nake yi a can ɗin? Me kike son sani yau na sanar dake? Dan ba tsoron ku muke ji ba? Auren kwad'ayi auren kuɗi ku ka yi da mu, kuma kuna samun kud'in ko ba ku samu? Basu ishe ku bane? to meye na sai kin ji kwakwaf?"
Jikin Saudat sai rawa yake wani ruwa2 tabji na tsattsafo mata ta qafart ta bata ii aune ba ta ji ya kwada mata mari sannan ya ce,
" Dan uban ki fitsari kika yi a tsaye? Ji yanda kika bata min takalmi ni da zan fita,Me kika sani game da mu?"
" Alhj ban san komai ba, sai dai zargi da nake yi"
Aje cup ɗin ya yi ya zaunar da ita a kujerar dinning dake kitchen din ya ce,
"Ehen ina jin ki zargin me kike yi?"
"Dama ina zarkin ko ku yan damfara ne, kai da Alhj Salihu"
" Kin tabbata zargin da kike yi kenan?"
"Allah shine"
" To bari ki ji, zargin ki ya tabbata, amma idan na ji wannan maganar ko a wajen waccan doluwar yayar taki da ba abinda ta sani sai b'arin zance, da son kuɗi ranar za ki mutu, kinji ko baki ji ba"
cikin tsawa ya qarasa zancen nashi, baki na rawa Saudat ta ce,
"Nnnnaaajii..."
" Da kyau,ni na fita miqon takardar da kk boye kan na karya ki"
Tashi ta yi ta dakko ta miqa masa ficewa ya yi ya barta a wajen,ya na fita ta durqushe tana ta kuka, lallai yau data gaya masa abin da ta gano game da shi da fa shikenan kashe ta zasu yi, yanzu ta gudu ma nan ma har gidan su zashi wataqila ma ta jawa uwar su a haɗa da ita a kashe, ta zauna ta yi shiru su yi ta cin kud'in haram kudin jini,
"kaiiiiii wannan Abuja ba ta yi ba, inaaaa"
Ni dama na sani a Damaturu na yi aure na huta"
Ta fada tana share majina.
************************
A cikin garin Abuja kuwa bayan Talle ya dawo da salma gidan da yake aiki ya ajiye ta a dakin shi na masu aiki sai ya fice ya bar gidan , tun da ya fita take zaune a wajen take faman aikin kuka,idanun ta duk sun kumbure,a nan inda take zaune baccin wahala ya ɗauke ta,Talle kuwa ba shi ya dawo ba sai wajen la'asar hannun shi riqe da koko da qosai irin ɗan yamman nan da ake yi, sai wata leda mai kaya a ciki kala uku da takalmi kala biyu sai jaka daya, da yan kayan kwalliya da ba a rasa ba, miqa mata ya yi, ba musu ta tashi ta isa gaban shi ta Karb'a, leqawa ta yi ta yamutsa fuska,Talle na ganin abinda ta yi ran shi sai ya ɓaci, cikin haɗe fuska ya kalle ta ya ce,
"Baki daku ba kenan ko, har da zan baki abun da ban sai wa Marka ba na tsahon shekaru ke kin samu amma ki ke kyabe baki ko"
A tsorace tace,
"Na gode"
Ta Karb'a ta ajiye sannan ta shiga dan bandakin dake maqale a dakin ta yi wanka ta canja kayan ta fito, koko da qosan ta ɗauka ta ci ta sha, sannan ta koma ta zauna, kallon ta ya yi a wulaqance ya ce mata,
" kin iya cewa wani ya yi sallah amma ke bata dame ki ba, ji kike ban gane ki ba, wa'azi a baki amma ke baki aiki da shi munafuka, irin kune kuna da yara kuna sa su sallah su qi yi, to basu ga kuna yi ba"
Miqewa ta yi kamar munafuka da tsaho kamar raquma ta tafi,zalo zalo taje ta yi alwala ta
Yi sallar ta koma ta zauna,kallon ta ya yi ya kama kunnen sa alamar zai yi mata gargad'i,
" zuwa gobe ogana zai dawo shi kaɗai yake zama anan, matan shi suna maiduguri, aiki ke kawo shi nan, dan haka in ya dawo da yamma ki shirya muje mu gaida shi, in muka dawo na gan ki a waje ko kusa da wajen dakinnan kin mutu ranar, dan na san ki idon ki idon kuɗi, kice zaki maqale ma bawan Allahn da bai san neman mata ba, na kula akan kuɗi komai yi zaki yi, tinda an iya bin qattin qauye masu bada dari da hamsin"
Hawaye take zubar wa sosai saboda tausayin kanta a ganin ta ba abinda yafi sharrin zina da sata baqin ciki a duniya, haushin ta bai wuce yanda yama qi ya saurare ta ba sam, ya tsaya ta masa baya ni yaqi, kawai sai ta maida kanta ta kwanta, bata qara furta komai ba har ya shirya ya fice, kuka take mai ban tausayi,cikin kuka ta ce,
" Oh ni Salma na saiwa kaina wahala daga 'yar shawarma da motar dana gani duk na rud'e yi yau ga inda na kawo kaina, Abuja ko wahala?"
