Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ni kuma nake ganin ba zan dauki hakan a yanzu ba, na gama indai kuka ne akan wani namiji ko shiga damuwa akan wani namijin ba zan sake bari wani ya saka ni damuwa ba. I can live without aure indai har zan iya tsare kaina da mutumcin na tarbiyantar da yayana, zan iya shiga aljanna, haka zuciyata ke raya min i feel like idan har Abdulhamid ya sake ni ba zan sake wani auren ba, zan cigaba da aikina ina kula da yayana, zan nemi ya sake ni bana bukatar sake zama da shi ji nai na tsani duk wani namiji a duniyar har na rika jin na matsu ya dawo gidan, kamar ance min da ya dawo zai rubuta takardarta ya ba ni.   Maganin da na siyo dan na sha na samu bachi ne ammn sai bachin rai ya hana ni sha. Wani irin kuzari da karfin hali nake jin yana ratsa ni, i feel like ko da duniyar nan za su taru su tsane ni i can live, even for the sake of my children right? Yes this is right time da zan nunawa duniya wacece ni, wannan lokacin ne ya kamata na amsa suna, i don't know what the future bring ban ce ba zan sake facing wani challenge ba, but zan iya jurewa zan iya daurewa daga lokacin na fara rayawa kaina cewar gobena mai kyau ce. Na yi kuka a lokacin da na ke fuskantar wulakanci a gidan Aminu, na yi kuka a lokacin da akai ma Namra fyade, na yi kuka a lokacin da Aminu ya sake ni, na yi kuka a lokacin da akai min fyade, amman hakan yana nufi sai na zauna nai ta kuka akan komai akai min na bar damuwa a raina? No be kamata na karaya ba, be kamata na lauyewa kaina hakkina dan ina mace ba! I have to say it out loud, i have to fight for my right. Kamin dare yai Abdulhamid ya shigo duk na matsu sosai, saboda irin abunda na kudirewa zuciyata, ban girka komai ba har dare, can bayan sallah isha'i sai gashi ya shigo gida kamar yadda ya saba, da ada ne ko be yi sallama ba ya shigo zan masa sannu da zuwa amman a yau sai na ji ba zan iya yi masa hakan ba. Ga duka alamu yau da yunwa ya dawo, domin yana dawowa ko dankinsa be shiga ba ya nufi dinning rike da wasu takardu a hannunsa. Ganin babu abincin a dinning din yasa ya juyo ya kalleni. “Ina abinci?” “Ban girka ba” Daga inda nake zaune saman kujerana bashi amsa kai tsaye. Be sake cewa komai ba ya tashi ya nufi hanyar dakinsa yana shiga na rufe masa baya, sai na same shi yana kokarin cire rigar shaddar da ke jikinsa, hango shigowata ta madubi da yai ne yasa ya tsayar da cire rigar ya juyo ya kalleni “Kina son wani abu ne?” “Ina son sanin result din gwajin da nai nake son sani” Juyowa yai da kyau yana kallona for like ten seconds sai kuma ha dauke idonsa daga kallon da yake min ya kalli wani gurin dabam. “Positive....” “Al-hamdulillah.... Abu na biyu kuma ina son ka san cewar komai yana da lokaci kuma yana da iyaka, a lokacin da na aureka babu wanda ya cilasta ni ra'ayin kaina ne, and now mun gaji we need some space” Sake kallona yai a karo na biyu kamar wanda be fahimci yarena ba, wata kila kuma yana mamakin furucina ne. “Saki na ke bukata...!” I say it.. “Are you sure? Ba ki bukatar sake shawara ko tunani” Shine abunda ya fito daga bakinsa, sai kuma ya matsa kusa da ni ya kai hannunsa biyu zai dafa kafadata, ni kuma nai saurin matsawa. “Bana bukatar ko daya” Sai da ya hade yawun bakinsa sannan ya furta. “Shikenan zan ga abunda zan iya yi akai” Yana fadar hakan ya juya ya cigaba da cire rigarsa ni kuma na fice na bar masa dakin. Ko kadan ban ji kuka a tare da ni ba kamar yadda na saba yin kukan a duk lokacin da wani abun bacin