Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Hammadi da Julde ya fita. Sai juyi takeyi zuciyar kamar an watsa mata ruwan kankara, amman kuma zafi take mata maimakon sanyi. A haka baccin wahala ya dauketa cike da mafarkin Bukar da rayuwar da zai tsinci kanshi a ciki a gidan Baabuga. ** Fada idan ka hango rashin nasara a cikin shi babu wani amfani, yanda ranta yake a bace haka take so na Datti ya kasance, amman yaki bata wannan damar, hanyar duk da zatabi don ganin ta bata masa rai ya toshe, daya biye mata, ko sau daya ne ya biye mata su fadama juna maganganu, ta fada mishi tarin abinda yake binne a cikin zuciyarta, ko sau daya ta fada masa bashi da tausayi, bashida adalci, ba kuma ya Lubna sufyan Hausabook.com 128 sonta tunda baya son nata, ko zata samu sassauci. Ganin yanda take wuni da kuncin zuciya, kuka ne abokin hirarta duk dare kafin bacci ya dauketa, yasa ta tsahirta ma kanta, ta dauki shawarar Abu na ta mayar da komai bakomai ba, tunda tana da sauran lokaci kafin a mayar da Bukar din. Ita ta zabi raba shimfida da Datti, ita kuma ta zabi komawa da kanta, baice mata komai ba. Riketa yayi a jikin shi yana jin kukan daya kwace mata, kukan da yasan akan Bukar ne shisa zuciyar shi bata motsa ba, kamar yanda ya fadama Hammadi ne, ba zai rike Bukar ba, kome zai faru ba zai rike yaron da ko sunan shi baya so ya hau harshen shi ba. Abinda duk Dije take tunanin zatayi don ya sama mata saukin fahimtar hakan zai barta tayi, tsayin lokacin duk da zata dauka zai bata shi, zai koma gefe ya jirata har ta gama ta dawo wajen shi kamar yanda tayi yanzun. Duk da har aka kwana biyu ya kasa sakin jikin shi, gani yake kamar zata koma Dijen nan da bai sani ba, Dijen nan da bata shakkar neman rigima da shi, Dijen da bai taba gani ba sai Lubna sufyan Hausabook.com 129 wannan karin. Amman shiru, hidima taci gaba dayi tana gudanar da rayuwarta kamar babu wani abu a ranta, har saida ya saki jikin shi. Rayuwa suka cigaba dayi yanda suka saba. A satin daya kama na bikin Hammadi da Pendo ne Dije ta tabbatar da cikine a jikinta, ciki me saukin laulayi. Da ta fadama Datti yayi murna ba kadan ba "Karka fadama Hamma dan Allah, saboda Adda...zatayi murna na sani, amman zai zama kamar muna tuna mata abinda ba zata samu bane, ga maganar bikin nan da dalilin shi" Kallon ta Datti yayi "Idan ban fada yanzun ba, zai fito kowa ya gani. Meye amfanin kin fadin?" Dan murmushi tayi "Nasani, abari sai ya fito din sun gani ni dai" Numfashi yaja, numfashin nan daya kanyi idan magana bata gama zauna masa ba, a wajen shi maganar cikinta abin farin cikine da yake son fadama duk wani da zai saurara batare da kunya ba, baisan me yasa take son boyewa ba. Idan ya Lubna sufyan Hausabook.com 130 samu ai kamar Hammadi ne ya samu, haka Hammadin ya fada da bakin shi "Dan Allah" Ta sake roko, ya dauki wasu dakika yana juya maganar kafin ya daga mata kai a hankali. Ashe kuwa gara ma da tace masa subar maganar a tsakanin su, dan cikin ba mai zama bane ba, a cikin watan shi na uku ta wayi gari da zazzabi mai zafi, zazzabin da bata kwana da cikin jikinta ba, amman ta sake kwana ta tashi da shi