tun igiyoyin aure suna kaina ina yawan nuna masa bana so amman baya fasawa. Ba wai bana son ya saka su karantar ba ne canja musu makaranta abu ne mai kyau wanda ni ma nai tunanin hakan sai dai bana son yadda yake son shige min ne da yawa, har ga Allah bana jin zan iya karbar wani tayi daga gurin Abdallah na so, taya zan so mutunen da na kaunace dan'uwansa kamar na mutu, mutumen da be san darajar aure ba kuma mutumen da be taba martaba ni saboda ina da igiyar aure ba, mutumen da a kullum fatar mutuwar aure yake min.
Adnan na aika a shago ya siyo min suga da madara da biredi na hada tea mai sanyi na sha, domin yau ban saka komai a cikina ba sai ruwa, a lokacin da zan fita ban ci komai ba ga shi na ci tafiya a kafa kamar marar galihu. Na yi sa'a bana sallah hakan kuma ba karamin dadi yai min ba, domin yau ko ta kan Amal ban bi na hau kafita na fara sheka bachi kamar wacce ta shekara batai bachi ba.
Ban farka ba sai 11pm a lokacin wasu sisters nawa sun yi bachi su kan yara ba a maganarsu daman can abu ne mai wahala su wuce 10 ba su yu bachi ba ko lokacin da muke gida suna ganin game balle nan da babu. Wani irin ciwon kafafuwa ne ya taso min kamar wata tsohuwa da kaina na zauna ina matsa abu saboda azaba. Na yi minti talatin a haka sannan na tashi na shiga bandaki na tsaftace kaina na canja pad na fito na nufi dakin Mama.
Na same ta tana hamma kamar dai ni da bachin be wadatar da ni ba, kusa da ita na zauna ina amsa mata cewar lafiya kalau gajiya ce kawai ta saka ni bachi.
“Ya jikin abokin aikin na ki?”
“Jiki ba dadi Mama ance ma wai jini zai iya taba kansa ni abun ya bani tsoro sosai, amman matarsa sai ci min mutunci take”
“Akan me? Miye hadinki da matarsa?”
Na jera mata komai kamar a gabanta ya faru, sosa abun ya bata mata rai har take yabon matar da rashin kunya da kuma tunani, mun dan dauki lokaci muna tattaunawa maganar kamin na soma mata shimfida da zancen Sadi.
“Wai Halimatu ba zaki share maganar nan ba? Yanzu fa aurenki ne ya mutu kin dawo cikin kenanki kin zauna su ma muna fatar rabuwa da su ke kin dawo maimakon ki fara tunanin yadda Goben ki zata kasance ki samu mijin aure shine kike neman batawa yarki da kanki suna? Ke yanzu kina ganin wani ma idan ya ji kina da yara hudu zai aure ki ne? Ai ba kowa ke son mace mai yaya ba ma, sannan wani ko ya so ki ba zai yarda ke je masa da yaya ba”
Kallo mamaki nai mata.
“Mama yaushe aurena ya mutu ma balle har ace wani ya zo nemana? Kuma ni yanzu ai ban shirya ma aure ba”
“Baki shirya ma aure ba? Kika magana kamar ba yar musulmi ba? Ke yanzu ko dan ki bawa Aminu haushi ai kyayi aure da wuri, sannan ga kanenki nan suma neman rabuwa na ke su ke kuma kin dawo har ki fara tunanin zama? Halimatu kina da tunani kuwa?”
Babu juyin duniyar nan da ban yi ba dan na fahimtar da ita irin matsalar da na fuskanta a gidan Aminu wanda ya saka aure ya fita a raina amman ta kasa fahimta, idan na dauko zancen kotu kuma sai ta tare ta nuna min ba haka har na gaji na taso na baro mata dakin. As usual na farka raina babu dadi babu walwalah daman na saba tashi a haka tun ina gida Aminu balle kuma yanzu da abubuwan suka kara min yawa.
Kudina na saka na siyo ma yarana koko da kosai na basu suka sha suka koshi, na san ba za su iya jiran na gida ba domin sun saba da cin abinci da wuri, balle kuma abincin gida na taru ba ba lallai ayi musu yadda zai wadatar da su ba. Bayan na gama da su na aika aka siyo min madara da biredi na hada tea ina sha. Wayata da ke gefena ce tai kara alamar sako tun daga saman screen din wayar na karanta da sakon tare da sunan mallakin sakin.
