Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ni kuma na shiga kitchen na dora miya domin ko da muka dawo Kausar ta toke mana tuwon. Daf da magariba Adnan suka dawo daga makarantar islamiya, daker na tattara su sukai sallah sannan na kwashe miyar na zuba musu nasu na sako nawa ni da Amal muka ci Namra kan ko ruwa kasa sha tai, hakan yasa na dauki wayata na kira shi. Sai da ta dade tana ringing sannan na daga. “Ya akai?” Shine abunda ya far tambaya, ni kuma na mika masa gaisuwa “Ina wuni?” “Lafiya Kalau” “Namra ce bata da lafiya tun jiya cikina na ciwo shine na kaita asibiti dazun suka bamu awon fitsari da hoto kuma suka rubuto mata magani” “Wa kika tambaya kamin ki fita? Da izinin wa kika fita?” Sai na kasa amsa masa domin na san bana da gaskiya a nan, be kamata na fita ba tare da na tambaye shi ba, sai dai na san idan na tsaya tambayarsa ba lallai ne yace na tafi ba domin duk wani abu daya fito daga bangarena baya daukar sa da muhimmancin wata kila ma zai ce kashin kudin ne zan ja masa. “Ka yi hakuri dan Allah” Be amsa min ba yaja tsaki ya kashe wayar. Ji kuma na sauke ina jin raina ba dadi a take abincin ya fita raina daman da safe ban iya karyawa ba. “Adnan je ka kira min Kausar ta siyo ma Namra magani a chemist” Da sauri ya tashi daman dan son yawo ne shi da Amal a take ta rufa masa baya har da gudunta. I decided na aiki Kausar din na bata kudin da ke hannu ta siyo mata maganin kamin shi ya gama fushinsa ya siyo mata. Adnan na fita sai ga Afrah ta shigo wato yar Hajara da bakar leda a hannuna. “Wai ga shi Momy tace a kawo miki” Karba kawai nai na aje ba dan ina tunanin amfani da shi ba, domin na saba amfani da irin abubuwan nan ban taba ganin ribarsu ba, sai dai na ji wasu matan suna labarin abu kaza yana da kyau ko yana yi, ni dai nawa mijin bayan nuna min idan ma na sh wata kila kuma ni tawa hallintar bara karbar irin waennan abubuwan. Afrah na fita sai aka sake turo kofar falon aka shigo wannan karon Sa'adatu ce kawata. “A a maraba da manya” Na fada ina dariya. “Ah ai kune manya kuna cikin irin wannan gida haka ga uwar daula ai kukan ku kukai dacen auren mu mata kawai muka rako duniya” “Uhmm” Kawai na iya fada domin yawancin mutanen da suke zuwa gidana suka ganin kyakkyawan falona da gidan sai su tai min kallon kamar na fi kowa dacen aure. “Bari dai na kawo miki ruwa” Na fada ina nufar kitchen, ita kuma ta hau tambayar ina Amal da sauran yaran. __________________ Anya da gaske akwai mata irin Halimatu kuwa? 🤔 7/20/21, 8:28 AM - Buhainat: *GOBE NA...* _My Tomorrow_ By Khadeeja Candy 4️⃣ “Sa'adatu kenan, kwana biyu ma kin daina dan lekowa, ko ya fara hana yawo ne?” Na fada bayan na mika mata ruwan sai ta wara ido. “Tab ya isa? Ai a hannuna yake sai yadda na ga dama na juya shi” “Too kaji manya a bamu sirrin” “Sirrin mai wuya ne Halima,amman Wallahi da ni nake da kyau ki da irin wannna jikin na ki sai na more” Kallon rashin fahimta nai mata. “Kamar ya ba?” “Ka more rayuwa mana, kai ta sha'aninka kana zuwa duk inda kake so” Ta fada tana janye mayafinta daga jikinta a take kirjinta ya bayyana, daman irin dinkin nan mai bayyana maman mace daga gaba. “Ai kin san halin wani namjin ba daya ne da wani ba, kin ga ke idan mijin ki mai sauki kai ne baban naki ba shi da dama” Na fada tare da kiran Aminu da babanta kamar yadda take kiransa kasancewar sunan mahaifinta ne. “Babu namijin da yake da dama Halima, ni kin ga mijina Wallahi zan iya tafiya wani garin na kwana iya