katsewa sannan ya daga da muryar da ke nuna be san mai magana.
“Abdallah kana ina?”
Yana jin muryarta ya gane ni ce mai magana.
“Halima.....”
Yayi shiru sai kuma ya amsa.
“Ina gida”
“Wane gidan?”
“Gurin Hajiya”
Kashe wayar nai na nufi hanyar fita daga ward din ina ta sauri kar na hadu da su Mama.
*Where are are the classy ladies 🤔 mata yan kwalissa ga awwaba scent tazo maku da hadadun turarukan wuta humra body oil turaren jiki na tsuguno da kayan gyaran jiki kaman dilka scrub organic soap 🧼 da sauransu akan farashi daidai aljihu say no karnin da warin damshi na lokacin damina zaaiya samunmu a wannan lqmbobin 09137294470 08034236800*
7/21/21, 11:11 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
6️⃣0️⃣
For the first time a yau zan tunkari Abdallah da maganganu a cikin gidan Hajiya babu tsoro ko fargaba a tare da ni, sai dai ga dukan alamu shi din ya kasa natsuwa sai kiran wayata yake ni kuma na ki na dauka domin face to face nake son ganinsa ba ta waya ba, kamin mai napep din ya isa har na matsu, yana saukeni na biyashi kudinshi na buga gate din sai na ji shi a bude, hakan yasa na tura kofar na shiga babu kowa a harabar gidan sai motoci ina ganin motarsa na tabbatar da lallai yana gida kamar yadda ya fada min. Kai tsaye na nufi kofar falon nai knocked sai na ja na tsaya, after some seconds ma sake kwankwasawa. A hankali aka bude kofar Abdallah ne ya fito daga cikin falon ya janyo kofar ya rufe yana kallona da mamaki a fuskarsa.
“Halima lafiya?”
Ya tambaya a hankali kamar mai rarrashin yarinya. A yau da na kalleshi sai na ganshi kamar ba Abdallah ba, duk wata kima da matarta da mutunci da nake ganinsa da ita a yau sai na nemeta na rasa.
“Ina mamakin yadda zaka fada min abunda ba shine a ranka ba, ina mamakin yadda ka tozarta yardar da nai da kai ka watsar da amincin da nai maka”
Karara mamaki da al'ajab suka bayyana a fuskarsa.
“Halima are you okay?”
“No I'm not, me yasa zaka fada min abunda ba shine a ranka ba, akan me zaka ce kana son farincikina bayan ba haka ba ne a ranka?”
Matsowa yai kusa da ni ganin yadda nake daga murya, idanuwana kuma na nuna tsantsar bakin raina.
“Wace irin magana ce wannan? Me yake damunki?”
Ya fada murya kasakasa.
“Kaine damuwata Abdallah, kai ne matsalata”
“What happen?”
“Ka rantse min baka san abunda yake faruwa ba....!”
Murmushi yai ya lumshe ido ya bude.
“Wai wannan banza... Ai...”
“Shi ba banza ba ne mijina ne na sunna!”
Na fada cikin wani irin zafin rai da ban taba sanin ina da shi ba. Sai ya sake yin murmushi.
“Na sani ne ai, har na taya shi murna remember?”
“Yes a ranar ka cije shi a hannu”
“Maye ni ne ko aljani da zan masa wani abun?”
“No amman kai kana da kofi, kai ka yi wa Abdulhamid ya kasa aure, ka taba min ba sau daya ba ba sau biyu ba, Abdallah na sani zaka iya kullatar Ahmad a rai”
“Yes...”
Ya amsa min kai tsaye yana hade fuska kamar ba shi ba.
“Ya fada min zai nuna min matsayinsa a gurinki, kuma ya fada ya cika na sani yayi forcing din ki ya aure ki, he deceive you ba ki san waye shi ba, how could he? Ya aure ki by force and ya holding hannunki a gabana bayan ya san na fi kowa son ki? How dare he?”
“No how dare you....! Ahmad be aure ni ba sai da amincewa ta, abunda kai masa ya nuna baka son farincikina, domin yan'uwansa da danginsa ni zarsu zarga idan hakan ta faru ya kake tunanin zan kasance?”