na tsayin kwanaki hudu, saboda barin ya jigatata. Batasan ko Abu ta gane ba, ta dai dafo mata zuma da kayan kanshi a ciki, ta bata a dan kwano tace tayi kokarin shanyewa da duminta. Sai da tayi mata hakan na kwana uku, cikin ikon Allah sai taji dadi, har karfin jikinta ta samu, kamar hadin zumar ya wanko duk wani sauran ciwo da take tare da shi. Har kasan ranta tausayin Abu ne fal, yanda take kokarin ganin ta saukakama kowa komai duk da rayuwarta da take a hargitse, hargitsin da bata zubar da digon hawaye ko daya a gaban Dije ba, itace ma tayi kuka ranar da dangin Pendo suka Lubna sufyan Hausabook.com 131 tafi da ita saboda irin maganganun da suka dinga yi da habaici saboda ta samu rabo da Hammadi "Allah daya bata bai manta dani ba Dije...idan rashin haihuwar shine alkhairi na akan haihuwar fa? Naji dadi da kasa bata rufe mun ido ba sai da naga rabon Hammadi... Hakan ma ya isheni" Ta fadi da wani murmushi a fuskarta daya kara karyama Dije zuciya. Sai dai wauta ta tunani irin na dan Adam da kan shafe giftawar mutuwa a cikin tsarin al'amura na yau da kullum, duk kuwa da sanin cewa zata iya sada zumuncin ta da takanyi batare da sanarwa ba. Ko gudun da watannin sukayi baisa sun kawo komai a ransu ba, samu da rashin da ya samu Abu, ya same su dukkan su, saboda Dije tayi kuka fiye da Abun, mutuwar saita tuna mata da zafin da ta dandana itama, komai na dawo mata kamar ranar ne ya faru. Wannan ma baisa sun hango mutuwar Pendo ba. Pendo da jinin Dije bai hadu da nata ba, Pendo da ko da mutuwarta ta daki Dijen fiye da yanda Lubna sufyan Hausabook.com 132 ta zata baisa taji ta sota ba, ta kasa goge laifukan dangin Pendo, kalar rashin darajar da suka yima Abu wani abune da ko ita kadai ta tuna sai wani daci ya mamaye zuciyarta. Da sun hango rayuwar Pendo ba mai tsayi bace kamar yanda suka dauka da sun sassauta burin su. Cikin da suke ta hauka akan shi, rabon da suke gani zai zama tsanin da zai mallakama Pendo duk wata ragama ta rayuwar Hammadi ga shi nan, ga 'yar nan, amman babu Pendo. Abun da suke ki dole idan lokaci yayi Hammadi ya karbi 'yar shi rikonta a hannun Abu zai dawo. Tun kwana biyu da rasuwar Dije bata jin dadin jikinta, dakyar ta iya zuwa sadakar uku, har Datti na mata fada kan cewa kukan da tayi ne yasa mata rashin lafiya. Sai daga baya suka gane laulayi ne, wani irin laulayi da bata tabayin irin shi ba, ko ruwa tasha saiya dawo. Datti na gama shiryawa yake zuwa ya kira Abu, sai yaga ta dagata, ta kamata sun tafi gidanta sannan zai rufe gidan ya fita, anan take wuni kwance, saiya dawo da dare zai biya ya dauketa, ranaku daidai ne Julde yake kwana a wajen su tunda ta samu cikin, shima idan Datti ne ya dauko shi, Lubna sufyan Hausabook.com 133 saboda ita bata da karfin kula da kanta ma balle kuma Julden. Kulawar su kacokan hannun Abu ta koma da takeyinta kamar bata san ciwon jikinta ba. Tasan hakan gidansu suka gani shisa suka kasa samun zuciyar cewa zasu dauketa a yanayin wahalar da take sha. Wannan damar kuma Baba ya samu ya dauki Bukar ya mayar gidan Baabuga, a cewar shi lokaci yayi, idan ma ba'a mayar da shi yanzun din ba gaba