tukunya ta ga ruwan ya fara alamun tafasa sai ta fara jefawa qanana, dan yafi son a jefa d'an wake qanana, rufewa ta yi sai da ya tafaso ya yi kamar zai zube ta buɗe marfin ta bari ya ɗan qara dahuwa sai ta kwashe a ruwa Mai kyau daga nan kuma ta tsame shi a mazubin ta mai riqe zafi, ta zuba wa su Innarmu ta bawa Nafeesa.
Nafeesa ta barwa wajen dan ta gyara ita kuma ta dakko nunannen tumatur ta wanke ta raba shi biyu tare da baɗe shi da sugar a tsakiyar shi ta hau goge fuskar ta da shi, nan da nan fuskar ta ta dau kyalli kyan ta ya qara fitowa.
Lalle Juwairiyyah ta deb'o ta zuba masa man kwakwa ta kwab'a shi da ɗan ruwa kaɗan ta dinga bin ko ina na jikin ta ta na murjewa,gaba ɗaya lamarin ta ya gama bawa Nafee mamaki,kasa shiru ta yi sai da ta yi magana,
"Tab a gaskiyar magana Yayah na shan daɗi aradun Allah, yau fa ba ranar gyaran jikin ki bane kamar yanda ki ke tsara abubuwan ki, bama fa ki wani dad'e da yi ba amma ji yanda ki ke faman dirzar fata kin koma kamar wata tauraruwa mai haske da kyau"
" Nafee kenan, ai ita mace ana son in mijin ta ya yi tafiya ko na kwana ɗaya ne ya dawo yaga ta canja kawai ko da sauyin ba yawa, balle kuma Nafee muna magana ne fa akan Yah Jabeer d'ina, My love, my everything"
Dariya suka fashe da ita tare da tafawa,Nafee nata tsokanar ta ta gama ta shiga wanka abun ta ba tare da ta biye wa tsokanar Nafeesan ba.
Ta na fitowa ta tsane jikin ta tare da shafa mayukan ta masu kyau da ta haɗa da kan ta dan gyaran fatar ta sannan ta yi shigar da yake matuqar so, doguwar rigar material ne aka mata irin na masu ciki ma'ana mai faɗi ta yanda ba za ta takura ba,an d'aure hannayen rigar dika ta wuya daga qirjin ta ɗan kama ta kaɗan, cikin nan ta bi ta shafe shi da mai sai kyalli yake gwanin sha'awa,kwalli da powder kawai ta shafa sai man leb'e, wani irin sassanyan qamshi mai ratsa zuciya take fitarwa saboda bata amfani da turare mai karfi.
( kwalli na da matuqar tasiri a idon mace, macen da ta saka kwalli ta kuma iya sarrafa idanun ta ta daban ce)
Dogon hijab ta saka akan kayan ta tada sallar magrib bayan ta idar ne ta zauna ta na azkar a hankali ta fara karanta qur'ani, ana kiran sallar isha'i ta kabbara zata yi sallah kenan Sallamar Jabeer ta daki kunnuwan ta dake buɗe suna jiran su ji muryar shi da ta yi kewa.
Jin shiru bata je tarbon shi bane ya sanya Jabeer leqawa parlour ganin tana sallah ne ya sanya shi ajiye kayan shi a cikin palourn ya tafi ya d'aura alwala shima ya tafi masallaci.
Ta jima ta na gode wa Allah da ya dawo mata da mijin ta lafiya qalou kafin ta yi tahiya ta Sallame sallar ta, ninke hijabin ta take yi bakin ta na tasbihi ga Allah ta shiga d'aki ta dan sake shafa humra da powder sannan ta hau kallon kanta a madubi, murmushi ta yi wa kan ta kafin ta koma parlour, ɗauke kayan da ya dawo da su ta yi ta hau dubawa nan take ta hau ware komai ta na ajiye wa a mahallin da ya dace da shi,hatta da kayan wankin da ya dawo da su sai da ta yi masu mazauni sannan ta dawo ta ɗauke wata leda da bata buɗe ta ga meye a ciki ba ta kai ta ajiye.
Ruwan wanka ta haɗa masa mai d'umi, fitowar ta kenan ta shiga parlour kafin ta kai ga zama Jabeer ya sallama ya kulle sashen nasu, kafin ya gama karanta ayatul kursiyyun a qofar gidan ta tashi da sauri ta na dariya qasa qasa ta b'oye a bayan qofa.
