Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
bambaro Talatu da take mata murmushi daga jikinshi da wani irin karfi da bata san tana dashi ba, ta wanke mata fuska da marin da ya gigitata. Kiciniyar kwacewa takeyi amman rikon da Mero tayi mata bana wasa bane ba, a girman jiki ta fita, haka a shekaru, shisa wannan karfin nata yake bata mamaki, sau nawa tana zaneta. "Mijina? Duk abubuwan da kike so ki hada dani tun tasowata bai isheki ba, saida kika biyoni Lubna sufyan Hausabook.com 367 kina son hada miji dani, ubanme na tsare miki? Me nayi miki haka?" Mero take fada cikin fitar hayyaci, ashe labarin haukan kishin mata da takeji wasa ne, danyen aikin da take tur dashi idan ance sun aikata sanadin kishi, tsari ya kamata ta nema dashi tunda gata yau idonta ya rufe, abinda zata illata Talatu take nema, ta shaketa tana jijjigawa tana kai mata duka duk inda zata samu a jikinta. Dakyar Julde ya iya mikewa yana rike Mero ya samu ya kwaci Talatu da ta fice daga dakin da gudu, bakinta da hancinta duk sun tara jini, sai dai dawa Allah ya hada Mero idan ba Julde ba. "Me nayi maka? Ban so ka ba? Ban baka dukkan zuciyata ba? Banyi hakuri da matan da kake bi a waje ba? Sai ita? Kanwar mahaifyata? Kanwarta? Wacce macece ba zaka bi ba Julde? Ka fadamun idan akwai macen da ba zaka iya bi ba idan kaganta!" So yake ta nutsu, amman takiya, duka take kai masa inda duk ta samu, ga wani irin kuka da takeyi kamar zata shide, jikinshi babu inda baya bari saboda bai taba ganin tashin hankali irin Lubna sufyan Hausabook.com 368 wanda yake gani ba yanzun, saiya daina kokarin riketa da kare dukan da take masa, kamar hakan take jira ta sake shi "Ba zan iya ba, na hakura da kai, ko kai kadai ka rage a duniya na hakura da kai Julde, ko sonka zai kasheni na hakura da kai" Tayi maganar tana juyawa ta nufi inda kayan shi suke ta dauko wata jaka ta zazzageta, sai take kara daukar kayan da ta zazzage tana mayarwa cikin jakar, rabi sun shiga, rabi basu shiga ba ta jata tana fitowa tsakar gidan da ita, Julde na binta da kallo kamar wanda aka dasa a wajen, ya kasa motsawa "Ga mijinki nan Saratu, ba zan iya zama dashi ba" Take fadawa Saratu da ta shigo gidan, don ta biyo, bata samu mai kitson ba, shisa ta yanke shawarar dawowa gida, kallon Mero tayi, bata taba ganinta a hargitse irin yau ba, duk kuwa da kaya a jikinta harma da hijabi. Jakar da take hannun Mero ta fara kallo, sai ta sake kallonta "Kema da kin hada jakarki zaifi miki alkhairi..." Lubna sufyan Hausabook.com 369 Cewar Mero, sai dai idanuwan Saratu yabar kan Mero, ya koma kan babbar robar da Meron take zuba ruwa a ciki, da abinda taga yana yawo akai, kafin zuciyarta ta tsinko har tafukan kafafuwanta da taji suna barazanar daukarta. "Mero..." Ta kira cikin wata irin murya, batasan ko dan yau bane karo na farko da Saratu ta kira sunanta ko kuma yanayin muryarta bane ba yasa taji ta fisgota daga duniyar tashin hankalin da Julde ya jefata, hankalinta ya dawo jikinta lokaci daya "Mero..." Ta sake kira idanuwanta akan robar ruwan, inda take kallo Mero ta juya ta kalla, zuciyarta ta tsaya na wasu dakika, kafin ta cigaba da dokawa da wani irin yanayi da bana lafiya bane