A can qauyen su Talle kuwa
da kyar Marka ta miqe ta je ta hada wuta ta shiga ruwan dumi ta gasa jikin ta,bayan ta gama ta zubar da ruwan ta yi daki, komawa ta yi ta ci gaba da kwanciya, wani qaramin yaro ne shafi'u daya d'aga cikin yaran tsofaffin matan Talle ne ya shiga d'akin ,yaron zai kai shekara goma, baya jurar yunwa shi, dan ko da su Huwaila na baccin gajiyar iskancin su da suke sheqewa da dare, ita Marka takan tashi ta yi abin kari da wuri, to yau sun ji shiru kowa dif a gidan, tura kai ya yi dakin ba sallama, to ba a Koya masu ba,Marka na kwance ta ware qafafu tana ta firfita da mafici,bata ji motsin yaron ba sai maganar shi ya na fad'in,
" Marka yunwa muke ji"
Da sauri ta sake zanin ta ta juyo kan shi,ta qanqance ido sannan ta ce,
"Me kace?"
Cikin dauriya yaron ya ce,
" cewa na yi yunwa muke ji"
Kiran shi ta yi tace ya je ya karba, yana isa data damqe shi ta hau duka, tare da fad'in,
" Yau sai na fanshe duka na da uban ka ya min a jikin ka ,baka da labarin ta'annutin da uban ka ya min shine har abinci ka zo ka na tambaya? Ga shi yanzu na san tinda ya dauke waccan jaja amaren sai na gan shi kuma, to kuwa yau zaka ci abinci har ka qoshi,"
D'im d'im d'im kawai ka ke ji na tashi a d'akin Marka ta na ta dukan dan mutane,
" Marka lafiya me ya yi miki haka ki ke dukan shi kamar kin samu jaki?"
Cewar wadda ta shiga d'akin ta na qoqarin kar bar yaron a hannun Marka da ta haukace da b'acin rai,ganin da gaske yarinyar take yi zata karɓe yaron a hannun ta gashi bata ji ta huce ba, kawai sai ta sakar wa Haulen wani mari itama a kuncin ta mai shiga ƙwaƙwalwa.
Makaranta na taqaice maku labari a ranar nan duk wanda ya yi gangancin shiga d'akin nan nema wa su Haule taimako sai ya karɓi nashi ɗaukan,idan ta na dukan wannan wani ya shiga sai ta saki na hannun ta ta kama sabo ta daka, haka ta dinga yi kamar wata mahaukaciya, sai da ta gaji jikin ta ya yi laushi sannan ta kwanta tana kukan baqin ciki kamar wani ne ya aike ta qulla wa kishiya sharri,cikin kukan ta ne ta ke fad'in,
"Wayyoo ni Allah na Marka yau na shiga uku na qulla sharri gashi ya zame mini bala'i,na yi abinda zai jawo wa kishiya baqin jini a wajen miji ni kuma sun tattara sun wuce binni sun barni a qauyen"............
