mamallakin hannu mace ce ba namiji ba ban fahimci hakan ba har sai da na juyo na kalleta na kuma tabbatar da macece ta hanyar sautin muryarta.
“Kamar Haima?”
Gabana ya fadi har na kasa amsa mata da eh ni din ce ko kuma a a ba ni ba ce, domin mutun biyu ne suke kirana da wannan sunan a duk fadin duniyar nan. Daga Abdulhamid sai Kabir, ba kuma zan ce a gurin Abdulhamid ta samu sunan ba, domin be taba kirana a gabab kowa da wannan lakanin ba, mutumen da be yarda na bayyana soyayyarsa ba taya zai fadawa wata ya taba kirana da wannan sunan a lokacin da na ke budurwa.
“Har na wuce ki na dawo saboda kin min kama da Haima, kuma wannan shirun da kikai ya tabbatar min da cewar ke ce Haima! matar da Kabir ya cika wayarsa da hotunanta kuma matar da aka ce ita yaje siyo ma abinci wannan hadarin ya same shi, wani abun mamaki kuma jiya da kika kira wayarsa sunanki yai appearing da Spacial Haima”
Wani dimmmm na ji kamar an dora min abu akao na kunya da nauyin kalamanta, hakika ni ma mace ce ba zan zo mijina ya kula wata mace ba kuma ba zan jidadi ba, sai a iya zamana da Kabir ban taba daukar hoto daga ni sai shi ba ko kuma ni kadai na tura masa to a ina ya samu hotona wata kila a media ko kuma a gurin wani wata kila kuma ya dauke ni ne a lokacin da nake aiki.
“Shin baki taba sanin Kabir yana aure da yaya ba?”
Ta jefo min tambayar da ban san ta ina zan tattara amsar da mika mata ba har ta gamsar da ita.
“Ya kamata ace na damu da lafiyar mijina a yanzu ko dan saboda yayan mu, amman saboda ke idan na tuno sai na ce masa Allah ya kara, ke ya kamata ace kin fi ni damuwa da shi, ko ba komai kin fini samun lokacinsa kin fi ni samun soyayarsa da kularwarsa, kin fini muhimmanci a gurinsa”
Tana fadar hakan ta fara takawa zata bar ni a gurin da dafin furucinta, cikin kuzari da hanzari na mika sautin muryarta dan isar da mata da abunda bata sani ba.
“Babu wata alaka tsakanina da mijin, abokin aikina ne kawai kuma ni ma matar aure ce har da yaya be kamata ki zarge ni ba”
Juyowa tai ta tsaya tana kallona kamar mai mamakin abunda ya fito daga bakina, a zatona zata yarda da kalamaina ne ko kuma ta dora su a ma'aunin tunani.
“Matar aure? Kina nufin irin auren nan da be hana mai yinsa aikata komai ko? Kina nufin irin ijiyar auren da wasu kan take su aikata alfasha da wasu mazan ko?”
Wani irin abu na ji ya taso min ina iya jure komai a cikin har da kazafin sata ko maita amman ba zan juri a kira mi karuwaba, domin na san illa da kazantar zina ban aikata ba dan haka ba zan yarda wasu su bata min suna ba.
“Ke malama ban san ki ba bana da wata alaka da ke, ko ki iya halsheki ba zan jure irin wadannan kalaman daga bakin kowa ba...!”
“Baki san ni ba ba ki da alaka da ni amman kina da ita da mijina ko? Banza marar sanin ciwon wawuya wacce igiyar aure bata hana ta aikata komai ba....”
Cikin daga muryar take fada min haka, ban san lokacin da na karasa kusa da ita na wanke mata fuska da mari ba, abunda ya janyo hankalin wasu mutanen izuwa gare mu kenan daman tun da ta fara maganar aka fara tsayawa yana kallon mu...
___________
Tofaaaaaaaaa.
Al-hamdulillah yanzu kan Al-hamdulillah na gama komai hankali ya dawo gurin typing.....✍️
7/20/21, 8:30 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
1️⃣1️⃣
“Ko yar iska ce ni na fi karfin iskanci da Kabir, mutumen da ke daukar the same salary da na ke dauka, mi ya samu mi ya bani na fi karfin abunda kike tunani na fi karfin aikata alfasha da aurena da yayana”
Na fada mata cikin zafin nama bayan na wanke mata fuska da mari, wata matar da ce da ban wayance wacece ita ba ta zo da sauri ta rike matar Kabir din tana kiranta da sunanta.