“Good Morning.”
Dauke kai nai ganin Abdallah na dauka ma ko zai yi zuciya ya kyaleni ashe ba shi da zuciyar ma, ina jin lokacin da wayar ta koma ringing na ki kulawa saboda bana bukatar kallon mai kiran ba, abunda ban sani ba ashe kawata ce Hajara take kirana ba Abdallah ba, ankarowa da hakan yasa nai saurin picking.
“Hello Hajara”
“Na'am Halimatu ya gida ya aiki? Ko baki kusa da wayar ne?”
“Eh ina breakfast ne ya yaran?”
“Lafiya kalau ga ni kofar gidanku ki fito mu gaisa”
Mamaki ne ya kamani.
“Kofar gida kuma? Miyasa ba za ki shigo ba?”
“Ke dai ki fito kawai”
Mamaki ne ya kamani ba dan kankane ba, taya Hajara zata so har gidanmu bata shigo ba tace wai na fito mu gaisa?
Wata kila wata maganar ce mai muhimmanci ita ce amsar da zuciyata ta bani a take na bar cin abincin da na ke na dauka hijabina na saka Amal ta biyo bayan muka fita tare. A bakin kofar gidan mu na yi arba da motar Isma'il sai dai ban kawo komai a raina ba a zatona ko tana cikin motar ne, haka ne yasa na karasa ya buga kofar gilashin motarta. Saukar gilashin motar sai yai min almara mijin Hajara ne kadai a motar ba tare da ita ba, mamaki ya hanani cewa komai sai sakar masa ido yai, shi kuma yana ta faman zuba min murmushi kamar auduga, bude motar yai ya fito yana ta kara min murmushi da haurensa na makka fari.
“Hajara tace min na fito tana kofar gida”
“Eh haka ne, amman dai ya kamata mu kamin a dora da bayani ko”
“Ba da kai ba da ita”
Na maimaita masa saboda ya fahimta amman sai ya kara dilmiyar da ni.
“Da ni zaki gaisa ba da ita ba”
Ya fada Yan mikawa Amal hannu ta zo sai tai bayana ta boya kamar wacce bata san shi ba.
“Ina fatar kina lafiya”
Nauyi baki na yi na kasa ce masa komai har ya sake jefo min wata tambayar.
“Ya gida ya yaran?”
“Lafiya Kalau”
Na juya da sauri sai ya kira ni.
“Halimatu... ”
Har na yi kamar ba zan juyo ba sai kuma na juyo na kalleshi. Bude motarsa yai ya dauko wata ledar ya miko min.
“Ga wannan inji kawarki tace a gaishe ki”
“Ka maida maita ka fada mata bana son gaisuwarta kuma ka fada mata karta sake aiko ka a kofar gidanmu da sunan gaisuwa”
Dariya yai yana gyara tsayuwar agogon hannunsa.
“Halimatu kenan, ba zuwa Hajara ne kawai ba, ni kana na ga akwai bukatar na kawo gaisuwa kuma na jajanta miki akan abunda ya faru”
“Da alama baka fahimci da wane yare nake maka magana ba, amman idan ita idan ka isar mata zata fassara maka”
Ina fada masa hakan ta juya na koma cikin cike da mamakin karfin hali irin na Hajara, shi ma kansa Isma'il din mamaki ya bani domin na lura ba shi da kunya irin yadda na ke da Hajara ai ko ni na tallata masa kaina a tunani be kamata ya amsa min ba.
Bayan na koma cikin gidan na shirya, na fito da zimmar zuwa gurin aikina ba, abun mamaki sai na kasa samun abun hawa kamar dai wacan karon, ganin haka yasa na canja shawara daga zuwa gurin aiki na nufi Hauwa International School, wato makarantar su Namra kamar da wasa na tari wani mai napep ya tsaya hakan ba karamin dadi yai min ba ban ko tsaya fada masa inda zanje ba na shiga ciki da murna yadda kasa wance bata saba shiga Napep ba, ina cikin fada masa inda zai kai ni wayata tai ringing, sai da Hajara ta jera min kira hudu sannan na daga rai a bace.
“Minene?”
