Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dinga rabuwa da ita ba laifin su bane laifin wannan shegiyar uwar tasu na tabbata ita ce zata zugo su dan kuwa in baka manta ba ba kalar labarin son kud'in uwar su da Basu bamu ba , na samu na deb'o Leda hudu ai dai ta gina jikin ta da kayan kud'in da ake samowa ko?" Dariya Alhj Salihu ya yi sosai sannan ya ce, "Ni kuma hudu da diba" "Shgeb sama, to shi kenan sai mun haɗu yanzu zan fito,tsallake ta ya yi ya fice dakin shi ya saka jinin a inda aka basu su saka, wata jakar fata ce da akai mata ado da ja kamar an qara riƙa ta sai rubutun Arabic a jiki wanda ko mutum ya karanta ba zai bashi wata ma'ana ba, rataya wa ya yi a jikin shi dan kuwa ba a son su aje ta a qasa ko da da mistake ne sai sun ba da wani wannan ya tashi aiki kenan idan jakar  ta taɓa qasa,ko kuma idan ba haka ba sai an kaiwa Oga Zaks matan dan ya diba da kan shi,domin ko kusantar su ya yi jinin nasu diban shi ake yi. Sun isa wajen Oga zaks da misalin ƙarfe ɗaya na dare, suna isa suka miqa masa jinin wata dariya ya barke da ita kamar ana yaga zani, ba ko daɗin saurara daga baya kuma ya haɗe fuska kamar bai taɓa dariya ba ya ce, "Aikin ku ya na kyau, shiyasa kuka fi sauran abokan harka shanawa, bakuda tsoro sam ,sannan bakwa jinkiri, ku gaggauta maza muje a bawa Dodon tsafi jinin kyawawa ya sha" Ta shi suka yi suka shiga wani daki, dan tsoro ina leqawa nai baya a 360 ba zan iya dakko maku rahoton komai ba anan, gidan Saudat na je, tana kwance rabin jikin ta na kujera, rabi na qasa, fuskar ta ta kumbura ta yi sintim, dan tafi ta kwanaki hayewa ashe Itan ma jibga ta sha amma yake wa abokin shi magana akan ya dena biye wa suwaiba ya na jibgar ta, nan take na ayyana a rai na wato shi Alhj  kalla hukuncin shi Kalla mari ne kawai, mari kam iya mari ta shashi da dikkan alamu, dan ina jin shi ya sata suma ma, ruwa na yayyafa mata na labe, a firgice ta miqe tana fad'in, "Ni bana son Yaran ma har abada, kayi hakuri ka daina kallan mari" Tana fadin hakan tana kuka fuska dagaje2 da hawaye ga majina da yawun azaba duk suna ta tarara,dube2 ta hau yi taga ba kowa a gidan sai ita kaɗai ,ta na miqewa ta ji wani irin jiri ya na ' dibar ta tare da tsananin ciwon kai, komawa ta yi ta kwanta, tana maida nunfashi, suwaiba ko bata farka ba sai da suka koma gida wajen qarfe hudun asuba. Yana isa d'aga ta ya yi ya kai ta toilet ya hada ruwan zafi ya saka ta, ihu ta saka na azabar da ta ziyarci jikin ta, dan kuwa jikin ta duk ya farfashe,kuka ta fashe da shi ta na ja da Baya a cikin kwamin wankan ta na fadin, " kayi hakuri mai sunan Annabawa na tuba, ba zan qara maka zancen yara ba har mu mutu, ka yafeni sharrin shedan ne d'azun ma Allah ya ƙara nesanta mu da sharrin la'ananne jefaffen Allah" Rufe mata baki ya yi yana hawayen munafurci yana bata hakuri shima, harda in ya sake ko taba hannun ta da sunan duka ne duk hukuncin da ta ga za ta masa ta masa, runtse idon ta ta yi tana jin yanda zafi ke shigar ta, nan take zuwa Abujan ma ya sire mata a rai, wannan wace irin azaba ce, in kaci daɗi na wata ɗaya sai an zai zaye maka shi a kwana daya? Yanzu yanda take jin ta kamar wadda akaiwa yasar wani abu, bata da qarfi ga ciwon kai da take ji kamar kan ya fice, barin ta ya yi ya tafi kitchen ya samu fruits ya markade ya tace ya kawo mata ya sa mata abaki yace ki