“Haba Maryam wannan abun da kike ba mutunci ba ne, ai ko da gaske mijinki yana aikata alfahari be kamata ki tsare mace a hanya kina mata wannan maganar ba, ballanta baki da tabbaci akan hakan kamata yai ki fara damuwa da damuwar mijinki a yanzu Kabir yana a halin tausayin a yanzu abunda likito suke fada jinin ya kai har cikin kansa zai rayu ba zai rayu ba haukacewa zai yi ko ya manta komai duk be dame ki ba sai wani abun da ba zaki iya canjawa ba! Haba Maryam”
“Wallahi Anty karuwarsa ce kuma saboda ita wannan hadrin ya same shi, yanzu kuma dan rashin kunya har ta sako kafarta ta zo ganinsa? Haba Anty da wanne zan ji da ciwonsa ko da ganinta”
Ta fada cikin kuka ni kan tuni jikina yai sanyi jin abunda ya same Kabir jinin ya taba kwakwalwarsa, abun ya tsorani sosai kuma ya jefani a cikin wata duniyar tunanin da fargabar yadda gobensa zata kasance. Takawa na fara yi ina tafiya na nufo gate din fita daga asibitin gaba daya ba tare da na sake cewa komai ba, kallo daya za ka min ka fahimci akwai damuwa a tare da kamar yadda tunani ya kawo min ziyara a yanzu. Kar dai ace saboda ya rabe ni hakan ya same shi? Kaddararta ta fara wuce iya ni kawai har ta fara taba yayana da mutanen da suke kusa da ni? Tambayar da na yi ma kaina kenan tambayar da ban san wanda zai amsa min ita ba. Guri na samu kusa da gate din na zauna a saman wani guntun dakali idona cike da kwalla, ban samu kaina a cikin tausayin wani mutum wanda ba jinina kamar yadda tausayin Kabir ya dirar min a zuciya yai min kawaya a ruhi, ya nemi jijiyoyin jinina da jiki ya rike.
“Halimatu”
Muryar Abdallah ce ta hankalto ni har na dago kaina na kalleshi hawaye na min zuba.
“Zama kikai a guri kamar wannan har kina kuka a public? Mutane fa suna ta kallonki”
Cikin wani irin sanyin muryar da natsuwa yai min maganar da sautin da ni kadai zan iya ji da kuma fahimtar kalmomin da yake furta min. Sauke kaina nai daga kallonsa zuwa kallon titi ina ta yawo da ido.
“Abdallah ina tunanin Gobena ne, ya zata kasance? Miyasa abubuwan nan za su faru ta dalilina? Na farko yata? Na biyu kuma abokin aikina? Abunda ya faru da Namra kamar jiya ne, ban sammaci wani abun da zai taba zuciyata kamar haka zai sake faruwa ba, idan wani abun nai nauyi ya sake faruwa da ni ina jin kamar ba zan iya jure ba”
Risinowa yai gabana yana kallon fuskata.
“Share hawayenki zo muje a mota ki min bayani maybe zan sama miki mafita”
Sai na sake dago kai na kalleshi a karo na biyu, a yau Abdallah yai magana ta hankali da nuna kulawarsa a kaina, ko da yake a can baya ma ai yana nunawa sai dai wacan karon ina ganin rashin dacewar hakan saboda akwai igiyar aure a kaina, kuma a baya duk wata magana da zai min ta Aminu ce da abunda ya shafe shi.
“Abdallah zan iya rikon ka kamar dan'uwan? Abokin shawara? Wanda zan labartawa damuwata ya nema min mafita? Dan Allah?”
Sai ya kasa ce min komai, ba dan komai ba dan sai dan ya san inda manufata ta dosa, daga lokacin da zai rike ni a matsayin yar'uwa to babu zancen soyayya ko aure a tsakaninmu, ni kuwa abunda na fi so kenan, domin ban tana yi ma Abdallah kallon so ko kauna ba balle har ta ga kai ga aure! Mikewa yai tsaye ya nufi inda motarsa take, sai a lokacin na lura da inda ya faka ta, tashi nai na bi bayansa ba tare da na share hawayena ba. Na bude front seat ma shiga shi kuma ya tashi motar ya koma da ni cikin asibitin, a daya daga cikin guraren da aka tanada domin likitoci su faka motocinsu ya faka motarsa sannan ya juyo ya kalleni.