“Amman Halima ba son shi kike ba, ta ya za ki auri mutumen da ya laka miki laifin kisan kai? Ko kin manta ne? Mutumen daya tashi sakawa a rufe ki gidan yari? Babu kalar maganar da be fada miki ba, Ina son ki Halima kin sani ina da kudurora akanki, i just want you to get a better life, kuma idan mu kai jira na wani lokaci wata kila Allah zai cika mana burinmu”
“Jiran shekara dubu nawa? Jiran ranar da Hajiya za ta so ni har ta amince na aure ka? Ko jiran ranar da Abdulhamid da bakinsa zai roki na aure ka? Ko jiran ranar da mutane za su ga dacewar haka su ba mu shawara aikatawa? Ba so na kake ba Abdallah kana son ka ne, a lokacin da na ke auren Aminu ka sani mijine uban yayana amman kullum sai ka fada min aibinsa, kullum sai ka fada min abunda zai bata min rai saboda na rabu da shi na aure ka, ka sani neman auren matar aure haramun ne Annabi ya hana amman ka nace kana ta min campaign kanka, babu abunda baka min dan na kashe aurena na aureka, wannan dalili ya hana ni auren shiyasa na zabi na aure dan'uwanka domin shi be taba min haka ba, duk kuwa da kasancewar shi ya fara so na kamin kowa, yana sane nai aure amman be taba ce min Halima ki kashe aurenki ki aure ni, Abdulhamid ya fika zuciya mai kyau, domin shi be taba cutar da ni ba, kawai ya kasa aminta da ni ne a lokacin da kaddara ta fada min, and now na sake auren wani ba kai ba, so kake na kashe auren na fito aure ka? Saboda ka cika son kanka kuma ka kasa yarda da kaddara, miye laifin Ahmad idan na aure shi kuma zan samu farinciki a gidansa? Ashe ba farinciki kake min fatar samu ba?”
Na karasa a tsawace hawaye na sauko min.
“Halima kamar ba ke ba”
“Ni ce dai, na zo na gargade ka ne, idan wani abu ya samu mijina...! Ba zan taba yafe maka ba, kuma hakan ba zai saka ya sake ni ba ba zan taba rabuwa da shi ba har a abada...! Domin ni na yarda da abunda ka kasa yarda da shi KADDDARA”
Na kare ina nuna shi da yatsa, sai ya girgiza min kai ya kara matsowa kusa da ni
“Haba Halima kina da raunin tunani, ta yadda idan wani ya kisa miki wata maganar sai ki hau ki zauna akanta, ki rika kokarin samawa wasu farinciki ba kanki ba, yanzu duniya ta wuce wannan kowa kansa ya sani, kamar kin manta waye Ahmad? Miya zai kitsa miki abubuwa a kaina kuma yardar da mutumen da kika gani a jiya sama da ni?”
“So kake GOBE NA ta lalace, so kake mutane su fara guduna suna ganina kamar wata annoba? So kullum nai ta dauwama a bakinciki da damuwa? Na gaji i deserve happiness”
“Shi nake kokarin ba ki, i promise you za ki samu farinciki a tare da ni, dukannin mafarkina da burina akanki ne, Halima ina miki son da wani da'namiji be taba miki shi ba....”
Yana karasa Hajiya ta bude kofar falon ta fito, a yanayin yadda na ganta da kuma yadda fuskarta ya nuna ta ji komai. A gabansa ta tsaya yana kallonsa shi ma kallonta yai sai yai kasa da idonsa.
“Da gaske kai ne silar ciwon Hassan?”
Ta masa tambayar tana masa wani irin mugun kallo, sai yai shiru ya kasa amsawa kuma ya kasa daga ido ya kalleta.
“Ka amsa min? Eh ko a a?”
Ta daka matsa tsawa jikinta har bari yake.
“Eh....”
Tasss ta wanke masa fuska da mari kamar daman jiran take ya amsa mata da eh din, hakan kuma be wadatar da ita ba har sai da ta sake marin dayan baren fuskar.
“Amman baka da tausayi baka da imani Husaini.... Allah ya wadaranka....”
Cikin kuka take mishi wannan maganar, shi kuma har lokacin be motsa daga inda yake ba. Sai kuma ta juyo ta kalleni tana hawaye.
“Fita ki bar min gida, ba ke ba yaya har abada, ko bana raye ka auri Halima ban yafe maka ba.....!”
Ta karasa tana nuna shi da yatsa, a rikice Abdallah ya kalleta ya kalleni sai ya fadi kasa ya rike kafafuwanta ya fashe da kuka kamar ba shi ba.
“Noooooooo Hajiya dan Allah..... Hajiya dan Allah, Hajiya dan Allah.... Hajiya dan Allah.... Hajiya dan Allah...”