rai ya same ni, but i feel bad ina jin na yi abunda be dace ba, miyasa ba zan jira har zuwa lokacin da shi din zai bukaci sakina ba? Why? Bana da wata hanyar ne sai wannan idan har zan jira to zan cigaba da kashe kaina ne da rai na. Can bayan na yi sallah isha'i ina kokarin kwanciya ya shigo dakina ya aje min takeway ya fice. AHMAD POV. Hajiya na kallonsa ta san danta yana cikin bacin rai, sai dai ta yi shiru ne saboda ta saba masa haka a duk lokacin da yake cikin damuwa idan har taji bata ji yace mata komai ba sai ta tambaya. “Hajiya yau ko?... No first of all ita wannan yarinyar da kika saka na kai gida wacece ita?” “Sai ka fara fada min damuwar” “Wallahi wata bad luck na hadu da ita yau, ban taba jin na tsani mace kamar yadda na tsani matar nan ba, i hate her... ” “Me tai?” Kadan ya gutsurawa Hajiya labarinta yana ta tsaki. “Kai ma ai be kamata kai haka ba, ko dan yarta na abota da yarka, sannan matar aure ce akan me zaka tare ta a hanya da sunan ba ta hakuri? Kai yanzu yadda kake da kishin tsiyar nan wani ya isa ko kallon matar ka yai?” Kallon Hajiya yake da mamaki he thought zata bashi gaskiya ta bawa wacan rashin gaskiya ne. “Okay....” Sai yai shiru, kamin ya sake tambayarta. “Ita wannan yarinyar fa?” “Yarinyar nan da ka gani bazawara ce” “What....?” Ya tambaya da mugun mamaki domin a tunaninsa budurwa ce, a yadda ya ganta yarinya karama. “Yes ta yi aure bata dace ba mijinta har dukanta yake kuma ta hakura ta zauna har sai da yan uwanta suka kashe aure, sannan gidansu mahaifiyarta ita ce ta hudu, so ta san  halin rayuwa tun da ta taso a gidan yawa kuma duk mace da zata yi hakurin zama da miji mai duka zata iya hakurin zaman aure a ko'ina, shiyasa na ke son idan ta maka ka aureta” “Aure yanzu Hajiya? Hajiya ba tai min ba, abu kamar ta tsinke ni bana son mace ramanmiya irin wannan, and kin san abunda ba zai taba yiyuwa ba ne na auri matar wani Allah ya sauwake, ba zan taba auren bazawara ba, ba zan iya auren matar da wani namijin ya aureta ya sake ta ba, ko kuma mijinta ya mutu har a bada, Hajiya ke ma kin san wannan” “To wai miye a zaurawan nan ne? Haba Gwarzo, na aje wannan akidar dan Allah ni fa yan matan nan na yanzu ba yarda zan yi da su ba, kara wacce tai aure ta dandana dacin auren zata fi iya zaman aure a gidan nan” “Ba dai bazawara ba Hajiya” Ya sake nanatawa sannan ya tashi ya fice daga falon, part dinsa ya nufo har yanzu zuciyarsa cike da take da bacin rai abunda ya faru. “Imagine wai ni matar nan ta tsaya ta fada wa maganar banza wai... Wani ni Ahmad hmmm” Yayi kwafa sannan ya tura kofar falonsa ya shiga gumi na karyo masa, daman can haka yake da ransa ya bace sai ya fara gumi jikinsa yai zafi sosai kamar marar lafiya, idonsa ma a take suke canja, zuciyarsa kuma tai ta wani zillo kamar ta fito, shi kansa idan ransa ya bace baya iya controlling kansa, that's why yake taka tsantsan yana gujewa duk wani abu da zai kawo masa bacin rai. AMINU POV. Hajiya ba ta yarda ba har sai da ta saka aka yi mata na ta bincike, a gurin malamanta da kuma malaman kawayenta, sai dai duk inda take abu daya ake fada mata cewar arzikin danta hana tare da matar da ya rabu da ita, wasu ma har kara rura wutar abun suke ana fada mata cewar da ace be sake ta ba da yana daf da samun wani abun. Sai dai hakan be gamsar da ita ba har sai da ta sake saka kawarta Hajiya Mairo a gaba suka tafi gurin wani malamin. Ba su tsaya bin layi ba abun ka da masu kudi, sai aka bi da su ta wata hanyar suka shiga cikin dakin