za'ayi. Haukane kawai Dije batayi ba, saboda Baba ya zabi lokacin daya dace, lokacin da ba zata iya tabukama kanta komai ba balle harta iya yin wani abu akan Bukar. Damuwar ce ta kara mata ciwo na daban, ga rashin cin abinci, saiya zamana har cikin ya shiga wata na biyar bata da karfin kirki, yawan aman ya tsaya, amman kukanta bai tsaya ba, damuwar da take ciki banda karuwa babu abinda takeyi. Hankalinta da duk na wani makusancita ba'a kwance yake ba "Ka dubo mun yarona Datti, dan Allah ka dubomun halin da yake ciki" Lubna sufyan Hausabook.com 134 Ta roka wani dare da take jin numfashinta yana barazanar tsayawa, kukan da takeyi kamar zata shide yasa Datti cewa "Zan biya in dubashi da safe...zan duba shi Dije, ki daina kukan nan kinga baki da lafiyar kirki" Tunda yake bai taba ganin irin wannan lamarin ba, wacce irin kaunace take yiwa Bukar din haka? Wacce irin kaunace da ta danne wadda takeyiwa kanta, ta danne wadda take yi musu, akan Bukar shi kadai tana kokarin halaka kanta da abinda yake cikinta, shi da Julde ta jefa su cikin wani hali. Babu abinda hakan yayi banda kara masa tsanar Bukar, tsanar duk wani abu daya dangance shi. Ko kadan bai niyyar zuwa ya duba mata Bukar ba, amman saiya tsinci kanshi a kofar gidan Baabuga da safen daya fita, harma da aikawa akayi masa sallama da Baabuga da bayan sun gaisa ya rasa ta inda zai fara tambayar shi Bukar. "Dije tace in duba mata ya Bukar?" Ya fadi yanajin wani daci a ranshi, murmushi Baabuga yayi, har ga Allah in zai fadi gaskiya bai san ya Bukar din yake ba, yara ne a gidan shi Lubna sufyan Hausabook.com 135 sun fi ashirin, wasu ma rabon daya saka su a idon shi anfi sati, sanda zai fita ba tsayawa yake ya duba su daya bayan daya ba, haka idan ya dawo. Da daddare Baban Dije ya same shi ya mika masa Bukar, bawai ya manta sun sami rabo da Dije bane ba, koba komai bai taba hada shimfida da matar da ta kasa gogewa a tunanin shi irinta ba. Bai dai kawo ma ranshi zasu mayar masa da Bukar ba sanin cewa suna da halin da zasu rike shi. Ya karba babu wani musu, yana mamakin kyawun yaron da irin sutturar da aka hado shi da ita, tun kuma da yaje ya mika ma uwargidan shi, bai sake bi takan shi ba. "Yana lafiya" Ya amsa yana kallon Datti daya daga kai, harya juya sai kuma ya dawo. Hannu yasa a aljihu yana zaro kudi, ya diba ya mika ma Baabuga "A sai masa dan wani abu shida sauran yan uwan shi" Hannu Baabuga yasa ya karbi kudin dan yana da bukatar su. Yayi ma Datti godiya. Ko daya koma gida da dare, akan tabarma ya samu Dije zaune ta saka fitilar kwai a gaba tana kallo kamar ta Lubna sufyan Hausabook.com 136 samu majigi, tana jin sallamar shi bata ma amsa ba tace "Ya Bukar din? Ka gan shi?" Karasawa yayi ya zauna a gefenta, yana kallon yanda kasusuwa suka fito a fuskarta saboda ramar da tayi, da zai iya da yayi mata karya ko dan ta samu saukin da yaga tana nema "Bangan shi ba, amman Baabuga yace mun yana lafiya. Na kuma bashi kudi..." Kai ta daga tana kai hannu ta share hawayen da ke shirin zubo mata. "Yace yana lafiya" Ya sake jaddadawa, kan dai ta kara daga masa, zuciyarta na kuna, da bata zauna gidan Baabuga taga