Ya maimaita hakan ya fi a kirga yana rike da kafafuwanta yana kallona kuka yake sosai kamar ba namiji ba, sai kuma ya mike tsaye ya rike hannayenta.
“Hajiya ina son Halima Wallahi baki san kudurina ba dan Allah karki shiga tsakaninmu haka....”
A take ta fisge hannunta ta sake wanka masa kyakkyawan mari. A lokacin ne yai shiru ya runtse ido.
“Ka gani ko? Dan Allah ka kyale min mijina.... Ina son abuna”
Na fada ina hade hannayena nima hawaye nake kamar shi, sai ya bude ido ya kalleni kamin ya juya yana kallon mutanen da suka fito daga falon suna tambayar ba'asi, Hajiyar kuma ya koma cikin falon tana kuka. Ni kuma na juyo kamar kazar da kwai ya fashewa na fara tafiya ina jin wani abu marar dadi. Sai da na kai gate din sannan na juyo na kalleshi har lokacin yana tsaye a inda yake yana kallona, juyawa nai na bude gate din na fita. Sai da nai tafiya mai nisa sannan na samu napep na shiga ta mayardar da ni asibitin ko da na isa ana kiran sallah magariba, kai tsaye na nufi ward din da Ahmad yake ina isa na tura kofar dakin na shiga, sai na samu Mama da Inna zaune a dakin ga Hajiyarsa da Kanwarsa Siyama da wata wasu mata hudu da ban wayance su ba, sai dai ina kyautata zaton yan'uwan Ahmad din ne, shi kuma yana zaune saman gadon wani kallo kawai yake aiko min wanda ke nuna ba lafiya ba. A sanyaye na shiga muka gaisa da mahaifiyarsa sai ta gabatar da ni a gurin matan, sannan tace min.
“Kin gwangwanin Gwarzo nan”
Hakan yasa na sake mika musu gaisuwa sannan na tsaya a kusa da Inna sai dai a duk lokacin da na kalli Ahmad sai ya dan harare ni kasa kasa, sannan ya sauko saman gadon ya shiga bandaki yai alwala ya fito, Hajiyarsa ta umarce ni da na shimfida masa carpet su kuma suka tashi suka fita tare da bakin. Inna da Mama suka mike tsaye Inna na ce min.
“To mu kan mun tafi Halimatu sai kin dawo Allah ya kara sauki”
“Amin inna sai na zo”
Sai da suka juya sannan ya kawo kunnensa kusa da nawa ya rada min.
“Ki ce musu nan za ki kwana”
Na lake kafada alamar ba zan fada ba, shi kuma ya kware min ido kamar mai yi da karamar yarinya. Sai da suka fice sannan na shiga bandakin nai alwala na fito na zauna bakin gado har sai da ya gama sannan ya tashi ya dawo saman gadon ni kuma na hau carpet din nai sallah, babu komai a addu'a ta sai nemawa Ahmad lafiya da rokon Allah ya tsare min shi. Sai da na shafa addu'ar sai ya miko min hannunsa na hagu, na rika na tashi tsaye sai ya dawo da ni kusa da shi na zauna, sai ya saka hannunsa saitin kwankwaso na yana ta wasa da shi, ya dora gemunsa saman wuyana sai yasa ta bakinsa ya janye mayafin kaina ya sauko kasa, bakinsa saitin kunnena.
“Na fadawa Hajiya ta sa a shirya miki ticket mu tafi tare”
“Amman Ahmad tun da ance ba a ga komai ba why not a yi addu'a kasan wani lokacin iska da kandu suna yin haka fa”
“Ba laifi ya zama iska ba, kin san Nigeria ba mu da irin wannan cigaban yanzu za a iya zuwa a can su yi gwaje gwajensu kuma a gano matsalar”
“No ba na asibiti ba ne”
“How do u know?”
Kamar mai rada haka yake min magana in each word sai ya tsotsi kunnena sannan yake fadarta wani sa'in kuma sai ya busa min iska a kunnen. A kalleshi a natse na ce.
“Baka fada min tun daga lokacin da ka gaisa da Abdallah ne abun ya same ka ba”
Sakina yai yasa hannun nasa ya rike fuskata.
“Ina kika je dazun?”
Na yi shiru.
“Ba gida kika je ba, na sani dominbda suka zo sun tambaye ki kuma Mama tace kin buga mata waya kina kuka, i suspect something fada min ina kika je? Don't lie to me”
“Magana nai da Abdallah....”
