Da gudu suka rumgume ni su dukansu wani kalar farinciki na ji wanda na dade ban ji irinsa ba, lallai ya'ya rahama ne, a take idona ya cika da kwalla ni kaina na san na yi kewar ya'yana, dukawa nai na dauki Amal muka shigo falon tare da su.
Bayan sun huta na dauko musu abincinmu, sannan na shiga dora wani domin ban san da zuwansu ba kuma nasan wanda za su cin ma ba isarsu zai yi ba, ina cikin kitchen din Hafiza ta same ni da zancen siyayyar da Aminu yake ta musu Namra a kwanakin nan, daman kuma Mama ta fada min a waya a duk lokacin da ya zo sai ta fada min domin ita ma mamaki abun yake bata kamar ni. Daga ni har sun mun rasa dalilinsa na nunawa yarana kulawa a yanzu, bayan siyayya ma duk bayan kwana biyu sai ya zo ya fita da su ko kuma ya duba lafiyarsu.
“Ni kaina Hafiza na rasa ganene dalilin Aminu na yin haka, mutumen da can ma be kula da yaran ba, har cewa yake na tara masa yara har hudu da kurciyarsa, yanzu kuma shine yake nuna musu kulawa abun yana bani tsoro”
“Ko ma minene nufinsa ba zai samu nasara ba, matukar dan ya cutar ke ko su zai yi”
“In-Sha-Allah, ba zai samu wata dama ta yin wani abu ba”
“Amman Anty miyasa kika daina zuwa gida? Baba ma kwana biyu ciwon kafafuwansa sai tashi suke?”
A take gabana ya fadi hankali kuma ya tashi abunka y'a da uba.
“Subhanallahi amman shine ba a fada min ko a waya ba?”
“Ba ke kadai ba ko su Anty Murja da suke nesa ya hana a fada musu wai za a daga musu hankali kawai, kin san ciwon nasa idan ya tashi yau ciwo gobe lafiya haka yake masa shiyasa”
“Allah ya bashi lafiya”
“Amin, Mama da Inna sai zancen ki suke su suka ce na zo da su Namra ma mu duba ki lafiya kike? Kuma gaskiya na ga alamar ba lafiya ba”
“Kamar ya?”
Na tambaya ina kokarin kirkiro murmushi.
“Haba Anty kalle ki fa, duk kin rame kin koma kamar ba ke ba, ke da kika da jikinki mulmul ma sha Allah amman yanzu ko ki na fi ki ki ba, duk kin yi baki kin lalace Gaskiya akwai abunda yake damunki”
“Babu abunda yake damuna Hafiza”
Ina fadar hakan na juyo na fito daga kitchen din domin bana son ta cika ni da tambayoyi. Ina fitowa Namra ta fara bani labarin Daddynsu yana zuwa gurinsu yanzu har ma siyayyar da yai musu, tana cikin lissafa abubuwan da ya siyo musu sai Adnan ya karbe daga nan sai Aiman har da Amal ma labarta min take abubuwan da Daddy yake musu, wani irin farinciki da annushuwa nake ganin a fuskar yayana, da alama hakan da yake musu a yanzu yana musu dadi, ko ni da nake babban na so mahaifina a kusa da ni balle su da suke kanana kuma babu ni a kusa da su. A nan Namra take nuna min new friend dinta mai irin sunanta.
“Momi kin tuna lokacin dana bata a gidansu aka kai ni, kin suna ita ce yarinyar gidan”
Sai a lokacin na tuna har na wayi fuskarka.
“Momi Daddynta yana sonta sosai komai siya mata yake, kuma har shi yake zuwa daukarta idan zata koma gida”
“A ina kika hadu da ita?”
“A school din mu take ita ce tana so na friend tace ita bata da friends kuma Momi ita ma sunan Mominta Halima, amman ta rasu.... ”
Hannu na mika mata alamar ta zo, sai ta taso daga inda take zaune a kan Center tebur ta nufo inda nake sanye da English Wears dinta kanta babu dankwali balle ayi maganar hijabi.
“Kin ganeni?”
Na tambaya bayan na rike hannunta, sai ta gyada min kai tana murmushi irin murmushin nan na yara masu kiriniya.