sha zaki samu qarfi sosai a jikin ki, bangaren da masu aikin su suke yaje,ya tashi mai girke2 dan ya mata farfesu, ko na naman meye ma a samu ta samu kwarin jiki, ai ko ba komai ta maida mugun yawu, sannan abinda ya kawo ta kenan, in ji shi, farfesun naman rago ya yi mata da yaji kayan haɗi, irin farfesunnan ne wanda mutum zai zaci gashi ne, yasha kayan lambu a ciki, qamshi da maiqo sai tashi yake, fresh milk ya zubo mata, ya koma toilet din bata shanye jus din da ya mata ba dika, dakko ta ya yi a hannu daure da towel ya dawo da ita gado ya cire towel din ya samo riga iya guiwa mai dan fadi ya zura mata, kanta ta jingina da frame din gadon idon ta lumshe, zuwa ya yi ya d'akko wannan had'in ya shigo da shi, ai tana jin wani qamshi mai daɗi sai ga idon Suwai a buɗe, wani yawu ta hadiya na kwad'ayi, Alhj Salihu ya ayyana, 'Shegiya dangin maita, ji fa uban dukan da taci amma ta ga nama har ta miqe' Isa ya yi gaban ta ya aje mata ya fara bata a hankali,ita kuwa sai taga baya sauri, d'aga masa hannu ta yi ta saka nata dayan hannu ko ta kan spoon din bata bi ba ta hau ci kamar tsohuwar mayya, ci take ba ko tsayawa sai da ta yi nak, ta kora da fresh milk, ta zame ta kwanta, lokacin Subh payer ta yi amma ko a jikin su daga shi har itan, haka suka kwanta bacci, manne da junan su,abin ku da wadda ta dad'e miji na gabza in ta nemi haqqin auren ta, yau ta samu a bagas dik da zafin da take ji haka ta miqa mai kanta, ranar ta yi murna da farin ciki ba iyaka, tini ta nemi zafin ciwon ra rasa, kusan abinda ya faru kenan a gidan Saudat,sai dai akwai wani plan da Suwaiba ta haɗa a qasan ranta na ganin me yasa ba su son su haihu,dole sai ta binciko dalilin da ya sa ba su son haihuwa. **************************** A gidan Talle kuwa cikin dare Salma ta ji kamar buga qofa ake yi,dan haka a hankali ta miqe ba tare da ta yi wanai kwakkwaran motsi ba, dan tare suke kwana da Haule yanzu, leqawa tayi ta qaramar bular jikin qofar d'akin nata,ta bular ta hango Yayan mijin nasu na waige2 yana kwankwasa qofar Marka, mamaki ne fall cikin ta na me ya kawo shi d'akin Marka da tsohon daren nan, dan kuwa duk yan kwanakin nan marka ke zuwa wajen shi, yau fushi take yi da shi shi yasa ya biyo sahu, saboda  daren jiya ya hana ta dari da hamsin da ta roqa yace bai da su, shine tace yau ba za ta ba, shi kuma gashi a mugun matse yake,jikin shi har wata rawa yake  sanda yake kwankwasa qofar, budewa ta yi tana magana qasa2 ta ce, " Dalla can sai ka tada yaran ma sun gan ka, ni shigo kayi ka gama ka tafi jarababbe kawai" Jan shi ciki ta yi su ka rufe qofar, aiko akan idon salma, kame baki salma ta yi tana fadin, "Tab ashe wannan matar munafuka ce? Ba ta da maqiyi da rana da ya wuce Baban Bangis,amma kuma ashe  da dare bata da masoyin da ya wuce Baban bangis, lallai ran da Su Badamasin suka sani akwai case a gidan nan ko kuma idan Talle ya ji labari" Tana cikin wannan tinanin ta fara jiyo qarar dan qaramin gadon na Marka irin na qarfen nan, sannan ga sambatun ta nan da bata iya shiru ita sai ta tona masu asiri, yaran akwai nauyin baccin tsiya shi yasa ma basu san wainar da ake toya wa ba, to an wuni shiririta kuma anyi bacci  late dole in sun kwanta su zama kamar gawwaki Marka a wayon ta hade yaran take dika daki daya saboda irin haka, kafin Salma ta zo ne d'akin tan yake na Yammatan, amma