da ya nuna yana son ya aure. Da sallama na shiga shi ya fara mika min gaisuwa sannan na zauna saman cushion dinta shi kuma ya tashi ya fita.
“Amarya ba kya laifi yau an tuna da mu”
“Kullum ai kina cikin raina”
“Ni ai fushi na ke da ke ni da nai miki kyautar miji sukutun kika gujemu kika kama dan'uwanki”
Ta fada bayan ta dire min kofin ruwa, murmushi nai sai na maida kaina kasa ina kallon carpet dinta.
“Kawata kamar kina cikin damuwa”
Dagowa nai na kalleta ina ta tunani ta ina za ki fara dora mata bayani.
“Ina ciki ba daya ba ma, amman naga kamar Abban Afrah na nan....”
Rufe bakina ke da wuya muka ji tashin motarsa, sai ta tashi ta sakawa kofar key sannan ta dawo kusa da ni ta zauna tana kallona cike da damuwa.
“Ban san wane zan fara fada miki ba, tsanar da mahaifiyar Abdulhamid tai min ko kuma ganin Kabir da nai a titi yana yawo a haukace? Ko fyaden da akai min, ko kuma son yayana da Abdulhamid ba yayi?”
Ina maganar hawaye na sauko min, rikicewa tasa ka ta kasa ce min komai, har na wadansu dakiku.
“Halimatu akai miki fyade ko kuma wanda akai wa Namra kike magana?”
“Ni dai akaiwa”
“How, when? Waya miki fyade?”
“Ban sani ba Hajara shi nake kokarin sani yanzu, kaina gaba daya ya kulle”
“Fada min yaushe abun ya faru?”
Ban boye mata komai ba tun daga a to z ganin ita din ta zama kamar yar'uwata, kuma daman can ina bukatar abokin tattaunawa.
“Amman miyasa kika boye masa Halima? Miye ribar boyewar? Mijinki ne kuma shi aka zo nema da ba a tararda shi ba akai miki haka ai ya kamata ya sani”
“Hajara kina ganin idan na fada masa zai zauna da ni? Ba zai iya zama da ni ba, na ji kuma na gani da yawa akwai matan da suke fansar ran mazajensu a yi mu su fyade saboda kar a kashe mazanjensu daga karshe mazanjen su rabu da su su kasa zama da su, babu namijin da zai ji anyi ma mace fyade tana a gidansa kuma ya cigaba da zama da ita, ballanta Abdulhamid da baya iya komai da mace”
A firgice ta kalleni.
“Kamar ya baya iya komai?”
Tun daga farko nai mata shimfidar labarin har zuwa auren mu.
“Amman Halimatu kin yi wauta, akan mi za ki auri miji kamar wannan? Ba ki san za ki iya jefa rayuwarki cikin hatsari ba?”
“Na riga na raba tun a gidan Aminu yana da lafiya amman sai mu kwashe wata hudu uku har biyar be neme ni ba, shi ma da yake da lafiya na daure balle wannan?”
“Ba daga nan take ba, a can baki da kwanciyar hankali, a nan kuma hankali a kwance yake za ki ci ki koshi dole wata rana ki ji kina bukatar mijinki a kusa da ke, bayan rashin lafiyar na Halimatu mutumen baya son yara kuma kika aureshi a haka, and kin san dan'uwansa yana son ki kuma kika take hakan kika aure shi? Fada min taya mahaifiyarsa zata so ki wata kila ita din ta san dan'uwansa yana son ki amman kika zabi ki auri daya ki bar daya, wanda be dace ki yi haka ba tun daga farko”
Hannu na saka na rufe fuskata ina kuka a hankali.
“Ki fada masa gaskiya na san ba zai gujeki ba, duk namijin da za ayi ma wannan Sadaukarwar ba zai taba gudunki saboda wannan ba, musamman idan yaji cewar shi aka zo nema”
“Idan kuma ba shi aka zo nema ba fa Halima? Idan wanda yai min fyade ya zo ne saboda kawai yai min fyade fa?”
“Akwai wanda kike zargi?”
“Dan'uwansa?”
Ta yi saurin rufe baki tana kallona.
“Ya taba miki maganar banza ne?”
“Be taba ba, amman zoben da na gani a hannun mutumen da ya min fyade yau na ganshi a gurin Abdullah har na kai hannu na dauka ya ce na bashi”
“Amman daman can yana da dabi'ar neman mata ne? Kuma jiya kawai kika gan shi da zobe?”