“Momi na fada mata yau za mu zo gidanki shine tace tana son ta ganki, tace daddynta ya kawota kuma ya kawo ta”
Namra ta fada da mamaki a fuskarta, domin ita bata tashi cikin irin wannan gatan ba, da mahaifinta zai mata abu ko kuma ya nuna mata kula balle har ya dauketa ya fita da ita.
“Daddynta yana sonta sosai Momi har da waya ya siya mata, yana bata chocolate komai siya mata yake, kuma gidansu har da motar wasan yara ya siya mata da lilo irin an scul dinmu”
Ta sake fada, ni kuma sai nai murmushi na shafa kanta domin na san abunda yata take ji, kwatankwacin abunda nake ji idan na ga wata mace ta yi dacen mijin aure.
“Kin yi dacen uba, Allah yai miki albarka ya jikan mahaifiyarki”
Da kanta ta amsa min da Ameen kamin ta saki hannuna ta nufi gurin su Adnan, da alama dai ta sake sosai da su kamar wasu yan'uwanta.
A gidan suka wuni tare da Hafiza sai dare suka tafi, duk yadda ta so na labarta mata damuwa ban yarda na bude mata cikina ba. Tafiyarsu da minti ashirin Abdulhamid ya dawo a lokacin ina zaune falo, bai yi knocked ba daman yanzu ya gane sai dai ya saka key ya bude kofar falon ya shigo. Na masa sannu da zuwa ya amsa min irin amsawar nan kamar an masa dole, a yadda na lura Abdulhamid yana zaune da ni ne irin zaman nan kamar na dole domin ba zaka ga zamantakewar aurenmu ka ce zaman ne na masoya ba. Na so na gabatar masa da zancen zuwa gida duba Abbah a wannan lokacin sai kuma wata zuciyar ta hana ni, na yanke shawarar da safe zan fada masa idan ya gama karyawa.
Ashe abunda ban sani ba Abdulhamid tafiya zai yi a garin da ban san ina ba ne, sai da safiyar ta waye bayan na gama hada masa abun karyawar na yi ta jiran ya fito shiru be fito ba, har tara da rabi ganin be saba kai wa hakan ba yasa na shiga dakinsa sai na samu dakin wayam babu kowa a ciki sai wata farar takardar a saman gadonsa, karasa nai na dauki takardar wacce ke saman kudin da ban san na minene ba har sai dana karanta takardar.
“Tafiya ta kamani zuwa Kaduna, zan dawo on Tuesday ko Wednesday ga kudi nan ki yi amfani da su.....”
Ina gama karanta takardar hawaye ya wanke min fuska, a yanzu bana da martabar da Abdulhamid zai kalli ya fada min cewar zai yi tafiya? Zauna nai bakin gadon ina tuna irin rayuwar da nai a gidan Aminu, a da na yi tunanin komai ya wuce, ashe abubuwan da zan fuskatanta suna da yawa, ko wace mace da irin jarrabawar da take tsintar kanta a cikin a gidan mijinta, wata mijinta neman mata yake, wata ya hana ta ci da sha, wata ya hana ta lokacinsa, wata ya hana ta kudin kashewa. ni kuma irin tawa kaddarar kenan.
“Al-hamdulillah”
Na furta sannan na share hawayena na taso na fito daga dakin, dakina na dawo na bude drawer ta na dauko maganin bachi na kurba kadan na kwanta, da niyar nai bachin kadan sai ga shi na zarce da dogon bachi ban farka ba sai la'asar. Azahar ma sai da na ramata sannan na dora da la'asar din, haka kuma be min dadi ba domin ban saba ramuwar sallah ba, idan ba da wani dalili mai karfi ba. Ganin ni kadai ce a gidan yasa ban wahalar da kaina wajen girka komai ba, daman can ba ci nake ba saboda shi nake girkawa kuma yanzu baya ma garin.
Wayarta na dauko na kira layin Baba, ringing biyu ya dauka na gaishe shi cikin girmama da kauna ya amsa min da kuzarinsa.
“Baba ya jikin?”
“Al-hamdulillah jiki da sauki sosai sai da suka fada miki ko?”