kawo ta yasa aka haɗe su waje ɗaya maza da matan,motsin qofa Salma ta ji Baban Bangis zai fito sai da ya fito Marka ta biyo shi tana miqa masa hannu ta na wani gantsaro girji, shi kuma yana qara shafawa, ya ce, " kamar na koma mu yi ta yi sai asuba na tafi" "Lallai ma Yaya kaima a gaida ka, duk wannan aikin da garar da ka diba bai ishe ka ba, in kana son ka koma ciki qaron nera dari kacal" Murmushi ya yi haqoran shi jajaye suka bayyana ya ce, " Aaaa dari tab na gama baki dari ukun yau, ni dai gaskiya ban da su"  "To kuwa kama gaban ka ka wuce ya ishe ka haka a barwa gobe" Yana qarasa fitowa gaba daya Salma ta fito da buta a hannu ita ma , hankalin su ne ya tashi gaba ɗaya da ganin ta tsaye ta na murmushi ta na bin su da wani shu'umin kallo,jiki na rawa baki na karkarwa su Marka suka zube a Saman guiwowin su suna roqon Salma, " Salame dan Allah ki rufa mana asiri, kar kowa yaji labarin nan" Cikin Isa da gadara Salma ta ce, " Anawa zan yi shirun ko ko haka nan zan rufe bakin nawa kuke nufin baku ban ko sisi ba tunda ke na ji ɗari uku ma aka baki" Jiki na rawa Baban Bangis ya sa hannu a aljihun shi ya dakko dari biyar guda biyu ya miqa wa Salma , "Ke ma ina naki  kud'in?" Da sauri Marka ta shiga d'akin ta ta d'akko dari biyar ta haɗa dana hanun ta ta bawa Salma, " Kallon su ta yi ta na juya kud'in ta ce wa Marka, "Marka ina son ki sani Talle ya kusan dawo wa dan jiya baki nan kina yawon ta zubar Badamasi ya faɗa sun yi waya ya ce zai dawo nan ba da jimawa ba, in ya dawo kika kuskura na ganku tare har kika haɗa  wannan qazamin jikin baki da shi warin ki ya mannu a jikin shi saina faɗa masa, dan ba zaki sa yanda ni na tsare aure na ba ina juran ya dawo mu raya sunna ki ja min amai kuma ba biyan buqata, kinji ni ko baki ji ba?" Wani yawu Marka ta had'iya na yau ta shiga uku an raba ta da gwarzon maza Talle, sannan a hankali tace, "Na gane kiyi wa Allah ki rufa mana asiri" " Baku da matsala in ma komawa zaku yi sai asuba din zan iya yi maku gadi" Da sauri suka furta, "Aaaaa tafiya zai yi/zan yi" Fakam fakam Yayan Talle ya bar sashen nasu, ita kuma salma  ta koma d'akin ta ta  bar Marka da cizon yatsan an amshe yan kudaden ta kuma gashi ba wai ta wani samu biyan buqatar ta bane, yau ta yi biyu babu, tura qofar ta ta yi ta koma dakin ta. Salma na shiga d'aki ta datse qofar ta zauna ta dinga babbaka dariya, a ranta ta na ayyana, 'Shikenan yanzu sun dawo hannun na sai yanda na yi da su' Shikenan yanzu da ta ji tana son kuɗi zata neme su kuma dole su bayar ko ta tona masu asiri, cikin murna ta dale gadon ta ta miqe. **************************** Yau garin na Kano an tashi da ni'ima sakamakon sanyi da ya ɗan fara shiga, garin ya yi daɗi ya yi kyau gwanin sha'awa,rana ta yi sanyi babu kuma zafi. Shamsiyya qawar su Juwairah da Nafee ce ta kawo ma Juwairah ziyara ta musamman dan tana son ta qara bata wasu shawarwarin game da yanda zata gyara nonon ta da suka lamushe kamar an yi gobara ta ciki an yashe komai sai fata, sannan ga kanta dake yawan karyewa gashin ta na zuba, bangare ɗaya kuma abu mafi mahimmanci da zai kaita ta taya su murna dan Nafeesa ta bata labarin samun cinkin da ta yi, murna take yi sosai itama da jin hakan. Shiryawa ta yi bayan ta gyara gidan ta tsaf kamar ba ita ba ta fito ta hau abin hawa ya kai ta har gidan su Juwairah da Nafeesa bayan ta