“Ban san shi da wannan dabi'ar ba, ko a lokacin da yake ta son na kashe aure be taba min maganar banza ba, ni ban taba lura da hannubsa ba balle har na tantace kalar zobensa, amman ba a shaidun mutum kuma yanzu yana ganin na auri dan'uwansa babu yadda zai yi”
Hannu ta kai ta dafa kafadata.
“Ki kyautata masa zato Halimatu ganin zobe kawai ba zai tabbatar da cewar shi din ne ba, ba ayi ma mutum daya zobe kuma idan har shi din ne mi zai saka ya aje zobe a inda za ki gani? Mi ma zai saka ya nemi yi ma matar dan'uwansa fyade? Dan'uwan ma twin brother? Haba Halimatu”
“Zai iya mana ko kin manta abunda Sadi yai ma Namra?”
“Saboda Sadi ya lalata diyar yayansa ba shi yake nufin Abdallah yai ma matar yayansa fyade ba, duk yadda duniya ta lalace akwai na gari, duk kuma yadda duniya take ciki da mutane kirki dole akwai bata gari, karki saka ranki a rudu ki sake janyo wata matsalar a tsakanin yan'uwa, ni yanzu abunda na ke so da ke ki shirya gobe zan zo na rakaki kije asibiti a duba lafiyarki domin irin waennan mutane wani lokacin baka san ko suna dauke da ciwo ba, kuma baki sani ba ko ciki ya shige ki tun da abun ya faru ya kamata kije ayi miki wankin mara”
A take hankalina ya tashi da Hajara ta kawo min maganar ciki, dacan ban kawo hakan a raina ba hankalina ya karkata ne a gurin fyaden kawai ba dan kuma na san bana iya daukar cikin ba, lallai na zama doluwa wani lokacin haka nake abu kamar marar kwakwalwa kuma marar ilmi, tabbas idan nai ciki na shiga uku kuwa.
“Yaushe rabon da ki ga al'adarki? Idan ma akwai cikin ai za ki gane”
“Bana iya ganewa saboda ina wata shida ban yi al'ada ba wani lokacin biyar, idan ina al'ada akai akai sai idan ina shayarwa, shiyasa na ke saurin daukar ciki idan ina shayarwa, amman bana jin wata alama da ke nuna ina da ciki bana jin komai a yanzu”
“Duk da haka muna bukatar zuwa asibiti saboda cire kwankwanta, ai wani cikin sai ya fara girma yake wahalarwa kin manta cikin Adnan? Shi da ma yake cikin farin amman ba ki sha wahala kamar sauran ba?”
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”
Shine abunda nai ta maimaitawa na dafe kaina ina kuka.
“Ki kwantar da hankalinki Halimatu, akwai mata da yawa da aka ketawa haddi ba ke kadai ba, wasu ta dalilin wani abu kalilan, ba ke kadai ce a cikin wannan halin ba, amman shawarar da zan baki ki fadawa mijinki gaskiya idan ma ya zabi rayuwa da ke ai ba akanki farau ba”
“idan na bar wannan gidan auren Hajara ban san ina zan sake shiga ba, ban san wa zan fadawa ba, a can mi zan tarar, idan kuma na zauna zaman gaban iyaye ba dadi da shi ba ko ga budurwa balle a gurin mai yara kamar ni, bana son a fara kirga min aure Aminu ma idab ya samu labari ai zai ce gashi nan har aurena ya mutu tun ba a je ko'ina ba, zaman zawarci ba shi da dadi Hajara dan zaman da nai na iya sakin da Aminu yai min zuwa auren Abdulhamid ban jidadin ba ga natsatsin iyaye, ga lalurar yara tun da mahaifinsu babu ruwansa da su, bana son na fadawa Abdulhamid wannan abun ya sake ni saboda haka, idan ma har na samu cikin zubarwa zan yi a sirrance na cigaba da zama da mijina, ina jindadin Abdulhamid kuma ina son sa bana son shiga wata matsalar a yanzu, idan na fada masa ba lallai ne ya yarda ba, saboda ba ni da wata shaidar, wata kila ma ya zargi cewar na kasa tsare kaina ne na kasa hakuri shiyasa na aikata hakan yanzu kuma nai masa wannan karyar, tun da Allah ya rufe min asiri kara na rufewa kaina ko na samu salama”
Kai ta gyada min tana share hawayenta.