kwanakin da naji sun min na dawo be isa ya ce min komai ba” “Too ku manya ne Sa'adatu” Na fada cike da sha'awa da kuma jinjina abunda ta fada, ko bata fada min da bakinta ba na san zata iya domin ta saba zuwa wani gari da sunan biki ko ganin yan'uwa ta bar masa yaransa sai ranar data ga dama ta dawo kuma ba zai yi komai ba. Abun har burgeni yake ni da wani lokacin ko makota sai Abban Namra ya hana ni zuwa. “Wai ya kika ba ni ruwa zalla a tsirara ba masu kala ne?” “Baban na ki ne be siyo masu kala ba” “Aa Babana fa komai kawowa yake karki cutar da shi, daman kin saba bakin sherinki ni bari ma na tashi daman bankwana na zo nai miki zanje Kaduna gobe In-Sha-Allah” “Kaduna kuma? Gurin me?” “Wallahi wani abun bikin ne ya taso mana zanje na kwana hudu ko sati ma a can” “Da yaran zaki je kenan” “Aa ni kadai zanje na shakatawata abuna yara su zauna gurin Babansu” “To indai baki yi hankali ba sai ya dauko miki wata” “Ai be isa ba Wallahi wa? Ni? Hmmmm ai na bashi wannan ya shanye” Ta fada tana wani turo dankwali tare da nuna min kasan kafarta. “Haka fa, na ji ance ana yi ko?” “Au tsayawa ji kikai? Ba ki ma aikata ba” “Ina ganin kamar akwai rashin dacewa a haka” “To yar sarkin Malamai” Dariya nai zan sake magana sai jin tsayawar motar Abban Namra mu ka ji, a take gabana ya fadi domin na san zai tambaye shi yaransa gashi tun da na aikasu basu dawo ba, kamin ya shigo falon hankalina ya tashi sosai saboda aiken da nai musu ga kuma fita kai Namra asibiti da nai ba tare da izininsa ba na san zai iya yi min fada a gaban kowa, ni kuwa abunda na tsana kenan ayi min fada a gaban wani musamman kawayena. Fuska a hade ya shigo falon ni kuma nai saurin mikewa tsaye na nufi inda yake ina masa sannu da zuwa tare da kai hannu na karbi jakarsa. Da kamar ba zai amsa min sannun da nai masa ba, sai dai yana gada ido da Sa'adatu sai ya sake fuskarsa. “Yauwa, a a diyata ce da kanta a gidan?” “Nice Babana ya garin ya gararin garin?” Ta amsa tana wani karkada ido, na yi zaton ko zata ja mayafinta ta rufe kirjinta ne kuma ta gyara ture kaga tsiyar da tai na dankwalinta amman ba ko daya, zama yai a kujerar da ke facing din tata yana murmushi. “Fatar kin zo lafiya?” “Lafiya kalau matarka ta bani ruwa masu sanyi amman ba masu kala na yi magana tace Babana be siyo ba” Sai juyo yai ya kalleni ina kokarin zama kusa da shi. “Ah ah drinks ya kare ne daman? Ai baki fada min ba” Kasa ce masa komai nai bayan kallon mamaki da nake masa rabon da ya siyo mana wani abu mai sunan lemu mu sha a gidan har na manta, amman yau saboda ya nuna yana siya har yake tambayar yaushe ya kare? Haka yake min idan ya ga mutane ni kuma bana iya karyata shi. “Jiya ya kare” Na fada ina hade yawun bakina. “Okay bari sai gobe a siyo ai ban sani ba, ina fatar kin ci abinci?” Ya karasa yana naida dubansa gurin Sa'adatu. “Aa ban ci ba” Sai ya juyo kaina. “Miyasa ba a bata abinci ba? Ko ba a gama ba? A kawo mata abincin mana” “Aa ni tafiya ma zanyi” Ta fada tana janyo mayafinta ta rufe jikinta tare da gyara dankwalinta. Sai shi ma ya mike tsaye da sauri yana ta kallonta. “Bari na rage miki hanya, ina takardar maganin take?” “Tana daki” “Je ki dauko sai na siyo daga can” Har na bude baki nai magana ganin da gaske yake zai wuce da ita sai kuma wata zuciyar tace nai kawaici na kyale shi. Dakina na shiga na dauko takardar maganin na kawo masa sai ya karba yana duba sannan ya kalleta ya ce. “Muje” “Matar Baba sai wani gamon kuma” “To Allah ya kiyaye