yi hakuri aure sai da hakuri, na ji sanyi sosai kuma ina jin na samu kwarin guiwar rike yayana da kyau domin na samu mai goya min baya.
Sun dade suna da maganar aurena da Aminu tun daga kan haihuwa ta ta fari har zuwa yau abubuwan da sukai ta faru da kuma abubuwan da suke gani ko ji, ni dai ban ce uffan ba domin har lokacin da kennana suka shigo suka saka baki ana yi da su ban ji ina furta ko da sunan Aminu ba a zance balle kuma har nai wata firar abunda ya shafeshi, sannan suna yi an saboda su nuna min kar na damu akan abunda ya faru.
Sai kuma sha biyu sannan kowa ya nemi gurin kwanciya, a lokacin Amal ta dade da bachi a kirjina, sai da na kwantar da ita a kasa saboda fitsarin da take sannan na fito falon Mama neman su Adnan.
“Ai tun dazun Abdallah ya tafi ta su gidansa, yace can za su kwana”
Mama ta fada.
“Har da Namra?”
“Eh har da ita”
“Akan me zai tafi da ita bana son tana rabar kowa a yanzu bari na kira shi...”
Ina juyawa Hafiza ta kirani.
“Anty Halima dan Allah karki kira shi yanzu, kin san dai indan kowa zai lalata miki yara ban da Yaya Abdallah, kuma saboda yana tausayin yaran yai so karki bashi kunya a yanzu”
“Bana iya yarda da kowa akan yarana yanzu, indai har kannen mahaifinsu zai iya yin wani abu na lalata da Namra, to kowa ma zai iya lalata da ita, rayuwar ya mace a yanzu tafi ko yaushe bukatar tattali, idan na nesa be lalata maka ita ba, na kusa zai iya samu damar hakan, idon kowa ya rufe a yanzu Hafiza, ba zaki taba gane abunda nake nufi ba har sai kin yi aure kin haihu sannan za ki gane tarbiya da tsare yaya abu ne mai wahala, ban son na sake aikata kuskuren da na aikata na barin Sadi da yarana har ya samu damar yi min tabon da ba zai gogu ba har na koma ga mahallincina, da na san cewar zuwa na gurin aiki zai haifar da haka da ban yi aikin ba, da na zauna da yayana a ko wane irin hali, a ko da yaushe ina aina yadda Namra zata ji idan ta girma ta samu irin wannan labarin, ida na kuma na sake bari wani ya sake faruwa? Laifin akan wa zan dora shi?daman tun farko be kamata na yarda da kowa akan yayana ba”
Na karasa tare da saka hannuna na share hawayen idona, sannan na kai dubana gurin mahaifiyata wacce ke kallona fuskarta da murmushi.
“Kinji kwatankwacin abunda nake ji a lokacin da kike budurwa ke da yan'uwanki da kuma yadda nake ji a yanzu da nake tare da kanenki, a kullum ina cikin fargaba da tsoron kar wani abun ya same su kar wani ya lalata musu rayuwa, ko daga nan zuwa gidanki suka fita hankalina a tashe yake har sai sun dawo sannan na ke samun natsuwa, shiyasa a kullum bana da burin da ya wuce ko wacce na ganta a dakinta, Halimatu kina jin abunda na ke ji a matsayina na uwa, ke ma uwa ce”
Dan murmushi nai kadan sannan na nufi dakinta na kwanta a kusa da Amal ina ta kallon fuskarta, kamin na sake tashi na nufi inda handbag dina take na dauko na danna number Abdallah sai na jita a rufe wata kila ya rufeta ne saboda ya san zan kira ko kuma ya saba rufe idan zai kwanta ne oho.
A wani abun mamaki a daren sai na kasa runtsawa har safe, bachi ya kauracewa idona ba dan kuma ina tunanin komai ba, domin ban ji tunanin kowa ya zo min rai ba a wannan daren sai Allah ya saka min saukin abun har na ke jin kamar bana da damuwa a tare da ni.
Misalin hudu saura na asuba na tashi na shiga bandakin domin yin alwala nai nafila kamin ayi assalatu, ina tsugunawa gurin fitsari sai jini ya fara min zuba a madadin fitsarin, sai da ya zubo min da dan yawa har da sare sannan nai fitsarin na wanke na tashi sai na ji abun be tsaya min ba.