malamin. After sun gaisa ya dauko kasa ya fara bincike domin shi haka yake ba ya bari mutum ya fada masa dalilin zuwansa, sai dai shi ya fada maka abunda ya kawo ka. Yayi kusan minti ashirin yana duba kasar sannan ya dago ya kalli Hajiya Mairo. “Waye Aminu? Gashi nan yau sun nuna min da Maganarsa kuka zo” “Tabbas hakika maganar Aminu ta kawo mu, yaron abokiyata ne kuma aminiyata” Ya gyada kai sannan ya kalli Hajiyar Zuwaira wato mahaifiyar Aminu ya ce. “Sun fada min komai, dan ki na fama da gurguncewar cigaban rayuwa haka ne?” Tai saurin gyada kai. “Haka ne” “To ai danki ya baro kyau tun ranar haihuwa, ga shi dauke da kwaryar alheri sai kuma ya bari ta fadi ta fashe” Hajiya Zuwaira ta yi masa kallon rashin fahimta. Sai yai yar dariya ya gyara zamansa. “Na san baki fahimta ba, wato tauraruwar danki sakaina'u ce, irin wannan tauraruwar bata iya haske har sai ta hadu da yar'uwarta mai iya daukar nauyinta, ma'ana mai taimaka mata ta haskaka, da danki zai hadu da taurari dubu idan be hadu da wannan tauraruwar ba gasri to abu ne mai wahala ya iya haskaka ya daukaka yadda yake so, daman ko wane dan'adam yana da tauraruwarsa to ita ta danki haka take” “To amman Malam.... ” Sai ya daga mata hannu. “Wacece Halima?” “Matar da ya saki ce ita ce uwargidansa” “To ita ce mai wannan tauraruwar gasri, tauraruwa ce mai tsananin haske da kaifi gaske, tana haska ko wane irin tauraruwa, ban ce dan ki ba zai arziki ba, amman da ace yana tare da ita ina mai tabbatar miki ko matar gobna bata ita ta nuna miki yatsa ba” “Amman Malam ai can baya tare da ita kuma yana al'amuranshi” “Amman ya kai kamar haka?” Ta girgiza kai alamar a'a. “To kin gani, zai iya samun mai irin tauraruwar amman abun ne mai wahalar gaske” Hajiya Mairo ta ce. “To amman Malam dole sai Aminu ne kawai idan ya aureta zai yi arziki ko kuwa idan wani ya aureta shi ma zai iya yin arzikin?” “Sosai kuwa ai kowa ta raba zai yi arziki, ita daman haka tauraruwar take” Cikin damuwa Hajiya Zuwaira ta ce “Yanzu babu yadda za'ayi tauraruwar tasa tai haske? Kenan dole sai da ita?” “Akwai mana, amman aiki ne mai wahalar gaske kuma za a ci kudi” “Karka damu indai har za a samu biyan bukata ba matsala” “Za ki siye sa daya, da fararen balbelu uku sai fafaren kaji bakwai, sannan za a biya masu aiki 30k” Murmushi Hajiya tai. “Wannan ai ba wata matsala ba ce, sai dai ba zan iya siyowa ba zan dai bada kudin sai ka siyo komai da kanka, sai dai ba ka fada mana nawa za a biya ka” “Ni sai bukata ta biya sannan za a biyani” A take a gurin ya lissafa mata kusan dubu dari biyu da za a bada na kayan aiki, sai ta karbi account dinsa da zimmar idan ta koma gida zata turo masa, bata bar gurin ba sai da ta aje masa 10k na shan ruwa. Har suka dawo ita da Hajiya Mairo ba su daina mamaki da jinjina lamarin ba. Ba ma kamar Hajiya Mairo domin ita nata tunanin dabam. ABDALLAH POV. Tun daga lokacin da suka samu matsala da Suwaiba ta canja masa, ya lura da hakan a dabi'unta da halayyarta da kuma yadda take mu'amalantarsa a yanzu.   