ba, taku biyu tayi, ta tsaya, ta sake takawa, ta tsaya, ba zatace da rarrafe ko da kafafuwanta ta karasa ba, ta ganta a tsugunne bakin robar ne, ta saka hannuwanta cikin ruwan da sanyin shi ya ratsata da wani irin yanayi, ta ciro Haidar, ba don ta taba ganin gawa ba, ko ta riketa da Lubna sufyan Hausabook.com 370 hannunta, amman kallo daya tayiwa fuskar shi tasan babu rai a jikin shi. Da ta tako kafafuwanta a cikin gidan Julde a matsayin mata, sai taji kamar an rusata ne an sake ginata Da suka raya darensu na farko tare da juna sai taji rayuwar su ta hade waje daya Da ta shafa cikinta bayan ta san akwai ajiyarshi a ciki, sai zuciyarta ta sake hadewa da tashi Da ta rike Haidar a ranar farko, sai taga yanda jininta da nashi ya gauraya waje daya Sai mafarkinta ya kara tsayi har tana hasaso har abadan din da zata kasance a tsakanin su Bata san ya ginata bane don ya kara rusata A rana daya ta rasa shi A rana daya ta rasa sauran abinda ya hada su Sai ta kalle shi, ya fito daga dakin yana tsaye, ya kasa karasawa inda take "Yanda kayi mun rami a zuciya, in Allah ya yarda duk lokacin da kake tunanin hankalin ka Lubna sufyan Hausabook.com 371 ya kwanta sai Allah ya aiko abinda zai birkita maka komai Julde..." Mikewa tayi da gawar Haidar a hannunta, tana jin zuciyarta kamar ta daskare a kirjinta, ta karasa har inda yake tsaye ta kamo hannuwan shi ta saka masa shi a hannun shi, wasu hawaye masu zafi na silalo mata "Ka datsemun igiyar da take daure damu Julde...idan na kara mintina a gidan nan mutuwa zanyi" Yanayin da yake gani a idanuwanta, kalamanta, gawar dan da bai taba yiwa soyayyar da yayi masa ba, duniyar duka da ta birkice mishi da wani sauyi da bai hango ba, muryar shi a nisance ta fito "Na sakeki" Numfashi taja, ta saki tana daga masa kai, komai bai dirar masa ba sai da yaga ta nufi kofa, yaga tana shirin ficewa daga gidan "Mero" Lubna sufyan Hausabook.com 372 Ya kira, bata juyo ba, bata da alamar zata juyi din don sauri ta kara, binta yayi da gawar Haidar a hannun shi yana kiran sunanta har waje. Ta tsaya tana juyowa tana kallon shi da gawar da ya rike a kirjin shi Babu wani abu da ya rage a tsakanin su Ya rabata da kanshi Ya ruguzata ta hanyar da batajin zata taba komawa dai-dai Ta rasa komai yau! Tana can tana hauka akanshi har danta ya fita, tasan Haidar, yana da kazarniya, tunda ya fara rarrafe ko wanka takeyi masa saiya kama bokitin ya mike, burin shi ya shiga ciki. Yana son ruwa, doguwar maganar farko da Saratu tayi mata randa ya fita daga daki tana sallah ne, kuma shine karo na farko da Saratu ta taka har kofar dakinta tana daga mata labule, ta ajiye mata Haidar da yake a jike sharkaf da ruwa "Idan sallah zakiyi ki goya shi, ki daina barin shi ya illata kanshi babu kowa a tsakar gida" Lubna sufyan Hausabook.com 373 Ko godiyar da tayi nufin yi bata furta ba Saratu ta juya tabarta a wajen, ashe ruwan da yake so, ruwan da ko a kofi ya gani saiya dauka ya sheka a jikinshi ne zai zamo ajalin shi. "Don Allah ka kyaleni Julde, karka biyoni, karka nemeni, Haidar din daya rage a tsakaninmu gashi nan a hannunka" Bai jita ba, binta yayi yana rikota, ta kuwa juyo ta wanke shi da mari, bai damu ba "Mero