“Hafiza ta zo jiya ta fada min, Baba ciwo ba abun boyu ba ne, musamman irin naka da idan kafafuwan suka tashi baka iya takasu, ya kamata aje asibiti a sake dubawa”
“Kafafuwan da sauki fa, yanzu nan ma Abdullahi ya dawo da ni gurin gashi, shi ke kaini aka gasa kafafuwan kullum, da sauki sosai ki kwantar da hankalinki”
“To Baba na so na shigo sai Abdulhamid yai tafiya, amman idan ya dawo ko kuma na yi waya da shi na nemi izininsa zan zo na dubaka”
“Allah ya miki albarka Halimatu, karki zoba da izininsa ba, ayi ta hakuri”
“To Baba Allah ya kara maka lafiya”
Da amin ya amsa na sauke wayar ina hawaye, duk yadda na so na daga waya na kira Abdulhamid na tambayi izininsa na zuwa gida sai na kasa, daga karshe na yanke shawarar tura masa sako. Ko minti biyu ba ayi ba ya dawo min da reply har da kalmar da nake zaton zolayace kawai ko kuma ya rubutu min ne saboda ya saba rubuto haka a karshen ko wane irin text da zai min.
“Subhanallahi Allah ba shi lafiya, ki je gobe, kuma idan na dawo zamu je mu duba shi, zan kira shi na masa ya jiki.
Ki kula da kanki i love you.....”
Daker na iya hadeye yawun bakina tare da wani abu da na ji ya tsaya min a makoshi. Sannan na tashi na shiga gyara gidan domin yau ban yi gyaran safe ba tunda wuni nai ina bachi.
Sai na kimtsa ko'ina na gyara komai sannan na shiga nai wanka, sai kuma na dawo gaban madubi na zauna ina ta kallon kaina, ni kaina ban lura da na yi rama sosai haka ba sai yau, ban ɗaga daga gurin ba sai da na ji wayata na ringing, number mama ce cikin sauri na dauka tare da sallama, bayan mun gaisa na sake mata ya jikin Baba ta amsa min da sauki tare da kara fada min Abdallah yana ta hidima da shi.
“Allah ya saka masa da alheri ya biyaki”
“Amin. Halimatu me ke damunki?”
“Me ya faru mama?”
“Kin daina zuwa gida, kuma Hafiza ta fada min kina cikin damuwa amman kin ki ki fada mata”
“Babu komai Mama kawai dai bana jindadi ne kwana biyu”
“Halimatu, ni fa mahaifiyarki ce, ko ms ke damunki ni ya kamata na fara sani kamin kowa, kuma idan ba ki fada min damuwarki ba wa kike da shi da za ki fada masa?”
Hawayen na ji ya cika min ido, tabbas ina bukatar mahaifiyata a kusa da ni kamar ko wace ƴa.
“Mama idan na zo gobe zan fada miki komai, maganar ba zata yiyu ta waya ba”
“To Allah ya kawo ki lafiya”
“Amin”
Na sauke wayar sannan na tashi na nufi wardrobe na dauko kayan bachina wando da riga na saka. Da kaina na tafi na rufe gate din gidan saboda yau ni ce kadai a gidan daman Abdulhamid ya saba rufewa yau kuma ba ya nan, bayan na rufe gate a dawo na rufe kofar falo na kashe kayan kallo da wutar falon sannan na shiga dakina na kwanta ba dan bachi ba domin na san bachi ba zai dauke ni haka nan kawai ba sai idan wani abun na sha.
Data ta na kunna na shiga media rabon da na yi chat ma har na manta, na samu sakkwanin da yawa musamman ta whatsapp, na groups da na private har na gaji da bibiyar grps din na kashe datar.
Misalin daya da yan mintuna da na ji kamar ana taba kofar falonmu, da farko tsoro ya kamani a tunanina ko aljanuna, sai da na jai motsin yayi yawa har da saka abu aka dukan kofar ana kokarin ballanta sannan na taso na fito daga dakin cikin karfin hali. Isowa falon tai daidai da balla kofar da akai domin kadan ya rage ba su cireta ba har ginin gurin sai da suka taba gurin balle kofar. Wadancan mutanen ne dai wadanda suka zo wacan karon, masu sanye da mask da kuma bingogi. A take a nemi tsoron da ke cikina na rasa, ashe akwai ranar da ko mutuwa za kai arba da ita baka tsoronta.
