yai min fyade be rage komai a zoben hannunka ba, na danna na cige ina ta boye abu saboda na samu natsuwa a zaman aurena, amman Abdulhamid ya masa yarda da ni, ba zubar da cikin nai ba zubewa yai saboda tashin hankalin batan Namra, amman yana ganin kamar na aikata alfasha da wani ne na zubar da cikin, shin idan na fada masa dan'uwansa ne ya aikata ya kake tunanin zai ji?”
Rumtse idonsa yai da mugun karfi ya fisgi kansa kamar ba shi ba. Be taba jin magana daci ba irin wannan, ba a taba munana masa zato ba irin wannan, amman a maimakon ya ga laifinta sai tausayinta ya kara rufe shi, tausayin da be san daga ina yake ba, gani yake yanzu kanta a chushe yake, bata fahimtar komai da kyau kuma tana da raunin tunani.
A lokacin da ya bude ido sai ya ji kamar ba a duniyar nan yake ba, maganganunta na ta maimaita kansu a cikin kunnuwansa. Zoben hannunsa ya kurawa ido, kokarin tuna inda ya tsiya zoben yake a office right! Wani mai kawo musu kaya ya kawo rings even though shi ba masoyin zobe ba ne ya tsiya daya ya saka saboda zoben ya masa kyau. Yes he remembers at first ma mai alphabet H ya dauka sai kuma ya ga rashin dacewar hakan then ya canja to A mai sunansa. Magana ya fara yi tana rabe masa hawaye na sauko masa.
“Na san kin san ina son ki... Na fada miki... Kuma... Kin san haka.... Amman soyayyarki.... Bata taba saka min sha'awarki ba.... Ban tana jin sha'awar na rika hannunki ba daidai da minti daya Halimatu..... Indai har dan jikinki ne.... Zan bukace ko a lokacin da kike gidan.... Aminu.... Ko a lokacin da kike zawarci.... Ba yanzu da kika auren dan'uwana ba.... Wallahi ban tana aikata zina ba.... Zuciyata bata taba raya min akanki ba..... Kullum burina da fata na aurenki ne.... Saboda ki huta ki samu kwanciyar hankali.... Tausayi kike ba ni Halimatu... Yana daya daga cikin dalilin da ya saka nake daukar dawainiyar yaranki..... Da ke kanki... Na ke damuwa da damuwarki..... Yes i love you.... I do love you..... I love more i did before... Amman yanzu duk wannan ya wuce saboda kin riga kin auri dan'uwana twins brother na..... And yes na so na aure ki saboda na samu da namiji ko ba komai hakan zai kara min kaunarki.... Amman yanzu duk wannan ya wuce.... ”
Lumshe ido yai ya bude har lokacin yana hawaye.
“Idan har zan miki fyade, ba zan bar wata alama da za a gane ni ba, bazan shigavgidan makotanku har a kashe wani da ni ba saboda kawai na biya bukatar da zan tashi a gaban Allah ina tsoron amsata ba, a lokacin da akai wa Namra fyade ji nai kamar yar cikina aka taba, da acce Mama bata saka baki ta hana abun ba, da sai inda karfin ya kare, then mi zai saka ke nai miki? Robe kadai ya isa ya bada hujja Halimatu? Ni kadai ne sunana yake tashi da A ko kuwa ni na fi kowa arzikin da za a kero min irin wannan zoben? Ni da na ke fargabar ki shiga tashin hankali kuma ni zan saka ki ciki? Siffar mutumen da muryarsa irin tawa ce? Komai na sa irin nawa ne? Miyasa za ki nunana min zato? Saboda na ce ina son ki....! Wallahi ko ke kadai kika rage a cikin mata Halimatu na zan bi dare nai ma matar dan'uwana fyade ba.... ”
Mikewa yai tsaye ya cire zoben hannunsa ya nufi center table din da ke tsakiyar falon ya dora zoben sannan ya tada kai ya kalli Halimatu.
“Karki kashe aurenki saboda ni, karki fadawa Abdulhamid wannan maganar, domin na san dan'uwana ya fi so na akanki, kuma karki fadawa Hajiya wannan maganar, itama na san ta fi so na akanki, ki yi tunani Halimatu karki jefa kanki cikin matsala lastly ki daina shaye-shayen da kike for the sake of your children...”