don Allah, ba zaki barni ba..." Ya fadi yana dorawa da "Kince mun ni da ke har karshe, shisa na saki jikina Mero, kince halaye na ne karshen abin da zaki duba, me yasa? Me yasa sai da na saki jiki zaki bar ni da kai na?" Hadi da sake rikota, ta shiga kokarin fisgewa tana wani irin kuka da yake fitowa daga lungun zuciyarta. Baya ganin komai sai ita, shisa baiga mutanen da suke fara taruwa ba, baiga yanda matan unguwar keta lekowa ba, ana kallon su. Balle kuma hayaniyar da akeyi, bayaji baya gani, hankalin shi kacokan yana kan Mero Lubna sufyan Hausabook.com 374 "Me kayi mata Julde?" Muryar Datti ta dirar masa, kafin hannun shi daya riko ma Julden kafada, juyowa yayi har lokacin yana rike dam da hannun Mero "Baba ka bata hakuri" Kai take girgizawa, idan bai saketa ba, tabbas numfashinta na gab da tsayawa, so take tabar garin Marake a yau din nan, tayi nisa da Julde da duk wani abu daya taba hadata dashi "Ka sakeni... Baba kace ya sakarmun hannu don Allah" Mero ta karasa fadi tana samu dakyar ta fisge hannunta, da hanzari tabar wajen, binta zaiyi muryar Datti ta tsayar dashi "Me kayi mata?" Juyowa yayi yana kallon Dattin, zuciyarshi na kara rarrabewa a cikin kirjin shi, komai na hade masa waje daya "Bansan kanwar mahaifiyarta bace Baba.. Bansan alakar su ba... Kaga Haidar, baiyi motsi ba tun dazun..." Lubna sufyan Hausabook.com 375 Yayi maganar da wani irin yanayi, kamar wanda ya samu tabin hankali, kallon shi Datti yakeyi "Yanda ka kunyata ni Julde... Allah ya kunyata ka a idanuwan mutanen da suka fi komai muhimmanci a wajenka... Nagode kaji" Cewar Datti yana juyawa, kirjin shi kamar an dora dutse yakeji, sai Julde ya bishi, yana ture mutane batare daya damu mata bane ko maza, har cikin gida inda ya samu Dije a tsaye "Daada kinji me Baba yace? Haka yace Allah ya kunyata ni a idanuwan mutanen da suka fi komai muhimmanci a wajena... Ki bashi hakuri, ba zan kara ba, kinga Haidar ma baya numfashi, Mero ta tafi tabarni, ki basu hakuri Daada, na daina, ki basu hakuri" Karasowa tayi ta karbi Haidar din da yanayin shi ya tabbatar mata da gawace, dankwalin kanta ta kwance tana kwantar dashi ta dago, wani irin numfashi Julde yake fitarwa kamar mai shirin shidewa, saita kama shi ta zaunar "Ba zan iya zama a garin nan ba Daada...tafiya zanyi..." Lubna sufyan Hausabook.com 376 Ya karasa yana kallonta, ba zai iya dora dan yatsa akan abinda yake ji ba, wani irin hargitsi ne da ba zai taba misaltuwa ba, kalaman Datti da na Mero ne suka hade masa waje daya suna shiga wasu wajaje a jikin shi da baisan dasu ba, sosai Dije take kallon shi, sai taji wani fili a inda yake a zuciyarta shima, kamar yanda Bukar da Yelwa suka bari Haihuwa jarabawa ce Kamar yanda rashinta ma yake jarabawa Sai dai bata hango yau ne mafarin sauran hargitsin da itama zai rabata da tushenta ba...! Gidan yayi mata fili, filin da ba'a iya waje take jin shi ba harma da zuciyarta. Idan ta rufe idanuwanta ta tuno lokuttan da take dariya kamar a duniya bata da wata matsala, sai taga kamar a wata rayuwar ce daban, wadda ta sha bamban da wadda take ciki yanzun. Tazarar da take tsakanin wancen lokacin da kuma yanzun tayi nisan da take ganin kamar