“Waye ku? Me kuke nema agurina? Waya turo k? Shi wanda ya turo ku me na tare masa?, miyasa ba ku zuwa sai a lokacin da mijina baya nan? Fyade kuka sake zuwa min? Ku sake sakawa mijina ya ki yarda da ni kamar wancen karon? Ku saka bindiga ku harbe ni zai fi min jindadi da kwanciyar hankali sama da ku same min wani cikin, ko waye kai ka san ni kuma ka san cewa mijin ba shi da lafiyar da zai iya kusantata shiyasa kake min haka saboda ka tarwatsa rayuwata, to Allah ba zai barku ba sai ya saka min.... ”
Ina rufe bakina daya daga cikinsu ya karaso kusa da ni ya buga min kan karamar bindigar da ke hannunsa abaki, wani azababben zafi na ji kamar babu bakin ma, ko kuma wacce aka cirewa hakora, a take jini ya samu hanya. Uku suka zauna a kujera yayinda sauran suke a tsaye.
Ban iya sake cewa komai ba, dan ban yi zaton bakina yana ajikina ba har lokacin, faduwa nai zaune na tara hannuna jinin dake zuba daga bakina yana ta tsiyayomin.
“Yau ba gurin mijinki muka zo ba, kuma ba mu san cewar mijinki baya gari ba, ba turo mu akai ba zuwan kanmu ne, kuma baki san daya daga cikinmu ba, sai dai na lura zuciyarki tana da tauri a yanzu”
Wanda ya buga min bindigar ne ya fada min haka yana tsaye akaina, muryarsa gargada take kamar wani boss kuma kamar yana taunar wani abu a baki, da alama ya boye ainahim muryarsa ne dan kar na gane shi, domin zuciyata bata yarda cewar wani ne dabam wanda ban sani ba. Risinowa yai ya kai hannunsa da cikin bakar safar hannu ya taba cikina.
“Amman da gaske kin yi ciki? Da gaske a akwai ciki a jikinki?”
Ya tambaya yana matsa cikin nawa da karfi kamin ya daga bindigarsa sama har sau uku, ban tana sani haka bindiga take da kara da kuma firgirtawarta ba sai yau, wani abu na ji cikin kaina daga nan ban sake sanin inda nake ba.!
7/21/21, 10:44 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
2️⃣4️⃣
A yanzun ma ina bukatar wani ya tsaya min? Har a yanzun ma akwai wata hujja da nakr bukata kamin na gamsar da Abdulhamid ko wani da yake kusa da ni cewar an shigo gidanmu? Bayan fasa min baki da sukai ga kuma halbi da balle kofar falo, ashe har da gate din gidan suka fasa mana, sai dai maganin bachin da na sha bachin da na sha be bar ni na ji bude gate din ba sai na kofar falo.
Sama sama nake jin maganar da su Mama da sauran kanena mata na yi, ban bude idona ba balle na iya tantance dare ne ko safiya ko kuma rana, sai dai a haniyar da nake ji kusa da ni har da Abdallah da wata macen da nake jin suna ta kira da Doc Safiyya.
“Halimatu....”
Macen ta kira sunana, sai dai ban iya amsawa ba saboda ban yi zaton akwai sauran magana a bakin da nake jin kamar babu shi a sauran halittar jikina, saboda zugin da na ke ji. Kamar a mafarki na ji ta taba bakin ba shi na bude ido na zabura na tashi zaune da sauri.
“Sannu...”
Shine abunda ya fito daga bakin Abdallah yana kallona da mugun tausayi. Ban san yadda bakin nawa yai ba amman ina jinsa kamar ya min nauyi ga wani uban zugin da yake min kamar an cireshi. Fita yai ya bar mana dakin likitar ce ta gyara min bakinta ta saka min bandeji sannan suka canja min daki zuwa wani.
A lokacin da aka shiga da ni a na kiran sallah asuba, tun da na lumshe idona ban bude ba har Abdallah ya shigo yana miki min waya.
“Mijinki yana son waya da ke”
Ban bude idona ba ban kuma yi wata alama ta zan bude din ba, har ya gaji ya maida wayar a kunnesa ina jin yana fada masa cewar bachi na ke. Yana fita Mama ta shigo da shesshekar kukanta ta zauna a kujerar da ke kusa da gadona, a lokacin ne na bude idona na kalleta idonta sun yi ja sosai alamar kuka tai da yawa.
“Sannu Halimatu...”