[18/07, 8:26 am] asiyahabibu93: 💅🏼 ' YAN ABUJA 💅🏼
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
Page 17:
Tun da Jabeer ya sai wa Juwairiyyah waya ba su samu suka haɗu da Nafee ba sai da aka kwana biyu,domin kuwa a washegarin ranar Nafee ta tafi gidan wata qanwar Innarmu ta yi masu kwana biyu, dawowar ta da yammar ranar ke da wuya Juwairiyyah ke nuna mata wayar cike da zumud'i da murna,cikin fara'a ta amsa sallamar Nafeen sannan ta qara da,
"Wa'alaikumussalam shigo shigo yar uwa kiga me yayana ya sai min da bakya nan"
Da sauri Nafeesah ta qarasa shiga itama cike da d'okin ganin me za a nuna mata, sanda ta gani itama 'yar qaramar qarar murna ta yi ta haye kujerar da Juwairah take tare da fad'in ,
kaiiiii amma Allah ya saka ma Yah Jabeer da alkairi, ya sai mana waya mun daina leqen ta qawaye"
"To malama ba wai an sai mana waya ba na dinga neman ta ina rasawa"
"Hhhhhh Allah baki hakuri ai wannan wayar inna ɗauke ta kema kin San zan ririta ta, yanda kk san jariri haka zan kula da iya sai kin neme ta sannan zan miqo maki, ko kuma idan tana buqatar a sa mata kudi"
Dariya suka yi a tare sosai, sannan Nafee ta ce wa Juwairiyyah,
" Yauwa wai ni ruwan meye wancan a butar qarfe na ga kin saka a garwashi? Tunda na shigo nake jin kamshin na tashi ko shayi za mu sha ne na musamman"
Dan dafe kirji Juwairiyyah ta yi sannan ta ce,
" Oh ashe ban cire ba dama? Dan je ki sauken dan Allah ki dawo na fada maki hajiya tambai"
" Ah tohhh dole ki min bayani dalla dalla dan kin san in baki fad'an ba baki da zaman lfy yau"
Fita ta yi ta sauke mata butar ta dora ruwan wankan ta , ta koma dakin, zama ta yi tare da tanqwashe qafa agaban Juwairah tace,
" To malama a bamu darasi, dan zama dake akwai diban ilimi"
" ke ko, ke ko, hmmm kina raina sanin da Allah ya baki ne amma kin fini ilimi ai, kefa duba ki gani yanzu ci gaba da karatun ki kike yi ni fa ina zaune a gida kullum ba wani ci gaba da karatun da na ke"
" kema zaki ci gaba ne watarana komai lokaci ne sis kar ki damu,oya ina jin ki meye wancan a butar qarfe?"
Dariya Juwairah ta yi sosai sannan tace,
" ke dai ba ki mantuwa to magani ne, maganin infection musamman na masu ciki, Mama Bilki naga ta yi lokacin cikin Ammar shine nayi, Oh har naji ina son ganin yaron nan "
"To na ji magani ne amma ai baki fad'an ya ake haɗa shi ba ko"
"Haka ne, kinga dai da fari zaki samu ganyen garahuni, da 'ya'yan hulba ki tafasa su sosai sai ki bari ya sha iska sai kina tsarki da shi, da yawan masu ciki suna fama da infection sosai, mai fidda ruwa kala2, amma da zasuna amfani da wannan zai masu magani duk da ba wai yana ɗauke shi dika bane kwata2 amma yana ragewa sosai, in aka hada da wasu magungunan na sanyin ana sha, kin ga na ciki na mutuwaaa na waje ma ana kashe shi, amma idan mace bata da ciki zata iya neman sassaqen sanya,bagaruwar mata,lemon tsami, d'anyar citta,kaninfari,masoro,kimba,danyen kurkur, ganyen magarya,sai ta haɗa su waje ɗaya ta dafa ta dinga shan ruwan, ta yi na sati biyu ita da mijin ta da kishiyar ta idan mai kishiya ce saboda su yi maganin abin a lokaci d'aya, in shaa Allahu Zaki ga an samu sauqi gefe d'aya ana tsarki da wancan ruwan garahunin,sannan wannan had'in ga masu neman haihuwa in dai matsalar ta danganci infection to da yardar Allah zai wanke mahaifa a samu ciki, sai dai kuma idan matsalar ba wannan bace sai a nemi maganin matsalar,"
"Yauwa 'yar albarkan Yah Jabeer ko ke fa, ba ga shi kin qara min ilimi ba ni ina ma na san wannan abun in ba yanzu ba, yauwa rannan ma na ji kina faɗa ma shamsiyya wani abu lokacin na fita ban ji me kuke cewa ba game da warin gaba dan Allah ki yi min bayani akwai wata a department din mu ba zaki so zama kusa da ita ba sam saboda wari"
" Ohh wannan ai ta na tare ko da babbar matsala gaskiya,in ki na so ki yi maganin matsalar warin gaba dole sai kin san kala kalar shi,na farko dai akwai na lalura, akwai wanda mace da kanta take jawo wa kanta"
"Hhhhhh ka ji Matar yaya wai mace ta jawo wa kanta to kamar yaya? Kana sane kabar jiki ya yi ta tsami"
Dariya suka yi a tare sosai suka tafa, sannan Juwairiyyah ta ce,
" Allah da gaske nake yi, yanzu misali Nafee, ke ce kin tashi a rana kin wuni da pant ɗaya a jikin ki, kin je fitsari kin yi fitsari baki wanke wajen sosai ba kin maka pant kin mayar, kin yi bayan gida kin maka kin mayar, sannan da jiqar da komai ki ke mayar wa, ki fadan min shi pant din d'an uwan ku ne da zai qi yin wari?"