“Hakan yayi idan ma kin samu cikin ki zubar kawai mu rufe wannan sirrin, Allah ya dafa miki ya rufe mana asiri”
Jinginawa nai da kujerarta ina jin zuciyata na wani irin kona marar misaltuwa.
Hajara ta yi ta saka min maganganun na kwantar da hankali da karfafa guiwa a gareni har zuwa lokacin da Abdulhamid ya zo daukarta, ba ni kadai ba shi kansa na lura kamar baya cikin walwala sosai, ni da shi mukai shiru cikin motar kamar wasu kurame ni da abunda nake ta sakawa a zuciyata shi kuma yana ta tukinsa yana kallon titi.
Daf da za mu isa kiran Mama ya shigo wayata, ba tare da tunanin komai ba na danna picking na soma magana cikin muryar da ke karantar damuwarta ga mai saurarenta.
“Hello Mama”
“Halimatu Namra na gurin?”
“Aa tace aka kawo ta ne?”
“Aa mun dauka ko taba nan ne, Teema taje gidanki bata tararda kowa ba”
“Eh mun fita ne tun safe lafiya”
“Namra ce ba a gani ba tun jiya”
Kamar saukar aradu haka na ji maganar ban san lokacin da na ambaci sunan Ubangijina da karfi ba, wanda hakan yasa Abdulhamid kallona da sauri.
“Kamar ya ba a ganta ba? Ina ta shiga? Waya fita da ita?”
“Tare da Hafiza suka je biki wai Hafiza tace ta same ta bakin titi bata zo ba, kuma taje gidan bikin ta duba bata can sun jiya muke ta nemanta har makarantar anje bata can”
“Amman tun jiya Mama ba a fada min ba?”
Na tambaya idanuwa na kawo ruwa.
“Wallahi saboda tsoron kar hankalinki ya tashi ne yasa ba a fada ba”
Sauke wayar nai ina kuka ina jin wani irin tashin hankali na ratsa ni marar misaltuwa har gumi karyo min yake.
“Lafiya?”
“Namra ta bata”
“Subhanallahi garin ya?”
Ban iya ba shi amsa ba saboda kukan da ya ci karfina.
“Yi hakuri za a ganta In-Sha-Allah bari na sauke ki gida yanzu”
Ya fada yana miko min tissue.
7/21/21, 10:43 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
2️⃣0️⃣
DEDICATED THIS PAGE TO Mai Dambu, Allah kara miki lafiya Gwanata❤ son so Fisabilillahi💞😍
*** *** ***
Kamin mu isa gidan har wani jiri nake jin yana dibana, zuciyata kam kamar ta fashe ga wani uban zafi da kirjina ke yi, kaina sai sarawa yake.
Ko parking din kirki be yi ba na bude motar na fita na shiga cikin gidan cikin tashin hankali kamar yadda su ma na tararda su cikin tashin hankali, gaba daya ban tarardar yan mata gidan mu ba da samarin biyun duk sun fita neman Namra Baba na tsakar gida rike da sandar damuwa kara a fuskarsa. A bakin balcony na zauna na dafe kaina. Inna na min bayanin yadda abun ya faru da guraren da aka je nemanta bata can. Mahaifinta ne ya fado min a rai.
“Ko Aminu ya dauke ta ba a sani ba?”
Na fada ina kallon Mama, a yayinda Abdulhamid ya shigo yana gaisawa da su.
“Mi zai saka Aminu ya dauke ta, mutumen da tun da ya bata baya be sake dawo ko tambayar lafiyarsu ba”
Cewar Inna sai Mama ta karba mata.
“Nima dai shi na gani, kuma a ina ma zai ganta?”
“Ko tana gidan Abdallah?”
Na fada ciki ina hawaye.
“A a bata can tun dazun da shi ake ta nemanta, shi ma yace kar a fada miki saboda kar hankalinki ya tashi, yanzu yanzu ma suka fita da Samira har.... ”
Baba ne ya tari numfashin Inna da ke maganar yana fadin.
“Ku ba Allah cigiya In-Sha-Allah za a ganta, idan ba dan sake irin na Hafiza ba taya zaka fita da yaro ka ce ya same ka titi bayan yaron be san gurin ba”
Komawa nai na zauna a gurin na fara rare musu kuka, idan ba kukan ba ban san abunda zan yi a yanzu ba.