Yana kaiwa nan ya juya ya fice yana share hawayensa da handkerchief. Amman hawaye suka ki tsaya masa har ya shiga motarsa, key yai mata sai da yai nisa da unguwar sannan ya faka motarsa gefe ya jingina kansa jikin kujerar motar ya Lumashe ido.
“Allah kai kadai kasan dalilin da ya sa saka min kaunar Halimatu, Wallahi na kasa ganin laifinta.....”
A fili ya furta zuciyarsa cike da tausayinsa, gani yake kanta ba daidai yake ba damuwar da take ciki bata iya barinta tai tunani da kyau, tabbas ta jefeshi da mummunan zato kuma ya ji zafin hakan yai bakinciki sai dai ya kasa ganin laifinta uzuri yake ta mata!
*5K WORDS 😲*
7/21/21, 10:44 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
2️⃣8️⃣
ABDALLAH POV.
Be iya zuwa gurin aikin ba kamar yadda ya tsara zuwa tun farko, gaba daya ji yake kamar ba shi da lafiya, ji yai baya bukatar ko'ina sai gidansa. A take ya dauki hanyar gidan, a ka'idan zai shiga gidansa yana shiga da sallama kuma fuska a sake ko da kau yana cikin damuwa yana kokarin yin hakan saboda yaransa, duk damuwarsa ko wata matsala nasa baya son tana shafar iyalinsa musamman yaransa Abdallah mutum ne mai tsananin son yara ko da ba na shi ba balle kuma na shi, wannan yasa duk irin matsalar da suka samu da Suwaiba matarsa baya taba bari yaransa su gane.
Babu kowa falon at that time, daman yara suna scul Suwaiba kuma tana dakinta, kai tsaye dakinsa ya wuce yana jin wani irin zazzabi na rufe shi, kwantawa yai saman gadonsa yai ruf da ciki ya rumtse idonsa sosai. Yana jin wayarsa na ringing ya ki ya duba mai kira ma balle yai deciding zai dauko ko a'a, ya kusan awa daya a haka sannan ya bude idonsa ya tashi zaune yana duba wayar, Abdulhamid ne ke kiransa. Sai da ya busar da iskar bakinsa sannan ya danna picking.
“Abdallah”
“Na'am”
Ya amsa yana gyaran muryar.
“Ya kuka yi da ita?”
Shiru yai for few seconds sannan ya ce.
“Tace ta fi bukatar sakin ko dan cutar da take dauke da ita”
Daga dayan bangaren Abdulhamid yai shiru kamar mai nazari har Abdallah ya dauka ko ya kashe wayar sannan yai magana.
“Idan kuma na ce bata dauke da cutar fa? Zata zauna?”
“Amman miye gaskiyar lamarin ne?”
“Maganar gaskiya bata dauke da cutar”
“Then miyasa ka ce tana dauke da ita?”
“Ina son na gane wani abu ne, kuma ina tunanin idan na ce mata haka zan ji wani abu daga gareta, amman na ga hankalinta sam be tashi ba, even i thought zata yarda ta zauna saboda tunanin idan ta fita za a kyamace ta, but then i realized idan har na cigaba da zama da ita, zan iya cutar da ita kuma ni ma zan cutu, domin har ga Allah zuciyata ta kasa natsuwa da ita, ta wani bangaren ina ganin kamar rabuwar shi ya fi alheri”
“Amman Abdulhamid miyasa za ka ce tana dauke da cutar, na kasa yarda da kai, wani lokacin sai kai ta abu kamar marar tunani”
“Idan taje wani gurin ta yi gwajin ai za a tabbatar mata idan tana dauke da cutar ko akasin haka”
“Ina fatar rabuwar ta zame muku alheri kai da ita”
Shine kawai abunda Abdallah ya fada ya kashe wayar ya kaita a goshinsa, babu abunda ke ransa sai irin halin da Halimatu zata shiga.
“What if Abdulhamid yana da lafiya? Da duk wannan zai faru? Da ko kin yi cikin ba zai gane cewar ba na shi ba ne, ni na jefaki a wannan matsalar, saboda ni ne silar wannan matsalar....”
Ya furta yana kara rumtse idonsa, kokarin da yake na kawarda damuwar abunda Halimatu ta fada masa ne, gudun kar wani abun ya same ta, and the most of all zai wanke Abdulhamid daga rikon da yai masa a zuciyarsa. Bude idonsa ya sake yi ya lalubo number Halimatu ya aika mata sako.
