Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
BY HAERMEEBRAERH Page 9: Tunani suwaiba ta zauna ta na yi bayan ta katse Kiran da ta yi wa Goggo, so take ta tuna abubuwan da suka faru amma kanta ya kulle sai ma wani irin bugawa da ciwo da ta ji ya na mata, komawa ta yi ta kwanta a hankali,ajiyar zuciya ta sauke a qoqarin ta na dena tinanin, " Babe what is wrong, na ga gaba ɗaya mood ɗin ki ya sauya" A hankali ta furta, "kai na ke min ciwo sosai, so nake yi na tina abubuwan da suka faru a tsakanin wannan watannin da akai auren mu amma gaba ɗaya na kasa" Cikin sigar lallashi ya kama hannun ta ya ce, "ki dena yawan tinani likita ya hana, saboda zai jawo maki ciwon kai mai tsanani, ki kwantar da hankalin ki kin ji, aikin da akai maku ne yasa kuka kai wadannan watannin ba tare da sanin inda kan ku yake ba, ni dinnan da kk ganni sai da nai sati uku a asibiti ban san ina kai na yake ba, abokina kuma wata daya da sati biyu, kafin mu ka ji sauqi ai ba karamin abu ne ya faru ba a ranar" Tausayin kansu ne ya kamata, lallai ashe hatsarin babba ne? A haka bacci ya ɗauke ta shi kuma ya yi palour yana murmushin samun nasara, waya suka yi da Alhj Kalla, cikin nishad'i suka fara hira, "Aboki ya ka qare da 'yar rigimar ka?" "Ba wata damuwa Komai ya tafi as planed, ban samu matsala ba, wannan shegiyar uwar tasu ce taso sawa mata ta tinani,amma na kawar da shi, yanzu haka bacci take yi" Sariya suka saka a tare sannan Alhj Ƙalla ya ce, "Ai ni tashi ta yi tana min shagwaba sai na ji kamar na manta da ciwon na dan more ta kadan, dan sai ta min kyau sosai, gaskiya mun iya zaɓe aboki na, kyawawa na gidan talakawa a b'oye talauci duk ya rub'ar da wasun su, su zo a fantama da su a samu kuɗi amma sai ka ga sun ki wai su na Allah, yanzu su wadannan da suka fito ba gashi sun haɗu da mu ba za mu shagwab'a su da nera? Ga kyau ka kuɗi Alaji" Dariya Alhaji Salihu ya yi sannan ya ce, " shegen sama, ana halin neman yanda za ai a rufawa kai asiri kana neman biyan buqatar ka, to amma fa mutumi na suna da gaskiyar su,mu ɗin ba rud'in shaid'an muke bi ba, ai tsoron Allah ne ya hana su fitowa gwanda su je lahira su shiga aljannah, mu ma dai kafin mu mutu mun tuba," (Kamar an sanar da su ranar mutuwar su) Dariya suka yi ta yi kamar abinda suke faɗa ɗin ba wani abun damuwa bane,Alhaji Ƙalla n e ya ce, " Anyway gate can dai na yi mata dabaru irin namu na manya ta bar zance fatan ta Allah ya bata lafiya, kasan har yanzu maganin bai gama sakin su ba, bacci take ta yi" "Haka ne, to sai dare in mun hade a gidan Oga, yau akwai meeting fa ka san" "Eh haka ne fa,to ba damuwa sai daren ma haɗe a can ɗin" kashe wayar suka yi kowa na jin daɗin samun nasarar da suka yi akan su suwaiba mutanen ABJ, yanzu tinanin su bai wuce yanda zasu na samun jini da aka ce suna kawo wa duk wata ba daga matan nasu, dan su ba sa son suna satar 'ya'yan mutane ana tsafi da su shi yasa suka yanke shawarar auren matan da za a dinga amfani da jikin su da kuma jinin su ana tsafin,dan satar yara a wajen su babban aiki ne da kuma wahalar wa,sannan su na tsoron kar watarana a kama su, dabara ce ta fado mai na yanda zasu na samun jinin daga wajen su, murmushi ya yi sosai,sannan ya ce, "Dan ta rashin haihuwa me sauqi ne, tunda ba ni aka cirewa mahaifa ba bare na damu, 'ya'ya dama takura ne a rayuwa ta, sanda na so haihuwa na nemo matar