Daker na gyada mata kai sannan na sake maida idon n lumshe, ban sake budewa ba sai da rana ta soma haskowa cikin dakin. A wannan karon ba Mama na gani ba Inna ce zaune a mazaunin Mama.
“Sannu”
Nan ma kan na gyada mata ina jin ya min nauyi kamar ba nawa ba. Da kanta ta je ta kira wani likita namiji ya zo ya duba ni ban samu matsala ta ko'ina ba sai ta bakina shi ma kuma gindin bindigar da suka buga min ne, kamar wata karamar yarinya haka na zama duk yadda aka so na ci abu sai na kasa saboda zafin da bakin ke min. Ruwa kawai na sha shi ma kadan, sannan na tashi na shiga bandakin da ke cikin asibitin nai alwala na gabatar da sallah asuba. Ina sallame sallar abunda ya faru ya dawo min, a wannan karon ban samu wata shaida kmar wacan karon da na samu zoben mutumen ba wanda na ganshi a hannun Abdallah, a yanzu abunda nake ta kokarin shine siffanta surar mutumen ko zan iya gano waye ne yake min haka, idan an siffanta shi da Abdallah sai idanuwa su nuna min kamar Abdallah ya fi shi jiki, wata kila kuma dimaucewa ce ta sa ba zan iya tantancewa yadda ya kamata ba.
Idan ba Abdallah ba waye? Wana tarewa wani abu? Amman miyasa zan yi ta zargin Abdallah? Saboda shi ya saka ki a gaba ya hana ki rawar gaban hantsi, ita ce amsar da zuciyata ta ba ni.
“Ba mu san cewar mijinki baya nan ba, wannan karon ba gurin mijinki muka zo ba, da gaske akwai ciki a jikinki?”
Su ne kalmomin da ke ta maimaita kanta a cikin kwalkwalwata, dalilinsu na ke bukata, da gaske ba su san cewar mijina baya gari ba? And idan ba a gurin Abdulhamid suka zo ba, me za su zo su yi gurina? Fyaden suka sake zuwa su min ko kuma wani abun dabam? Ban raba dayan biyu ba Hajiya tai sallama ta shigo tare da yar autarta wato kanwar su Abdallah, Inna ce ta amsa mata, ni kuma na juyo daga saman carpet din da nake zaune na kalleta. Ba shakka na ga tausayi a fuskarta tana ta min sannu ina gyada mata kai domin har lokacin ban yarda wata kalmar ta fito daga bakina.
“Ta ci abincin?”
“A a ruwa kawai ta sha shi ma kadan”
Inna ta bata sai ta sake cewa.
“Allah dai yasa ba su mata komai ba”
“Aa bakinta dai ne suka fasa, ina jin ko sun buga mata abu ne”
“Ayyah, Allah dai yasa ba su taba ta”
Wannan karon sarai na fahimci gun da tambayar Hajiya da dosa, ba lafiyata take nufin an taba ba, martaba take magana, da farko na ji ba dadi wata zuciyar na fada min cewar danta take tayawa kishi ko kuma take yi ma fargaba, ta wani gurin kuma tana da gaskiya domin mai kaunar ka ne kawai zai iya kulawa da wannan. Ba ita kadai ba na san mutane da yawa ma za su kawo wannan tunanin a zuciyarsu wata kila har da Abdulhamid din.
“Aa ba su mata komai ba, bakin ne dai suka taba”
Inna ta bata amsa sai Hajiya ta dora da bayanin yadda aka kawo ni asibiti.
“Ni ai ina kwance sai ga kiran Hassan, tsoro duk ya kama ni domin be saba kirana irin wannan lokacin ba, gashi kuma yace min zai yi tafiya har ya kira ni ya ce min su isa, cikin tsoro na dauka sai na ji shi ma hankalinsa a tashe muryarsa har rawa take wai na kira Husaini na fada masa yaje asibiti,na ce wace asibitin lafiya, a nan ya fada min wai makocinsa ya fada masa yan fashi sun shiga gidansa har sun yi harbe harbe”
A nan Inna ta tari numfashinta da cewar.
“To ya akai ya san sun shiga?”
“Ai makoncin nasa ma sun shiga gidansa suka karbe zinari, kuma suka shiga gidan da ke kallon na su Halimatu shi mai gidan ma sun kashe shi, to shi wannan wanda ya kira Hassan din shi ya kira yan sanda kin san shi ma dpo ne, ko da suka zo har sun gudu sai ganin gate din gidan Hassan akai a bude, shi ma na makocinsu a bude iyalai sai kuka suke”
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, to wai turo su akai ko me?”