hanya” Na fada ina binsu da kallon zuciyata na mugun tsoyuwa. Sai da suka fice daga falon na koma gurin windows din ina hangensu har suk shiga motar yaja sukai gaba, ajiyar zuciya na saki tare da sakin labulen falon sannan na dawo saman kujera ya zauna, na san Sa'adatu zata dauki hankalin Aminu saboda bata da jiki kamar ni kuma ita fara ce sosai kamar dai yadda yake yawan fada min yana son mace fara marar jiki ba irina ba. Tunanin yadda zan yi na rage kibar ne ya fara zuwa min a rai shi farin na san mai sauki ne zan iya siyen mayukan fari na shafa nai fari amman rage kibar ne zai ba ni wahala domin na gwada abubuwa da dama na rage kibar har yau ban dace ba, sai a yanzu na tuno da wani maganin rage kibar da na siye, tashi nai na nufi upstairs, ina shiga dakin na nufi gurin dana rataye jaka na dauka bude n dauko maganin na sauko kasa na shiga kitchen na zuba ruwan zafin da suke a filas na zuba maganin na kasa sugar kadan na fita shi, sannan na zauna ina sha a hankali, zuciyata cike da fatar ya karbe ni ni dai duk abunda zai shiryani da mijina mu yi zaman auren na jindadi da kaunar juna ina son shi, ina ji a raina inda har idan na kawarda kibar nan da ke jikina nai fari fes Aminu zai so ni to na shirya yi ko da kuwa zan kashe kudi da yawa. Ina cikin sha na jiyo Namra tana amai da sauri na aje kofin na fito da sauri na rikata, amai take babu kakkautawa, a take hankalina ya tashi daman abu kadan ya saka ni faduwar gaba ko kuka. A cikin falon tai aman har ta gama sannan na rika ta na kaita bandakinsu na wanke mata jikinta na saka mata wasu tufafin. “Momy sanyi na ke ji kum cikina ciwo yake” Ta fada cikin kuka jikinta na ta kyarma. Rigar sanyi na dauko na saka mata na kwantar da ita saman gadonsu na lullube ta sannan na fito na gyara falon. Sai da na gama gyaran sannan Adnan da Aiman suka dawo daga aiken da nai musu tare da Kausar din. “Ina kuke je kuka tsaya tun dazun?” Na fada cikin tsawa a take tsoro ya rufe Adnan. “Momy ko da muka je bata cikin gidan sai muka jira har ta dawo muka fada mata, ki yi hakuri dan Allah” Abunda sukai min be kai ya saka raina baci ba balle har na dake su, amman sai zuciyata ta rufe a take a gurin na mari Adnan kamar wani babba na ciro wayar caja na saka na zanesu tas suna da kuka da ihu Aiman na ni yake ta kira amman nai kunne uwar shegu da ihun na su kuma na tirsasu su yi shiru. “Kausar ki bar shi kawai daman magani za ki yo ma Namra kuma Babansu ya karbi takardar maganin” Da to ta amsa min ta fice da sauri ganin kamar raina a bace yake. Ni kuma na koma kitchen din na hada wa Namra tea wai ko zata iya sha amman ta kasa sha, sai kuka take hakan yasa hankalina ya tashi na sake gwada kiran Abbansu wayar tai ringing har ta gama be dauka ba. Be kuma shigo gidan ba sai sha biyu da mintuna kamar yadda ya saba, ni kuma har lokacin ban yi bachi ba ina rumgume da Namra ga Amal a bayana wacce ta cilasta ni goyonta saboda bakar rigima irin nata. “Sannu da zuwa” “yauwa” Ya amsa min fuskarsa ba yabo ba fallasa sannan na wulgo min ledar maganin ya nufi hanyar dakinsa, kwantar da Namra nai daga saman jikina zuwa jikin kujera na tashi na nufi inda ledar maganin take na dauka zuciyata nata soyuwa, na rasa gane wane irin zama na ke da Aminu, kamar waenda akai auren dole ko kuma basa kaunar junansu haka yake mu'amala da ni, ko za a yanka ni ba zan iya fadar abunda nai masa ba wanda ya saka yake min wannan wulakancin. Ta jikin kwalin maganin na duba yadda ake badawa na zuba