“Na zurfafa a son ki na sani, na nuna miki son kaina na sani, na kaurara da yawa na sani, kina da gaskiyar ki yi yarda da duk wani abu da zuciyarki ta fada miki, amman ina dada jadadda miki karki kuskura fadawa Abdulhamid wannan maganar”
After the sms ya kwanta saman gadon yana jin kamar ba shi da wani kuzari. Abubuwan da ta fada masa is painful suna ta kona masa zuciya, after like two hours ya kira wani a asibitin ya fada masa cewar ba zai sami damar zuwa ba a yau. Tun da ya kwanta babu fuskar da yake ganin sai ta Halimatu old memories yake tunawa daga lokacin da take yan mata ba tai aure ba, a lokacin duk be fara son ta ba har tai aure shi kuma ya bar kasar duk be fara son ta har ya dawo yai aure ya haifi yarsa ta fari be fara sonta ba, sai da suka hadu a family meeting a lokacin tana da aurenta har ta haifi yara uku, tun daga ranar Allah ya dora masa sonta, yanayin jikinta mu'amalarta kyauta da komai nata sai ya rike burge shi, musamman da ya samu labarin waye mijinta da irin kalubalen da take fuskanta a gidan aure sai ya fara tausayinta yana ganin kamar shi ya dace ta aura ta samu jindadi, kamar yadda yake jin cewar idan ya aureta zai iya haifar ɗa namiji tunda ita duk tana haihuwar maza da mata, and bugu da gari ga sonta da yake.
But why he fell in love with her? Sai yanzu yake ta ganin laifin kansa, he know maybe da be so duniyarta da tunaninta be bata haka ba ta bata munana masa zato ba. Har scul bus ta kawo yaransa daga makaranta yana a dakinsa kwance, yana jin hayaniyarsu amman damuwar da ke ransa ta hana shi tashi ko da zaune balle har ya fito falo.
After yayi sallah azahar a cikin dakin Suwaiba ta shigo ta zauna kusa da sallayar tana karantar damuwar mijinta.
“Lafiya dai? Na ji ka dawo tun dazun kuma baka fito ba”
Kallonta yai yana kirkirar murmushin da yaki ya fito a kumatunsa balle har ya tsaga bakinsa, a kokarinsa na boye mata damuwarsa ya kirkiro mata wasa.
“Ba fushi kike da ni ba”
“Wannan dabam, kana cikin damuwa ga idonka nan ya nuna”
“Bana jindadi ne, dazun da na fita sai da nai amai shiyasa na dawo”
“Ka sha magani?”
Hannunta ya kama.
“Ina likita har ake tambayar na sha magani?”
“Na kawo maka abinci?”
“No ba yanzu ba”
Kamin ta sake cewa wani abun su Inteesar suka shigo dakin ita da kanwat suka fado jikinsa. Sai Suwaiba ta rika kokarin daga su.
“Kyale su tafiyarki”
Ya fada yana shafa kansu, tashi tai ta fice tana musu fada wai kar su dami Daddynsu ba shi da lafiya duk kuwa rashin gamsuwar da tai na cewa ba shi da lafiya din da gaske.
Sama sama ya tambaye scul sannan ya ciro wayarsa ya cire mata key ya mika musu su game so that su kyale shi ya samu natsuwa, a gurin ya kwanta su kuma suka tashi suka bar dakin suna murya Daddy ya ba su iPhone dinsa su yi game.
Har yanzu jikinsa ya kasa sakewa yana ta jin kansa kamar marar lafiya irin wanda ya dade kwance yana jinya, tsakanin fitar su Inteesar da kwantarwarsa be wuce 40 minutes ba Suwaiba shigo dakin rike da wayarsa fuskarta a jagule.
“Abdallah miye haka?”
Saurin bude ido yai jin muryarta kamar mai shirin yin kuka, sakon da ya aikawa Halimatu ne dazun take nuna masa, tuni kwalla sun cika idonta. Tashi yai zaune yana kallon fuskarta, gaba daya sai abun ya kara jagule masa shi ya manta ba be goge ba, and ko da ma be goge ba why zata karbi wayarsa a hannun yara ta masa bincike?
“A lokacin da nai zargi cewa kai ban yi daidai ba, yanzu miye haka? Yar'uwarka kuma matar dan'uwanka Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un....”
Hannu ya kai ya rikota ya zaunar da ita bakin gadon sannan shi ma ya tashi daga kan tile din da yake ya zauna bakin gado ya rike hannayenta.