Shigowa jabeer ya yi bakin shi ɗauke da sallama fuskar shi cike da annuri saboda ganin gidan qal fiye da yanda ya saba ganin shi,cikin murmushi ya hau dube -dube alamun neman ta yake, gajiya ya yi da tsayuwar ya kama qugun shi ya ce,
" Juwaireren Mama ko ki fito ko na zauna a qasa na yi ta maki kukan wahal da idanu da ruhi na da ki ke yi, dan na kula da alama baki son gani na ni kaɗai ne na yi kewar ki"
Ta bayan shi ta lallab'o ta fito ta yi masa wata iriyar runguma wadda tasanya shi sauke ƙanƙk'arfar ajiyar zuciya, juyawa ya yi gaba ɗaya ya d'aga ta sama, suna ta dariya, sumbatar ta ya dinga yi ya na nuna tsantsar yanda ya yi kewar ta,daga baya ya tafi suka samu waje suka zauna a kujera,inda Jabeer bai bar Juwairiyyah ba sai da ya zaunar da ita a Saman cinyar shi, yana shafa cikin ta tare da yi wa cikin nata hira kamar wanda yake hira da mutum babba, dariya kawai take yi ita kam, daga baya ta rage sautin dariyar ta tace da shi,
"Sannu da zuwa fitilar da ke haske cikin gida na, a gaskiya dole na dinga godewa Allah da ya ban kai a matsayin miji, Yah Jabeer tafiyar nan ta kwana biyu da ka yi ya sa na tabbatar wa kai na ba zan iya rayuwa mai ma'ana ba idan babu kai, i missed u so very much"
Ta qarasa maganar ta tare da qanqame shi tana hawayen farin cikin dawowarsa lafiya kamar wani wanda ya shekara baya gari, d'ago ta ya yi yana jin wani sabon qaunar ta na ratsa shi, dan kuwa kalaman ta sun ratsa zuciyar shi sun samu wajen zama ya kuma tabbatar da iyakar gaskiyar ta ta faɗa masa,
"Yi shirun ki my princess, ki daina kuka, Yah Jabeer na Juwaireren Mama ne ita kaɗai har abada, bana fatan na wayi gari na ga baki kusa dani,ke ce farin ciki na Juwairiyyah ke ce komai na, dan haka kar ki taɓa jin tsoron rasa ni saboda ni naki ne har abada,na mallaka maki gangar jiki na, ruhi na da zuciya ta ki yi yanda ki ke so da su dika "
Wata sabuwar runguma ta qara yi mashi da ta saka shi jin daɗi sosai, d'aga shi ta yi ta ja hannun shi zuwa wanka ta taya shi ya yi wankan ya yi brush suka fito, sannan ta taya shi shiryawa.
Bayan sun gama ne suka nufi kan shimfid'ar da suke cin abinci suka zauna, duk abinda take yi masa ba qaramin daɗi yake ji ba, qima daraja da mutuncin ta na qaruwa a idanun shi,ita mace ce mai yawan kyautatawa,shi kuma namiji ne mai son a kyautata masa kuma mai yaba kyautatawar da ake yi masa,dan haka binta kawai yake kamar raqumi da akala.
Ta na buɗe mazubi na farko idon shi ya sauka a kan d'an wake murmushi ya saki mai sauti sama ya kalla cikin ran shi ya na godewa Allah tare da tunanin shin me ya aikata mai kyau a rayuwar shi Allah ya bashi Juwairiyyah a matsayin mata ya ninka wannan aikin alkhairin dan Allah ya bar masa ita su yi ta rayuwa tare har abada?
Hadiyar yawu ya yi dan ganin ɗan waken da har wani kyalli yake dan santsi sannan ta zuba mai wannann hadin da ta yi na dankali, zobon da ta dafa da abarba, cittta kaninfari, cucumber, goruba da sugar ta zuba masa, kafin ta gama dubawa Jabeer ya fara ci yana lumshe ido kawai tsabar yanda abincin ya yi masa daɗi, sai wani sautin santi yake fitar wa dan kuwa bata gane abinda yake faɗa, Juwairiyyah kuwa dariyar jin daɗi ta dinga yi.