A take fuskarsa ta canja.
“As how?”
“Akan ciwon ka ne”
“Oh ya Allah, taya za ki je ki yi magana da shi? Kin san ko tunawa nai akwai son ki a zuciyarsa sai naji kamar na kone, akan me za ki je ki yi magana da shi? Lims why? Is not allowed ya ji muryarki ma ji drees dinki ma, gown ce fa sai mayafi Babe why?”
Ya karasa kamar yai kuka, hakan kadai ya isa ya karantar da ni irin zafin kishin da Ahmad yake da shi, so idan har zan zauna da shi dole nai tsaka tsantsan da rayuwarsa.
“Saboda na san shi yai maka kofi, kuma da na masa maganar ya amsa min da cewar shi din ne, tun da yana jin haushinka na san dole zai maka, shiyasa na ce maka ba na asibiti ba ne, ya yi ma dan'uwansa kuma ni ma ya sha min”
“Ba kofin ya dame ni ba, maganar da kika yi da shi ta dame ni, Allah kadai ya san abunda ya ce miki kila ma yace Halima ina son ki”
Na dan zaro ido.
“Aa be ce ba fada fa mukai da shi”
“Fada did he touch you”
“Oh oh No ba irin wacan fadan ba, fada na baki”
Ture ni yai daga jikinsa.
“Daga ni dan Allah”
“I'm sorry, amman na damu da halin da kake ciki ne”
Ya fada ina kada kafata domin tafiyar abu nake ji kamar ƙuda, ina jijjiga kafar na ji abu ya fado mai nauyi, saurin mikewa nai tsaye sai ganin kunamu nai har uku a inda kafafuwana suke, ban san lokacin da na daka tsalle na dale saman gadon ba ina ihu.
“Ka gani ko? Ya fusata da ni shine yai min kunamu nan”
“Shiiiiiiiiiiii karki bari Hajiya ta ji maganar nan”
Ya fada yana rufe min baki.
“Shiyasa na fada maka cewar ciwon hannunka nan ba na asibiti ba ne, ayi maka addu'a zai fi sai ka mu sauki”
Na fada kamar zan fashe da kuka, jana yai jikinsa ya rumgume.
“Amman kin san yanzu an riga an gama shirya komai Hajiya ba zata yarda a fasa ba, kuma zuwan ma yana da amfani ko ba kuma hakan zai kara tabbatar da maganarki kuma Hajiya ba zata zargi komai ba”
“Amman taya za a samu maganin kofi a asibiti? Ahmad kai tunani mana”
“Okay fine zan yi magana da Hajiya sai nace mata a hada da addu'a hakan ya miki?”
“Eh ni ma kuma za ki rika maka fatiha kafa bakwai kullum da safe a ruwa kana sha idan zaka iya shan yawuna”
“Hmmmm har abunda ya fi yawunki ma zan iya sha, kin san minene”
Ya fada yana shinshinata tare da dora hannunsa saman cinyata.
“A a bana son sani”
Sai yai murmushi ya sauka saman gadon ya dauki takalminsa da hannunsa na hagu ya kashe kumamun dake ta yawo a cikin dakin sannan ya dawo ya zauna a inda nake yana kokarin kai hannunsa kirjina aka tana kofar da sauri na dauki mayafina na rufe kaina shi kuma ya dauke hannunsa daga jikina.
Yunus ne ya shigo rike da ledodi a hannunsa, after sun gaisa da Ahmad ya gaisa da ni sai kuma ya soma zolayata.
“Amarya ashe ashe ba mu sani ba....”
Wani kallo Ahmad yai min hakan yasa ban biyewa wasan da yake min ba.
“Yunus ka fa san ni bana son wasa da iyalina please take note”
The way da yai masa maganar babu wasa ko kadan a tare da shi, sai dai hakan be hana Yunus din yin dariya ba.
“Daman na zo ne na dauke ta ayi mata hoto Hajiya tace a shirya mata komai da ita za a je”
“Ban gane ka dauke ta ayi mata hoto ba? Ta dai baka hotonka karami ko?”
“Ba shi kadai ba ka san za a mata passport”
“Okay kuma kai zaka kaita ayi mata”
“Alhaji bana da matsala idan kai zaka shige gaba ayi mata komai, yanzu dai ya jikin naka?”