“Bari naje na duba makarantarsu...”
Cewar Abdulhamid yana kokarin juyawa sai Inna tai karaf tace.
“Ai har can Abdallah ya tafi....”
Baba ya sake saurin tarar numfashinta.
“A a be je can ba, islamiyarsu dai yaje, zaka iya zuwa can ka duba”
Sai da Abdulhamid ya fice sannan Baba ya hau yi ma Inna fada wai ta cika tsoma baki a maganar da babu ruwanta. Ni kam sam ban ga illar maganarta ba kamar yadda ita ma kanta da Mama ba su ga haka ba, wata kila kuma akwai abunda Baba ya hango.
“Mama zan je gidansu Aminu na duba ko tana can”
“To da Abdulhamid din be wuce ba ai sai ya karaki”
“A a shi yaje can din ni zan duba gidansu Aminu”
Na bawa Mama amsar ina mikewa tsaye.
“Mi zai kaita can ma”
“Nema ne ai Mama”
Ban tsaya na jira su kara kashe min jiki ba na zari jakata na fito cikin gidan kamar wata mahaukaciya. Kamin mai napep din na kai ni gidan su iyayen Aminu har na matsu abunka da wanda je cikin tashin hankali. A bakin gate ya tsaya ni kuma na shiga cikin gidan da sallama. Kana gani na kasan hankalina ba a kwance yake, ba Hajiyar Aminu ba ko kanensa sun yi mamakin ganina a cikin gidan, ban musu magana ba kamar yadda suma suka saki ido suna kallona kamar wata bakuwarsu. Har cikin falon na shiga na gaishe ta ita ta amsa min da dan mamaki sannan na tambaya ko Namra tana nan.
“Namra da kuka kekashe kasa ke da yan'uwanki kuka ce ba za ku bayar ba, bayan kun gama ikirarin an bata ta mi za mu dauko ta tai mana? Ai mun yafe miki ita ki dafa ki ci ko ki saida babu abunda za mu da ita”
Mikewa nai tsaye cikin bacin rai na ce.
“Ke kika fi kowa abun yi da ita saboda jininki ce, kuma tambaya kawai na zo saboda idan tana nan na tafi da ita saboda kula da tarbiyar”
Mikewa tai tsaye ta nuna ni da yatsa.
“Ke Halima ki shiga hankalinki karki ce za ki so har cikin gidan nan ki min rashin kunya, ki bar ganin an kyale ki Wallahi kika min iskanci sai an karbe yaran nan daga hannunki”
“Da kuwa kin bude abunda yake rufe, da kin tona asirin danki dan sai duniya ta ji abunda ya aikatawa yar dan'uwansa”
Na bata amsa a fusace sannan na juya na fice na barta tana ta surutanta, inda na bar mai Napep din a nan na same shi.
“Kai ni igala quarters”
Na fada bayan an shiga Napep din, yana tafiya ina nuna masa inda za abi har ya sauke ni a kofar gidan Aminu, bayan Hajiya ban san ko tana gidan ba neman be ba a cire tsammani wata kila ma ya ganta a wani gurin ko kuma ita ta fadi can a kai ta ba tare da mun sani ba.
Mai gadin yai na'am da ganina yana ta washe min hakora da tambayar yaushe gamo.
“Dan Allah Malam Garba tambaya nake ko kaga Namra a gidan nan?”
“Namra dai ta wajenki?”
“Ita, ta bata tun jiya”
“Subhanallahi Wallahi ban ganta ba, amman ki tambayi Alhaji ai yana ciki, Hajiyar ma tana ciki”
Fadar Hajiya ma tana nan ciki ya tabbatar da cewar Aminu yayi sabon aure kenan.
“Aa bana bukata na gode”
“Allah ya tsananta rabo”
“Amin”
Na amsa ina hawaye, ina shiga cikin napep din kuka ya kwace min.
“Hajiya Lafiya?”
“Yata ta bata tun jiya kuma ba a ganta ba... ”
“Subhanallahi a ina?”
“A gurin biki taje ita da kanwata”
“Aiko na ji ana cigiyar wata yarinya a fm dazun, amman ban sani ba ko ita ce”
Da sauri na kalleshi.
“Yaushe? A ina? Ya sunanta?”