“Idan har hakan zai faranta miki rai Halima zan yi, amman ki sani zan cutu domin ba abunda nake so kenan ba, sai dai zan jira har lokacin da zaki fahimci da gaske na ke, fada min minene damuwarki?”
“Abokin aikina yayi hadari saboda ni, kuma yanzu na ji cewar akwai yiyuwar jimin ya tana kansa wata kila ya haukace ko ya manta komai ko ya mutu”
Na fada kai tsaye ina share hawayena. Sosai ya nuna min damuwarsa.
“Subhanallahi miya same shi haka?”
A take na labarta masa komai har zuwa fadan da mukai da matarsa. Na yi zaton ko zai tausaya masa ne sai na ga murmushi a fuskarsa.
“Kin kasa yarda cewar kina da kyau da kan iya jan hankali wasu mazan izuwa gareki saboda Aminu yana yawan fada miki cewar baki da kyau ko? Kina da kyau Halima seriously kina da jikin da ko wane namiji zai so ki kasance a tare da shi, ina tunanin abunda ya ja hankali abokin aikinki kenan har ya kai ga mallakar hotunanki da sakawa sunanki spacial saboda ke din ta musamman ce”
Na yi kasa da kaina ina tuna lokacin da Aminu yake fada min cewar kibar jikina ta masa yawa shi yar siririyar mace yake so wacce ke kamar zata kare, mace da zai nuna mata soyayya ta nuna masa yai zaman jindadi da ita ba zaman tara masa yaya ba.
“Bana son ki saboda kawai wadannan abubuwan da na lissafa miki, no ina fada miki hakan ne saboda ki yarda cewar ke din kyakkyawa ce kuma Allah be rage ki da komai ba”
Maganar da yai ce ta dawo da ni daga duniyar tunanin da na fara zuwa, hakan yasa nai kokarin kawarta maganar.
“Taya zan fahimtar da matarsa cewar ni ba karuwarsa ba ce”
Sai da ya danna horn din motarsa kamar wani ne a gaban mu alhalin babu komai a gabanmu sai fulawoyi.
“Ki sakawa ranki sallama for now Halimatu, ki cire zancen cewar saboda ke wannan abun ya samu abokin aikinki, kuma ki manta da zancen fahimtar da matarsa, ki daga musu kafa na wani lokacin idan ya samu lafiya kamin lokacin sai ki je ki ganshi kuma ki fada masa ya fahimtar matarsa sannan kuma ki gargade shi daya cire kansa akan duk wani abun daya shafe ki, Halima kin san abunda nake so da ke?”
Na girgiza masa kai alamar ban sani ba.
“So na ke ki manta da komai da kowa a gabanki ki maida hankalinki gurin aikinki kuma ki kula da yaranki sai kuma zancen Namra shi ma ki jajirce wajen ganin kin kwato mata hakkinta barin wannan maganar zai bawa kanen mahaifinta damar yi ma wata yar ne”
“Amman Mama tace na bar maganar saboda kar na jawa Namra abun kunya idan ta girma”
“Halima ya kamata ki gane wani abu, ke fa uwa ce idan ba ki yi abunda zai kwantar miki da hankali akan yayanki ba to be kamata ki bar damuwa a ranki ba, duk wanda zai nuna miki yadda za ki kula da yaranki a bayanki yake, duk wanda zai damu da abunda ya damu danki ko yarki a bayanki yake, ke fa mutunce ya kamata ki san da wannan, ki yi wani abun da zai zame miki kwanciyar hankali kuma ya zamo abun koyi a gurin wasu matan, bari kashi a ciki baya maganin yunwa hankalinki ba zai taba kwanciya ba har sai kin hukunta wannan mutumen right?”
Na gyada masa kai gaskiya ya fada, ni kaina ina son yin hakan sai dai yadda Mama ta nuna bata so yasa na fara cire rai daga yin abun.
“Zan tsaya miki Halimatu, zan goya miki baya zan miki duk wani abu da kike bukata kuma zan baki kariya i promise you this”
“Zan tattauna da Mama har sai na ji ta bakinta yardar Allah na tare da yardar iyaye, bana son na yi wani abun da zai zamewa mahaifiyata ciwo”
“Yes hakan na kyau, sai dai wani lokacin iyayena suna nuna mana abunda suke gani a kamar zai cutar da mu alhalin ba cutarwa ba ne Allah ya taimake mu”
“Amin ya Rabb na gode Abdallah”
Na fada ina dubansa sai shi ma ya dubuni ido cikin ido wani tsan na ji na rashin jindadi for the first time yau na ji nauyi da kunyar Abdallah ya dira saman kaina.