na bata ta sha sannan na dauketa daga falon na sake maida ita dakinsu tare da yan'uwanta na kwantar da ita, kana na nufi gadon Amal na kwantar da ita ita ma nai mata addu'a na tofa mata sannan na janyo kofar dakin na fito. Dakina na koma na sauya tufafin jikina daga atamfa zuwa wani yadi mai kyau da kyalli na fesa turare na gyara fuska na shafa janbaki da dan man baki kadan dan yai kyali sannan na fito na nufi dakinsa. Da sallama na shiga ya amsa min yana cin abinci ba tare da ya kalleni ba. Sai na zauna gabansa ina ta kallon yanayinsa shi kuma hankalinsa na kan wayarsa. “Ya akai?” “Ba ni da hali na zauna da kai da sunan hira ko kallonka sai ka tambaye ni minene? Ban san abunda nai maka ba Abban Namra amman gaba daya ka canja min kamar ba kai ba, ni dai na san ba auren kiyayya mu kai ba amman irin zaman da muke da kai kamar na kiyayya” “Da bakamar yanzu ba ce Halima, auren soyayya mukai kuma ai zaman soyayya muke ko? Ko na kiyayya ne? Ke kanki kin san da bana son ki ba zan zauna da ke ba, kuma rayuwa tana sauyasa ke kanki ai ba kamar yadda kike ada kike a yanzu ba kin canja” Hawaye ne ya fara min zuba. “Canjin jikina kadai be isa ya saka ka wulakanta ni ba, ban sani ba ko na aikata maka wani laifi mai girma da ban sani ba, ko kuma a sani ni ina ganin kamar ba laifi ba ne, dan Allah ka yafe min Abban Namra, na kasa sabawa da zamankewar auren da muke, na kasa fahimtar juya min baya da kai ka yafe min idan wani abun nai maka dan girman Allah” Be ce min uffan ba har ya gama cin abincin ya sha ruwa sannan ya dago kansa ya kalleni ya ce. “Indai kina son mu shirya da ke, to ki aje aikin nan babu yadda za ayi kina aiki kina mu'amala da wasu maza a waje ni kuma kina zaune a gidana kawai a matsayin mata, gashi nan har idonki ya fara zarewa kina fita ba tare da kin tambaye ni ba abunda baki saba ba, Allah kadai yasan kalolin mazan da kike gamuwa da su” “Ka rika kyautata min zato, ko da yaushe kana yawan cewa ina mu'amala da wasu mazan a waje, kana yawan ganin kamar ina aikata fasikanci ne da aurena, ba zan iya aikata zina ba ba zan iya da hakki hudu ba, naka na iyeyena na yayana da kuma na Ubangijina, ina aikin nan ne saboda daukewa kaina wasu lalurorin kai ma ka sani, muna da hidima da yawa a gidanmu iyayena ma suna bukatar taimakona” “Dauke ma kanki wasu lalurorin? Miye bana miki ci ko sha?” “Ba ci da sha ne kadai abunda mace take bukata a gurin mijinta ba Abban Namra, akwai kulawa da wasu bukatun na yau da kullum da kuma ta yan'uwa da iyaye, amman indai har aje aikin nan zai saka ka shirya da ni mu koma muna zama da juna cikin amince da kauna, zan aje sai na kama sana'a” “Aa idan kin san idan kika aje aikin wata sana'ar zaki kama kar na ki aje aikinki daman ai ban isa da ke ba” Kasa cewa komai nai har kuma lokacin hawaye nake, Aminu wani irin murdadden mutum ne wanda baya fahimtar abu idan baya so ba. Taya zai hanani aiki kuma yace ba zan yi sana'a ba, kuma ba zai dauke min duka lalurorina ba? “Ga cikin nan na ce miki a zubar kin ki yarda, haba wane irin abu ne haihuwa hudu a shekara goma sha biyu, ai gashi nan duk kin bude kin wani tsufa, kuma yanxu ana ta abinci ai ba ta haihuwa ake ba ina zan iya da lalurar yara biyar a yanzu, idan kin yaye ki sake daukar wani kuma? Haba abu ai yayi yawa” Ya fada min kai tsaye, sai a yanzu na gane dalilin kauracewa shimfidata da Aminu yai. Mikewa nai tsaye na juyo da zimmar fitowa na baro masa dakin, sai na ji ya ce. “Zanje Kaduna gobe gurin