A dole na nufi dakin kanena na tashi Marwa ta bani pad na saka sannan na dawo na zauna na dauki carbi Mama ina ta ja, marata na dan murda min kadan-kadan.
Haka nai ta dauri har kusan takwas da yan mintuna na safe, ina bawa Amal koko wayar Abdallah ta shigo.
“Hello Assalamu Alaikum”
“Wa'alaikissalam Momy ina kwana?”
“Lafiya kalau Namra an tashi lafiya?”
“Lafiya Kalau”
Ta amsa min da muryarta radau har tana yar dariya.
“Momy ga maman su Nabeela”
Ta mikawa matar Abdallah wayar muka gaisa, sannan ta bawa su Adnan da Aiman, daga bisani ya karba ba tare da ya min magana ba ya kashe wayar. Number Hajara na kira na labarta mata abunda yake faruwa sai ta saka salati da sallami tana fadin sai ta zo. Bayan na gama da matsalar Amal na aika yaro aka siyo min pad da pants a shago na shiga nai wanka na fito na saka tufafin jiya, sannan a shiga dakin Baba na gaishe shi tare yi masa ya jiki.
“Al-hamdulillah, na yi waya da Almu direba, zai zo anjima kadan sai aje kwaso miki kayanki, makulin gidan yana gurin Aminu ne?”
“Eh dayan yana can daya yana gurina”
“To za aje tare da ke saboda kar a hado da na shi, ki kwaso yana yaranki da na ki sai a kawo a nan,kamin na dawo ma ya tarar an kwashe komai na ki”
“To Baba na gode”
“Babu komai Allah ya bamu hakurin zama, kin san shi zaman gida sai da hakuri musamman ma gida nai kanne da yawa haka, sai kin yi hakuri d yan'uwanko kamin Allah ya kawo miki wani na gari”
“In-Sha-Allah Baba”
Na jidadin yadda ya nuna min kulawa sosai, tara da yan mintuna direban ya zo da babbar motarsa irin wannan ta kwasar kaya, tare da ni da kanena uku aka je muka kwaso komai sai da mu kai wa gidan tas da kayan sannan muka dawo, a unguwa kuwa kowa sai kallon yake ganin an kwaso kayan wanda be san da maganar ba ma yanzu ya sani. A dayan dakin da ake zuba kaya aka zuba gado na da kujeru da sauran tarkashe kayan sakawata kuma na kai su dakin su Marwa domin shi ne ke da girma sosai har ma na samu gurin shimfida katifa ta, na raba yan tsoman karana gefe. Tabbas na ji babu dadi a wannan lokacin domin bbu wanda zai so baro wadatacen gidansa ya dawo wani guri ya raba. Bayan mun gama na sanja wasu tufafin na bar Amal a gida na nufi gurin aikina. Kowa yayi mamakin ganina a wannan lokacin dmin ban saba zuwa da aiki a late ba ko ma naje late ba kamar haka ba, domin sha daya saura. Mun gaisa da Kabeer da Emanuel kamar yadda muka saba da halshen turanci kamin Kabir ya koma yana magana da ni da hausa daga can inda yake zaune ni kuma ina zaune a teburina.
“Ya jikin na ki?”
Shiru nai wata kila na fada masa bana jindadi ko? Oho na dai manta.
“Al-hamdulillah”
“Kin karya kuwa?”
Nan ma shiru nai kamin na bashi amsa, na manta when last wani ya tambaye ni ko ya damu da na ci abinci.
“Eh na karya”
“Baki karya ba Haima na sani”
Na fada yana dariya sannan ya mike tsaye yana fadin.
“Bari na sauka kasa naje restaurant na siyo miki wani abun”
“Aa Kabir na karya ban bukatar komai...”
Be saurareni ba ya fice yana ciro wayarsa daga aljihu, dafe kaina nai kamin na dauki takadun da na tarar a gurin an shiga da su office din Oga Dahiru, da sallama na shiga na mika nasa gaisuwa sai ya amsa min yana kallona.
“Kwana biyu ba ki zo office ba”
“Bana jindadi”
Na fada ina mika masa files din hannuna.
“Kin ga likita?”
“Eh malaria ce”
Wani kallo yai min kamar be yarda ba, sai kuma ya karbi file din yana murmushi.