“Babu alakar komai a tsakaninmu”
“To wannan wane irin sako ne? Miye ma'anarsa? Na kasa gane wace irin alaka ce a tsakaninku? Idan nai zargi ka ce min ba haka ba, Abdallah da me na rage ka?”
“Ba ki rage ni da komai ba, idan ina wani abun da be kamata ba zaki fi kowa sani”
Fashewa tai da kuka ta runtse ido, kamar yadda shi ma ya rufe idon ya hada kansa da nata yana hawayen da be yi zaton za su sake zubo masa ba.
“Ashe ba za ki iya shaidun mijinki ba? Ba kisan abunda mijinki zai iya yi da wanda ba zai iya ba? Wani ba zai zo yace miki ga mijinki can a dakin wata karuwa ba ki karyata shi? Har yanzu ba ki san waye Abdallah ba Suwaiba?”
Bude idonsa yai yana kallon idanuwanta da ke rufe suna zubar da hawaye still goshinsa da nata suna hade guri daya.
“Me kika son nai miki ki yarda da ni? Rantsuwa kike son nai miki? Ko qur'ane kike son na dafa miki? Ko kuma Halimatun kike son na dauko miki da kanta ta fada miki?”
Kai ta girgiza ta jimke hannunsa sosai a cikin nata alamar ta yarda da shi, sai dai har yanzu kukan take mai sauti. Kansa ya daga ya janta jikinsa ya rumgume yana hade yawun bakinsa tare da saka dayan hannunsa ya share hawayensa.
“Wani lokacin wani abun yana faruwa da mu saboda yana daga cikin kaddararmu, wani na dan lokaci ne kawai na jarabawa, wani kuma har a abada zai zauna da kai”
A fili yai furucin yana sauke ajiyar zuciya, kamin ya koma zancen zuci.
‘Da ace na san zan hadu da ke Halima da ban dawo kasar nan ba, ko da na dawo da ban zauna garin nan, hakika duk wanda aka jarrabe shi da son wani an fi kowa yi masa babbar jarabawa, Allah kadai yasan abunda yake nufi da ni’
Ya kara rumgume matarsa yai ya kai bakinsa saitin kunnenta.
“Babu komai a zuciyata yanzu sai tausayin Halimatu, ki kwantar da hankalinki ki daina damuwar kanki da matsalar nan dan Allah”
“Dama kaunarta kake yi Abdallah wata kila da zan fi samu natsuwa fiye da ka fada min cewar tausayinta kake, tausayi ya fi so tsatsa a zuciya Abdallah”
“Ki daina saka kanki a cikin damuwa, Halimatu ta riga ta auri dan'uwana, ba zan taba iya aurenta ba a yanzu ko da ko Abdulhamid ya rabu da ita, duk wani abun da zan mata ko nai ma yayanta zan yi mata ne kawai dan kyautata da kuma tausayinta da na ke, Halimatu yar'uwata ce ko ba komai dole na taimaka mata ballantana akwai yan'uwanta, kuma duka familynsu babu wani mai karfi da Halimatu zata iya jingina da shi yai mata irin abunda na ke mata”
Ta gamsu da bayanansa abunda bata gamsu da shi ba, shine zancen cewa ba zai auri Halimatu ba ko da Abdulhamid ya sake ta, ko da dai hausawa suna cewa ana barin halak dan kunya, amman a yadda Abdallah yake damuwa da lamarin Halimatu abu yana daure mata kai, ta sani abun kunya a gurinsa ace dan'uwansa ya saki mata shi ya aura, dan uwan ma twins brother dinsa, amman ta kasa yarda tausayin Halimatu kawai yake ta san ba tausayi ne kawa ba har da so, wannan abun ya tsaya mata a zuciya, abun da ciwo ace kana tare da mijinka zuciyarsa tana begen wata.
HALIMATU POV.
I thought ba zan sake zubar da kwalla ba, i promise my own self ba zan sake shiga damuwar wani namiji ba, but i feel like ban kyautawa Abdallah ba, i feel like na yi kuskure na fada masa haka, miyasa ba zan bari har sai asiri ya tonu ba? Amman da na bar maganar a cikina da har yanzu zargin Abdallah yana a cikinta. And now da ba Abdallah ba ne wanene? Babu wanda zan iya zargi a iya hangena da tunanina, wata kila yan fashin ne da gaske! Amman miyasa ya shafa cikina har ya tambaya da gaske ina dauke da ciki, miyasa yace wannan karon ba gurin mijina suka zo ba? A gaban madubi nake zaune ina kallon kaina hawaye na sauko min, nazarina ya ki ya kare, tunanina ya ki ya gano komai. Ban matsa daga inda na ke ba har sai da na ji motsin motar Abdulhamid.