sauka ta sallami mai adaidaita sahun ne ta shiga ciki, bangaren innar mu ta fara shiga ta gaishe ta, bayan sun gaisa ne ta mata murnar abun alkhairin da ya same su sannan ta shiga ciki wajen Juwairah, a can ta hango Nafeesa tana alwalar la'asar, Juwairah na d'aka tana gabatar da tata sallahr......... [18/07, 8:26 am] asiyahabibu93: 💅🏼    'YAN ABUJA    💅🏼         WRITTEN BY HAERMEEBRAERH page 15: Ranar litinin da safe ne su Suwaiba da Saudat suka shirya tsaf dan zuwa asibiti su ga meke faruwa har yanzu ba su samu ciki ba balle a kai ga sa ran haihuwa, shiga suka yi ta alfarma sai walwali suke da ka gan su ka ga matan manya. Qarya suka yi wa mazajen nasu suka sanar da su zasu tafi shoping ne, Dunes Supermarket suka nufa cikin isa da qasaita irin ta isassu kuma hamshaqan mata, Alhj Salihu ne ya biyo su a b'oye dan ya tabbatar da ina zasu je, ganin sun isa super market ne da gasken ya sa hankalin shi kwanciya sai ya kira ya Alhj Kalla ya sanar da shi cewar da gaske shoping suka tafi, Suwaiba ta kula da binna ta da yake yi duk kuwa da qoqarin boyewar da ya yi ta yi kar ta gan shi,wannan shine dalilin da ya sa ta ce ma driver ya kai ta can super market ɗin a hanya ta yi wa Saudat message akan su tafi can din daga baya sun san shawarar da za su yanke. Bayan sun isa ne suka fito a motocin su suka shiga super market su a dole siyayya za su yi,suna shiga suka hau waige Saida suka tabbatar ba direbobin su ba su gani su cikin sauri suka fita ta wata qofar suka samu taxi suka ce ta kai su asibiti mafi kusa,nan take kuwa aka kai su wani private hospital dake kusa,bayan gwaje gwaje da aka yi masu a tashin farko likitar ta gane ai ba ma mahaifa a tattare da su an cire ta. Sanda ta sanar da su suwaiba hauka ne kawai ba su yi ba saboda tsananin  damuwa da shiga tashin hankali, kuka suka saka sosai kamar an masu duka, jikin Saudat sai rawa yake dan ta fi Suwaiba son yara,ita Suwaiba dama ita ba wai ta wani damu da su ba ne, amma kasancewar yanzu ta ji bata da mahaifa kwata2 hankalin ta ya dagu sosai, tashi sukai bayan sun gama biyan komai suka dawo supermarket din suka debi wasu daga abubuwan da suke buqata musamman na gyaran jiki, Suwaiba kuwa acici kayan kwalam da maqulashe ta jida sannan suka je suka biya kud'in aka zuba masu kayan su a leda,jerawa suka yi su na tafe suna magana,suwaiba ce ta ja hancin ta sannan ta ce wa Saudat, " Da mu zauna ba mahaifa ba kayan more rayuwa ai gwanda mu kwashi rabon mu muci tin da bamu da magada" Fadin hakan ke da wuya sai Saudat ta saka kuka har ta na shassheqar kuka, cikin faɗa Suwaiba ta ce, " Malama kar ki taran jama'a, meye na kukan kuma a cikin mutane, daga cewa mu more rayuwar mu,an fa tabbatar mana da ba za mu haihu ba,to in dai haka ne me zan haihu ba zamu more rayuwar mu ba? Ki fa duba ki gani ba mahaifa ba haihuwa ba kuɗi,to haka ki ke so mu zauna cikin wahala? Sanin kan ki ne ma mazajen mu suka san bama haihuwa mun shiga uku, in gaba suka so qara auren su za su yi, ba gwanda mu ware ba mu saki ran mu mu tatsi abinda muka tatsa, tin da mun taba zaman Abujan mun ji abinda ke cikin ta, kinga sai mu canja sheqa da uwar kud'in mu wa ya isa ya taka mu?" Gyada kai Saudat take ta yi kamar wata qadangaruwa, ta fahimci suwaiba Sarai,kawai ta na wani tunani ne na wannan zancen rashin mahaifar tasu abu kamar na had'in baki ace basu