rayuwar da akeyi ba da kila sai hankalinta yafi kwanciya. Ko nama Datti ta siyo ta kai bakinta sai Bukar ya fado mata, tasan tunda aka kaishi gidan baiji dandanon nama a bakin shi ba, gidan Baabuga yayi kama da gidajen da ba'a ganin nama da wani abu mai galihu sai shekarashekara, a lokacin bukukuwa na sallah. Iya abinci aka tsaya Bukar yana cikin garari, balle Lubna sufyan Hausabook.com 137 suttura da wajen kwanciya, ga rashin kulawar da tasan yana ciki. Shisa babu wani horo da namiji zai yima mace daya wuce ya saketa ya kuma rabata da yaranta, saboda gabaki daya nutsuwarta ya rabata da ita, tunanin halin da suke ciki ba zai taba barinta bacci me kyau ba. Dije ta daina kokarin ganin wani ya fahimce ta akan maganar Bukar, tana dai jin kamar karshen duniyarta ne ya zo. Kamar tana samun karfin bude idonta ne da duk safiya don ta haifi abinda yake cikinta kafin ta rufe shi na har abada. Har Abu daina kokarin yi mata maganar Bukar tayi saboda "Hmmm..." Kawai take iya cewa sai hawaye. A haka randa cikinta ya shiga wata tara da kwana biyu ta fara nakuda a tsai-tsaye, nakudar da bata taho mata gadan-gadan ba saida ta kwana hudu tana wahala. Ranar ma wuni tayi ta sake kwana, sai da kowa ya fara karaya da lamarin, Hammadi da yake da raunin zuciya sai da yayi kuka duk da bai ganta ba, Abu ya gani da yanda tayi zuruzuru saboda tashin hankali, idanuwanta duk sun Lubna sufyan Hausabook.com 138 dashe alamar yawan kukan da ta sha, suna hada ido ta girgiza masa kai alamar har lokacin babu wani labari. Kukan jinjiri ya fara sanar musu da ta sauka, saida Datti ya tsugunna yana wani irin mayar da numfashi, da gudun Abu ta fito take fada musu mace ce aka samu, an kuma fito musu da ita bayan an mata wanka, a karo na farko da Datti yayima Hammadi kara yana nuna ma Abu alamar da ta bashi ita ya fara dauka. Yaji dadi sosai, murnar shi bata boyu akan fuskar shi ba, daya mika ma Datti ita idanuwa ya kura mata yana kallo, Julde yayi kyau, har aka dinga maganar a cikin kauyen, amman baiyi kyau irin na yarinyar da take rike a hannun shi ba. Har saida Datti ya kalli Hammadi adan tsorace yana fadin "Kaganta Hamma" Saboda ya tabbatar bashi kadai yake ganinta ba, kai Hammadi ya daga masa "Ance ba'a gane kammanin jinjiri. Amman tana kama da Inna, fuskar Inna nake gani a tata" Lubna sufyan Hausabook.com 139 Saida ya fada Datti ya gani, yaga kamannin, yaga kyawun Innar shi da ba zai manta ba, kyawunta da yake zama abin magana akai duk inda zasu shiga "Shisa zata ci sunan Inna" Datti ya fadi, yana kuma cikawa, yarinya taci suna Karima. "Muna da wani tsayayyen gari kuwa? To in dai za'a tambayeni zan iya cewa Yelwa" Inna ta taba bashi amsa, ba zai manta ba farkofarkon dawowar su Marake ne "Ina ne Yelwa?" Dariya Innar tayi "Wani kauye ne a karkashin Shendam ta jihar Plateau, Innata da Babana anan suka zauna suka haifeni, shine gari na..." Akwai sunaye da yawa da zasu iya yima Karima alkunya da shi, saiya zabi Yelwa. Lubna sufyan Hausabook.com 140 "Ki rage fita da yarinyar nan saboda bakin mutane da kuma miyagu, idan bikine ko suna ki barta wajen Abu, idan tare zaku je ki biyo ki