“Ya jikinki?”
Ya tambaya still idonsa a kaina.
“Al-hamdulillah”
“Ina fatar kin ji sauki sosai”
“Na ji sauki”
“Mashallah. mama tace min kin tafi tafi aiki ashe ganin wani kika zo”
“Na fada mata da ga ganin Kabir zan wuce gurin aiki ne maybe ta dauka na wuce ne, ka biyo da gida ne?”
“Yes na zo na duba jikinki ne kuma ina son nai maganar karatun su Adnan da ke as her mother”
Kallonsa nai ba tare na ce komai ba sai ya cigaba da maganar still idonsa na kaina.
“Ina son canja musu makaranta ne zuwa wacce su Suhaima suke yi idan kin ba ni dama amman kuma kin aminta”
“Aa Abdallah na gode da kulawa ka dawo da su gida, ni zan duba musu wata makarantar dabam”
Ina kokarin kai hannu na bude ganbun motar na fita sai ya danna lock motar ta rufe hakan yasa na juyo ya kalleshi shi ma ni yake kallo da kyau.
“Na fadi wani abun ne daya bata miki rai? Ko na yi wani abun ne marar dadi?”
“Ba ko daya, yayana ne babu ruwanka da su”
“Amman yanzu kika gama fadar cewar zan zama miki dam'uwa? To miye laifi dan na saka su Namra a scul”
“Bana so, yarana ne dan Allah ka kyale su, zan iya kula da abuna zan iya musu komai”
“Ba zan cutar da su Halima kamar ba ki san ni ba”
“Ka kyale ni dan Allah Abdallah bana bukata”
Na fada ina hade hannayena tare da fashewa da kuka.
“Miye abun kuka daga wannan maganar?”
Ya karasa yana unlock din motar, ni kaina ban ga wani abun kuka a cikin lamarin ba, sai dai ina jin a yanzu kamar bana da wata garkuwar shiyasa kukan ya fi kusa da ni. Bude motar nai na fita ina share hawayena.
Na isa gurin aikina cikin wani irin yanayi marar misaltuwa, yanayin da ba zan iya fadarsa ba, hakika inacikin damuwa bayan ta yarana da tawa yanzu kuma ta Kabir ta hau kaina. Wunin ranar ban iya tabuka komai ba saboda yawan kallon mazaunin Kabir da neka sai na rika ganin kamar yana nan ko kamar zai shigo irin yadda ya saba. Sai dai idan na tuna cewar yana can kwance asibiti sai na ji babu dadi. Ko dan saboda sabo idan abokin aikinka baya kusa da kai kanki babu dadi balle irin wannan mai dalili. Tun da na fara aikin shekara hudu ban tana jin aiki ya gundure ni ba, ban taba jin na tsani aikina kamar yau ba, idan na kalli inda Kabir yake zaune sai na ji babu dadi ba ni kadai ba har Emanuel ya damu da hakan saboda yanayinsa da na gani, ban tana jin damuwa da lamarin Kabir kamar wannan karon ba, tausayinsa ya hanani sukuni kamin lokacin tashi aikina yai har na tsalwala.
Biyu da mintuna na tashi daga aiki daman wani lokacin nakan tashi haka wani lokacin har uku saura ko uku da wani abun. Tafiya nakecikin kamfanin ina tunanin abunda zai sake samu na, domin ina jin a jikina kamar kullum wani abun zai yi ta samuna ko wani na kusa da ni marar dadi.
7/20/21, 8:30 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
1️⃣2️⃣
“Hajiya barka da tashi ya kafafuwan?”
A natse yake mata magana kamar yadda ya saba, ita kuma ta dago ta kalleshi da kyau tana tauna ragowar goron da ke bakinta.
“Hassan kwana nawa rabon ka da gidan nan?”
Shiru be amsa mata ba. Hakan ya bata damar cigaba da yi masa fadan a zuciyarta kuma tausayinsa ne fal a ciki.