“Halimatu kenan, Thank you you can go”
Na juyo na fito daga office din ina ta mamakin kallon da yai min da kuma murmushin da ke fuskarsa. Ina kokarin zama a kujera ta gabana ya fadi na rashin dalili har sai da na kira Allah sannan na samu natsuwa, aikina na cigaba da yi har na tsawon minti talatin sannan Hafsat ya shigo office din mu hankalinta a tashe tana fadin.
“Ku kuna nan zaune ba ku san an kade Kabir ba”
Na riga Emanuel mikewa tsaye domin da hausa tai furucin kamin ta sake fada da turanci, sai naji abu kamar daga sama.
“Taya?”
Na tambaya hankalina a tashe.
“Gashi can waje ban san yadda akai ba amman har kafarshi ta cire gashi can ana saka shi a mota za a kai shi asibiti... ”
Ban san lokacin da na rufe bakina na watsa da gudu zuwa sakan ma'aikatar ba, tsakanin ni da Emanuel sai aka rasa wanda yafi wani saurin saka ya ganshi, sai dai dukan mu mun yi rashin sa'a domin tuni an saka shi a mota an nufi asibiti da shi, babu komai a tsakan titi sai shimkafa da ya siyo min da kuma jini, ban san lokacin da na fashe da kuka ba har sai da Raliya abokiyar aikina ta rikoni muka dawo cikin ma'aikata, a lokacin kasa yin komai nai kuma ban yi tunanin binsa zuwa asibitin ba a wannan lokacin sai sauraren marata dake murdawa na ke, kamin na dauki jakata na fito na tari napep na koma gida.
Ina isa na tarar su ma sun gama na su fadan da Familyn Aminu akan yayana, wai sai an basu yara Baba kuma yace idan suna son yara su tafi kotu, sun labarta min abunda ya faru sai dai sun lura nawa hankalin ba a gurin nan yake ba a yanzu, gani sai wani duke duke nake saboda ciwon marar da nake ji.
“Lafiya Halimatu”
“Mama marata ke masifar ciwo”
Ta yi saurin janyo kujera ta ba ni.
“Zauna sannu”
Na zauna ina jin kamar ba zan iya zaman ba, domin ko ciwon nakuda be kai wannan ciwon da nake ji a yanzu zafi ba. Wayata dake cikin jaka tai ringing sai dai ban kula wayar ba saboda ba ta wayar nake a yanzu ba.
“Salma je ki taro Napep muje asibiti”
Mama ta fada cikin tashin hankali ganin yadda nake cizon baki saboda azaba domin ta san ni da juriya. Kamin a taro napep din mu shiga zuwa asibiti sai na ji kamar zan mutu har da kuka hannuna akan marata sai murjawa nake. Mun yi sa'ar ganin likitar nai mata bayanin abunda nake ji a take ta saka a bani gado sannan ya rubuta min magani ta kuma fada min cewar abunda ke cikina ne yake kokarin zubewa za a min wanki mara.
___________
Kwana biyu nan ina busy shiyasa bana post kullum amman da zarar komai ya zama normal zan cigaba kamar yadda aka saba In-Sha-Allah.
7/20/21, 8:29 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
🔟
Ba mu dawo gida ba sai 6pm na yamma, domin bayan mace ta min wankin mara sai da likita ya bani damar hutawa na awa biyu da rabi zuwa uku sannan muka dawo gida.
Da dare Hajara ta kawo min ziyara ta nuna min damuwarta da kulawa sosai kamin addu'arta ta biyo baya, mun dade muna fira da ita sai goma na dare mijinta ya zo ya dauketa. Bayan tafiyarsu da kamar mintuna talatin Abdallah ya kirani a waya har na yi kamar ba zan daga ba sai dai tunawa da bana da aure a yanzu ya yake min hanzarin kin daukar da nake yi a baya, wata kila ma Namra ce take son magana da ni ko Aiman.
Da nai picking ban ce masa komai ba, ko sallama da hello da ake idan an kira mutum ko kuma shi ya kira wannan karon bance ba, sai kawai nai shiruna ina jiran ya fara min magana. Shi kuma ya gagara cewa komai kamar wanda ya kira domin kawai yaji saukar numfashina, jin hakan yasa na kashe wayar na mike tsaye na nufi dakina ko kuma nace dakinmu ni da kannena. Tufafin jikina na canja na saka marar nauyi saboda yanayin garin da nake gani da kamar akwai hadari saboda zafin da yai yawa. Amal kuma na saka mata nata kayan bachi na kwantar da ita ina lallaba tai bachi sai ta fara min kukanta na banza daya saba yi wani lokacin idan za tai bachi.