kawota gida" Shine abinda Innar A'i tace mata lokacin da taje yawon arba'in ta kuma kwance goyon Yelwa tana mika ma Innar A'i da ta karbeta tana kura mata idanuwa. Ko ita haka take saka Yelwa a gaba tana kallo, tana jinjina ma ikon Allah da ya fitar da halitta kyakkyawa kamar Yelwa daga jikinta. Julde na da haske, Yelwa ma haka, amman farin yarinyar wani irin sirki gare shi da zakayi zaton ta hada jini da buzayen kasar Agadez "Mahaifiyar babana buzuwa ce" Datti yace mata randa tayi maganar, sai dai da alamar wasa a muryar shi da kuma dariyar da yayi bayan maganar, sai ta kasa tantance tsokanarta yakeyi ko kuma hakikanin gaskiya yake fada mata, ga kan Yelwa ya cika da gashi zaka rantse basuyi askin sunan da Abu tace Lubna sufyan Hausabook.com 141 "Wanzamin nan bashida tausayi ko kadan, jibi yanda ya sude kan yarinyar nan kamar sabuwar kwarya dan Allah" Har suka dinga mata dariya saboda tayita mitar dake nuna alamun da an biye mata ba za'ayi askin ba. "Allah ya kare rayuwarki daga mugun baki" Innar A'i ta fadi tana sake juya Yelwa, watakila da a wani wajen Dije ta haihu ba gida ba, zatace ko sunyo musaya ne sun dauko yar data hada iri da larabawa, amman a gabansu Yelwa ta fado bayan doguwar nakudar da mahaifiyarta tasha "Kyauta, kyautar Allah ce kawai" Ta gasgata zantukan Abu, Abu da bata iya boye tsantsar soyayyar da take ma Dije da ahalinta a gaban kowa. Dije kuwa dariya takanyi idan suna irin maganganun nan, to saboda gudun bakin mutane kuma sai ace ba zata fita da Yelwa ba, miyagun da ake cewa har tsuntsaye suna zama su dira gidan da suke so, su lashe kurwar wanda tsautsayi ya giftawa, boyon Yelwa na me zatayi musu? Tunda dai zasu iya rikida su shigo gidan, Lubna sufyan Hausabook.com 142 ko ma ba'a tsuntsaye ba, sun kawo talla har cikin gida, kuma ba ganewa zatayi ba. Da zuciyarta daya take fita, abinda zai faru tasan ba zasu tsallake masa ba. Tayi niyyar sai tayi isha'i zata wuce gida, shisa ta kara mike kafa, bata hango Baba zai rushe mata wannan shirin ba, sai da yammaci daya shigo gidan ya ganta, yayi tsaye saida yaga ta mike ta goya Yelwa, tayi ma su Innarta da Innar A'i da yake ma fadan suna kallon yammaci yayi har haka suka bar Dijen ta sake mike kafafuwa maimakon su korata gida. Harta kai soron gidan kafin ta karasa ficewa tana jiyo shi bai bar fadan ba, murmushi ta danyi tana kama hanyar da zata kaita gidanta. Kafin tunanin Bukar kamar ko da yaushe ya diro mata yana danne komai. Idan tace komai harda kafafuwanta da tunanin ya jagoranta har kofar gidan Baabuga da bata farga ba sai da tasa kai ciki da sallamarta. Hararar da uwargidan shi Nana ta watsa mata nasa wani abu ya tsirga mata, saboda har ranta bata fito daga gida da tunanin kafafuwanta zasu daukota su kawo gidan Baabuga ba, zuciyarta ce, da kuma son ganin Bukar da takeyi Lubna sufyan Hausabook.com 143 "Ina wuni" Ta gaishe da ita cikin harshen hausar da tasan tana ji, amman sai ta tsaya da kullin gyadar da takeyi tana kallonta kamar bata tabajin yaren da tayi magana da shi ba "Ya kuke? Ya yara? Daman nazo wucewa nace bari in shigo mu gaisa in kuma duba Bukar" Wannan karin