“Haba Halimatu ai ko dan ya kamata ki mutunta Mijina”
“Naga alamar ke da mijin na ki kamar ba ku da hankali Hajara, na gargade shi ke ma kuma na gargade ki karki sake yi min wannan wasa”
“Ni dai van kora dan wani gargadin ki ba, na kira ne kawai na fada miki ban fada masa abunda ya fito dake daga gidan mijinki ba, kuma ban fada masa abunda ya samu Namra ba, kuma ni mijina ba zuwa yai ya fada miki cewar yana son ki ba, cewa ina son ki abu ne mai tsada a gurin mijina ya fara gadaki ne ya ga ruwanki...”
Ta karasa tana dariya sannan ta kashe wayar ba tare da jiran irin amsar da zan bata ba. Kadan ya rage mamaki ya kashe ni anya Hajara na cikin hankalinta kuwa kuma ta san abunda take kokarin aikatawa? Wai daman da gaske take da take zancen mijinta ya aureni? Ko kuwa dai gwadani take? Idan gaskoya ne ko karya ni ba zan iya auren mijin kawata ba, yar'uwata ma zance domin Hajara ta fi karfin kawa a gurina. Har na isa makarantar nai abunda zan yi na gama na kama hanyar aikina ban daina mamaki ba da kuma jinjina karfi hali irin yana anya irin matan nan suna nan kuwa? Ni sam na kasa yarda da gaske take ma.
*BAYAN WATA DAYA.*
Babu makarantar da ban leka ba nai yawo da takardun transfer su Adnan ba amman aka ki karbarsu a ko'ina, daga private school har na gobnati abun har tsoro ya soma ba ni, a duk makarantar da na kai su sai su kamar za su karba sai kuma su bullo da wani abun, wata makaranta ma ko kallona ba sa yi yadda kasan wacce akai wa wani magani haka nai ta shimlalo a gari neman makarantar da zata dauki su Adnan da Namra amman ina!
Hakan yasa n watsar da zancen karatunsu na maida hankalina gurin aikina duk kuwa da kasancewar bana jindadin aiki a yanzu saboda rashin Kabir ba kuma dan na shaku da shi ba sai dan tuna abunda ya same ni yana ni walwala a cikin office din, musamman da aka kawo wani da zai maye gurbinsa, ko da wasa ban sake gwada zuwa duba shi asibiti ba, sai dai na kan gwada kiran wayarsa kuma bana samu, ta hanyar wani abokinsa da ke aiki a inda nake na samu labarin cewar an kai shi kano a asibitin kwakwalwa saboda abun ya taba hankalinsa, na tauyasa masa ba kadan ba na kuma tausayawa matarsa da duka danginsa musamman da na samu labarin cewar iyayensa duka biyu basa raye, ta wani bangaren kuma ina tausayin kaina domin ban san me gobena ta tanadar min ba ban san abunda zan tarar nan gaba ba.
*Lahadi*
Kasancewar yau ranar hutu ce kamar dai jiya sa ta kasance asabar, dukan mu muna zaune gida har kanena ana ta zancen duniya, yawancin firar da muke ta rashin tsaro da ke addabar al'ummar mu ne da kuma tsadar rayuwa da muke ciki, ina zaune Abdallah ya shigo ya gaishe da Mama da Inna kanena kuma suka gaishe shi ya amsa musu amman bakina be hadu da na shi ba, ba baki kadai ba idona ma ban daga na kalleshi ba balle har na mika masa gaisuwa. Tashi nai ya nufi daki yana rike da hannu Namra waccena lura tana sakewa da shi sosai a duk lokacin da ya leko mu, Mama ta tashi ta bi bayansa suka shiga falon tare, ina nan waje zaune amman hankalina yana can inda suke duk na bi na tsargu sai kace wacce tai wani abun gulma.
Bayan yan mintuna Namra ta fito hannunta rike da chocolate.
“Momy wai ki zo inji Mama”
Na tashi cikin kuzari na bi bayanta, ina shigowa idonsa na kaina kamar daman can rayuwarsa ta takaita akan kallona ne kawai.
“Miya hanaki saka su makaranta”
“Na kai su ba a karba ne”
Na fada ina dan turo baki a shagwabe abunda ban saba ba, kuma ban san dalilin zuwansa a yanzu ba.