Wata iriyar dariya Nafee take yi, cikin dariya ta ce,
" Whhhhhh alqur'an dole yayi wari, amma dai misalin nan dama ba dani aka buga shi ba a canja gaskiya a saka Salma"
" wulaqanci Yayar tawa, Allah sarki mutan Abuja ana can ana shan daɗi an manta da dangi"
" Hmmm ke dai bari buri ya cika, Allah muma ya sada mu da mafi alkairi"
" Ameen dai"
" To yanzu fad'an ya za ai ayi maganin wannan warin dan Allah dan akwai yar makarantar mu na faɗa maki, da kin zauna kusa da ita sai kin ji wannan warin,ni ba zan ji kunyar faɗa mata duk bayanin da Zaki yi min ba, da azo ana ta gulmar ta ko ana gudun ta ta na jin haushi ai gwanda a faɗa mata matsalar ta da maganin matsalar ta gyara ko? Wataqila bata samu iyayen da ke koya mata ba kin san wasu iyayen ba su koya wa yara su komai kin dai gane me nake nufi"
Ta faɗa tana nuna hanyar sashen Innarmu,qunshe dariya suka yi sannan Juwairiyyah ta ce
" Allah sarki, aiko gwanda ki sanar da ita, dan aboki na gari ke wayar da kan abokin shi idan ya ga irin haka na faruwa da shi,to kina ji ba,na son a rana a baki canja pant ba ki canja sau biyu, ya zama na kina da tsimma ko towel qarami a toilet din ki wanda in ki ka yi fitsari ko bayan gida zaki tsane wannan ruwan bayan kin yi tsarki tunda yanzu yawanci banɗakunan na masu da shi ne tsarin ginin za ka iya ajiye qaramin towel,sannan in kin zo tsarki ki fara da gaba ko da baki yi komai ba, sannan baya ya zama na qarshe, karki hade wajen a lokacin wankewa, in kika gama ki goge wajen sai ki maida pant din ki, in rana tayi kika yi wanka sai ki canja,in da hali da dare ma kan ki kwanta ki caja, ba yanda za yi a same ki da wari ko da baki shafa misk ba, balle a same ki kina wanke wajen da ruwa mai dumi da ki ka zuba musk, ko ki saka ruwan d'umi kaɗan bayan kin gama wanka ki tsiyaya zuma asalin mai kyau ki wanke gaban ki da shi,yana daga taskar magunguna da ya kamata muna amfani da shi, bake ba warin gaba in dai kina wanke wa da ruwan zuma kina saka misk, kina tsanewa in kinyi bayan gida, ina fatan na amsa tambayoyin ki gaba ɗayan su yanzu Hajiya tambai"
"Hhhh kwarai da gaske Juwaireren Mama da Yah Jabeer kin biya ni kin amsa har da wanda ban ma zata ba ke dai Allah ya barki da yaya, ya sauke ki lafiya"
Cikin jin daɗin addu'ar Nafee ta hau shafa cikin ta sannan ta amsa, tashi ta yi ta shiga bayi dauke da butar ta a hannu, bayan ta fito ne take ce ma nafee,
" Nafee na ga kina zare ido, kar fa ki je ki yi fitsari ko ba haya ki hau tsarki da ruwan almiski kin dai san ba ya tsarki , ana tsarki ne da ruwa mai tsarki kuma mai tsarkakewa,ah toh gwanda na yi maki bayani dalla dalla kamar yanda ki ka ce, yauwaa kin San fa gobe ne ranar gyaran jikina ina zan samu dankalin turawa pls na wa ya qare,dan Allah in an samu ki zo ki taya ni kin dai ga yanda na koma ba zan iya yi ba ni kaɗai"
"Haka ne bayanan ki, maganar dankali kuma kar ki damu zan samo maki kan goben in shaa Allah,in ba ke ba ma wa yake ta wani gyaran jiki a wannan yanayin,ji cikin ki fa ya girma amma kk maganar gyaran jiki, ki bari ki haihu mana"
" Tab a'a ni dai ki samo min, in babu ma ina da zuma da sugar sai na yi amfani da su kawai lemon zaqi ko ɗaya ne ko biyu Zaki samo min"
"To Allah ya kaimu da rai da lafiya bari na yi wanka na fita makaranta"
"To Allah ya bada sa'a, bari na dan huta nima".