da mahaifa iya da yar uwar ta ? Anya babu wata a qasa kuwa? Lallai ba zata huta ba kuwa sai ta binciko ta san mene dalilin da ya sa suka rasa mahaifa a lokaci d'aya da yayar ta bayan ta san ko a da da suka yi yawon su ba su taɓa yunqurin zubar da ciki bama balle cire mahaifa, suna gama tattauna wa a tsaye nesa da drivers ɗin su suka yi sallama da juna suka koma gidajen su. ************************* Yau fa gidan Talle shar da shi domin ta shi kawai suka i suka ga Salma na bada umar ni ko ta ina kuma Marka bata ce komai ba,ta ɗauki ido ta zuba mata ba ta uhuummm ba kuma ta ah ah. Tun da ta ga yara sun tashi daga bacci ta sa masu hankalin a gaba sai da suka gyara d'akunan baccin su ta na yi ta na masifa kamar yanda ta ga Markar na yi,daga nan ta ware manyan ta sanya su shara nan suka haɗu suka share gidan tsaf,daga nan ta sa aka deb'o toka a murhu aka cika a shaddar gidan aka kwab'a wata da omo aka wanke bayin nasu tasss. Kiran kowa ta dinga yi da Sunan shi ta na bada umarni kowa ya d'akko wankin shi,nan fa suka fara fito da wanki tsibi tsibi kamar a gidan wankau,ta na zaune a qofar d'akin ta tana kallon yanda 'yan matan ke kallon Marka suna jiran su ji ta tsawatar amma shiru, ga wani uban kwarjini da Salma ta yi masu ko rashin kunyar ma sun kasa yi mata,da kudin da ta Karb'a a wajen su Marka a daren jiyan da shi aka siyo sabulun wankin, bayan sun gama wanki ne Salma ta sa su a gaba Saida kowaccen su ta yi wanka. Abun nasu sai ya zama gwanin sha'awa gidan ya yi fes da shi yaran ma sun yi acan acan,sai da Salma ta tabbatar kowa ya yi fesss sannan Itama ta shiga ta fesa wannan ta ta fito ta shirya tsaff cikin kwalliya,ganin haka ne ya sanya Marka leqa Salma da ta ke dakin ta ta na huce gajiya, dan kuwa ta bada kuɗi a siyo kayan miya a yi girki,Saida Marka ta tabbata ba za ta fito da wuri ba ta deb'i ruwa a bokiti Itama ta je ta yi wanka,ita da kan ta sai ta ji iska na ratsa ta. ko da ta gama shirya wa Itama sai ta bi lafiyar gado dan ta dan matse ido kafin a yi girki,kwanciyar ta ke da wuya  Huwaila da Jummala suka shiga dakin mamar su ta da ya sha gyara suka hau tambayar ta wai me ke faruwa ne yau a gidan ko dai asiri salame ta yi mata ne? Marka ce ta kalli hanyar kofar d'akin ta ta gyad'a kai tare da fad'in, " Um Um Um Um Um" Wannan kalmar kawai take ta maimaitawa tana kama bakin ta, alamar su yi shiru maganar babbace , kame bakin nasu ko suka yi ba su qara tambaya ba dan sun san wacece Marka duk abinda zai ta tashiga hankalin ta haka ba qarami bane,Marka ko cikin zuciyar ta cewa take, 'Yarinya ni ce fa uwar shed'anu, ki gama wannan mulkin naki na yan kwanaki, kiga abinda zai faru dake nan gaba kaɗan, dani kk zancen' Da yamma sakaliya suka ji qarar motar Talle,yaran fita suka yi da gudu dan tarbon Baban nasu, Huwaila na can Ita da Baban gida a wani lungu na gidan suna sana'ar tasu, su ka ji qarar motar Tallen, a firgice suka saki juna suka yi hanyar fita daga lungun kowa na zare Idonu. Talle kenan mai gayya mai aiki shine ya dawo gidan nashi bayan tsahon lokaci, Salma na jin haka ta miqe tana rangwada ta je ta taro shi, dawowa suka yi cikin  yaran yaran nata gaida shi yana amsawa. D'akin Marka ya leqa ya ganta ta yi wanka dakinnan fes kamar ba shi ba, wata uwar dariya Talle ya saki sannan ya ce, " Hajiya Marka, Markar Talle ,Marka Ikon Allah, wato