“Ai da an sani a bawa Ya Abdallah ya hada da ke ya tafi mu huta”
Cewar Kanwata Haulat tana hararar Amal daman can basa shan inuwa daya da juna. Ni kuma nai murmushi na mika hannu na dago Amal na rumgumeta ina rarrashinta.
“Ya Abdallah yazo dazun lokacin kina asibiti”
“Ya kawo su Namra ne?”
Na tambaya ina kallonta.
“A a ba da su ya zo ba, shi kadai ya zo yana tambayarki sai Inna ta fada masa kina asibiti za a miki wanki mara”
Tana rufe baki kiran wayarsa na shigowa a wayata, nan ma sai dai nai kamar kar na dauka sai kuma wata zuciyar ta hana ni, picking nai na kara a kunne tare da sallama. Be amsa min ba kuma be ce min komai ba sai dai daga cikin wayar ina iya jiyo yadda yake ja da aje numfashi da karfi. Katse kiran nai na kwantar da Amal sannan nima na kwanta bayanta ina ta tunanin Kabir ko a wane hali yake ciki a yanzu inata auna zafin barin da na da kuma kafarsa da aka ce ta cire da gaske ma ta cire din ko kuwa dan karawa labarin magi dagishiri yasa tace haka? Number wayarsa na gwada kira da fari ta yi ringing har aka daga sai dai ina yin sallama sai aka kashe kiran na sake bugawa na ji wayar a rufe. Damuwa sosai ta shiga raina, ko ba komai ai mun yi zaman mutunci da Kabir idan na tsallake ko kuma na cire son tana jikin ko yi min maganar banza da Kabir yake kokarin yi ban san shi da wani hali na assha ba, tun ba jiya ba yana yawan damuwa na al'amurana, duk wani abun da ya dame ni zai nuna damuwarsa sosai a kaina, idan kuma akan wani laifin ne a gurin aiki to zai yi kokarin tare min ko ya wanke ki ko a gurin waye ne. Ko a kan wannan kadai ya kamata na damu da Kabir balle kuma saboda yaje siyo min abinci wannan abun ya same shi, ko da ciwon kai ne ya same shi ta dalilina dole na damu balle kuma hadari, abun sai ya hade min a guri daya har na rasa wanne zan fara tunani bayan damuwar da ke cina yanzu kuma wani abun ta samu Kabir ta dalilina.
Har garin Allah ya waye Kabir na cikin raina ban jidadin rashin zuwa ganinsa da ban samu yi ba, kusan rabin mafarkin da nai na Kabir ne sai dai ba zan iya fahimtar sakon mafarkin ba, kuma na alakanta hakan da kwanta da nai ina tunaninsa.
Duk da bana sallah haka ba be hana ni tashi da asuba da wuri ba kamar yadda na saba, ko bana sallah na kan yi addu'oina na safe idan ina lokacin period ne.
ABDALLAH POV.
