Murmushi tayi, idan tace ba da nufin tazo taga mijin da Mero ta aura ta shigo Marake ba zatayi karya. Tun ranar da suka hadu ta gansu, taga kyawun da suka kara kamar ba'a karkara suke ba take son taga wanda ta aura haka. Mero bata da muni, amman kuma bata da kyawun da Haidar zai biyo haka, yaro bulbul dashi, ga hanci, ga idanuwa, ga wani danbaki karami kamar an shafa mishi jambaki. Kowa Mero ta aura me kyaune, dansu ya nuna haka, kuma yanayin sutturarsu da yanda take ta ciro kudi tana bayarwa ana siyo musu abin bukata, ba wa kanta da yaron ba kawai harda yan cikin gidan ya tabbatar mata da ba mai rufin asiri bane ba, maikudi ne. Lubna sufyan Hausabook.com 364 Sai dai bata hango Julde bane ba, wannan danfulanin da taso kwacewa a hannun J-town wasu yan shekaru baya. Ta hango ta rikitashi da salonta, ta yaudare shi da kissosin da ta koya har sai ya bar matar shi idan yana da ita ya nemi aurenta, saboda yana da kyau, yana da wani irin kyau da ta kwana biyu bata ci karo da mai irin shi ba. Ta ga ya daina yin kitso da gashin shi yanzun, amman lokacin da ta ganshi akwai kitso akan shi, kitson daya kara masa kyau. Yanzun da ta ganshi babu kitson kuma sai taga kamar yafi kyau, ya kara girma, shekarun sunbi jikinshi sunyi wata irin kwanciya data kara fito da halittar shi ta cikakken namiji. Sai bata sake ganin shi ba, har tayi aure bayan haduwar su yakan kutsa cikin tunaninta lokaci zuwa lokaci, zai wahala ka hadu dashi ka manta shi da wuri, komai nashi mai tsayawa a raine, ciki harda yanayin mu'amalar shi da ta jima bata goge mata ba. Bata sa ran irin wannan haduwar zasu sakeyi ba. Me yasa Mero zata dinga samun komai ne haka? Me yasa komai zai dinga tafiyar mata dai-dai? Shisa ta tsaneta tuntuni, a makaranta ta kasance mai kokari, Lubna sufyan Hausabook.com 365 kuma duk yanda zata gallaza mata da wahala kaga hawaye a idanuwanta, sai tayi da gaske take ganin gazawar Mero. Ta biyo mahaifiyarta da har yanzun kowa yake yabon halayenta, da ko bayan rasuwarta basu daina kwatancen halinta da duk wani abu da Talatun zatayi ba, duk da ita batayi wayan saninta sosai ba. Da gaske har ranta bata son Mero, so take taga wani abu ya hargitse mata ko yaya ne. Ashe zata samu dama haka "Ganinka ya tunamun da abubuwa da yawa Julde...kasan yanda na dade ban manta ka ba kuwa? Yanda ka jima a tunani na, ashe zan sake ganinka?" Duka maganar nan tanayi ne cikin wani irin sauke murya da ya kara kashe masa jiki. Mace, in dai macece baisan yanda zaiyi da jikinshi akanta ba, ya rasa abinda yake damun shi haka. So yake ya tureta daga jikinshi da take ta sake shigewa, kamshinta ya cika masa hanci, duk ta lakaikaye shi, tana sake dumtsa hannunta da yake cikin nashi har lokacin. Ba zaice ga abinda ta cigaba da fada ba, ba zaice ga lokacin da jikin Lubna sufyan Hausabook.com 366 shi ya fara amsa mata ba. Ya manta komai, babu komai cikin kanshi sai yanayin nan da yakan shiga duk idan ya kebance da mace, yanayin da yake danne komai da kowa, yanayin son sanin yanda take, son gane bambancinta da sauran mata. Shisa baiji shigowar Mero ba, baiji tura dakin da tayi ba "Kanwar mahaifiyata Julde..." Muryarta ta ratsa ilahirin dakin da jikin shi, kafin komai ya tsaya cak, ya kasa motsi, har ta kwance Haidar da yake goye a bayanta ta ajiye shi, ta karasa cikin dakin sosai tana

Chapter 14 of 27