dorata akan wasu yan shekaru yayi kadan. Saboda babu Lubna sufyan Hausabook.com 377 yanda za'ace farin ciki ya bace daga rayuwar dan adam lokaci daya haka. A yanayin da zuciyarta take ciki ko wani taji yayi dariya mai sauti saita kalle shi, sai taji kamar ta girgiza shi tace masa ya kara yin wata, yayi iya wadda zai iya saboda lokaci na iya zuwa da sai dai ya hasaso dariyar a tunanin shi. Yara uku, uku kacal da suka zame mata jarabawa, masu guda biyar fa? Takwas, goma, maza masu ashirin harda doriya fa? Addu'ar da take yiwa iyayenta da kasa ta rufe ma idanuwa saita ninku, wanne fama sukayi da ita kafin su aurar da ita, haka samun yara yake da wahala daman? Lokacin da ta kafe kan auren Baabuga, abubuwan da Baba ya dinga hango mata ashe shi kadai yasan me yake ji a zuciyar shi. Kokarin da iyaye sukeyi akan 'ya'yan su nagartattu da wanda suka baude hanya duka ba zai taba misaltuwa ba. Su kuma yaran ba zasu taba gane girman wannan kokarin ba sai ranar da suka haifi nasu, idan sun haifa din ma an jaraba su ta hanyar wannan yaran. Duka yaushe ne take rike da hannuwan Yelwa, yaushe ne Yelwar bata iya aiwatar da komai Lubna sufyan Hausabook.com 378 batare da taimakonta ba, yaushe ne Yelwar ta kalli cikin idanuwanta kamar ta dauki zantukanta, sai ace ta nemeta ta rasa, ba kuma ta da wata dabara ko abu da zata aiwatar akan hakan. Ta yaya zuciyarta zata warke daga wannan ciwon? Ta ina zata fara? Rabonta da baccin kirki harta manta, cike suke da mafarkai mabanbanta akan Yelwa da halin da take ciki. Idan ta farka ma itace a ranta, tilon 'yarta da batasan inda take ba. Kamar bata da wannan ciwon a zuciyarta, kamar Julde bai sani ba ya zabi ya kara mata wani tunanin akan wanda yake cunkushe da ruhinta. "Tsakanin Kano da Marake wasu awanni ne da ba zasu hanani zuwa ganinki ba Daada..." Ya fadi yana rike da hannayenta "Idan nace karka tafi zaka fasa? Kai kadai ka ragemun da nake gani, kai kadai nake gani Julde" Lubna sufyan Hausabook.com 379 Shine abinda taso tace masa, shine abinda ta fada a cikin kanta, amman harshenta yayi mata nauyi "Inajin Marake ne mafarin komai, Daada inajin idan har ina cikin kauyen nan zuciyata ba zata samu sararin sauyin da nake bukata ba... Ina so in shaki iska a wani waje da baya zagaye da tunin akan abubuwan dana rasa... Bana so in cigaba da kallon kofa ina jiran mutanen da banda tabbaci akan dawowar su" Ya zata hanashi tafiya bayan ya fadi haka? Bayan har a cikin idanuwanshi da suke cike taf da hawaye tana iya hango zuciyarshi da take a karye, a karye da abubuwan da suka fi karfin shekarun shi. Kwananshi uku a cikin dakinta, alwala ma sai dai ta kawo masa ruwa da roba yayi a cikinta, inda ya idar da sallah nan yake komawa ya kwanta, banda ruwa, abinci sai tayi da gaske zata samu ya tashi yaci cokali biyu ko uku ya sake komawa ya kwanta. Idan ta leka fuskar shi, idanuwan shi a rufe suke, badon hawayen dake bin gefen fuskarshi ba, zata dauka bacci yakeyi. Lubna sufyan Hausabook.com 380 "Nagaji, nagaji sosai Daada, kibarni in kwanta" Bata hanashi ba, amman a cikin kwanaki ukun nan ko wanka baiyi ba. Ranar na hudun ma Saratu ce ta shigo, itama duk tayi zuru-zuru kamar wadda taga wani