“Al-hamdulillah zan mata komai”
Ya fada yana kallona. Sun dan dade suna fira kamin yai mana sallama ya tafi. A lokacin ne na zuba mana abincin a plate daya ni da shi, be wani ci sosai ba hakan yasa nima na ji ba zan iya ci ba, ya bukaci na hada masa tea.
“Shiyasa ka rame baka cin abinci”
“Sai na samu lafiya zan ci abinci na koshi na more”
“Ba gashi na zuba maka yanzu ba ka ci ba”
“Ba wannan abincin ba, wacan abincin wanda aka dade ba a hadu ba, kuma na yi marmari da yawa”
Murmushi nai ba tare da na kalleshi ba na cigaba da hada masa tea, da na kawo masa masa be karba ba sai yace na bashi da kaina, haka na rika ba shi tea kamar wani karamin yaro.
“Sha mana”
Na kurba kadan na bashi ya sha, bayan ya gama mukai sallah isha'i. Ban tashi daga saman carpet din ba sai ga Hajiyarsa ta shigo tana tambayar ko akwai abunda muke bukata.
“Sai dai ko shi ni ai gidan zan tafi”
“A a nan za ki kwana, wannan kuka da kuka min dazun idan kika je gida ai sai ki yi mafarkin kukan kuma”
Ta fada tana murmushi ni kuma nai kasa da kaina kunya ta rufe ni, Ahmad kan dariya yasa kamar ba shi ba.
“Ashe dai ana so na”
Kasakasa na wasa masa harara. Sai Hajiya tai murmushi.
“Allah dai yai muku albarka kuma ya ba ka lafiya ka koma gida cikin iyalinka”
Daga ni har shi muka amsa da amin, sannan tai mana sallama ta fice. Duk yadda na so ya kwanta saman gadon ni na kwanta kasa sai yaki, ala dole sai dai mu kwanta saman gadon a tare ko kuma shi ya sauko kasa mu kwanta.
“Gadon ai ba zai dauke mu ba”
“Ai ba dole sai mun wadata ba, ko kuma mu kwanta kasa”
“Ya za'ayi kana rashin lafiya ka dawo kasa ka kwanta?”
“Kin san dai ba zai yiyu mu kwana daki daya kuma a daban daban ma wannan ai haramun ne ma”
“Inji wa?”
“Inji ni”
Ya nuna kansa, ban san lokacin da na saka dariya ba. A dolen dole muka kwanta kasa ni da shi, muka lulluba da Bedsheet daya yadda ya rumgume ni a jikinsa yana shafa ni kai ka rantse da Allah ba ciwo yake ba.
Da asuba sai da na dumama masa ruwa yai wanka ni kuma na shiga nai alwala ko da ya fito na gama sallah na gaishe shi na shimfida masa carpet din yai sallah bayan ya gama na karanta masa fatihar ya sha sannan na hada masa tea.
Misalin bakwai da wani abu direbansu ya kawo mana breakfast ba laifi nan ma da na zuba mana ya ci wata kila saboda mun ci tare ne ko kuma dan na yi magane jiya yasa yau ya ci oho. Sai tara da wani abu mahaifiyarsa ta shigo, ni kuma na fita na basu waje. Ina tafiya wayata tai kara alamar shigowar sako, number Abdallah ce.
“Ina fatar mijin da kika aura ya rike ki amana Halima, i wish you all the best
....”
Shine abunda ke rubuce a cikin sakon, ban miya sa ba sai duk na ji wani iri. Har na koma dakin jikina a sanyaye yake.
“Na yi magana da Hajiya akan ko a daga tafiyar nan har gaba sai ce ba zai yiyu ba, amman dai ta aminta za a saka da addu'a din”
Ban ce masa komai ba na hau saman gadon na zauna na dora kaina sama wuyansa.
“Babe are you okay?”
Na kalleshi.
“I'm fine, Allah ya baka ikon rike ni amana”
“Amin”
Ya sumbaci goshina.
“Ba zako taba kuka da ni ba In-Sha-Allah i love you so so so much”
Ya fada try to hug me with both hands.
“Baka jin ciwo ne?”
“Da sauki dai gaskiya”
Murmushi nai na rumgume shi. Ban dauka da gaske yake ba har sai da muka je tare da shi aka min komai na tafiyarmu a yadda nake ganinsa na jidadi domin baya nuna alamar ciwon ko da akwai ma yana boye min, domin ya fada min duk bayan awa uku sai hannun ya taso masa da ciwo amman yanzu kam Al-hamdulillah.