“Ana rayuwa haka? Ko wane bawa ai da kalar kaddararsa, amman sai ka rika saka kanka a damuwa ba kai ka dorawa kanka abun nan ba”
Kunya ce ta lullube shi, duk kuwa da ya san gaskiya Hajiya take fada masa and he know rashin lafiyarsa na daga cikin abunda ya fi ko wane daga masa hankali, tun abun baya damunsa yanzu har ya kai matsayin da idan aka auna jininsa za a iya cewa ya hau, babu inda be nemi magani ba a duniyar nan amman babu alamun sauki balle ma saukin, babu abunda be yi ba tun daga na hausa har zuwa na gargajiya amman shiru kamar an shuka dusa. Shi yanzu abun tsoro ma yake ba shi domin yana ayyana a ransa kuma yana jin kamar ba zai taba warkewa ba, burin da ko wane mai rai yake da shi na son yai aure shi kan na shi yana nesa da shi, tun ana kiran yaushe zai yi aure a family da friends har ta kai yanzu dai su tsarge shi suna kiransa da tazuru wasu kuma su ce masa mijin aljana wanda hakan ba karamin ciwo yake masa ba.
“Karka yanke kauna daga rahamar Hassan, daman ita rayuwar duniya tana cike da jarrabawa, kuma kowa da irin tasa, karka fasa neman magani kar kuma na ce ba zaka nemi aurenba, ka kwada neman auren kamar yadda kake a da, wata kila a dace wata kila kuma kamin lokacin auren yai sai Allah ya baka mafita”
Ya gyada mata.
“Zan cigaba Hajiya, duk dai ina jin kamar ni haka Allah yai ni”
“Babu wata cuta da bata da magani a duniyar, idan ka cire tsufa da mutuwa shine kawai basa da magani, a kullum ina cikin yi maka addu'a kuma In-Sha-Allah za a karba mana ko ma an karba, kowa da irin jarabarwarsa Hassan ga yar'uwarku nan aure ya mutu ai duk cikin jarabawa ne bayan ta fito kuma ciki ya zube wata kila ma kuma ta zubar da cikin ne ta huta da wahalar duniyar”
Kallon rashin fahimta yai Hajiya, idan tace yar'uwasa zai fara kawo sisters dinsa da suke daki daya kamin ya hango na wani gurin, a cikin familynsu ma sisters dinsa ma ai suna da yawa abunka da mai yawan yan'uwa.
“Wace Hajiya?”
“Halimatu...... ”
Haka ya ji sautin sunan sahibarsa kamar daga wata duniyar, Halimatuu... Ya maimaita cikin mamaki da bakinciki jin abunda ya faru.
“Taya? Garin ya?”
“Ai kasan abunda ya faru da Namra ko to shine sanadi yau kusan kwana uku ma da faruwar abun ko hudu kuma cikin da ta fito da shi ya zube har sai da akai mata wankin mara anjima na ke son zuwa na ganta”
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, ai kamar saki daya ne ya rage ko?”
“Saki daya ne kuma ya karasa kai wannan mutumen ba shi da imani sam ”
Wani irin na rashin jindadi ne ya ziuarci Abdulhamid, sai yaji kamar kanwarsa da suka fito ciki daya aka saka, a take ya fara ayyana irin yadda Halimatu zata ji halin da zata kasance duk kuwa da ya san dama can ya san ba dadin zaman auren take ji ba. Wanda yake yawan alakanta hakan da kansa domin yana ji a ransa da ace yadda yai soyayyarsa da Halimatu a boye da ya samu cikar burinsa da yanzu shi take aure da yanzu duka yaran na shi ne,ya dade yana fargabar zuwan wannan ranar yau ga ranar ta zo da ba zai iya yi mata komai ba.
_Bana da tabbacin wanda zan aura zai rike ni amana Abdulhamid, amman ina da tabbacin kai idan ka aure ba zaka wulakanta ni ba, bana jin idan ka aureni zaka iya rabuwa da ni har sai idan mutuwa ce ta dauke daya daga cikin mu_
Cikin kuka take masa maganar muryarta har rawa take.