“Daman ai ba za akarbe su ba tunda kika bata min rai”
Ya fada yaa ta kallona da idonsa kamar maye, sai a yanzu na fahimci inda zance ya dosa, kar dai kwahi yai min aka ki karbar su a makaranta saboda shi twins ne shi da Abdulhamid.
“Kwahi kai min kenan? Ai ni kwahin ka ba zai kama ni ba”
“Kwarai shiyasa ranar ai kika samu Napep ta kawo ki har gida”
Har yanzu kallona yake yi irin kallon nan kamar ni din tv sa ce.
“To wani abun kika masa kenan?”
Cewar Mama tana murmushi, ni kuma na maida hankali gurin kiran wayata da ke shigowa.
Abdulhamid ne rubuce a screen din wayar, hakan ya saka gabana faduwa ba dan komai na sai dan Abdallah na zaune a falon, kusan tun lokacin da na fito nai bari Abdulhamid be taba kirana da sunan yi min jaye ko sannu ba, ba zan ce dan be ji ba, domin ko last time da Hajiya ta zo ta fada min cewar Abdulhamid ya kawo ta amman be shigo cikin gida ba.
“Hello....”
“Haima”
Gabana ne ya yanke ya fadi jin ya kira ni da sunan da na manta when last ya kirani da sunan.
“Na'am... ”
Na amsa kamar mai koyon magana.
“Kina lafiya?”
“Lafiya Kalau”
“Ina fatar kina gida, gani nan zuwa amman ba zan shigo cikin gida ba magana kawai zan yi da ke na koma”
“To... ”
Ina amsawa ya kashe wayar, idon Abdallah na kaina tana ta min kallon tuhuma, ni kuma na gagara tsayuwa na gagara zama sai yawo na ke da ido kamar marar gaskiya, ba dan komai ba sai dan bana son Abdulhamid ya zo ya tarar da Abdallah, duk kuwa da ban san abunda zai kawo shi ba na san dole daya daga cikinsu ya zargi wani abu. Musamman Abdallah da ya fiye shiga hanci da saka min ido.
#TeamAbdulhamind
#TeamAbdallah
#TeamAminu 😜
#TeamHalimatu
7/20/21, 8:30 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
1️⃣3️⃣
“Kamar baki da gaskiya Halimatu...”
Sai da na kalli Mama sannan na kalleshi.
“Bana da gaskiya kamar ya? Wannan wace irin magana ce Abdallah?”
Ya dan tabe baki yana ta wasa da hannun Amal kamar ba shi yai maganar ba. Kamar an daki hannuna sai na yi yai min majiyar, ban san lokacin da na saki wayar hannuna ta subuce ta fadi kasa, a take ta watse a saman tedar da ke falon kamar abar da aka taka da mota ko aka sakawa dutse aka daddaka. Subhanallahi Mama ta furta ni kuma na risina a gurin ina kallon wayar ina jin kamar na fasa kuka tuni idona suka cika da kwalla, har ga Allah na tsani na rasa wani abun da na ke matukar so ko yake da muhimmancin sosai a rayuwata, na san phone ce amman ina jin babu dadi domin samun irinta a yanzu ba abu mai sauki a gareni a lokacin da na ke gidanmu dawainiya ta zata min yawa yanzu fiye da, ga kuma zuwan da Abdulhamid zai yi ban san abunda zai kawo shi ba wata kila ma baya son kowa ya san da zuwansa.
“Ya akai wayar ta fadi?”
Mama ta tambaya sai an amsa mata muryata na gargada alamar ina daf da fashe da kuka.
“Ban sani ba Mama a hannu ta zame ta fadi”
“Laa shikenan wayar Momy ta fashe bamu da wayar game”
Namra ta fada tana wani bude baki, Abdallah kam ko dago kai be yi ya kalleni ba sai wasa yake da yatsun Amal kamar be san abunda ya faru ba.
“Momy yanzu da wace wayar za mu rika game...?”
Wani bakin haushi na ji ban san lokacin da na dakawa Namra wacce tai maganar tsawa ba.
“Da wayar ubanki... ”
Sai a lokaci Abdallah ya dago ya kalleni sai kuma ya kalli inda wayar take ba ce min komai ba sai dai fuskarsa ta nuna alamar bachin rai, mikewa yai tsaye yana saa dayan hannunsa a aljihu.