da zan haihu da ita na aura," Dariya ya dinga yi kamar mahaukaci sabon kamu ni ko nace hmmmmm kwadayi mabudin wahala. ***************************** A gidan Salman Talle kuwa, ko in ce Tallen Salma, ko kuma Tallen Marka, ana can ana badaqala uwa ba hantara uba baya nan sai ya ga dama ya leqo ya koma. Huwaila ce ke duqe gaban murhu ta na hura wuta, can ta d'ago ta yi wurgi da maficin hannun ta ta na buga qafa a qasa ta ce, " Ni dai Marka gaskiya na gaji da yin abinci kusan kullum a gidan nan habaa ai ni ba baiwa bace,kullum ni nake abinci talla sannan na yi na gida ?" "Nima haka gaskiya, wannan yar rainin ajawalin na zaune a d'aki kullum sai dai mu dafa mu bata, ga Baban ma baya nan sai sanda ya ga dama yake zuwa" "Tab ai ko yau ita zata yi tuwon dare ko ta ji a jikin ta, ni hutu ya samen, dan ba zai yu na nemo na tuqawa ba kuma na dafa na ba ku ku ci ba inaaaa, dole Itama ta fito ta girka ai gidan mijin ta ne itama" Ihu 'yammatan suka sanya suna fad'in, "Sai Markaaaa, uwar gidan Talle, an buga an barki" Dariya da shewa suka sake sanya wa kamar wasu 'yan daudu, ita kuma marka ta wani d'age qafa tana zaune a qasa ta turo dankwali gaba, tana kada qafarta da ta yi fururu kamar tunda aka haife ta bata san menene nan shafi ba, " Je ki kiran ita Huwaila yanzun nan" Da hanzari Huwaila ta miqe kuwa tana gyara daurin qirjin ta, tana tafe tana banqaro qirji, qugun kamar an daurawa tabarya zani, ta na Isa qofar d'akin Salma sai ta tsaya a bakin kofa ta daga labule ta cake tare da kama qugu ta ce, " Amarya ki zo Marka na son magana da ke yanzun nan" Salma na kwance ta ji Huwaila na mata magana cikin raini sai ta ji kamar ba zata amsa ba dan kuwa duk tana jin su, sai dai kuma wani irin mugun tsoron su take ji yanzu, dan duk wani rashin mutunci da yake faruwa a gidan ya na shiga kunnen ta, yau da gobe duk tana jin su, fitowa ta yi dan ta tsira da jikin ta, dan yanda suke ikirarin dukan ta kullum tasan za su aikata,ga uban su baya nan, ko yana nan bata jin a tarbiyyar gidan Talle zai ɗauki mataki sun dake ta sun daki banza a banza ne kawai, "Auuu kinzo shine ba zaki yi magana ba ma ki ka tsaya qiqam akan mutane haka?" Cikin tura baki gaba ta ce, "Gani" Saida Marka ta kalle ta asheqe sannan ta ce, "Salma ki ke ko wa? Ni kin San ba sabgar ki nake shiga ba balle na riqe Sunan ki,ki bude kunne da kyau ki ji, daga yanzu ke zaki dinga girkin gidan nan na safe da rana da dare, su yaran sun ji da na siyarwa, ba zai yu na yi ta wahala ba a gidannan, ke kina nad'e a gado, sai dai na dafa na miqa maki, ki cinye ki gyara d'aki ki yi wanka ki koma ki kwanta, ai ba abinda ya kawo ki gidan miji kenan ba, bautar aure kika zo yi, dan haka kula da yaran tsakar gidannan ma yana ciki, tsarkin kashin su da yi masu wanki, duk naki ne yanzu, in dai hutun amarci ne sati ɗaya budurwa, bazawara kwana uku, ke ko ban san ame zan saki ba, tsabar adalci irin nawa wata biyar da kwana hudu na baki kika huta, dan haka daga yanzunnan ba sai anjima ba ki dau aikin ki" " Wooo ke wooo ke markan Talle" Yaran suka dauka suna ta mata kirari tana kad'a qafa tana hura hanci su kuma suna dariya, kallon Salma da ke tsaye ta na kukan zuci ta yi ta ce, "Ban ji kin amsa ni ba fa" Cikin rawar murya Salma ta ce, " To" Ta juya zata tafi ta ji wani daga yaran na fad'in, " Naaa gaaamaaa" Kukan da take ta yi a zuci ne ya taso mata