_Ki yi hakuri Haima, ba zan iya cutar da ke ba, ba zan iya aurenki na zaunar da ke a gidana ba bayan na san bana iya yin komai da mace, idan nai hakan na cutar da ke kuma duk abunda zai biyo baya laifina ne ba na ki ba_
_Wallahi zan jira ka zan zauna da kai har zuwa lokacin da zaka samu lafiya, ko wane masoyi yana da burin yin wani abun na faranta rai na sadaukarwar ga masoyinsa, Abdulhamid ka ba ni dama dan Allah zan aureka a haka kuma zan jira har zuwa lokacin da zaka samu lafiya_
_No ba zaki gane abunda na ke nufi ba, ban tsammaci cewar zai kan wannan lokacin ban samu lafiya ba_
_Ka hanani bayyana soyayyarka, daman saboda ka san ba zaka aure ni ba ko? Yanzu kuma ka hanani aurenka_
_na hana ki bayyana soyayyata saboda na san wannan ranar zata so wata kila na samu sauko ko akasin haka, kin ga yanzu da ban samu sauki ba babu wanda ya san mun yi soyayya da ke, da ace na samu sauki kuma da yanzu ne zan bayyana soyayyata, ki fahimce ni mana Haima Wallahi ina kaunar ki amman ba zan iya hana ki auren lafiyayyen miji ni na aureki, ba kuma zan hana ki auren kowa ki jira ni ba domin ban san lokacin samun lafiyata ba, kuma iyayenki a yanzu ma sun damu su aurar da ke, Allah ya riga ya rubuto ba zan aureki ba...._
Duk wani magana da Hajiya ke yi be ji ko daya ba saboda ya lula a duniyar tunanin abunda ya faru tsakaninsa da tsohuwar soyayyiyarsa yana murza zoben da ta saka saka mata da kansa a wani lokaci can baya.
“Hassan....”
Da sauri ya dago ya kalli Hajiya domin ya ji kiran kamar daga wata duniyar.
“Na'am Hajiya?”
“Ba ka ji abunda na ce ba ne?”
“Na ji.... Na ji.. Na ce eh ba ki ji ba ne?”
“Saboda me?”
“Haka nan kawai”
“Haka nan kawai sai ka ki zuwa aiki? Abun ya fara taba har da aikinka ne?”
Sai a lokacin ya fahimci abunda Hajiya take magana akai domin a dazun amsa mata kawai yake ba tare da yaji abunda take fada ba. Mikewa yai tsaye yana murmushi.
“Zan je aiki mana Hajiya, ban fahimta ba ne sai yanzu”
“To Allah ya tsare yai muku albarka”
“Amin Hajiya sai na dawo”
Ya fito yana jin cewar a yanzu ne ya dace ya nemi magani ko dan Halimatu, idan ma bar warke ba zai aureta a hakan matukar a yanzun zata aminta domin yana jin cewar shi kadai mutumen da zai iya yarda ya aureta da yaya a yanzu kuma ya mantar da ita komai.
HALIMATU POV.
Wani abunda ya bani mamaki rashin samun abun hawa tun daga kan babura har napep duk wanda na tara ba ya tsayawa. Abun har mamaki ya bani na rika shafa kaina ina lalabawa wai ko basa ganin nane amman sai na jini a mutum kuma ai ina ganin mutane an kallona sai dai tsayawa su dauke ni ne basa yi. Tun ina tsaye ina taro har ta kai ga na fara takawa ina bin gefen titi, da na gaji da tafiyar sai na samu guri na hutu, na sake cigaba da tafiya sai yamma lis na isa gida ban taba jin gajiya irin ta yau ba damin ban taba shan wahalar tafiya kamar yau ba. Na tararda kowa da kowa na tsakar gida kamar yadda aka saba yin shimfida a harabar gidan a zauna ana ta fira da dare dare. Suna ta min sannu da zuwa ni dai ban bi ta kansu ba na wuce zuwa falon Mama sai na samu Abdallah a zaune yana game da wayarsa Namra na gefensa tare da Aiman da Adnan sun zagaye shi Amal kuma na saman cinyarsa tana kallon wayar, tsayawa nai ina kallonsa shi ma ya dago ya kalleni fuskarsa ba yabo ba fallasa.
“Sannu da tafiya”
Sannan ya mike tsaye yana gyara rigar shaddar da ke jikinsa.
“Kin ce na dawo miki da yaranki ko? To ga su nan sai ki saka su makarantar ai”
Yana fadar hakan ya raba gefena ya wuce ni kuma na bishi da kallon takaici da mamakin karfi hali irin nasa, yara dai nawa ne kuma na zabi na saka su da kaina to ina ruwansa, tun ba yau ba Abdallah na da son shiga rayuwata
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 55