“Mama ni zan tafi, kuma yaran nan a yi kokarin saka su makaranta domin barin su hakan nan ba zai yiyu ba ya kamata a san abun yi lokaci na ta tafiya”
Wata uwar harara na watsa masa saboda haushinsa da na ke ji, wacce be san ma ina yi ba domin be kalli inda na ke ba da Mama yake ta maganarsa, ita kuma tana nanata masa cewar za a saka su makarantar, hannu ya saka aljihu ya ciro kudin da ban san ko nawa ne ba ya aje mata a hannun kujerar da take zaune sannan ya karaso inda na ke duke ina ta kallin wayar da na gagara tattarawa na kwashe ya ce.
“Halimatuuu mu kwana lafiya”
Har na yi kamar na bude baki na aika masa da bakar magana sai kuma wata zuciyar ta hanani ganin a gaban Mama ne da kuma yara. Tare ya fita da Amal da Namra Aiman ma ya bi bayansa.
“Halimatu kina jin yana miki sai da safe amman kika gagara karba mishi miye haka?”
Mama ta fada cikin yanayin damuwa da rashin amsa masa da ban yi ba.
“Mama ba ki kohi yai min wayar ta fadi ta fashe ba”
“Kohin zai saka waya ta fadi har ta fashe? Ai naga ko kallon ki be yi ba kuma ba wata maganar ta bacin rai kika masa ba balle ace, abu ne dai da Allah ya kawo”
Ban sake cewa komai ba na tattara wayar na mike tsaye na nufi dakin Mama na zauna bakin gadonta kamar wacce aka kwashewa tunani a kwakwalwa, babu komai a raina sai bacin ran faduwar wayata, ina zaune a gurin yara suka shigo da yan dari biyar biyar a hannu wai Uncle Abdallah ya basu, ni dai ko kallonsu ban yi ba balle har na karbi kudin na adana musu saboda bakin haushin Abdallah da na ke ji.
Ban yi dabarar na karbi wayar daya daga cikin yan matan gidanmu na kira Abdulhamid ba sai da aka sallame sallar isha'i, a lokacin kuma yan zaman majalisar kofar gida sun soma shimfida tabarsu su zauna. Idan ma nace zan yi magana da shi sai dai na koma ta kofar gidan makotan mu wanda hakan ba zai min dadi ba domin a hanya ne.
Ban yi kasa a guiwa ba na karbi wayar Hafiza na lalabo number Abdulhamid a wayarta na aika masa da kira, kamar jira yake a take tai picking din call din yana rangadamin sallama, bayan na amsa na koro masa da bayanin wayata ta fadi har ta fashe.
“Oh ni na dauka ko kashe wayar ki kai, domin nata kira ban samu ba”
“Wallahi faduwa tai ta fashe screen din ma ya watse gaba daya”
“Subhanallahi garin ya?”
“Ba zan iya fada ba, ni dai kawai tana hannuna ta subuce ta fadi kasa, ka zo ne?”
“Na zo, sai dai ban karaso kofar gida ba saboda bana son kowa ya san da zuwana, dan ki kawai na zo”
“Ka tafi ko kana nan?”
“Na tafi amman na fi karfin one hour a gurin kamin na tafi”
“Ayyah ban jidadi ba”
“Karki damu zan shigo gobe In-Sha-Allah”
“To Allah ya kai mu”
“Amin mu kwana lafiya”
Ba bari na sake cewa komai ba ya katse kiran, ni kuma na sauke wayar ina ta tunanin abunda zai kawo shi gurina ni kadai, wata kila kum zai yi min jajen abunda ya faru ne ko kuma ya bani wata shawarar, ban raba dayan biyu ba Hafiza ta shigo dakin na mika mata wayarta bayan n goge call din domin Bana son ta san da wanda nai wayar. Sai kuma na nufi inda jakata take na bude na dauko dubu biyu saboda ina son siyo man goge baki da Vaseline din mu daya kare. Hijabina na saka ina Kwalawa Namra kira ta zo ta raka domin ta fi sauran natsuwa da abun hankali, sai dai duk yadda nai ta noke noken na fita ni kadai ban samu sa'a ba har sai da Amal ta gan ni ta biyo da gudu tana kuka, a dole na tsaya na rika hannunta sannan na nufi dakin Mama na shaida mata cewar zan je shagon titi na siyo man shafawa da kuma na wanke baki.