abu daya firgitata. Dakin Daada ta nuna mata, ita ta shiga, takai awa biyu a ciki, sannan ta fito, kamar ta kara ramewa fiye da lokacin da ta shiga dakin. Abinda Daada bata sani ba shine da Saratu ta shiga, ta dafa Julde da yake kwance yafi sau goma yana ture hannunta "Ka tashi, ba su kadai kake dasu ba Julde... Bashi kadai bane yaronka, akwai Salim, akwai Fadila... Ka tashi don Allah, basu kadai kake dasu ba, basu kadai suke bukatarka ba..." Ta karasa muryarta na karyewa, tana riko hannun shi da yake son kwacewa, dakyar ta iya kamo hannun shi, ta dora a cikinta da kamar hakan yake jira abinda yake ciki ya motsa har yaji motsin ta cikin tafin hannun shi "Ya kake so muyi? Idan muka rasaka ya kake so muyi?" Lubna sufyan Hausabook.com 381 Mirginowa yayi ya juyo, saita dago shi, baiyi kokarin kwacewa ba harta dora kanshi a cinyarta "Zuciyata na mun ciwo... Saratu zuciyata namun ciwo" Ya karasa dumin hawayen shi na gangarawa har kan cinyarta "Ina nan, kayi kuka idan zakaji sanyi, kayi duk abinda zai kawo maka sauki, amman karka barmu" Kukan yayi, a jikinta. Kuka yayi kamar karamin yaro, kuka yayi kamar ba namiji ba, namiji mai mata da yara. Kuka yayi da tunda yake duniya bai taba yin irin shi ba, har a kasusuwan jikinshi kuma yake da yakinin daga ranar zai wahala ya sake kuka mai yawan wannan. Har saida bacci ya dauke shi sannan Saratu ta zame jikinta daga nashi tana fitowa. Da Magriba shima sai gashi ya fito, ya kalli Daada yana mata murmushi, kafin ya fita daga gidan gabaki daya. A ranar ya fara shirin barin Marake, ta dauka Datti zai hanashi, sai dai harya zo ya tsugunna a gabanshi yayi Lubna sufyan Hausabook.com 382 masa sallama bai daga ido ya kalle shi ba, baice komai ba. Kuma har yau da shekara uku kenan, ko Julde yazo duk juma'a bayan mako biyu ko uku, daga shi har abinda ya kawo Datti baya kallansu. Balle kuma ya amsa gaisuwar da Julden zaiyi masa, da Dije tayi masa magana cikin wata irin gajiyawa yace "Ban isa ba, akan Julde. Ya nuna mun hakan fiye da sau daya. Alkawarine nayiwa kaina, bakina ba zai kuma ba, in dai akan shine, yaje shi da rayuwar daya zaba" Ranar ne kuma ta juye masa abinda yake cikinta, abinda ta dade tana rikewa "Kaso mafi girma na abinda ya same su kaine, zan dauki sauran daya rage saboda na zabi zuba muku ido maimakon yin iya bakin kokarina wajen nuna muku kuskuren da kukeyi. Ka so su, nice shaida, sai dai soyayyarka ce ta fara ja musu matsalar da suke ciki Datti, soyayyarka da ta hana ka nuna musu wata rana zasu nemi abinda zaka iya hana su, zaka nemi abinda zaka Lubna sufyan Hausabook.com 383 so suyi maka biyayya, duk basu son wannan ba..." Ta sa hannu ta share hawayen daya zubo mata kafin ta cigaba "Saika nuna musu indai kana raye babu wani abu da zasu nema su kasa samu, sai kayi tunanin tarbiyarsu a hannunka take, shi yasa ka ganin aibun yaran mutane, saboda kaine, Datti, kafi karfin abinda kake ganin yaran wasu nayi ya sami naka. Ranar da suka fara nuna maka bakafi karfin su ture maganarka ba, saika kara kuskure akan wanda kayi, daka gwada lallashi, ka gwada fada, saika ga lokaci ya kure maka, sunyi bushewar da lankwasa su yake dai-dai da karyewar su, saika daure