“Wallahi ban rike sunanta ba amman dai dazun ina sauraren fm a napep na ji ana cigiyarta”
Ya karasa yana kunna fm din.
“Dan Allah ka taimaka ka kai ni can mu binka kasan inda fm din take?”
“Eh na sani Allah yasa ita ce”
Kamar nai tsuntsuwa na tashi na isa fm din haka naji, abun ka da guri mai nisa daga igala quarters zuwa Damba sai tafiyar ta zame min kamar ta wani gari, muna isa na fita na shiga ciki na fara tambayar mutane hankalina a tashe, sai wani ya shiga ciki ya duba takardun cigiyar ya rubuto mana number wayar da aka bada sannan ya fada min sunanta. Ina jin ya ambaci Namra wani dadi marar misaltuwa ya lullube ni.
“Sai kinje Samaru ki tambaya gidan Alhaji Muhamad Gwarzo”
“Na gode”
Tun kan ya gama magana na juya da sauri na fito na shiga napep din na fada masa unguwar da zai kai ni, a hanyar mu ta tafiya kiran Aminu ya shigo wayata, na gane ne numbersa ne saboda na haddace ba dan number tana da suna ba. Har na yi kamar ba zan dauka ba sai kuma wata zuciyar ta hana ni na danna picking na kara a kunne na.
“An ga Namra?”
“Ashe kana iya damuwa da ganinta ai na dauka ka manta da kana da yaya”
“Halima bari kiji na fada miki wallahi duk yata ta bata ko wani abun ya sameta sai na wulakanta ki, sai na sa kin yi nadamar haihuwarki da akai a duniyar nan Wallahi Wallahi dan haka ki nemo min yata tun wuri”
Be jira abunda zance ba ya katse kiran, wani uban haushi ne ya cika ni har na ji ina ma dai ace ban dauki wayar ba.
Da tambaya muka gane gidan, domin number da aka bamu mun yi ta kira ba a dauka ba, daga baya ma sai aka kashe wayar. Wani irin katon gidane mai katon gate irin na manyan mutanen nan da suka ci arziki har sukai kashinsa, kai idam ma baka sani ba za kai zaton gidan fillar kai ne saboda girmansa da tsaruwarsa, ko ina na gidan an kawatashi da fulawoyi da kuma irin dagayen itacen nan masu haska gida.
“Sannu Malam dan Allah yata na ke nema kuma ance tana nan”
Na fadawa mai gadin bayan nai kwankwasa kofar gidan ya bude min na shiga ciki.
“Ina aka ce miki?”
“Ce min akai gidan Alhaji Muhammad Gwarzo”
“Eh nan ne shiga ciki”
Kai tsaye na doshi cikin gidan, a maimakon na shiga part din farko sai na nufi dayan part din da shi nake hango kofarsa tsabanin babban part din da na kasa ganin kofar shigarsa, wata kila kuma ta karamin ake shiga.
Kofar falon na hango a bude tun ka na karasa, na yi iya yadda shari'a tace wato yin sallama da na ji ba amsa min ba na kunna kai cikin katon falon mai cike da sanyin ac da daddadan kamshi sai dai ban fasa sallamar duk kuwa da ban ga kowa ba.
Ina kokarin juyawa na fita wani mutun ya fito daga wani bangare na falon yana rike da plate da ke dauke da soyayyen kwai sai kofin tea. Wani shegen short ne a jikinsa kirjinsa kuma a tsirara dan babu riga a jikinsa. Da gila ya tambayi abunda ya kawo ni falon.
“Yata ta bata aka ce tana nan gidan Alhaji Muhammad Gwarzo... ”
Wani kallo na watsa min daga sama zuwa kasa sannan ya zauna ya aje plate din hannunsa a saman center table din dake kusa da shi yana cigaba da kallo, zuwa can kuma ya dauke kai ba tare da ya ce da ni komai ba.
“Yata nake nema na fada maka”
Banza yai min kamar ba zai amsani ba, sannan ya ce.