da karfi,nan take ta tuna da tinda take bata taba ɗaukan Ammar ba ma balle ta kai ta ga yi masa tsarkin kashi, gashi yau za ta yi wa ɗan wasu tsarki, kuma an maida hakan aikin ta. Cikin Isa Marka tace, "Ba ki ji bane ana sanar da ke an gama kashi ki je ki wanke sai kin gama qamar da dan mutane?" Sim sim sim Salma ta wuce zata je wanke masa kashin,Haule ta taso tace wa Salma, " Aunty bar shi na wanke masa" Marka ta sauke qafar ta da ta ɗora a d'ayar ta kalli Haule ta ce, "Ke uwar kitifi uwar kinibibi, ina ruwan ki da hukuncin dana yanke? To a hir din ki kar kina min haka ranki zai mummunan baci, ita na ga dama ita zata wanke" Salma ce ta kalli Haule da murmushin yaqe ta ce, "Na gode Haule zan masa kije kawai ba komai" Wanke wa yaron kashin ta yi zuciyar ta na matuqar tashi, tana fitowa daga band'akin wajen zubar da na poo ɗin yara suka kwashe da dariya har da uwar tasu suka tafa, murhu Salma ta nufa ba tare da ta tanka su ba to me ma ta isa ta ce? Ta na Isa ta duqa ta ci gaba da hura wuta ta dora ruwan tuwo, ranar dai a taqaice ba ita ta kwanta ba sai goman dare, jikin ta ba inda baya yi mata ciwo dan aikin wahalar da ta tiqa, tuwo ta tuqa da ya kai yawan kwano ɗaya da rabi har na dumame, dan haka tana kwanciya ta hau bacci kamar wata matacciya. ************************** " Dan Allah Juwairah ki yi sauri mana, duk wannan wankan naki na qa'ida sai ya sa ba mu fita da wuri ba" Nafeesa ke jiran Juwairah da ta gama girkin rana wajejen qarfe sha daya na safe,ta kammala gyaran gidan tsaf tana son yau ta je ganin Maman ta , Nafee tace zata yi mata rakiya, dan haka ita har ta shirya amma Juwairah na can na wanka, can bayan kamar minti takwas ta bude ta fito daga bayin ta na fad'in, " kin san Allah, ba dan kina jirana ba sai na qara five minutes, ya zan na yi wanka jikina bai fita ba, kowanne bangare a jikin mace fa ana son amasa wanki mai kyau, musamman lunguna da saqon jikin mace ke har kunne da cikin kunne sai na wanke, haka kurum Yah yazo min soyayya a kunne ya ji d'acin datti" Cike da tsokana Nafee ta ce, "Inyyee iyayen love, aiko ba zan gangancin wanke kunne na ba ruwa ya shige min a banza a barni da zuwa asibiti da jin azaba" "Hhhhhh dad'ina dake komai baki iya ba, in zaki yi ai dabara zaki yanda ruwa ba zai shiga ba, tinda kinga yawan goge kunnen nan likitoci na ta hanawa bai da kyau, to sai ki samu ki karkata kunnen ki gefe d'aya, ki wanke ta baki bakin da lungu da saqon shi, in kk gama kik d'auraye sai ki saka towel ko zani ki tsane ruwan tas, in kika gama da b'ari ɗaya sai ki wa bari ɗayan ma haka, kinga ba ruwan da zai shiga kuma kin wanke shi fesss" " kaiii Juwairah wayon ki da sanin yakamatan ki na ban mamaki, dan na kula wataran Mama Bilki ma mamakin ki take sosai akan halayyar ki" "Hmmm tashi to mu wuce na gama shirya wa" Tashi suka yi suka tafi bayan sun leqa sun yi wa Su Innarmu sallama ita da Baba Balarabe, qara masu kud'in mota ya yi yace su gaida mutan gidan in sun je, kar su yi magariba a can su dawo gida amsawa suka yi suka yi godiya suka tafi. Da sallama suka shiga gidan, cikin zumudi ta fada dakin nasu, Mama Bilki ce ta fito dauke da fara' a sakamakon gane mai sallamar da ta yi, a hanya suka haɗe suka rungume juna suna ta murna, Ammar ne a gefen maman, da sauri ta dauke shi tana masa kisses ko ta ina,cikin farin ciki ta ce, " I missed u so much