Kowacce mace ta na so idan ta yi abun kwarai a Yaba mata, dan haka yabon Jabeer a wajen ta ba karamin abu bane, hannu ya miqar ya ɗauki zobon da aka saka a randar sanyi ya yi sanyi dan kuwa Juwairiyyah bata da fridge ya kai bakin sa ya kurba, saurin buɗe idon shi ya yi sannan ya mayar ya kulle, ya ci gaba da santin da yake yi, a hankali Juwairiyya ta ce,
" Yah Jabeer menene, yayi d'aci ne ko wani abu ka ji da be yi maka ba a ciki na ga ka buɗe ido da sauri?"
Ta yi maganar tana zaro ido waje dan a tinanin ta ko ba yi masa bane,da hannu ya yafice ta ya ce,
"Matso kiji me ya yi"
Yana ɗan yatsina fuska saboda ya ja wasan da kyau,nan take ta ɗan ji zuciyar ta ba daɗi, saboda gani take ta b'ata zob'on garin iyayin yi masa had'e-had'e, dan ba ta san dama ana saka cocumber ba qirqira ta yi, matsawa ta yi kanta a qasa, Jabeer ya ce,
"To ai sai kin rufe idon ki sannan zaki iya jin me na ji nima ba ido rufe ki ka ga na sha ba ? matso sosai na baki da kai na ki ji ya ya yi"
Matsawa ta sake yi ta rufe idon nata, ji ta yi ya hau sumbatar ta har sai da ta ga wasu taurari na gilmawa a idanun ta ta kasa motsawa, a hankali Jabeer ya ce mata,
"To buɗe idon naki mana Princess wannan tukuicin kyautatawar ki a gare ni na baki duk da na san ba zan taɓa iya biyan ki ba,ni ba mai kuɗi bane bare na maki kyautar kuɗi gida ko mota, albarka kawai zan yi ta sanya maki tare da fatan alkhairi,sannan zan yi qoqarin sanya ki farin ciki har qarshen rayuwar mu"
A tare suka kammala cin abincin su ya na ta santi tare da yaba mata, anan ne Juwairiyyah ta gane lallai mace ta yi sa'ar mijin da idan ta kyautata masa ya yaba mata ma ba qaramin abu bane, duk wahalar da za ta yi dan taga ta kyautata masa ba zata tashi a banza ba.
(Abinda ya yi qaranci kenan yanzu ya na wahala maza su yaba wa matan su, mace sai ta jima ta na wahala dan faranta ran namiji amma kallo ma bata ishe shi ba balle ya yaba mata,amma idan ya ga wata a waje wadda ba muharramar shi ba ya dinga yaba mata ta na gwale shi, kuma haka zai ci gaba da yabawar wataqila ma har da tukuici kamar wani mara zuciya, ya bar halal ya tafi yabon haram)
Sad'af sad'af na miqe zan bisu amma 'yar nan ta banko qohwa ta ruhe wai kar na bi su sai gobe mun haɗu.............
[22/07, 8:44 am] asiyahabibu93: 💅🏼 ' YAN ABUJA 💅🏼
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
Page 24:
Saudat ce zaune a tsakar gida bata jima da aiken yaro ya siyo mata gasasshen kifi mai haɗe da chips da ake gasawa ba a wani suya spot a farkon shigowa layin nasu da ta saba ci tun lokacin 'yammatancin su, Goggo Sarai kawai ta iya bawa ta sa saura a gaba ta na ci ta na kora maltina mai sanyi, Salma mai ɗauke da ciki ce ta haɗiyi yawu saboda ranta ba qaramin biyawa ya yi ba,amma haka ta danne kwad'ayin ta dan ta san ba bata Saudat za ta yi ba,sai da ta ga ta kammala ci ta wanke hannu ta koma ta zauna a kujera ta na latsa waya sannan ta isa wajen ta ta gaishe ta, a daqile ta amsa ta na karkad'a qafar ta ɗaya da ta ɗora Saman d'ayar,cikin wani maqasqancin kallo ta ce da Salma,
"Meye ki ka zo ki ka tsaya min a ka,idan gaisuwa ne ai mun gaisa ko sai a yi gaba tunda an sauya uwa,idan kuma wani abu ki ke da buqata ki yi gaggawar sanar da ni dan bana so a tsaya min aka"