*****************************
A Abuja garin shugaban qasa kuwa Talle ne ya sanya manya kaya har da hula shiga dai ta kamala ya yi ranar ya sanya Salma yin shigar kamala Itama suka shiga sashen uban gidan shi dan ya gabatar da Salma a matsayin iyalin shi, cikin wata murya mai cike da ladabi Talle ya ce,
" Alhj wannan itace mata ta da kuka Karb'a min auren ta a garin kano, dama na dawo da ita nan ne dan na dinga samun kulawa, zama ni ɗayan ba daɗi"
Talle ya fada yana sosa qeya, murmushi uban gidan na shi ya yi sannan yace,
" Allah sarki ai ba damuwa, hakan da ka yi kayi tinani mai kyau,sannan kuma ka kyauta, ina maku fatan alkairi, Allah ya bada zuri'a dayyiba"
" Ameen"
Gaishe shi salma ta yi kanta a qasa tana wasa da gyalen ta,shi kuma ya amsa ba tare da ya kalli in da take ba, kuɗi ya qirgo dubu goma ya bata, yace gashi ta sai wasu abubuwan da take buqata, amsa ta yi hannu na rawa,dan kuwa rabon ta data riqe kuɗi haka ai ta manta, tashi suka yi suka fito, suna isa daki ya miqa mata hannu fuskar nan ba walwala, ita ma ta d'aure tata fuskar ta ce,
"Me zan maka kuma"
Ta karasa maganar ta cikin tsiwa,
" Kee! ni za ki tambaya me zaki min, to in baki san me zaki min ba bari na fada maki, kawo su nan"
Alamun da ta gani na ba wasa yasa ta miqa masa kud'in tana hawayen baqin cikin ganin samu ga rashi a lokaci d'aya, murmushi ya fara yi saboda jin dumus ɗin kuɗi da ya yi,
" Ko ke fa salameme na, yanzu ai kin ga ko dari biyar na baki ai yafi na qattin qauye masu baki dari da hamsin ko"
Juyo wa ta yi cike da bala'i tana kallon shi kuma sai ta fasa yin maganar da ke bakin ta ,wani irin tsoron shi ne kamata saboda yanda yake kallon ta,gani ta yi yana cire kayan shi ya na nufar ta, hankalin ta ne ya tashi dan ko bata shirya ba masa ba har a wannan lokacin ciwon jikin da take fama da shi bai tafi dika ba, gashi shi in ya fara abu bai san ya bari a huta ba, sai ya gajiyar da mutum, kuka ta fara tana fad'in,
"Ni na bar maka ɗari biyar ɗin dan Allah ka bari sai nan da kwana uku, na gaji banda lafiya fa ka sani"
Dariya Talle ya yi sosai ya maida kayan shi, ya kalle ta ya ce,
" Da kyau matar manya matar Ɗan Abuja, ku baku da buqatar kuɗi ai, ni na fita to ga wannan ki leqa waje akwai shago ki siyo kwaki da sugar ki sha, ina jin har canjin gyada zaki samu ma a ciki"
Nera ɗari biyu ya wurga mata ya fice yana wata tafiyar yan duniya a shagide, kuka Salma ta durqusa a wajen tana yi tare da fadin,
"Wai ni ina yan uwana ne, suna can suna jin daɗin su sun manta da rayuwa ta, basu san a halin da nake ciki ba,Oh Allah ka kawo min ɗauki, Allah na tuba, Juwairah kin huta, da baki bi zabin aure irin nawa ba, gani ina cin ubana a garin da na taso da kwadayin yin auren a cikin shi, na manta da neman zaɓin alkhairin Allah a lamura na,wataqila da na nemi zaɓin Allah da ko mummunar jarabawa Allah ba zai haɗa ni da ita ba a Abuja,sai na biye wa son zuciya gashi ina ganin b'acin zuciyar har da gangar jiki na, wayyooo Allah na na shiga uku ni Salma ina zan saka kai na?"