Shi kau iya kokarin da yake na ya fahimtar da ita ne ta daina ganin laifinsa ko kishin Halimatu, a iya ganinsa shi be ga dalilin wannan kishin da take ba, be san abunda zai saka ta ji haushi dan yayi ma yar'uwarsa alheri ba, tun da ita ma babu abunda ya rageta duk wani abu da take bukata yana yi ma kuma yai ma yan'uwanta, sai dai duk bata ga na kowa ba sai na Halimatu. Duk yadda take kokarin avoiding dinsa shi kuma kara shige mata yake yana nuna kamar wani abu na bacin rai be taba shiga tsakaninsu, daman can haka yake idan yai fada da ita kokarin mantawa yake saboda kullum auna tunaninta yake yana ganin be kai na shi ba, a ganinsa mace mai rauni ce kuma ba komai suke iya tsayawa su yi tunani ba, duk yadda abu ya zo musu haka suke karbarsa shiyasa shaidan yake yin galaba akansu. Idan har ya ce zai rike ta a ransa zata iya shiga matsala, matukar ya rike bacin ran mutun a zuciyarsa sai wani abun ya faru da mutun domin yana da kofi, idan har ka bata masa rai za ka ga daidai ba, shi kansa har mamakin kansa yake wani lokacin abu yake kamar wani maye. sai da yai shirin office saf sannan ya nufi dakin matarsa yana kamshi turare mai dadi. Yana shigowa ta wani dauke kai be damu ba ya karasa kusa da ita ya kama hannunta ya sumbata. “Zan tafi office sai na dawo” Bata ce masa koma ba, shi ma kuma be jira ya ji wani abu daga gurinta ba, daman be yi tsammanin ta fada masa wani abun ba ko da Allah ya tsare ne ba tun da fushi take da shi, ba kamar da ba da har bakin mota take rakoshi. Daga gidanshi gidan Hajiya ya nufa as usual daman sai ya biya ya gaisheta yake wucewa office, ko a dawowa ma idam time be kure masa ba sai yayi mata sallama yake dawowa gida. Ya dauki Hajiya kamar wata abokiyasa yana jindadin fira da ita sosai duk wano sirri na shi ko shawara ita ce, kamar yadda ita ma ta fi shakuwa da shi fiye da Abdulhamid.   Ba kasafai Abdulhamid yake zuwa da safe gaishe da Hajiya ba, wani lokacin sai da rana ko dare, wani lokacin ma sai ya wuni be shigo ba sai dai yai mata waya. A kujerar da mahaifiyarsa take zaune ya zauna yana mika mata gaisuwa. “Lafiya Kalau ya aka tashi ya yaran” Ta amsa masa fuskarta da alamun magana. “Abdulhamid” Daman haka yake masa he can't say Abdulhamid ina kwana saboda yana jin age mate dinsa ne, tun da yake a rayuwarsa be taba bude baki yace wa Abdulhamid ina kwana ko ina wuni ba, sai dai ya kira sunansa. “Likita ykk” “Lafiya kalau” Ya amsa yana kallon yanayin Hajiya da kuma shi kansa Abdulhamid din. “Lafiya wai?” “Lafiya kalau wai Halimatu ce tace ta gaji da zama da shi saki take so.... ” Ji yai kamar an zuba masa ruwan sayi a kai a take tsigar jikinsa ta tashi. “Saki?” “Eh” Hajiya ta amsa masa. “Why?” Abdulhamid ya daga kafadunsa alamar be san dalili ba. “No dole akwai wani abu, akwa abunda kai wa yarinyar nan Abdulhamid haka nan kawai Halimatu ba zata ce ka sake ta ba, i know who's her” Hajiya ta tabe baki tana fadin. “Ni nace dai ko ta gaji da zama da kai haka nan ne ba” “No bana tunanin haka duk dai na san matsalar ce tai haifar da komai, amman wata kila tana jin kunyar kan ta ne akan abunda ya faru” Cewar Abdulhamid, a take Abdallah ya gyara zamansa yana girgiza masa kai. “idan har akan matsalar ne be kamata ta saka kanta cikin damuwa ba, matar da zata bar yayanta ta bar aikinta ta yarda ta aureka bayan kuma ta san irin lalurar da kake tare da ita, be kamata dan wani abun ya same ta ka barta ta shiga damuwa ba, and she told you ba su yi raped dinta ba, miyasa ba za ku yarda da ita ba?, Abdulhamid Halimatu kamar amanace a gurinka kuma matarka ce ka zaunar da ita ta nuna mata baka da matsala da hakan kuma ta kwantar da hankalinta, Abdulhamid yarinyar nan.... ” Be karasa ba Abdulhamid ya tari numfashinsa. “Halima ba yarinya ba ce, yaranta hudu ta san me take yi. She told me babu wanda yai forcing dinta ta aure ni and now she want divorce” “Ai sakin ma shi ya fi alheri” Abdallah ya juyo ya kalleta cike da damuwa. “No Hajiya ke kika