ganin Kyakkyawar amarya ta ne ya nutsar dake har ki ke wanke da gyara gida, yo ni dana san haka ne ai dana dawo da jimawa, da ban tsaya wajen qadangarun bariki suna amshen 'yan kud'ad'e na ba," Qafar sa ɗaya ya d'aga zai shiga d'akin na Marka Salma ta koma ta tsaya a bayan shi tana kallon Marka da wani irin mugun kallon ya na shiga zan tona maki asiri, da sauri Marka ta miqe ta ja baya ta na fad'in, " Aa Talle in ka zauna d'akin nan ba ai wa yarinyar can adalci ba kuma, wancan karon ai a wajena ka fara zama ina ganin wannan karon wajen ta zaka fara zuwa" Tsantsar mamakin Marka ne ya kama Talle har ya sa shi sake baki ya na kallon ta, qarasa ya yi wajen ta ya taɓa wuyan ta dan ya ji anya lafiyar ta qalaou kuwa? Jin ta ya yi daidai ba alamun zafin jiki ko wata lalura,girgiza kai ya yi ya na tsananin mamakin sauyawar da Marka ta yi kad'a kai Talle ya yi sannan ya juya ya nufi d'akin Salma dan tana ma Marka kallon nan ta juya ta bar wajen,hira ya dinga yi mata da ba wani ganewa ta ke yi ba, dan gaba ɗayan shi tsami yake yi kamar wanda ya yi aikin qarfi kafin ya dawo. Dabara ce ta fad'o mata tashi ta yi ta na yanga ta fita, shi kuwa Talle wata shashashar dariya ya sake ya na bin mazaunan ta da kallo, ta na fita ta ɗauki bokiti ta zuba ruwa a bokiti babba, ta koma d'akin ta dakko brush guda biyu ta saka toothpast a jiki ta je kusa da shi zuciyar ta na tashi amma ta jure ta zauna a cinyar shi tana shafa shi ta ce, " Babe taso mu je mu yi wanka magariba na yi, kaga in munyi sai mu yi sallah ka zo na yi maka tausa dan da alama ka gaji sosai" Gyada kai ya dinga yi kamar qadangare ya daga ta yana son ya dauke ta, da sauri ta sauka dan in ya sata a kafadar nan tashi sai ta yi aman hanji ta tasss saboda tsamin zufar da yake yi,cikin kirsa ta ke masa nuni  da yara, kawai ya je ya fara shiga zata biyo shi ta masa wankan daga baya, tafiya ya yi yana washe baki, rabon da a masa irin haka tin tana amarya a cikin garin Abuja. Ai kuwa da Salma ta samu dama ta kora yara Mazan su tafi masallaci,matan kuma a shiga a yi sallah  sai tayi wuff ta faɗa band'akin,wanka ta masa sosai, ta bashi brush ya wanke bakinnan fes,sai ga Talle an yi shar, shima kar ba ya yi ya mata wankan ta wanke bakin ta, ta fara leqawa taga ba yaran maza 'yan matan na d'aki suna hira da Marka sai ta fito, daga baya shima ya biyo ta dakin, shirya shi ta yi tace ya yi alwala ya je masjid, amma sai Talle ya buɗe baki cikin b'ata fuska ya ce, "Ka ji min yarinya da ke kike sani na yi sallar? To banga dama ba haɗawa zan da isha'i in na gama abinda zan yi" Cikin kwantar da kai Salma ta ce wa Talle,   " Ah ah ba ni nake saka ka ba Allah ya baka hakuri, ni so nake dama kayi da wuri saboda in na zo maka tausar nan bana son abinda zai sa na tsaya ne ka ga idan baka yi sallahr ba dole ana tsaka da tausa ka ce na tsaya ka je ka yi sallahr shi yasa na ke baka shawarar ka yi yinsa wuri amma tinda baka so kwanta na yi maka tausa" Cikin yauqi da kwarkwasa ta qarasa maganar ta,tini Talle ya washe baki kamar dolo, miqewa ya yi zai tafi masjid, yajiyo maganar ta tana fad'in, " Babe in ka je ka jira ayi isha'i kawai ka ga in ka shigo sai asuba zamu sarara ko ya kace" Ta qarasa ta na kashe masa ido ɗaya, wata dariya Talle ya saki kamar wawa ya ce, " Maganar ki dutse sweety na se na dawo" Koda ya isa

Chapter 9 of 25