kuka take ta yi mai ban tausayi, yunwar dake cin ta ce ta dawo da ita cikin hayyacin, tashi ta yi ta wanke fuskar ta, ta saka mayafi ta je ta siyo garin ta da sugar da gyada, haɗawa ta yi tana sha tana kuka,ganin duk talaucin su a can gidan iyayen ta ba su shan gari, amma yau gata da gari ba isasshe sugar , share hawayen ta ta yi, ta jingina da katifar su, a haka baccin wuya ya dauke ta.
****************************
Parlour ne na alfarma da ya sha kayan more rayuwa kala da kala, matan biyu masu ji da kyau da nera na zaune su na shan kayan marmari da lemo irin na manyan kwalaben nan mai tsada, saudat ta kalli yayar ta ta da tsabar kwanciyar hankalin da take ciki ya sa ta dan yi qiba kaɗan irin mai ban sha'awar nan ta murje fata sai sheqi take, alamun bata da wata matsala a rayuwar ta, dan gyara zama Saudat ta sake yi a karo na ba adadi sannan ta ce,
"Ni kam Adda Suwaiba ki na tunanin kai ziyara gida kuwa? Ina gani fa ya kamata mu je ganin gida yanzu haka, haba tinda muka zo yau watan mu na takwas kenan fa muna cikin na tara amma bamu taba zuwa gida ba sannan ba a taɓa zuwa mana ba, ga labarin Salma shiru, har yanzu ko waya bamu yi mun ji daga gare ta ba"
Iska Suwaiba ta furzar sannan ta kora jusi ta ajiye glass cup ɗin ta ce,
"Hakane kam ya kamata muje muga ya su Goggo suke, batun Salma ki daina damun kanki tana can suna cin amarcin su a qasar waje da dikkan alama, kin san mijin ta ma ba laifi akwai kudi, wataqila ma basa qasar nan fa"
"Haka ne kuma Allah dai ya jiyar da mu alkairi, amma nikam na tambaye ki mana,"
"Uhumm Ina jin ki"
"Dan Allah baki taɓa zargin komai game da mazan nan namu ba kuwa?"
Ɗan yatsina fuska Suwaiba ta yi sannan ta ce,
"Kamar ya fa?"
Tina wa da ta yi in ta sake Suwaiba ta san me ake ciki kashin su ya bushe, dan haka sai ta yi saurin kauda zancen ta basar tace,
"Ba komai yanzu dai mu tambaye su, yaishe zamu je gida"
" Ba rana balle wata"
Amsar da suka ji kenan ana basu bayan an bude qofa an shigo,cikin haɗe fuska Alhj Ƙalla ya kalli Saudat ya ce,
" Ke tashi mu tafi gida, ai an sada zumuncin haka, ku da kuke son Abuja kamar ran ku in ban manta ba, Saudat kan mu yi aure cewa fa ki kai, in Allah ya baki miji kuka tare a Abuja sai kin shekara biyar baki je ganin gida ba, ko ba ai haka yi ba?"
Cikin qunar rai da kwallar da ta maqale mata tace,
" Anyi haka, amma a da ai ban da isasshen sanin ya Abujan take kuma gani nake zan iya amma ni yanzu gaskiya gidan mu nake son zuwa naga uwata"
Wani hatsabibin kallo ya watsa mata wanda ya sa ba ta san sanda ta durgusa ta dauki jakar ta ba ta yi hanyar fita, sallama ya yi wa abokin shi wanda daga jin warin da suke yi zai sa mutum ya san sai da suka biya suka yi mankasss sannan suka dawo gida.
Nikam nace Saude Allah shi kyauta karki daku yauma.......😂
[18/07, 8:26 am] asiyahabibu93: 💅🏼 'YAN ABUJA 💅🏼
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
Page 18:
Tabbas gaskiyar mutane ne da suke cewa wani talakan bai iya samun waje ba, da ya samu waje sai ya dinga wulaqanta mutanen da bai kamata ya wulaqanta ba.
Goggo Sarai na daga cikin irin wadannan mutane masu wulaqanta duk wanda suka ga sun fi qumbar susa,rashin iya cin arziqi da baqin ciki ne ya
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 25