haifar da wannan matsalar kika saka Abdulhamid ya rika ji a ransa kamar an yi raped matarsa, and now kina kokarin ki karfafa nasa guiwa ya sake ta haba Hajiya be.... ” “No tun kamin ayi wannan abun i suspect something, and yes na kai ta an mata hiv test and the result din positive, maybe dai tana jin kunyar kanta ne.... ” Da mugun mamaki Abdallah yake kallon dan'uwansa. “Don't tell me you don't trust your wife...? Why all the insult bro? Taya za kai ta ayi mata hiv test? Kasan halin da za ta shiga?” “Ba zaka fahimta ba ne Abdallah, ni na san abunda yake nan, and matar nan yanzu har shaye-shaye take fa, na ga kwalaben maye a dakinta, and wani lokacin zan tarar tana ta bachi kamar wacce ta mutu, idan ta farka idonta har canjawa yake” Kamar an saka scissors an yanke jiyojin jikinsa haka ya ji, be taba jin tausayinta irin yanzu ba, yana jin da ace shi ne Halimatu ta fada masa cewar ba'ayi mata fyade ba babu abunda zai hana shi yarda da ita, even if an yi mata fyaden ma zai iya zama da ita a haka. “Akwai abunda yake faruwa a tsakaninku Abdulhamid, wanda ba ka son mu ji kuma ba lallai ne sai mun ji ba, amman ka dubi girman Allah ka ji tausayin yarinyar nan, ace har ta fara shaye-shaye amman kake maganar sakinta? Abunda ya same ta kaddara ne miyasa ba zaka nuna mata hakan ba? Rashin lafiyarka ma ka nuna mata zaka nemo magani, i promise you zaka samu sauki soon...” shiru Abdulhamid yai for a while kamin ya sake bude bakinsa ya ce. “I think rabuwar shi ya fi alheri a tsakaninmu dukan mu za mu samu kwanciyar hankali” Wani irin kallon Abdallah yai masa. “Ta auri mutunen da be cancanta ya zama mijinta ba, Abdulhamid ban yi tsammani haka daga gareka ba... ” “Ba ka fahimta ba ne Abdallah tun kamin wannan abun ya faru Halima tai ciki, kuma ta zubar da shi ba tare da na sani ba....” “Ciki? pregnant.... Ciki?” Ya maimaita har sau uku, sai kuma yai saurin mikewa tsaye ya nufi window falon ya tsaya a gurin yana shafa kansa, gaba daya zuciyarsa ta gama narkewa da tausayin Halimatu yanzu kam. A hankali ya busar da iskar bakinsa yana sauraren yadda Abdulhamid yake labarta abunda ta fada masa da kuma kin yardar da yai da ita. Lumshe ido yai ya bude, so yake yacewa dan'uwansa Halimatu tana da gaskiya amman taya? Shi kansa ba shi da hujja, iyakar abunda yai imani da shi, shi kam ya yarda da Halimatu ko da bata kafa hujja da komai ba, and ya san idan har Halimatu za ta aikata zina to zata aikata ne tun a lokacin da take gidan Aminu. Juyowa yai ya kalli dan'uwansa. “Amman ka yi magana da ita? Abdulhamid ko da da gaske Halima ta aikata haka ta cancanci ka zauna da ita, macen da zata bar yayanta, ya bar duk wani abu mai muhimmancin a gareta ta yarda ta aureka da matsalarka ta gama maka komai, kama yai ka tambaye ta ka bincike ta wata kila ta iya gane wanda yai mata wannan abun sai a bincike shi amman duka ba ka yi wannan ba sai kawai ka juya mata baya? And now kana maganar ka sake ta? Ka yi convince dinta ka nuna mata sakin ba mafita ba ne a gareta, ta shiga damuwa da yawa, Abdulhamid, Halima deserve a happiness” “Ya isa haka Husaini wuce ka je gurin aikinka” Hajiya ta fada a tsawace tana daga masa hannu. Ya gyada mata kai yana hade wani irin abu daya tsaya masa a kahon zuciya. Ko minti biyu be kara cikin falon ba ya fito ya shiga motarsa, Halimatun dai ce ta tsaya masa a rai ya kasa rika ko da sitiyarin motar har na tsawon lokaci ba yi wata halitta da yake tausayi a duniya kamar Halimatu ba. How he wish shi ne a step din