Tare da shi da direban da ke jan mu ya sauke ni kofar gida, sannan shi kuma ya wuce. Da na shiga gida sai Hafiza ta rika zolayata kamar ba kanwata ba iskanci kala kala ko kunyar Mama da Inna bata ji, ko da yake daman can Hafiza ba wata doguwar kunya ce da ita ba. After na yi wanka na canja tufafin jikina ina gyarawa su Amal kayansu Inna ta shigo tana tambayar wai da gaske ne taji a gurin mama cewar da ni za a tafi.
“A a aiko hakan yayi Allah ya bashi lafiya”
“Amin”
“Inna”
“Na'am”
Har ta juya na kirata ta juyo.
“Dan zauna dan Allah”
Ba musu ta zauna saman katifar da muke bachi, a nan labarta mata abunda nake zargi a ciwon Ahmad da kuma a abunda ya faru tsakanina da Abdallah a maimakon ta yaba min sai ta rufe ni da fada.
“Sakaryar banza sha sha ba, marar tunani, komai Abdallah yai miki kar karki manta dan'uwanki ne kuma saboda yana son ki yai, ai ko a munafurce mutum ya nuna maka kauna ya fi wanda ya fito kirkiri yace baya son ka”
“Amman Inna shine fa yai masa wannan kofin”
“Idan shi din ne ai sai ki bishi da lalama ba da hauka ba, Abdallah ya gama miki komai a rayuwarki Halimatu be cancanta ki saka masa da wannan ba, ke dai kan baki da tunani sam sakarya kawai”
A fusace ta fice ta bar dakin ni kuma sai duk na ji babu dadi, na rasa abunda zan yi na ji sanyi a raina na rasa tunanin da zai nuna min na yi daidai ko akasin hakan.
ABDALLAH POV.
Tun da Hajiya tai furucin nan sai ya ji kamar an zare masa rai a cikin jiki, har lokacin kuma ya kasa ganin laifin Halima, iya abunda yake tunani Ahmad ya kira mata abubuwa ne akansa ita kuma ta yarda shiyasa ta zo har cikin gidan Hajiya tai masa kalamai marasa dadi.
Sai dai daga lokacin da Hajiya tai masa furucin cewar ko bayan ranka ya auri Halima bata yafe masa ma ya cire zancen aurenta ya aje a gafe, hakan kuma ba zai saka kaunarta ta goge a zuciyarsa ba, sai dai yana da yakinin idan ba Halima ya aura ba ba zai taba samun cikar burinsa ba na haihuwar da namiji, a iya kwallafa rai ya kallafa mata rai da zato da kuma tunanin idan ya aureta burinsa zai cika na haihuwa da namiji kuma zai samu damar kusanci da abar son sa.
“Yanzu na gane ba laifinta ba ne, har da naka kana da son ka Abdallah taya zaka runtse ido ka tsaya kai da fata akan cewar sai ka aureta? Matar da dan'uwanka ya saka? Kuma dan'uwan naka ma twins brother dinka? Kuma yana raye? Bayan kasan bana son yarinyar nan, hakika na tsorota da lamarinka, idan har zaka ita cutar da dan'uwanka to ni ma zaka iya cutar da ni”
“Subhanallahi Hajiya wace irin magana ce wannan? Abdulhamid shi ya fara cutar da ni, domin yayi min kofin ba zan taba haihuwar da namiji ba, kuma Hajiya kin san yadda nake son namiji, yana daya daga cikin dalilin da yasa nake son na auri Halima”
“Kum illata kanku kun cutar da kanku, amman kai kafi cutar da dan'uwanka, ko da baka haifi namiji ba ai kai ka yi auren har ka haihuwa? Shi fa? Dubi inda ya kare yanzu da yana ko ya ce da ban kalli yar na ji sanyi ba? Amman damuwarsa bata dame ba ka, kai neman da namiji kawai kake? Babu ruwanka da matsalarsa, kana kallon yadda yake ta fafutukar neman magani amman baka taba tausaya masa ba Allah ya wadaranka Abdallah, ka so matar aure, kuma matar dan'uwanka saboda selfishness reasons, Halima ce kawai mata a duniya? No saboda ka musguna ma dan'uwanka ne kuma kana ganin idan ka aure ta zata iya haifa maka namiji tun da last child dinta mace ce kuma tana haihuwar maza da mata ne, Wallahi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 50 Chapter of 55