my baby brother, how ar u doing my love?" Dariya yake ta yi kamar ya gane ta yana ta surutai irin na yara masu son yin magana, dariya ta yi ta aje shi a cinyar ta suka hau gaisawa, Nafee ma gaida Mama ta yi, tana mai jin daɗin yanda taga soyayyar 'ya da uwa a tsakanin Juwairiyyah da Mama Balki, Goggo ce ta fito ta na shewa ta na dariyar shaqiyanci ta ce, " A'a mutanen kano ta dabo ci gari jalla babbar hausa, ne a gidan namu yau kuma?" Goggon ta qarasa tana dariya, Nafee da ta san irin zaman doya da manjan da ke tsakanin Goggo da su Mama Balki sai ta karɓe maganar ta ce, " Kano ko da me kazo an fika ba, in mutum ya faɗi alkairi yanzu mu bashi amsa dan gidan ya tarar amma in ya kuskure nan ma sai muje maqota mu yi aron rashin mutunci mu bashi amsa da kalar yaren shi" Nafee ce ta qarasa maganar ta ta na murgud'a baki da fari da idanun ta, Mama ce ta kalli Nafee ta ce, "Kul Nafeesa, ai uwa ce Goggo a wajen ku, kome zata yi kar ku tanka ta, ku barni da ita nice daidai ita" Goggo Sarai ce ta buga cinya ta tafa hannu sannan ta ce, "Hahaiiiiiiiiii Casssssss a hakan? A hakan ne kike daidai da ni? Daga shekaran jiya da yarana suka min waya zuwa yanzu kudin da suka shigo mun ta akawun ( account) ba qanana bane, ke kuma fa? Me ta kawo maki, tuwon dusa miyar lalle?" Dariya ta kwashe da shi sosai harda riqe ciki,Baba Baballiya ne ya shigo ya ji abinda ke faruwa cikin ɓacin rai ya ce wa Goggo, " ke dai anyi sallamammiyar mace saratu, yanzu me kike yi kenan? Kin tsaya kina rashin mutunci gaban yara, ke da baki da kamun kai, baki son a zauna a gidannan lafiya, kullum sai kin nemi tijarar da ki ka qirqira aka yi a gidan nan kar ki zaci ban sani ba ina sane da duk abinda ki ke yi, ashe yauma ba zaki sawa kanki salama ba?" Juwairiyyah ce ta tashi da sauri dan ta kauda maganar da Baban nasu ke yi ta ce, "Oyoyo Baba na da gudu ta je wajen shi ta rungume shi, shima rungume ta ya yi ya kama hannun ta suka zauna, qasa ta duqa ta gaishe shi, Nafee ma haka amsawa ya yi cikin nishadi" Ganin haka sai ran Goggo ya sisi, ta kalle su ta ce, "Ehhhhh lallai ne yau 'yar so ta zo, ka balbale ni da bala'i a gaban su mana, yarana tunda suka tafi baka neme su ba, amma wannan nunar ranar kullum sai ka tambaye ta, yau kuma ji yanda kk rungumar yar cikin ka kamar a gidan qabila" " Ke malama in baki da abin faɗa mai kyau fita ki ban waje, Jahila kawai wadda bata san me ake kira da musulunci ba balle ta san abin cikin shi" Magana Goggo ta buɗe baki za ta yi,Baba ya daka mata tsawa, ba yanda ta iya dolen ta ta fita tana qunquni, ci gaba da gaisawa sukai yi sosai ya zauna suka yi ta hira da 'yar tashi,haka dai har lokacin tafiyar su yayi, Mama ta tashi ta hau dan harhad'a mata wasu abubuwan iya qarfin ta dai, sallama suka yi tana kuka suna lallashin ta suka rabu. Su kuma su Juwairiyyah suka koma gida,ko da suka isa gidan sun zaci za su tarar Innarmu ta dora girkin dare sai suka ga sab'anin haka, murmushi Juwairah ta yi ta shiga ta canja kaya, sannan ta fito ta hura wuta ta dora taliya a cikin kayan da mama ta basu, ta hada da ganyen alayyahu da albasa, ta daka yar daddawa kaɗan dan ba isasshen maggi to daddawar zata taimaka abincin ya yi daɗi , nan da nan ta kammala ta fada wanka abunta kamar ma ba ta yi ba. Hikimar gyara daki kenan a wajen mace kafin ta fita unguwa, in kika gyara gidan ki tsaf in da hali