Murmushin takaici Salma ta yi,nan take ta hau tuna baya yanda yayun nata ke ji da ita suke ɗora ta a hanyar karb'ar kud'in maza, ba su jin kunyar nuna mata yanda za ta yi wa namiji kwarkwasa da taɓa bikin shi san ya bata kuɗi shi ne yanzu dan ta zaɓi hanya mai kyau suke gudun ta, cikin magana mai cike da ladabi ta ce wa Saudat ɗin,
" Adda Saudat dan Allah zuwa na yi ki ɗan bani koda dubu d'aya ce ina son in ɗan ja jari ne ko Saida gishi da omo ɗan qulli ne in fara yi a cikin gida, saboda zaman haka baya min daɗi ba kud'in kashewa,ke ma kuma ina mai baki shawara da ki nemi abun yi da kud'in da ya rage maki tun kafin su qare saboda yanzu kin ga kin saba da kudi, randa kike da buqatar su kika rasa ba qaramin damuwa zaki shiga ba"
Tunani Saudat ta shiga yi mai zurfi, can ta nisa tace,
"Gaskiya kin ce wani abu kema, zan baki dubu biyar ki ja jarin, ni kuma zan fara kasuwanci ta waya da naga qawaye na da na yi a whatsapp da facebook suna yi, ana samu sosai in ka riqe amanar mutane, sai kaga ka samu riba mai yawa kana daga zaune"
"Yauwa Addana na gode sosai, sai wata magana kuma mai mahimmanci da nake so mu yi ni da ke, ina son ki gane Mama Bilki mace ce mai kirki tana matuqar son mu, sai dai tabbas tana kishi da Goggo, wanda wannan dole ne a zaman kishiyoyi dama,shiga wannan kuma ba hurumin mu bane mu kau da kai akan wannan mu bar su su yi kishin su after all miji ɗaya suka haɗa,abinda kawai za mu yi shine mu yi masu biyayya dikkan su a matsayin su na iyayen mu,"
Shiru Saudat ta yi domin maganar qanwar ta ta yau tana shigar ta dan gaba ɗaya ba qarya a ciki amma akwai nau'i na girman kai da taya Goggon su kishi a zuciyar ta,dan haka sai ta yatsuna fuska ta ce,
"Hmmmm zan duba maganganun ki na gani"
Sannan ta miqe ta d'akko mata kud'in da ta alqawarta zata bata ta bata, duk abinda ya faru akan idon Goggo Sarai ya faru, sai dai bata ji kalaman da suke yi ba ta dai ga an bawa Salma kuɗi,magana take cikin b'acin rai,
"Habaaaa Salma ai innice ke yanda na canja uwa, yan uwan ma canja su zan yi, auhoooo ba zaki iya canja yan uwa ba saboda su masu arziqi ne Zaki yi roqo za a baki , amma ita uwar ki tinda talaka ce shi yasa ki ka sauya ta"
" Ni fa Gogga ba haka bane, ya kamata ki buɗe idon ki ki gane inda gaskiya ta dosa, ki daina rufe idon ki ki na yin abinda bai kamata ba"
"Rufen baki sallamammiya kawai, an yi asiri da tuggu kala2 an raba ni dake, to ki je nima na huta da dawainiya da ɗan wani"
Juyawa ta yi tabar wajen Salma kuwa cikin qunan rai da baqin cikin halayya ta uwar ta ta shige d'akin Mama Bilki, wadda ta ji komai da ya faru, fad'awa kan cinyar ta Salma ta yi tana kukan takaicin hali irin na uwar tasu, shafa kanta kawai Mama Bilki take, bata furta mata komai ba,cikin kuka Salma ta ce,
" Mama ni fa ba kwad'ayi ne ya sa na tambayi Adda Saudat kudi ba, na tambaye ta ne kawai saboda ki na ganin ko tirare bani da shi, ga shi yanzu sai da alimun ko lemon tsami nake amfani a hammata ta a madadin tiraren,da ace ina sana'a yaushe zan zauna haka? Tunanin da na yi na ina sana'a kudin zasu taimakan wajen kula da abinda ke ciki na da ni kai na shine ya sa na tambayi Addah Saudat kuma ta bani dubu biyar na ja jari, shine Goggo take fad'an maganganu marasa daɗi akai na da abinda ke ciki na"
" Hakuri zaki yi Salma uwa ba abin wasa bace, dole mu yi mata biyayya matsawar ba sab'on Allah a duk abinda ta sanya mu,dan haka ki yi hakuri, to tin da kin samu jarin yanzu me zaki na yi na siyarwa?"