Bandaki na shiga na wanke fuskata na fito bakin gado na zauna.
Sai ga shi ya shigo ya zauna kusa da ni, ban kalleshi ba amman jikina ya ba ni cewar kallona yake.
“Abdallah ya fada min kin ce kin fi son sakin, ni kuma ba zan ki yi miki abunda kike so....”
Yana fadar hakan ya saka hannunsa aljihu ya dauko takardu guda biyu ya miko min.
“Ina miki albishir din cewar ba ki dauke da cutar hiv na fada miki haka ne kawai saboda na ga reaction dinki”
Hannu na saka na karba at first na yi zaton ko takardar gwajince sai nai arba da abunda ya kusan raba zuciyata gida biyu.
_Ni Abdulhamid na saki matata Halimatu saki daya a yau_
Bayan rubutun saki sai kuma na kwanan wata a kasa, Wallahi na yi zaton kukan a lokacin amman sai na nemi shi na rasa babu ko alamunsa a tare da ni, a dayar takadar kuma cheque din kudi ne dubu dari biyar.
“Wannan na minene?”
“In case of....”
Ya amsa min muryarsa na rawa. Sai na girgiza masa kai ya dora cheque din a saman gadon.
“Bana da bukata”
Ina furta hakan na nufi wardrobe dina na bude na dauko akwaiti na fara zuba kayana, abubuwan da ya kamata ace na zuba a ciki ba su na zuba sai tarkace jikina na ta rawa kamar wata marar gaskiya. Ina kokarin rufe akwatin ya zo ya rike akwatin sai na daga kai na kalleshi, hawaye fal a fuskarsa a maimakon ni da aka saka na yi kuka ban yi ba, sai shi da yai sakin yake kuka.
“Zan kula da komai, idan kina bukata za ki iya yin iddarki a nan”
“Bana da bukata”
Sai ya kada min kai kamar wani yaro da mai bashi umarni, mikewa nai tsaye na dauko hijbina sai ya rike.
“Ba za ki bari sai da dare ba?”
“Gida na ke son zuwa”
Nan ma kan ya gyada min.
“Bari na kai ki, zan saka a kwashe komai na ki a kai miki”
Ya fada yana ficewa daga dakin, ni kuma na bi bayansa rike da jakar hannuna, da kuma takardar sakin, har lokacin ban ji kuka ko wani abu makamancin kukan a tare da ni ba, sai dai zuciyata ta yi wani irin nauyi kamar dutse. Ko da na fito har ya tashi motar ya bude min front seat, ni kuma na bude back seat of a shiga na zauna, sai ya fito ya rufe front seat din ya bude gate ya fita da motar sannan ya koma ya rufe ya dawo cikin motar. Sai da yai nisa da tukun ya faka motarsa gefen titi ya jinginar da kansa jikin sitiriyarin motar ya fashe da kuka kamar karamin yaro. Kamar hadin baki sai nawa idanuwan suka cika da kwalla.
“Why? Why all this?”
Ya furta cikin sautin kuka, sai ya dago kansa ya jingina da kujerar motar, ina iya jiyo lokacin da ya sauke ajiyar zuciya ya kai hannu ya share hawayensa ya cigaba da tukin, sai da muka iso kofar gidan mu sannan ya juyo ya kalleni.
“Zan iya maida auren idan kina so”
Kai kawai na iya girgiza masa alamar a'a ma bude motar na fita, sai da na taka har bakin kofar gidan na saka kafata, sai na ji babu abunda na ke bukata sai kallon Abdulhamid. Juyowa nai na kalleshi, lokacin da ya turo da motoci aka dauke ni aka kai gidansa nake tunawa yau kuma gashi ya dawo da ni da kansa, zancen mahaifiyata na bata son a fara kirga min aure ya fado min a rai, da na san zan haka GOBENA zata kasance a gidan Abdulhamid da ban aureshi ba, ban ji ina tsanarsa ba, sai dai na nemi soyayyarsa da ke zuciya na rasa, hawaye yake kamar yadda ni ma nake yi. Hannu na saka na share hawayena duk kuwa da na san fuskata ba zata iya boye kukana ba, sannan na shiga ciki gidan, iyakar kokari na yi dan na tsayar da hawayena amman abun ya faskara haka na shiga gida ina hawaye.