Abdulhamid da ya nuna mata soyayya da kauna ya rumgumeta har sai ta manta da duk wani bacin rai a duniyar nan. Ya dade a gurin kamin ya tashi motarsa ya danna horn a bude nasa gate ya fita da motar, titi ya hau yana tunanin inda zai je direct asibiti gurin aikinsa ko kuma gurin Halimatu? He need to talk to her, sai kuma wata zuciyar ta ce nasa no, kuskure ne yai magana da ita a yanzu, ba zata fahimta ba, son da yake mata ma yana jin a ransa cewar ya aikata baban zunubi kuma yana jin kamar ya ci amanar dan'uwa, wannan kadai ya saka shi a damuwa. And maybe idan yai magana da ita ta fahimta ta daina zancen sakin, he can talk to her as her brother wata kila ta fahimta. Haka yake ta sake sake a ransa, daga karshe ya yanke shawarar kiranta a waya, sai dai kuma idan ya kirata a waya dan'uwansa ya ji he may think something else... But yes he can talk to her as Abdulhamid brother as his best friend, as her husband best friend. Har cikin ransa baya son ta rabu da Abdulhamid saboda ba mafita ba ne a gareta, and idan ta rabu da shi yanzu zuciyarsa kan iya bijiro masa abunda ba mai yiyuwa ba ne akanta. Wayarsa ya ciro ya aikawa Abdulhamid sms. “Can i talk to her? As your brother” Immediately yai masa reply. “Yes i trust you” The truth word break his heart sai yaji ina ma be tambaya ba. But yes mace ta bukaci saki a gurin miji ai ya kamata yan'uwansa su ji daga gareta su ji dalilinta. Sai da ya saita natsuwarsa sannan ya dauki hanyar gidan Abdulhamid yana ta tunanin a irin halin da zai samu Halimatu. Zuciyarsa sai raya masa take kar yaje, ya faka motarsa a bakin gate sannan ya fito ya tura kofar gate din ya shiga cikin gidan. Ya dade tsaye a kofar falon sannan yai knocked. For like five minutes ta bude kofar suna hada ido, idonsa ya cika da kwalla wani irin tausayinta yake ji yake kamar ya dauke ta ya hade ta manta da komai. “Abdulhamid ba ya nan” “Gurinki na zo” Sai ta saki kofar falon shi kuma ya turo ya shigo cikin falon ya zauna a kujerar da ke kusa da kofar falon. Daga inda take tsaye fuska babu annuri ta ce “Ina jinka” Sai ya nuna mata kujera alamar ta zauna, ba musu ta zauna a kujerar da ke nesa da shi sosai, after ta zauna ya soma magana a natse. “zan yi magana da ke as Abdulhamid brother, Abdulhamid ya zo mana da magana marar dadin ji daga gareki, b zan iya nanata maganar ba amman ina fatar ba haka zan ji daga bakinki ba.... ” Bata ko jira ya karasa ba ta dora da nata. “Haka yake ko ba zancen saki ba?” “Amman Halimatu wannan ba mafita ba ce a gareki and... ” “And what? Idan ya sake ni mutuwa zan yi?” Kasa ce masa komai yai, gaba daya ta canja a tsaye take kamar ba ita ba. “Be kamata ki canja rayuwarki ba akan abunda ya same ki, kowa ya san kaddara ce, ki tattara komai ki aje a gafe ki barwa Allah labarinsa, dabi'un da kika dauka yanzu ba za su kai ki ko'ina ba and mijinki yana son ki yana cikin damuwar abunda ya same ki....” “Babu abunda zaka fada min da zai saka na canja kudirina Abdallah, bana son jin wata magana daga gareka ko wace iri ce, let it go can't hold me back anymore, duk abunda ya faru ai kai ka janyo you try to act innocent, da ba ka aikata min abunda ka aikata ba, da yanzu komai be faru ba, na rasa gane wane irin mutum ne kai Abdallah na kwarai mai son taimakona da yarana, ko kuma mai son ruguza rayuwata?” Still now be iya ce mata komai ba, gaba daya jikinsa ya gama sanyi, be fahimci inda zancen ta ya dosa ba. Ita kuma bata fasa fayyace masa komai ba. “Mutumen da

Chapter 21 of 55