“Ba zaki aika kanenki si siyo miki ba?”
“Ina son fitar ne Mama”
“To Allah ya tsare”
Na amsa da amin sannan na kama hanya ina rike da hannu Amal Namra kuma na gefena na hagu dukansu suna sanye da riga da wando ne yan kanti. Cikin tsananin kunya na ratsa kofar gidanmu na wuce saboda taron da maza yan zaman majalis sukai yi. Wanda na san a nan ma ba zan rasa wanda zai yi gulma ta ba, koma na ce gulmarmu yan gidan gaba daya domin mun tara yan mata Masha-Allah, wanenda aka dade ana zancen wai mai kudi suke jira wasu kuma tuni suka fara yi kanena zargin masu nemansu duk na neman auren suke zuwa ba iskanci ne kawai ke kawo su, ni kuma na dade da yin zurfi wajen sanin cewar aure da haihuwa da mutuwa da rayuwa duka na Ubangijin Annabi Adamuna, wato Allah S W T wanda ke rubutowa bawa abunda zai same shi tun gaban bawa ya zo duniya.
Lokuta da dama kan jarabi bawa da abu ba dan Allah baya son bawan ba sai dan gwada karfin imaninsa da kuma aikinsa. Idan na tuna mahaifina da mahaifiyata ina samun kaina a cikin wani kogo mai cike da tausayinsu musamman ubana wanda na san shi mutane za su zaga, kuma shi zai fi kowa shiga damuwa, domin bayan yan dakin Mama akwai na dakin Inna waenda sukansu yan mata ne da suka kasance a karkashin inuwarsa. Gashi lafiyar kafafuwa ma bata wadace shi ba.
“Momy a nan za mu yi ta zama? Daddyn ba zai zo ba?”
Maganar da Namra tai ka katse min zancen zuci da na dade da yin zurfi a cikinsa, gabana ya fadi ba faduwa ta tsoro ko fargaba ba, ba faduwa ta irin amsar da zan bata ba, ko kuma abunda zan mata ta fahimta ba, faduwa dai irin ta ko wace uwa mai yayana yana daya daga cikin dalilin daya hana ni fitowa a gidan Aminu gudun irin rayuwar da yayana za su yi idan bana gidan, sai dai kuma yanzu da suke hanuna kuma ya rufe idonsa daga kallonsu balle waiwayarsu ya rayuwarsu zata kasance? Mama tana yawan fada min ba ko wane namiji ne zai auri da yayana ba, idan ma ya aure ni ba zai yarda na zauna da su ba, anya idan na bar su a gida za su samu kulawar da nake musu fatan samu? Ya makomarsu zata kasance lallai juma'ar da za tai kyau tun daga laraba ake gane ta, indai har yau ba tai musu kyau ba ya gobensu kenan?
“Momy ga fa shagon can, ko ba shagon Takur ba?”
Namra ta fada tana girgiza hijab dina, wani irin numfashi naja na sauke hawayen kam tuni suke wanke min fuska sai dai ban fahimci hakan ba sai da Namra tai min magana ganin ina kokarin wuce shagon da ban san mun kawo ba sai yanzu.
“Eh shi”
Na fada ina share hawayena sannan na karasa gurin shago, sai da ya sallami duka mutanen da suke gabana sannan na mika nawa kudin na fada masa abunda za a bani ya mikon na siya ma Amal da Namra biscuit na rike biyu domin na san indai Adnan da Aiman sun gani sai sun tambaya ina na su? Bayan na karbi canji na juyo tare da yarana muka kamo hanyar dawowa gida. Tunanin dai na dazun ya sake fado min a rai, har na kasa fahimtar shi Aminu ya yafe min su ne gaba daya hakan ya saka ya kwashe har wata daya ba kira ba aike ko kuwa yana jira sai su kara girma ne ya karbe su?
Karar qaraurawar keke na ji kamin na yi kokarin kauchewa tuni keken ta bugeni ni kuma na gibi Namra ni da wadanda suke kan keken muna fadi kasa, saurin tashi nai cike da kunya Allah ma ya tsare ba mutane sosai a gurin da na ji kunya kam. Mutumen da ke rike da keken yayi saurin karaso inda na ke ya daga Namra yana kabe mata jikinta tare
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 9 Chapter of 55