Da gangan yake yai magana ya yi shiru yana ta sauraren yadda numfashinta ke fita fuskarsa na yalwantuwa da murmushin da shi kadai ya san sikarsa, bayan ta kashe wayar ya sake kira sallamar da tai masa ta saukar masa da natsuwa da kwnaciyar hankali daman can muryarta kawai yake son ji, domin ba shi da wani abun da zai ce mata, bayan son yai mata jajen ɓarin da tai ta waya, ɓarin kuma ba karamin dadi yai masa ba, domin ya kusanto masa da nesa kusa zuciyarsa na raya nasa a yanzu yana cikin ko wane mataki da zai iya nunawa Halimatu soyayyah, domin bata da auren a yanzu kuma ta cika idda indai har jinin ya tsaya mata. Kansa ya daga sama yana kallon tauraren da sukai ma sararin samaniya ado. Sannan ya maida wayar aljihunsa tare da zuba duk hanneyensa aljihun wandon, Halimatu ba zata so shi ba, ba zata taba amincewa da shi kai tsaye ba, domin yayi kuskuren nuna mata kauna a lokacin da take da igiya uku ta aure akanta har ta koma biyu har da zama daya, shi yake yawan fada mata mijinta yayi kaza ya yi kaza, yana yawan nuna mata Aminu ba irin mijin daya dace ta aura ba ne, ya dade yana jira zuwan wannan ranar ya dade yana addu'ar Allah ya raba auren Aminu da yar'uwarsa Halimatu saboda kawai shi ya aureta, yana ji a ransa kuma yana yawan rayawa a zuciyarsa cewar shi kadai ya dace ya zama mijin Halimatu, domin shi ne mutumen da zai iya nuna mata kauna zallarta ya kare mutuncinta ta martaba, and he know exactly how to lighten the candle of happiness in her life. Tun daga lokacin da ya dawo kasar nan tare da iyalinsa ya kyalle ido ya ga Halima sai Allah ya dauki sonta mai tsanani ya saka masa, har ya zama bashi da sukuni da walwala idan ban ganta ba ko be ji daga gareta ba, tun yana kokarin cire abun a zuciyarsa ya kawarda komai har ya gagareshi, har yake ji da ace ya san lokacin da take budurwa ko kuma yayi arba da ita tabbas da Halimatu bata da wani mijin bayan shi, domin tana da siffar da yake so a jikin mace komai na rayuwarta burge shi yake, the way she dressed, yadda take tafiyarda rayuwarta ga hakuri da kawaici ga magana ma so calmly, even simple makeup din da take burge shi yake.
Daga lokacin da ya gano kalar mijin da take aure kuma sai tausayinta ya samu muhalli a zuciyarsa, kuma ya samu makamin yaki da igiyar aurenta.
Ba abu ne mai sauki Halimatu ta karba tayinsa a yanzu ba, shi kansa ya sani domin haka ba zai yi kuskure nuna mata haka a yanzu ba ko kuma furta mata kalma so ko aure a yanzu ba, duk kuwa da kasancewar ta dade da jin daga gareshi saboda ya fada mata ba daya ba ba biyu ba cewar yana sonta yana kaunarta a lokacij da take da igiyar auren a akanta har take masa kallon mahaukaci ko kuma marar tunani, wannan dalili ya saka Halimatu tsanarsa fiye da kowa a familynsa.
Ba irin wannan lokacin ya kamata ya nuna mata so ba, wata kila ma bata sha'awar auren a yanzu, sai dai ya shirya nuna mata kulawa da kwantar mata da hankali da kuma kaunar yaranta.
“Daddy ba zaka shigo ba?”
Juyowa yai yana kallon yarsa Suhaima fuskarsa dauke da murmushi, ya kai hannunsa ya daga sama.
“Eyyyy ba ki kwanta ba Mamana?”
“Yes mu na ta kallo da Aiman, amman kowa yayi bachi sai ni da kai da Aiman muka rage”
“Okay je ciki ina zuwa”
Ya fada yana sauketa kasa sai ta juya da gudunta ta koma ciki, shi kuma ya sake ciro wayarsa sai dai wannan karon ba Halimatu ya kira ba Hajiyarsa ya kira duk kuwa da bashi da tabbacin cewar zata dauka wata kila ma ta yi bachi. A mamakinsa sai tai picking call din da muryarta radau babu alamun bachi.
“Hajiyata ba ki kwanta ba?”
“Ban kwanta ba Husaini kai me kake a farke?”
Jimmm yai na wani lokacin sannan ya ce.
“To ni ma dai ba zan iya fada ba for now, amman dai na kira na fada miki cewar Halima ta yi miscarriage ya kamata ki dubata gobe inda hali, kin ga ko sakin da akai mata Hajiyata ba ki je kin mata jajaye ba”
Daga dayan bangaren Hajiya tai murmushi mai sauti sannan ta dora da.
“Zanje gobe In-Sha-Allah shikenan? Jikin nata dai da sauki ko?”
“Ban sani ba, amman naje dazun ban tararda ita ba wai tana asibiti ni kuma bana son su fara zargin wani abun ne shiyasa ban je ba, amman ni ma gobe zanje ma dubata”
“To sai ka biyo ka dauke mu mu tafi ai”
“Aa Hajiyata zuwanki dabam na Abdallah dabam”
Ya fada da murmushi a fuskarsa sannan yai mata sallama ya sauke wayar, fira da mahaifiyarsa ko yayansa na daya daga cikin abunda yake saka shi ciki nishadi da farinciki ko da kuwa yana cikin damuwa ne. Juyowa yai ya nufo balcony ya tura kofar falon ya shiga. To His surprise sai ya samu uwargidansa tsaye jikin window dakin tana kallon waje sai dai shigowarsa yasa ta juyo ta da dubanta gurinsa. Ya dan wara ido yana murmushi daya saba yi mata.