ma ki yi girki kan ku fita har na dare tunda baki sani ba ko ku jima musamman idan da mutane a gidan, da kin dawo to wanka zaki yi kawai ki zauna ki huta abinki, ba ruwan ki da zama cikin qazanta, da kuma taraddadin aiki a gaban ki,in dai da ran ki da lafiyar ki to ki qoqarta ki na tsafta. Juwairiyyah na fitowa daga wanka Jabeer ya dawo, fita ta yi ta amshi ledar hannun shi ta ajiye suka yi barka da dawo war su yanda suka saba, sannan ta ja shi bayi, sabon wanka ta sake domin cewa ya yi bata fita ba sai ya sake yi mata, tana dariyar gano wayon shi da ta yi tace, "To shikenan ka gama nima sai na maka naka muje muci abinci dan na gaji yau da wuri zan kwanta" "Tab yarinya ki daina zancen bacci da wuri ma in zaki bari" Yana maganar yana matsa cinyoyin ta da yake wankewa, yar qara ta yi ta shagwaba ta faɗa jikin shi, tana goga cinyar ta ta a jikin shi,ta ce, " Yah Jabeer akwai zafi fa" Yanda ta yi maganar a saitin kunnen shi ne ya sanya shi jin wani ya tsarga masa har tsakiyar kanshi , janye ta ya yi a jikin shi ya jiqa mata soson ya bata ya ce, " Yi sauri ki wanke ni nima ba zan iya jira ba baccin nake ji" Dariya ta yi ta amsa tana masa wankan cikin wani salon da ya amshe soson ya aje gefe ina ganin haka na ari qafafu wajen masoyan Juwaireren Mama na qara gaba a guje........ [18/07, 8:26 am] asiyahabibu93: 💅🏼     'YAN ABUJA    💅🏼 WRITTEN BY HAERMEEBRAERH PAGE 10 Dare ne yanzu a cikin garin Abuja,manyan Alhazawa ne masu ji da nera a wajen shaqatawa na wani babban hotel da ke cikin garin su na hutawa da 'yammata da samari, sai kai komo manyan 'yan mata masu ji da kan su suke yi a gaban Alhazawan saboda suma a dama da su wajen cin kud'in da aka samu na yaki halal yaki haram. Alhj Salihu da Alhaji Kalla ma ba a bar su a baya ba, dan kuwa su ma suna tare da 'yan matan su da bazan iya tantancewa arna ne ko musulmai ba saboda shigar banzan da ke jikin su,watace a cikin 'yammatan da na ji an kira da 'yar Gwal na kalla da kyau,daga nan na gane hausawa ne ma ashe ba arna ba,amsawa ta yi ta juya ta na kallo 'yar uwar tata da ta kira Sunan ta, nuni ta yi mata da ido, bin inda aka nuna mata ta yi da ido suna murmushi, "Mene ne na ga kuna wani dariya kamar wasu wadan da suka tsinci damin kudi a qasa?" Inji Alhj Kallah kenan da ya ga sanda suka yi murmushin, 'Yar gwal ce ta hau cinyar Alhj Salihu tana wani karairaya tana shafa shi sannan ta ce, " Alhaji na kuɗi muke so ne shi yasa, gaba ɗaya qawayen mu sun wuce mu a komai na more rayuwar duniya bayan duk tare muke wannan harkar kuma muna tare da manyan mutane kamar ku,gaskiya zai zama abin kunya ace ko motar hawa bamu da ita su da suke bin qananan kwari su na jan mota mu kuwa kullum sai dai mu yi waya ku aika a d'akko mu ko mu hau taxi, gaskiya yawa ne Alhaj" Tana magana tana kai bakin ta jikin nashi ta na masa wani salo mai ɗaukar hankali,wani irin nunfashi Alhj ya fitar da bai san yana ruqe da shi ba,a hankali ya ce, "Haba 'Yar gwal yanzu dan wannan qaddamar buqatar shine kuke wani abu kamar baqi, ai in kuna son abu kamar umarni zaku bamu kawai, dan haka,....." kafin ya qarasa maganar shi 'Yar Gwale da qawar ta suka tashi tsaye suka kama hannun Alhazan nasu dan kai su d'akunan da suka saba sheqe ayar su tinda sun ji buqatar su za ta biya, kuma Alhazan ba su yin alqawarin karya. Tin a hanya suka fara romancing din su, ina ganin