Dije tayi maganar cikin harshen fulatanci tana yawo da idonta cikin gidan da yake kaca-kaca, kwantsin kayan wanke-wanke ko ina, harda wata miyar kuka mai munin gani da ta zube a kasa, bakuma a damu da ko kasa a zuba mata ba, an bar wajen harya bushe kudaje sunyi dandazo suna shagalinsu "Lafiya... Baya gidan to" Wani rugugi Dije taji cikin kirjinta "Baya gidan? Yana ina? Ina yaje?" Ta jero tambayoyin cikin taradaddi "Ina zansan inda yake ko inda yaje? Sun fita wasa da yara" Lubna sufyan Hausabook.com 144 Nana ta amsa a zafafe, Dije bata bi takanta ba ta juya tana nufar inda ta fito, dogon tsaki da zagin da Nana ta rakata dashi na isa kunnenta, amman bai mata zafi ba, batajin akwai wani abu da za'a fada ko ayi mata a lokacin da zataji zafin shi kwatankwacin zafin da takeji a kirjinta a lokacin. Bukar take hangowa a yawon gantali, irin gantalin da yaran gidan Baabuga sukeyi, ta tuna ranar da aka zabga da zafinta bai gushe ba har yammacin da take gabannin faduwa, ta kuma tabbatar zaiyi wahala idan da takalma a kafar Bukar, ko yaci abincin rana ko baici ba, wannan duk wani abune da bata da tabbas akai. Hannu takai tana share zafafan hawayen da suka zubo mata, idan tabi ta bayan gidan Baabuga zaifi mata saukin zuwa gida, a maimakon tabi ta hanyar da ta fito, kusan zai zamana kamar tayi zagaye. Hawayenta sun kasa daina zuba, zuciyarta ta cunkushe da tunani kala-kala, gefen mayafinta tasa ta share hawayenta da suke hana mata ganin hanya da kyau, kiris ta fada kwatar dake bayan gidan Baabuga, bayan da tayi tana kusan take wani dan yaro da yake kwance jikin katangar gidan, Lubna sufyan Hausabook.com 145 yanayin kayan jikin shi da daudar su na nuna alamun cewa almajiri ne. Kai ta girgiza kawai tana tsanar iyayen da suka turo karamin yaro kamar wannan almajiranci. Har tayi gaba ta dawo, bambancin rayuwar gidan Baabuga da wannan shine kawai akwai tabbacin zasu ci abinci, ko basu koshi ba za'a dafa sau ukkun nan, ko babu dadi rana bata taba fitowa ta fadi ba'a dora tukunya ba. Dan rankwafawa tayi tana kamo dantsen hannun yaron, zafin zazzabin dake jikin shi na ratsa kayan shi yana shiga tafin hannunta "Kai baka da lafiya ne ha..." Sauran maganar ta makale mata bayan ta dago shi gabaki daya ta kalli fuskar shi, taga fuskar Bukar ko abinda yayi saura a fuskar tashi saboda bakin dauda da yayi, sumar shi da yake da yalwarta ta cakude kamar sabon mahaukaci, kafafuwanta taji sunyi sanyi har suna barazanar kasa daukarta, bangon wajen ta dafa tana kokawa da numfashin da take ja tana fitarwa a wahale "Bu.. Bukar" Lubna sufyan Hausabook.com 146 Ta furta tana rabo hannunta daga bangon ta hada duka biyun ta tallafi fuskar shi tana dubanshi, tana duban gudan jininta, tana jin wata tsana ta taso mata tana zama a kirjinta, amman bata da wanda zata jefa da wannan tsanar, sai dai ta rarrabata a cikin jikinta, saboda itace sanadi, ita tabar rayuwar Bukar haka, itace bata tsaya tayi fada yanda ya kamata da Datti akan rike Bukar din ba. Dagashi tayi tana sabar shi a kafadarta, bata taba ganin nisan gidanta irin yau ba, harta karasa kuka takeyi, duk da maimakon ta shiga