wani aiki, wata kila nai kwana hudu ko sati” Ban juyo ba ban kuma ce masa komai ba, na baro masa dakin na dawo falo na zauna na rungume hannayena ina wani abun a zuciyata, idan nace zan kashe aurena hakika ban san wane hali yarana zasu fada ba, ban kuma san wane kalar mijin zan aura ba, idan kuma na cigaba da zama da shi zan saka kaina cikin damuwa ne kawai marar misaltuwa, domin ko a yanzu idan aka auna na san ba za a sara samuna da hawan jini ba, shekara goma sha daya ba yau ko jiya ba ne. “Idan kika cigaba da zama da mutumen nan, hawan jini ne zai kama ki, zaki kai wani mataki da baki iya komai daga lokacin kin tashi aiki, ba zaki iya tsinanawa kanki komai ba, ban ga dalilin da zai saka ki yi hakurin zama da mutunen nan ba wai wani zaman yayanki shi be san da yayan ba ne yake musguna miki? Ko ke kadai aka dorawa hakkin kula da su” Dafe kaina nai tunawa da maganar da Abdallah yai min akan Aminu, wani bangaren yana da gaskiya idan na ce nai hakurin zama ni ce zan cutu idan kuma na bar gidan still zan cutu da rashin yayana a kusa da ni. “Ko wane aure yana da kalubale Halimatu, ki yi hakuri ki ta addu'a ki karbi kaddararki da hannu biyu, idan kin bar Aminu kina da tabbacin shi mijin da za ki aura ba kamar Aminu ba ne? Idan ba ki hakurin zama da uban diyanki ba ba zaki iya hakurin zama da kowa ba, kuma daga haka za a fara kirga miki aure” Haka Mama take yawan fada min idan ina mata complain din Cewar na gaji da zaman auren nan. Yanzu kumaga sharadin Aminu na aje aiki idan har ina son ya shirya da ni, ba ni da tabbacin idan na aje aiki zai kula ni domin tun kamin aiki ya fara min wannan wulakancin, idan kuma na bar aikin wasu abubuwan da nake iya yi ma iyayena ba zan iya daukar dawainiyar ba, wasu abubuwan da nake iya yi ma kaina dole za su gagareni. Haka dai nai ta tunanina kala kala har kusan biyu na dare sannan na tashi na nufi dakina, wutar dakin na kashe sannan na hau saman gadon na kwanta na lumtse idona ba dan ina jin bachi zai dauke ni ba. Dilllll wayata tai kara alamar shigowar sako bude idona nai na ka hannuna saman aljihun gadon na dauki wayar ina dubawa. _Ki yafe min dan Allah, na kasa bachi saboda na san yau na bata miki rai, amman ban yi zimmar daba ki da wata manufa ba, ina ganin kamar ni da ke mun zama daya ne, kuma ni na dauke shi a matsayin wayewa ba wai dan wani abun ba, sai dai naga kamar ranki ya bace ki yi hakuri dan Allah ki shafa min kan yaran nan ki gaishe su_ _Kabeer_ Ina gama karant sakon hawaye ya wanke min fuska, wani wanda ba mijina ba shi yake damuwa da fushi da bacin raina har ya gaishe da yarana. Rumgume wayar nai a kirjina ina jin wani irin kyautata da ganin kimar Kabeer. __________________ Anya Halimtu zata aje aikin kuwa? Ko kuwa dai zata zabi zama da Aminu a haka? Wai mi yake damun Namra ne? 🤔 7/20/21, 8:29 AM - Buhainat: *GOBE NA...* _My Tomorrow_ By Khadeeja Candy 5️⃣ Iyayena na gari abun alfahari idan kai dace da iyaye hakika ka yi babban dace, bayan su kuma sai miji shi ma idan kai dace da miji na gari ka samu ingantacciyar rayuwa idan Allah yai maka falala ka sake dace da yayana nagari ko kai an gama maka komai a rayuwarka. Al-hamdulillah ban san yanda tarbiyar yarana zata kasance ba bayan girmansu amman ina fatar su tashi akan tafarkin da na dora su akai, idan na samu haka ko da shi kadai zan iya gode Allah, duk kuwa da na san babbar jarabawar duniya ita ce ta rashin dacen miji. Ban taba jin kewar budurci ba irin yau, ji nake kamar