su da bakinka, kayi musu dauri na gaske da bakinka, su sukayi motsin Datti, matsatsin daurin da kayi musu da suka motsa sai suka karye da kansu... Gashi nan mu duka muke tayasu jinyar" Idanuwa Datti ya rufe, kalamanta na shigar shi, yanajin kamar jininshi na kara gudu a cikin jikinshi, kuskuren shi da yaketa dannewa ne take fito masa dashi tana goga masa a ko ina na Lubna sufyan Hausabook.com 384 jikinshi, tana tursasa shi ya fuskanci abinda a wannan bigiren bashida karfin fuskantar shi "Kuskuren namu ne, kuskuren mune duka..." Baice komai ba, harta shiga daki baice mata komai ba, kuka tayi marar sauti a cikin daki, yai nashi a tsakar gida. Kowa da kalar ciwon da yake ji. Datti najin yanda kamar bai taba wata rayuwa babu yaranshi a cikinta ba, yanajin yanda sauran shekarun duka yayi sune cikin zaman jiran ranar da zai zama uba, da tazo sai yake jin yana da kudi, yana da asali, yana da duk wani abu da zai isheshi ya karesu daga dukkan abin ki, yana kuma da girman zuciyar daya kaunace su da dukkaninta, yanzun da komai ya hargitse masa sai yake kara jin yanda duk wani numfashi da zai ja ya fitar kamar gayyata ce yake yiwa ajalin shi. Dije najin karshen duniyarta ne yazo. Sai Bukar shima ya fado mata. Borno yace mata, ammam Borno a ina? Gabas? Yamma? Kudu? Arewa? Ko a tsakanin duka hudun? Shima idan neman shi ta fita yi bata san ta inda zata fara ba, yana lafiya? Me yasa ya dade fiye da kowanne lokaci? Lubna sufyan Hausabook.com 385 Yaushe zai dawo? Kullum tunaninta akan shi baya wuce wannan zagayen, wanne hali yake ciki, yaushe zata sake saka idanuwanta akan shi. Sai taga kamar tunanin nata ne ya fisgo mata shi ranar yammacin wata Alhamis da zata cigaba da tunowa, saboda itace Alhamis ta karshe da ta saka shi a idanuwanta. Sai dai ba wannan Alhamis din bace kadai zata kafa tarihi a rayuwar Dije "Daada Am" Ya kirata a maimakon sallama, cikin muryar nan tashi mai sanyin gaske. Cikin wani yanayi daya sata bude idanuwanta ta kuma dago daga kishingidar da tayi a tsakar gidan tana kallon shi, murmushi yayi mata. Murmushin shi da yake cike da sanyin halin shi da kuma wani abu da na shine kawai, na Bukar da bakowa Allah yake halitta da shi ba. "Daada..." Ya sake kira, numfashi taja, ta fitar, ta sake ja tana fitarwa "Bukar" Lubna sufyan Hausabook.com 386 Ta amsa tana sake kallon fiye da fuskarshi wannan karin, yadine a jikinshi kalar bula, amman yayi wata irin dauda kamar wanda yayi birgima a kasa, saita kalli kafafuwanshi, takalmane yake sanye dasu yan soso, sababbi kamar ranar ya fara takasu, amman kafarshi kurace tamkar yayi kwanaki baiga ruwa ba, bana wanka ba kawai harda na alwala. Tun da take dashi, ko a lokacin yarinta bai taba dauda irin wannan ba. Bata taba ganin shi haka ba, jakace a hannun shi daya, saiya sata duban dayan hannun nashi, zuciyarta nayo tsalle ta daki allon kirjinta tana komawa mazauninta da wani irin yanayi. Yarone, hannuwan shi duka biyun rike dana Bukar, sai dai ya labe a bayan kafafuwan shi, sai daya jawo shine ya fito fili, amman akwai tsoro a cikin idanuwanshi, sai taga kamar Bukar, saiya tuna mata lokacin da Bukar yake da shekarun shi, zuciyarta na wata irin cika, taji