Tashi zaune Salma ta yi ta share hawayen ta sannan ta ce,
" Mama Bilki ni da ina son na fara saida gishiri da omo da ɗan qulle qulle na gida, amma yanzu da na samu wannan kud'in mai yawa sai na ji ina son in fara Saida Meatpie, naga kina da injin yin taliya, kuma na kula kayan flour ana cinikin su, in ba su ba ban san me zan iya yin sana'a akai ba kuma"
Murmushi Mama Balki ta yi sannan ta ce,
" Hakan ma shawara ce mai kyau, Allah ya sanya albarka a ciki"
" Ameen mamana"
Kwantar da kanta ta sake yi a jikin ta ita kuma tana shafa gashin kan Salman a hankali.
******************************
Yau kusan sati ɗaya da kwana uku kenan Suwaiba na kwance tana jinyar qirjin ta da aka fafe wa albarkatun wajen, Alhj Salihu dayaga zata farka sai ya danna mata allurar bacci ta koma, ko ya shaqa mata wata powder ta koma baccin, a haka ta yi wadannan kwanakin,shine yake yi mata wanka ya canja mata kaya,sannan ya saka mata ruwa da allurai na kashe zafin ciwo da anti biotics,ya zama babban likita kawai a cikin gidan shi dan ya kula da Suwaiba, a haka sai da ya kula wajen ya warke tas sannan ya kyale ta da allurai na bacci da yake mata.
Ranar da ya bar ta kuwa bai yi mata allurar baccin ba da ta farka sai ta ji kan ta kamar an ɗora mata abu mai nauyi, da kyar ta tashi daga gadon ta ta isa gaban madubi a hankali ta d'aga rigar ta ta na kallon qirjin ta, nan take wasu hawaye masu azabar zafi suka hau zuba a kuncin ta, ina dukiyar Fulanin ta suke ne, me ya same ta?
Duk abinda take yi akan idanun Alhaji Salihu take aikata su, cikin rashin k'warin jiki ta koma ta kwanta a Saman gadon nata tare da nitsar da kan ta cikin pillow kuka take yi sosai mai taɓa zuciya, zama ya yi a gefen ta ya kama hannun ta ya na lallashin ta, a hankali ta d'aga kan ta ta na kallon shi,da kyar ta buɗe baki ta ce masa,
" Sweet wai me ya same ni ne, wanne mummunar qaddarar ce ta hau kirji na ni suwaiba ?"
" Shiiiiiiii kar ki na yin magana sosai, hatsari muka samu a gidan, yan fashi ne suka suka shigo a ranar da ki ka dawo kina bacci suka yanke maki nono, ni kuma dana dawo na ganki kin suma shine na kai ki asibiti aka maki aiki daga nan na dawo da ke gida nake ta kula da ke"
A firgice ta miqe daga kwanciyar da take ta ce,
" Dama abinda ya faru kenan? Yanzu tsabar rashin imani su rasa me za su cire min sai wannan waje mai daraja?"
Ta fada tare da zaro idanun ta da ke ta zubar da zazzafan hawaye, cikin kukan nata ta ce,
"Na shiga uku ni Suwaiba,ya zan rayu ba mahaifa ba nono,yanzu nan gaba me zan rasa kuma, Alhj na fa san kai ne sanadin rasa nono na ba wani 'yan fashi,Saudat ta fad'an min ban ji ba ban yarda ba, saboda ina son ka, ko da ina son kudin ka na yarda cewa a yanzu ina son ka so na gaskiya,zan iya rayuwa da kai ko ba mahaifa shine hakan be ishe ka ba sai da ka qara da wata kadarar tawa yanzu ta ya zan rayu ba nono ba mahaifa"
Rushewa ta yi da wani irin kuka mai ban tausayi, cikin tausaya mata Alhj ya fara magana"
"ki yi hakuri Baby yau zan........"