Inna da Mama da Baba da Hafiza duka suna tsakar gidan zaune ko wane fuskarsa dauke da far'a da alama nishadi suke. Baba na kishingide saman tabarma Inna na tsaye jikin kofar kitchen din dake tsakar gidan, Mama kuma na zauna a saman kujerar mata kusa da Baba Hafiza ce zaune a kofar dakin Mama tana shan rake, suna ganina da yanayi sai duk jikinsu yai sanyi.
Gaban Baba naje na gurfana rike da takardar a hannuna ina hawaye na kasa daga kai na kalleshi.
“Shi aure yana da rayuwa da mutuwa kamar mutum da rayuwa, idan lokacin mutuwarsa yai babu mahani, kuma abu kalilin kan iya sakawa ya afku ko ya mutu, ko da dalili ko babu, dan haka ki sawa rayuwarki sallama ki dauka cewar ajalin aurenki a gidan Abdulhamid ne yai”
Da sauri na dago na kalleshi, jin magana mai dadi da kwantar da zuciya da samar da natsuwa daga bakinsa, tun kan na furta ya fahimci cewar aurena ya mutu. A take na share hawayena ina gyada masa kai alamar na gamsu.
“Saki nawa yai miki?”
“Daya ne Baba daya yai min”
Na furta muryata na rawa, sai Mama tai karaf ta ce.
“Amman me kika masa mi ya hada ku?”
Kamin na ce komai ba Baba ya daga mata hannu.
“Ba yanzu ba, tashi ki je ciki ki huta, Allah yai miki albarka”
Ban san lokacin da murmushi ya kubuce min ba, kaunar mahaifina ta kara cika min zuciya, ya famshe ni daga tambayar da ban san mi zan fada a matsayin amsa ba.
“Madallah da kai Baba, ina ma ko wane uba kamar kai yake? Madallah da uba irinka, madalla daka zama jigo ga Halimatu....”
Na fada ina hawaye cike da shaukin sonsa, Hafiza ce ta taso daga bakin kofar da take zaune ta zo da gudu ta rumgume Baba tana kuka tana fadin.
“Ina kaunarka Baba Allah kara maka lafiya”
Dariya yai ya tashi tureta daga jikinsa ya tashi zaune. Ni kuma na dago na shiga dakin Mama. A dare Mama bata iya hakura ba har sai da ta ji dalilin mutuwar auren, ni kuma ban boye mata komai ba cikin har da fyade da kai min da abubuwan da suka faru, sai dai ban yarda na fada mata cewar Abdallah na ke zargi ba.
Na ga rashin jindadin mutuwar auren a fuskarta, daman wace uwa ce zata zo auren yarta ya mutu? Balle Mama da take daukar abu ta saka a rai, su Salma da Hafiza ma da suke yan mata ba su yi aure ba abun ya dame ta balle kuma ji ace aure na biyu ya mutu. Sai dai duk da hakan ta nuna min zama da Abdulhamid din ba mafita ba ne sakin ya fi tunda har yana zargina. Da yamma Su Adnan suka dawo daga islamiya, ganina suka hau murna kamar wacce suka shekara ba su gani ba, ganin na kai har bayan i'shai yasa Namra ta fara tambaya wai nan zan kwana.
“ A nan zan kwana, yanzu na dawo kenan sai illla ma shaa Allahu”
Wani irin tsalle ta daka ta dire tana murna ta kama hannuna ta rike.
“Momy da gaske?”
Na gyada mata sai ta kara rumgume ni tana ta murna.
“Yeee mun huta Momy ta dawo”
Iya murnar da yata take na ganina a kusa da ita ya isa da tabbatar da cewar yarana sun yi marmarina duk kuwa da suna zuwa su ganni ko na gansu idan bukatar hakan ta kama, sai dai ko wane d'a yana bukatar mahaifiyarsa a kusa da shi, amman ni na bar su na auri Abdulhamid, a yau ya saka min da haka! Da tunanin abun na kwana a zuciyata har safe.
Washe gari Baba ya kira ni a dakinsa ya tambaye ni abunda ya faru, a nan na tsige masa tun
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 22 Chapter of 55