gidanta, gidan Abu ta shiga "Adda kinga Bukar.... Kalli Bukar dina Adda..." Dije ta karasa maganar wani irin kuka na kwace mata, tasowa Abu tayi tana karbar Bukar daga hannunta, zuciyarta na wani irin dokawa ganin yanda yaron yabi jikinta kamar babu numfashi a jikin shi, karasawa tayi ta kwantar dashi kan tabarma, jikinta ko ina yana bari, ruwa ta dibo ta dawo ta zuba a hannunta tana shafa ma Bukar din, zuciyarta take ji a tafin hannunta saboda tashin hankali, sai da tayi hakan kusan sau hudu sannan yaja wani dogon numfashi yana bude Lubna sufyan Hausabook.com 147 idanuwan shi da sukayi fari qal kamar bashida wadataccen jini. Ita kanta Abu saida ta sauke numfashin sannan ta samu nutsuwar mikewa. Dije ta kama ta zaunar a gefen shi, tana gama tuwo ta cika wata tukunya ta dora kan garwashin da sauran itacen tabarta, tasan komin zafi Hammadi saiya kashe ruwa yake iya yin wanka, duk tsokanar da zatayi masa ba zai kulata ba "Hammadi kana bada maza, dan ruwan sanyin nan ba zaka iya watsa ma jikin ka ba, yanzun da yaqi ne kuma fa?" Idan yana jin biye mata zaiyi dariya yace "Yaqi daban, batun wanka da ruwan sanyi daban, azo yakin mana kigani, sai dai labari yazo miki ana ga Hammadin Abu can yana zubar da maza" Kuma wankan nan biyu a rana sai yayi, kafin ya fita, sai kuma kafin ya kwanta, idan ta cika tukunya ta rufe, sauran garwashin yana rike ruwan zafin har lokacin da zai tashi wankan, saita kwalfe, idan yayi zafi da yawa ta sirka Lubna sufyan Hausabook.com 148 masa, idan baiyi ba tabar masa haka. Cikin wannan ruwan ne ta dauko bokiti ta diba tana sirkawa, ta dawo ta dauki Bukar, sai da tayi masa sabi uku tana tunanin anya tunda aka mayar da shi gidan Baabuga yaron nan kuwa yaga ruwa? Ita kanta saida tayi kwalla ganin daudar da take wankowa cikin kan yaron kawai, daudar da yayi kanta cuta ce ta daban. Cikin kayan Julde ta samu wasa ta saka masa, ta shafa masa mai, sai ga yaro ya fara dawowa hayyacin shi, sai dai duk yayi kasusuwa, ga kuma zazzabin har lokacin bai sauka ba. Duk abinda akeyi Dije na zaune tana sharar kwalla, da ido kawai take bin Abu, harta sake hada wuta ta dama masa kunun kanwa da yaji sikari, dan tasan da wahala ya iya cin wani abinci mai nauyi, da kanta ta dinga bashi, baifi ludayi biyar ya sha ba ya girgiza mata kai yana komawa ya kwanta. Bata matsa masa ba "Ki tashi kiyi alwala..." Ta ce ma Dije da bata musa ba ta mike, tana tuna Yelwa na goye a bayanta, da yake bata da rigima, Lubna sufyan Hausabook.com 149 in kaji kukanta yunwa ce ko kuma an tsomata a ruwa za'ayi mata wanka. "Ba zan mayar dashi ba Adda, sai dai in hakura da auren Datti, amman wallahi ba zan mayar dashi gidan Baabuga ya mutu ba" Ta karasa maganar tana goge fuskarta da bayan hannunta, jin saita shiga bayi yasa ta kwance Yelwa tazo ta kwantar da ita. Ko da tayi alwala ta zo ta gabatar da sallah, ji tayi ita kanta bata yadda da ingancin sallar da tayi ba, saboda rabinta tunanin yanda zata fuskancin Datti ne, shisa ta kara sakewa, zaune tayi a inda tayi sallar har aka kira isha'i, ta mike ta gabatar da ita. Ko da Abu tayi mata tayin abinci kai ta girgiza mata, rikicin