katse shi ta yi cike da bala'i ta ce,
" Kar ka sake kira na da wata baby again, i hate u Alhaji, na tsane ka, na tsane ka da dikkan rayuwa ta"
Kukan ta ci gaba da yi mai ratsa zuciyar mai tausayi kai har da mara tausayin ma,matsawa ya yi ya kamo ta jikin shi, da sauri ta zame ta ci gaba da cewa,
" Kar ka taɓa ni azzalumi kawai,ka kuskura ka sake taɓa ni ni ma sai na yanke maka inda ba zaka taɓa amfanuwa ba a jikin ka"
Cike da matsanancin fushin da bai taɓa sanin suwaiban da yake wa kallon doluwa na da shi ba ta yi maganar,nan take wani irin shakkar ta ta shige shi, miqewa ta yi cike da jiri zata fita, cikin sassanyar murya Alhaji ya ce mata,
"Ina zaki je kuma"
"Gidan mu zani, na gama auren ka, na kuma gama aure a ABUJA har abada daga yau,daga rana mai kamar ta yau bani ba Abuja"
" Lallai ma Suwaiba, abinda baki sani ba shine, ba inda zaki qara fita ko nan da can ne kuwa sai da sani na, dan kuwa ni a yanzu ba zan iya rayuwa ba ke ba, kin ga kuwa sai ki shirya zama da masoyin ki na gaskiya, na amince ni zan jure rashin albarkatun qirjin naki tunda ni ne sanadi"
"Za kuwa ka mutu dan ba abinda zai hana ni barin gidannan, ko kana so ko baka so sai na bar gidan nan, in ka barni na tafi lafiya ba hukumar da zan haɗaka da ita, amma in ka hanani ba abinda zai hana ni haɗaka da hukuma zaɓi ya rage ya naka"
Wani shu'umin murmushin rainin hankali ya mata ya ce,
"To ai baki san wani abu ba, qungiyata babbar qungiya ce suwaiban,ni ɗin ba wai qaramin mutum bane ko baki gani bane?manyan gwamnati da yan kasuwa ba wanda babu a cikin qungiyar mu, ba yanda za ai ki had'a ni da hukuma kuma a samu hukunta ni din, mata kalar ki da wanda suka fiki komai sun fi dubi kuma mun masu wannan aikin balle ke, dan haka hakuri zaki yi kawai mu qarasa rayuwa dake a haka, in kin tafi wa zai na baki abun daɗin da nake baki? wa zaina debe maki kewa? wa zai zauna dake babu nono? Hakura zaki yi kawai mu zauna a haka tun da kuɗi ki ke so ni kuma zan ci gaba da jiyar dake daɗi da dukiya ta"
Tallabo wuyan ta ya yi ya na kallon fuskar ta,iya kuwa gaba ɗaya ta qame ta dauke kan ta daga ganin shi hawaye kawai ke zuba mata, ga wani irin tsoron shi da ke kwance a qasan zuciyar ta, yau ya zata yi ta kub'uta daga hannun wannan azzalumin?
Kuka ne ya kwace mata sosai, key din motar shi ya ɗauka ya fice ya bar mata gidan, anan inda take tsaye ta durqushe tana kuka mai ban tausayi.
*****************************
Talle kam ya saka marka a tsaka mai wuya ita da yayan shi, dan baya son maganar ta fita waje shi yasa bai ce masu qala ba,sai kawai ya fito da wata mugunta, gonar shi ta daji mai shegen nisa ya ke sa su zuwa gyaran ta, duba da cewar damuna ta kusan zuwa, a cewar shi ya na da majiya qarfin zuciyar cim amana irin su ba abinda zai sanya shi biyan kud'in gyaran gona,in sun ga dama in sun shiga dajin ma su ci amanar shi ya yafe masu amma tabbas sai sun gyara masa gona kafin damina ta sauka.
kullum can suke tafiya ba abinci ba ruwa, amma shi zai je a machine din shi da abincin shi da ruwan shi ya yi shawagi ya sa ido ya ga ya aikin yake tafiya,su kuma su Baban gida gonar shi ta can wani qauyen dake kusa da su ya tura su, saboda ya yi yarjejeniya da su akan hakan, in ba haka ba ya kaisu birni ga hukuma a huhunta su akan yi wa 'ya'yan shi ciki da suka yi,da jin haka suka amince suka yi biyayya suma.
Kan kuce me Marka ta fita hayyacin ta, 'yan mazaunan nan da ake kad'awa ana jan hankali da su duk sun zube, duk ta dame qashi ya fito mata ko ta ina,mutanen gari kuwa sai gulmammaki suke yi akan abinda ke faruwa a gidan Talle, kowa da ruwayar shi akan abinda ke faruwa amma ba wanda ya san gaskiyar lamari.
Kowa ya rasa gane dalilin Talle na aikata haka, da damar mutane sai suka alaqanta hakan da tsantsar rashin mutuncin shi, su Huwaila kuwa kullum sai sun yi surfen abinda za ai tuwo da shi sun dake da
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 16 Chapter of 25