hawaye masu zafi na tarar mata a idanuwa, jan hannun yaron Bukar yayi har suka karasa inda Daada take zaune, jakar ya ajiye a gefe, yana zama akan tabarmarta ya kama yaron ya zaunar a Lubna sufyan Hausabook.com 387 tsakaninsu. Sai yanzun da suka zo dab da ita ta kula bashi kadai yayi daudar ba harda yaron, kayane na yan binni a jikinshi, da alama zasuyi tsada ko ba'a fada mata ba, don tana ganin irin kayan a jikin su Salim idan Julde ya bayar an siyo musu daga binni. "Aure nayi Daada... Ga Nawfal" Ya fadi yana mika mata hannun yaron da ta rike, hawayenta na zubowa. Tanajin shekarun da ta rasa na rayuwar Bukar suna ninka mata, yayi aure, bata sani ba, yana da mata, ko sunanta bata sani ba, ga Nawfal, da ko baikai shekaru uku ba ya kusa. Bukar ta kalla, haka tata jarabawar tazo, rasa abubuwa a tare da yaran da suka fito daga jikinta "Abubuwa da yawa sun faru Daada, abubuwan da zanso ace ina da cikakken lokacin da zan miki bayani yanzun, amman babu, sai dai idan na dawo..." Bata san me yasa a duk abinda ya fada ta zabi tambayar shi "Ina zaka tafi?" Lubna sufyan Hausabook.com 388 A maimakon tarin tambayoyin da suketa kaikawo a cikin kanta ba, amman ita tafi sauran. Yanzun yazo, yanzun taganshi bayan wasu shekaru, me yasa yake mata maganar sake tafiya ko numfasawa baiyi ba balle ya huta. "Na barta, zan koma mu taho tare ne...banda lokacin da zan kara batawa Daada, rayuwarta na cikin hatsari" Cike da rudani da rashin gane inda zantukanshi suka dosa take kallon shi, sai dai kalaman shi na gaba ma rudata suka sakeyi suna jefa wani firgici a zuciyarta "Wani abu a zuciyata yana fada mun shi kadai ne kwan da nake da rabo a duniya Daada, ga amanar dana, gatan da na hasaso ma rayuwar shi mai yawa ne, ga amanar shi nan kafin in samu dawowa, dalilin da zaisa ni barin shi mai karfine..." Kafin kuma tace wani abu ya janyo jakar dake gefen shi ya mika mata "Ga wannan Daada, duka abinda yake ciki mallakin shine, amanar ba taki bace wannan, ta Lubna sufyan Hausabook.com 389 Hamma ce, zai damkata a hannun shi a lokacin daya dace... Banda lokaci... Banda lokaci da zan tsaya in bashi da kaina" Sai fadi yake bashida lokaci kamar yana ganin agogon da yake dauke da kwanakin rayuwar shi. "Bukar kayi mun magana yanda zan fahimta... Babu wani abu da nagane a cikin zantukan ka...rayuwar wacece a hatsari? Meye a jakar nan? Me kake nufi da ga amanar danka nan? Kai kuma fa? Ina zaka je?" Tambayoyine masu yawan gaske da suke turereniya da junansu wajen fito mata, sai dai mikewar da Bukar yayi ta katse mata su "Bani da lokaci Daada... Idan na dawo zan fada miki" Ya amsa yana mikewa "Ka zauna a wajen Daada in dawo Nawfal" Hannun shi daya Nawfal ya mika, Bukar din ya sumbaci nashi hannun kafin ya dora akan na Nawfal yana kuma janyewa. Hannun Nawfal ya daga ya manna a kuncin shi na dama, na haggu, Lubna sufyan Hausabook.com 390 da kuma kan goshin shi. Kamar wani abune da suka sabayi, kallon su Dije takeyi, ta kasa ko da kwakkwaran motsi, komai yayi mata tsaye, musamman da Bukar ya juya, harshenta ya nade a bakinta, ta kasa ko da kiranshi balle kuma tayi yunkurin hanashi tafiya, ya juyo ya kalleta, kamar shine kallon karshe, ya