Inna ta tambaya sai Hajiya ta tabe baki
“To waya sani, shi dai wannan Alhaji ance ba su karbi komai ba kashe shi kawai sukai wai sun ce ransa kawai suke so, shi kuma na wannan Alhaji Munir din sun karbi gulagulai da kudi, shi ma Alhaji Munir din sun fasa masa kai ai, ko da suka kawo Halimatu Asibitin nan kansa na jini shi ma an bashi gado aka ce”
“Subhanallahi, ko shine na ji Anty na cewa na leka na ganshi? Allah sarki Allah ya tona asirin ko su waye”
A zuciyata na amsa da amin, ina ta tsarguwa da kallon da Hajiya ke min.
“Amman ke ba su dauki komai a gidan ba ai ko?”
Na girgiwa Hajiya kai alamar a'a
“Ikon Allah sai suka fasa miki baki kawai dan zalumci, kai mutum.....”
Ta karasa da fuskar tausayi, ni kam tuni hawaye sun cika min ido har sun fara wanke min fuska. Ban sake maida hankali akan duk wata fira da suke da Inna ba, domin tunani ya rabu biyu, makomata na ke hangowa da kuma kokarin wanke Abdallah da zuciyata ke yi. Anya zai iya aikata kisa? Taya mutum mai aikin kamarsa ma zai iya shiga fashi da makami? Me zai kai shi shiga? Yes wata kila ba shiga yai ba gaba daya ba, what if labawa yai a cikinsu saboda ya samu biyan bukatarsa? Can kuma wani bangare na zuciyata ya jefo min wata tambayar? Miyasa sai Abdallah na ke zargi? Mi zai saka dan'uwa yai ma matar dan'uwansa haka? Miyasa be min a lokacin da nake gidan Aminu ba sai a nan? Saboda a can yana ganin zan iya fitowa wata rana kamar haka na aureshi amman a yanzu babu wannan damar? Na riga na auri dan'uwansa dan uwan ma twins brother dinsa....
Na kasa yarda cewar shi kadai din ne, zuciyata kuma ta kasa natsuwa cewar ba shi din ne ba, na kasa zargin kowa sai shi.
Sai da Hajiya ta fice sannan na samu natsuwa da sukunin mikewa tsaye na nufi gurin windows domin ba Hajiya kadai ba, Inna bata cikin dakin a wannan lokacin, tsakanin kalaman Hajiya da zargin Abdallah da kuma tambayayin da mutumen yai min da kalaman Hajiya sai na rasa wanne zan fara tunani? Wasu abubuwa na ji suna min yawo a cikin kai ga wani uban nauyi da zuciyata tai. Kaina na jingina jikin window ya lumshe ido ina jin kamar zan samu mafita a nan. Ajiyar zuciya na sauke ya fi a kirga sannan bude idon da ke cike da hawaye ina ta kallon mutane da ke kai kawo harabar asibitin, duk wanda na hango burge ni yake domin na san damuwarsa ba ta kai kamar tawa ba, murmushi nake hangowa a fuskar wasu wasu kuma dariya na ke gani a fuskarsu abunda ni na gagara samu.
Wani na soma hangowa kamar Kabir kamar ba shi ba, sai da na kara maida hankalina sosai gurin kallonsa da yanayinsa na hauka da yake ciki ya tabbatar min da Kabir din ne, har yanzu tsingiltar take yana tafiya ya nufo cikin asibitin, sai ga securities din da sauri su ka zo suka rika shi suka fitar da shi daga asibitin.
Neman natsuwata da damuwata nai na rasa, gaba daya sai hankalina na koma gurin Kabir din. Ban san kuka nake mai sauti ba, har dai da yarana suka shogo na ji muryar Adnan yana min magana.
“Momy kuke kike yi?”
Juyowa nai na kallesu na gyada masa kai alamar eh kukan nake, domin a bayyana hake kuma ba zan iya boye shi ba a wannan lokacin, gaba dayansu suka fashe da kuka har Amal da take karama ganin nima ina kuka, risinawa nai a gurin na
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 18 Chapter of 55