“Suhaima ta ce kina bachi”
Ta wani marairaice kamar karamar yarinya marar.
“Taya zan iya bachi Doc be kusa da ni, na yi na dan guntun lokaci sai ya farka bachi ma ba dadi”
Murmushi yai ya katsa kusa da ita yana mai jin son uwargidan har cikin ransa, ya kai hannunsa ya rumgumeta ta baya ya dora kansa saman wuyanta.
“That's right Teema”
Ta yi saurin juyowa ta kalleshi.
“Teema kace fa?”
“Eh ba sunanki ba ne?”
“Amman ai ba haka kake kirana ba sai dai ka ce min Baby ko Madam ko Mom Suhaima”
Dariya yai ya jiyarda ita ya sake rungumeta ta baya.
“To Baby yau yan tsokarna sun motsa ne shiyasa”
“Da wa kake waya?”
“Da Hajiya”
“Amman ka dade a waje fa”
Ya sauke hannayensa daga rikon da yai mata ya saka hannayensa aljihu.
“Ina ta tunanin mutuwa ne, mutuwa kawai ake a yanzu any how abun har tsoro yake ba ni, ina ta tunanin makomarmu ne”
Ya fada yana hade yawun bakinsa domin shi ma yasan karya yai. A take Teema ta bata fuska damuwa ta bayyana a fuskarta jin furuncin daya fito daga bakin mijinta, hakika mutuwa abun tunawa a ko wane dare ko dakika sai dai ba kowa ne ke tunawa da ita ba sai masu imani da tunanin ya goben su zata kasance.
“Allah dai ya saka mun cika da imani, nima abun na taba ni Wallahi”
Ta fada bayan ta sauke ajiyar zuciya. Hannunsa ya kai ya riko hannunta ya nufi hanyar dakinsa da ita.
“Ina Aiman? Suhaima tace sune kawai ba su yi bachi ba”
“Na saka su bachin dole ai, kun zauna gaban tv kamar a gurin za su tabbata”
Hannunta ya saki ya nufi dakin yaransa, a bakin kofar dakin ya tsaya yana kallon Suhaima da Lubna sai kuma yayan Halimatu wato Namra da Aiman da Adnan, a ransa ya rika kwatatta yadda abun zai burge idan da ace shi Halimatu ta haifawa yaran nan gaba daya musamman Aiman da Adnan domin shi Allah be ba shi yaya maza ba, yan mata biyu matarsa ta haifa masa. Zuwa tai ta tsaya bayansa tana kallon yaran.
“Minene?”
“Ba komai”
Ya kai hannu ya janyo kofar dakin sannan ya nufi dakinsa Teema na biye da shi a baya.
HALIMATU POV.
Karfe takwas na safe kofar shiga dakin da Kabir yake tai min, domin na kwana da shi a raina da na farka kuma sai na ji bana bukatar ganin kowa sai shi hakan yasa ban wani tsaya karyawa ba na nufo asibitin daman can abinci be dame ni balle kuma yanzu da damuwa ta zame min ci da sha, kuma ta zame min abokiyar fira.
Ba ni kadai aka hana shiga ba, har da sauran masu ganin marasa lafiya da masu kawo abinci balle kuma ni da ban kawo komai ba. Muna tsaye a gurin har kusan tara da wani abu ba bar mu mum shiga ba sai dai an bar masu dauke da abinci sun shiga, ni kan sai na samu guri kusa da inda kofar take na zauna, na bawa kofar baya zaman jiran gawon shanu domin ban san lokacin da za a bada damar shigar ba, sai dai bana jin a yau zan wuni ban saka Kabir a ido ba ba dan komai ba sai dan damuwa da halin da yake ciki a yanzu wanda silata ne komai ya afko. Ji nai a dabani da wani hannu mai sanyi da alama mamallakin hannun ya taba ruwa mai sanyi ne ko kankara, ashe
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 7 Chapter of 55