kalleta da fatan rayuwa ta sake ara musu lokacin makamancin yau din, kafin ya fice daga gidan, ya bace ma ganinta. "Kamar Bukar nagani ya fita" Datti daya shigo ya fadi yana dawo da ita cikin hayyacinta "Ya sake tafiya... Bukar ya sake tafiya" Sosai Datti ya sake shiga cikin gidan yana kallon su, ita da Nawfal. Badon Nawfal din da kuma jakar da take gani ba, da zuwan Bukar zai mata kamar mafarki, kamar daya daga cikin mafarkan da ta saba nashi. Amman ga shaida nan, yazo, ya sake tafiya tana kallon shi bata tsayar dashi ba. Hannun shi Nawfal ya mikawa Datti, ya kalli hannun, ya kalli fuskar Nawfal da ko ba'a fada ba yasan jinin Bukar ne, ga Lubna sufyan Hausabook.com 391 mamakin shi saiya kama hannun yana mikar dashi, saiya daga shi ya rike shi a jikinshi "Ya sunan ka?" Ya tambaya da fulatanci "Nawfal... Kai ya sunanka?" Ya amsa, murmushi Datti yayi, murmushin da Dije ta dade bata gani ba a fuskar shi, ya sake gyarama Nawfal zama a jikin shi suna magana cikin yaren da yafi komai soyuwa a wajen Datti Kamar Bukar bai zo ya sake tafiya kamar walkiya ba Kamar duniyar bata sake birkice mata ba Sai ta kalli Nawfal da yayi dariya, yanayin fuskar shi da sautin dariyar na mata iri daya data Bukar Datti take kallo da yake kwance, motsin kirki ma baya son yi, yanzun saiya wuni cikin gida baj fita ba. Kamar babu wani abu daya rage masa a waje, duka duniyar shi na cikin gidan, na tare da Lubna sufyan Hausabook.com 392 ita yanzun da babu yaransu. Sauran gonakin su na cikin Marake akwai masu kula dasu da suke karkashin Julde, kome suke da bukata yana kawo musu. Datti ma bai nuna hakan na damun shi ba, tunda ya daina fita in ba da wani dalili mai karfi ba. Akwai hasken fitilar da suka kunna,amman tunda Julde ya dauke Nawfal kamar duk wani haske da zata kunna iya idanuwan Datti suke tsayawa. Kamar Nawfal din wani haskene da suka kwana biyu basu gani ba. Kuma Nawfal din wata alama ce da ta tabbatar mata da kadaicin da Datti yake ciki, idan har zai ture tsanar da yake yiwa Bukar ya rungumi Datti haka, tabbas kewar ganin yaran shi a gabanshi da yake ta wuce yanda zata iya hasashe. A karo na farko yanayin shi na sakata tunanin duk yaran da suka binne, da sun rayu watakila da basuyi kadaici haka ba. Da ba zasu rasa a cikinsu ko da kwara dayane da zai zauna tare dasu ba, da basu ji kamar a filin duniya basu da kowa sai junansu ba. Akwai wani mataki na shekaru ko rayuwa da yara suke kaiwa sai su dinga dauka babu wani abu da iyayensu suka fi bukata sama da Lubna sufyan Hausabook.com 393 kyautatawa, rage musu ko ma dauke musu duk wani nauyi da yake kawunansu, ci, suttura da ma duk wani abu na jin dadin rayuwa. Albarkar nan da ita sukan bi hadi da addu'o'i da suke nuna jin dadin su na wannan kyautatawar. Amman yawanci a kasan zukatansu akwai muradi na daban, akwai kewar da gudun yanda yaran nasu zasu dauki maganar in sun fito da ita yasa suke kara danneta. A karo babu adadi, zasu dauki kasancewa da yaransu na wuni daya akan wannan tarin sutturar da suka kawo suka juya a cikin wasu yan mintina, ko suka aiko da ita. Amman yara sun kasa fahimtar wannan, rana daya bayan makwanni biyu, uku, harma hudu yayi mata

Chapter 15 of 27