ace yau ni din budurwa ce da na sake zaben wani mijin ba Aminu ba, na kwana rungume da sakon wani a kirjina saboda rashin kulawar mijina, da ace na san rayuwa zata sauya min haka bayan aure da na zabi zama a budurcin har na bar duniyar nan, bachi be dauke ni da wuri ba, haka kuma ban dade ina bachin ba na farka, kaina har wani nauyi nake jin yana min ga wani uban ciwon zuciya da nake jinsa har cikin kashin bayana. After sallah nai addu'o'in da na saba sannan na nufi kitchen domin hada ma yarana abincin zuwa makaranta, misalin bakwai saura na safe ya shigo kitchen din rike da jakarsa sai ya tsaya a jikin kofa, ni kuma nai kamar ba san da mutum a gurin ba har sai da yai gyaran murya sannan na juyo na kalleshi “Ina kwana?” “Lafiya kalau, ga wannan ki rike da wuri zan tafi saboda bana son rana yai min” Ya fada yana miko min dubu uku, kallon kudin nai na girgiza masa kai. “Ka kara akwai kudin da za su ishemu har ka dawo” Be ce min komai ba, ya aje kudin saman kitchen cabinet ya juya, a karon farko yau zai tafi wani gari amman na kasa ce masa Allah ya tsare sai binsa da nai da kallo. Juyowa yai ya kalleni. “Da ki min addu'a da karki min duka uwarsu daya ubansu daya, sai abunda Allah ya rubuto zai same ni, mugun nufinki ya koma kanki” Yana fadar hakan ya juya ya fice, ni kuma nai murmushi ina jin bakar maganar da ya fada min har cikin raina. Kaina na daga ina kallon kitchen din yadda tsarin gidanmu yake da siffar masu arziki ko kyautar rabin miliyan nai ba za ayi mamaki ba saboda ana ganin mai arzikin nake aure, amman yau zai yi tafiya saboda bakar keta irin nasa ya dauki dubu uku ya bani. Dauke kai nai domin na san idan na ce zan cigaba da tunani zan iya faduwa a gurin ko kuma wani abun ya same ni. Bakwai da rabi na shiga na tashi yarana nai musu wanka sukai alwala sukai sallah sannan na shirya su cikin uniform dinsu na makarantar boko ban da Namra da har yanzu bachi take jikinta kuma da dan zafi. Kasa suka sauko suka karya tare da Amal sannan na shiga dakina na saka hijab na fito na saka su gaba muka nufi gate. Sai dai mun yi sa'ar haduwa da mijin Hajara kamar jiya. “Ina Namra yau?” “Bata jindadi” “Subhanallahi Allah ya sauwake” “Amin” Sai ya saka yaran a motarsa har da Amal suka tafi, daman ta saba idan yan kwarai suna kanta tana yarda ta bisu su tafi idan ya dawo sai ya kaita gurin Hajara. Juyowa nai na dawo cikin gidan, sai na shiga dakina nai wanka ina cikin shiryawa wayarta tai ringing, dauka nai na duba sai ga number Abdulhamid hakan yasa ni picking na kara a kunne. “Hello” “Good morning Halima ya gida ya yaran?” “Lafiya kalau” “Na miki sako ta whatsapp wai baki hau ba so i decided na kira ki” “Lafiya dai?” “Account number dinki na k so dan Allah zan dan saka miki wani a ciki” Dauke wayar nai daga kunnena na duba dan kara tabbatarwa idab Abdulhamid din ne, ganin shi ne yasa na maida wayar a kunne na ce. “Abdallah yace ka saka min?” “Abdallah kuma?” Shiru nai na kasa cewa komai, na san tawayensa Abdallah shine mai yi min irin wannan dabi'un yana yawan fada min ba dadi Akan Aminu da aure daga daga cikin dalilin daya saka nai blocking dinsa ta ko'ina. “Halima Abdallah yace zai baki kudi ne?” “A a, eh yace amman an dade” “Rokonsa kikai?” “Eh” “Miyasa baki tambaye ni ba? Ba na fada miki ki rika fada min idan kina bukatar wani abun ba?” Na yi shiru ban ce komai ba. “Ki turo min account number dinki yanzu” “To na gode” Na sauke wayar daga kunnena ina tunanin dayan

Chapter 3 of 55