da take ji ya gama cika mata ciki, bata da wajen saka wani abu. Balle da taji sallamar su Dattin, muryar shi na danne ta Hammadi, alamar yana cikin nishadi, sai taji ta kara harzuka. Saboda Hammadi ne kawai tayi musu sannu da zuwa, ko Julde da yazo ya fada jikinta daga shi tayi, girman Hammadi a idanuwanta na hana ta wanka ma Julde mari saboda ta fara batama Lubna sufyan Hausabook.com 150 Datti rai, sai yafi biye mata ko zata fada masa maganganun da zaisa zuciyarta ta sauka. "Dagani dalla...kai baka san ka girma ba" Ta fadi tana sake ture Julde, da yake yana da kulafaci baiyi zuciya ba ya sake binta. "Waye wannan a kwance?" Datti ya tambaya yana zama kan tabarmar da Abu ta shimfida musu "Kai dai kuci abincin tukunna" Ta fadi da sauri tana katse Dije da ta numfasa ta bashi amsa, bai musa ba, abincin ta zuba tana kawo musu. Suna ci suna hirar da Datti yake kokarin sako Dije ciki ganin yanda ta koma gefe kamar bata gidan, hakan da yayi baisa ta kula shi ba, zuwa yanzun sai dai yaba wani labarin halayenta, ranta a bace yake ba sai ta fada masa ba. Bai dai san dalilin bacin ran bane, yasan bashi bane tunda lafiya lau sukai sallama da safe. Har sai da ya wanko hannun shi ya dawo ya zauna, ya dauki kwanon ruwa ya kafa a bakin shi kenan ya tsinkayi muryarta Lubna sufyan Hausabook.com 151 "Bukar ne na dauko, bashi da lafiya, na dauko dana, ba kuma zan mayar da shi ba..." Tayi maganar tanajin wani daci a makoshinta, saida yasha ruwan shi sannan ya sauke kwanon yana kallonta, fitalar kwan dake ci a tsakar gidan bata haska masa fuskarta yanda yake so, amman yana fatan ita tana ganin fuskar shi, saboda taga yanda maganarta ba mai yiwuwa bace ba, ta karanci fuskar shi, ta kuma gani a idanuwan shi ba zai zauna da Bukar ba "Mayar da shi kuwa zakiyi, bashi da lafiya ba matsalata bane ba, na rigada na gaya miki ba zan rike shi ba, wallahi babu wanda ya isa yasani rike dan Baabuga" Ya karasa maganar yana mikewa ganin Hammadi na shirin saka musu baki "Idan ba zaka rike dan Baabuga ba, dana fa? Datti dana fa? Ko ka manta ba dan Baabuga bane kawai, nima dana ne, Bukar dana ne kamar yanda yake dan Baabuga, idan ba zaka rike dan Baabuga ba, ka rike nawa tunda nima ga naka nan ina rike da su..." Lubna sufyan Hausabook.com 152 Wata dariya Datti yayi, dariyar da bata da alaka da nishadi, asalima kirjinshi ya dauki wani irin zafi da maganganun da tayi "Dije ni zaki gayawa Bukar danki ne ke da Baabuga? Ni zaki kalla kina fadamun ke da Baabuga dan ku ne? Ni?" Rigar shi Hammadi ya dan kamo "Ka zauna Datti, ka zauna muyi magana gabaki daya..." Mikewa Dije tayi itama, idonta ya rufe, ta dauki kunyar Hammadi ta ajiye a gefe, idan Bukar din ya mutu ta kula ita kadai take da asara ba Datti ba "Sai me dan na fada maka? Karya nayi? Gani nayi kamar ka manta shisa nake tuna maka... Yarone na dauko shi ba zan mayar da shi ba kuma wallahi, sai dai ka sawwake mun ni da shi duka sai mubar maka gidanka, in dire maka naka yaran ka nemo wadda zata rike maka su..." Sosai yake kallon Dije yana mamakin yanda ta saka idanuwanta cikin nashi tana fada masa maganganun nan,

Chapter 6 of 27