haka na yi baya na koma gidan Suwaiba naga wainar da take toyawa. Hango suwaiba na yi tana zaune ta baza kaji a gaba da fresh milk tana darje baki, hankalin ta kwance ba ta da wata damuwa da ta wuce ta faranta ran ta da dukiyar da mijin ta ya ke da ita,hannun ta ɗaya riqe da waya tana dannawa, bayan ta gama cin naman ta ne ta shiga band'aki ta yi wanka ta yi brush, ta saka kayan bacci dan ta yi bacci, amma sam bacci ya qi ɗaukar ta,komawa ta yi palour ta kunna kallo, ta na kallo tana duba lokaci, wannan rayuwa anya za ta yuwu a haka kuwa? ace miji ba zai dawo da wuri ba sai dare ya raba? Tashi ta yi ta dakko fruit salad data hada ta saka a fridge, ta zauna tana kallo tana shan abunta, bayan ya qare ne, ta ajiye bowl din a gefe, sai hamma take tana miqa, duk ta gaji da zaman shirun, wayar ta ta ji tana ringing, miqa hannu ta yi ta dauka, Sunan Saudat ta gani na yawo a screen ɗin wayar ta ta, "Saudat love" Shine sunan da ta yi saving No Saudat da shi. " Hey sis" "Hi" "Ya ki ke, da yayan nawa?" " Muna lafiya, Ya Alhjn ki?" "Muna lafiya" "Dama kiran ki na yi na ji ko Baby na gidan ku, tsoro nake ji, gidannan ya min girma ni kaɗai masu aiki na bangaren su, duk dare sai na dinga ji kamar kirana ake," Ta faɗa cike da tsoro,shiru Suwaiba ta yi kafin daga baya ta ce, " Sis kiyi hakuri baya nan, nima zaman jiran mine nake yi yanzu haka, duk yanda akai suna tare, ki kwantar da hankalin ki ki mori abinda ya kawo ki, tin kan lokaci ya qure maki" Saudat amsawa tai da "To" Sallama suka yi suka kashe wayar Suwaiba ta tashi ta yi d'aki, bata jima da kwanciya ba, lokacin qarfe 2:45am ya shigo bakin shi duk warin giya, tsabar kwarewa da suka yi dan shan barasa ko layi na marisa  ba sa yi,sai dai a gane ta idanun su da ke yin jawur, da kuma saurin fushin su,Suwaiba ce ta miqe ta nufe shi a zafafe ta ce, "Wai wannan wanne irin wulaqanci ne Sweethert, tinda nazo gidan nan i can't remember the last time we had xxx, amma da na yi maka magana sai kace lokacin ban da lafiya a bari na wanke to yanzu da na ji sauqi ka kasa sauke nauyin dake kan ka, amma kai da dikkan alamu har yanzu kayi auren ma wasu kake bi a waje baka dena ba,ga wani sabon hali da na ga kana yi na shaye shaye wai ashe  har da giya ka ke sha wadda ni ban san kai din dan giya bane kuma d'an maye,wannan ai iskanci ne da wulaqanci" Suwaiba ta qarasa maganar cikin d'aga murya da masifa, a karkace Alhaj Salihu ya kalle ta ya ce, " Ni ki ke kira dan iska,ni ki ke kira dan iska ko, ba dai ni ki ka cewa dan iska ba suwaiba ? Yau Zaki ga iskanci ganin idon ki Suwaiba" Miqewa ya yi ya janyo ta ya hau duka kamar an aiko shi, a haka ya cire mata kayan jikin ta ya wurgar duk ya yaga su saboda kiciniya da dambe, wurgara gado ya yi ya ta kanta, Suwaiba kuwa ba abinda take da ya wuce kuka da neman taimakon tare da ban haƙuri, "Dan Allah Mine ka yi hakuri nice yar iskar ba kai ba, ba zan qara ba , ka taimaka min, ka duba auren soyayyar da muka yi da kai ka yi hakuri" kwad'e bakin ta ya yi ya ci gaba da abinda yake yi sannan ya ce, "Auren soyayya ki kai da wa? ko dai auren kwad'ayi auren kudi? Karki zaci ban san ke da uwar ki da qanwar ki kwad'ayayyu bane,  Ina sane da komai, ni ba qaramin mutum bane, kamar yanda ku ka yi auren kuɗi mu ma mun aure ku ne dan kyan ku da biyan buqatar kammu,kowa kin ga ya samu abinda yake

Chapter 6 of 25