“Idan kin ganta ai sai ki dauka”
“Idan bata nan ka fada min bata nan ba sai ka wulakanta ni ba domin ba bara na zo yi ba”
Na fada a fusace, ina tuna inda na taba ganinsa. Uffan be ce min ba ya dauki tea gabansa yana sha tare da maida hankalinsa gurin katuwar plasma dake manne a wallpaper falon. Juyowa nai a hasale na fito daga falon marasa na murdawa, kamin na isa dayan part din sai da na rike cikina kusan sau uku. Ina isa na zauna a gurin na runtse ido ina sauraren radadin da take min. Daker na iya tsada hankalina har na lura da kofar falon, cike da karfin hali na unkura na mike tsaye na isa bakin kofar ina kokarin kai hannu na nai knocked aka bude kofar daga can ciki. Fuskar Mutumen dazun din nan ne da ke wacan part din da na baro, sai dai wannan karon akwai jallabiya a jikinsa, mamaki ya kama ni shi din ko kuwa su ma twins ne kamar Abdallah da Abdulhamid? Ko kuma wata hanyar ya biyo ta can ciki ya isa wannan part din? Sai da nai kamar ba zan masa magana ba, sai kuma wata zuciyar ta hana ni abunka da nama.
“Dan Allah yata nake nema aka ce min tana nan”
Be ce min komai ba ya fito daga falon ya sauko stairs din ya nufi gurin wata mota dake fake kusa da inda nake zaune.
“Tana nan ciki”
Ya fada bayan ya bude motar. Unkurawa nai na tashi na nufi kofar falon na shiga ina takawa a hankali saboda abu nake jin kamar zai zubo min. Na yi mamakin karamci da sakin fuskar da na tarar a fuskar Hajiyar gidan ina yin sallama ta amsa min tana min sannu da zuwa kamar ta san ni, Namra na ganina ta taso da sauri ta nufo inda nake tana dariya.
“Momy”
Rumgumeta nai na lumshe ido.
AHMAD POV.
Da gangan yake son ya shiga motarsa ya yi tafiyarsa saboda kar ma mahaifiyar yarinyar ta ga fuskar yi masa godiya ko yi masa wata maganar. Ji yake kamar ya fada mata bakar magana son ransa aka my wufintar da yar da tai amman ba shi da damar wannan tun da shi ba uban yar ba ne kuma ba shi da alaka da ita. Ko ba komai dai ya san hankalinta ya tashi tun da ga shi har tana zubar jini.
Tun kamin ya karasa gate aka bude masa gate din, ganin wani tsaye da mota a bakin gate din gidan yasa ya tsaya ya sauke gilashin motar yana kallon Abdulhamid da na shi gilashin yake sauke.
“Malam lafiya?”
“Wata yarinya muke nema aka ce tana nan gidan mun kira number da aka ba da a sanarwa muka jita a kashe shiyasa na zo”
“Kai ne mahaifinta?”
“No ni ne dai nake auren mahaifiyarta”
Abdulhamid ya amsa kai tsaye, sai Ahmad ya kalleshi da kyau sannan ya dauke kai.
“To ka tsaya nan za a fito maka da matarka”
Ya karasa yana kallon wayarsa. Number sis dinsa ya lalubo ya aika mata kira, in few seconds tai picking.
“Sis ki fadawa matarta mijinta yana jiranta a waje”
“Okay Ammn bro bleeding ta ke, ya dan jira ta shiga bandaki”
“Ki fada mata na ce”
Yana fadar haka ya kashe wayar ya karawa motarsa wuta ya hau titi, Abdulhamid na zaune cikin wata mai kama da Ahmad din ta budo karamar kofar gate din ta leko shi daga can cikin motar da yake zaune tace.
“Kai ne mijinta?”
Abdulhamid ya gyada mata kai.
“To ka dan jira ta fito tana bleeding amman ta dan shiga toilet ne”
“Ta ji ciwo ne?”
“No i think ta samu miscarriage ne... ”
Ta fada tana dan zare.
“Miscarriage...?”
Ya maimaita.
“Yes ban dai tabbatar ba, amman kasan idan am samu tashin hankali yana iya causing wannan matsalar, amman ba lallai ne ya zube duka ba, amman dai shawara ka kaita asibiti yanzu dan tabbatarwa”
Tun da ta fara yake kallon yadda take ta zuba masa zance har ta gama, daman daga ganinta irin yan matan nan ne masu surutun fadi baa tambaye ka ba.
“Okay”
Ya amsa mata zuciyarsa cike da mamaki, kai ta gyada masa sannan ta juya ta koma ciki, kamin ta isa falon wayar da ke hannunta tai ringing alamar kira. Soul mate ne rubuce a saman screen din, murmushi ne ya bayyana a fuskarta jikinta har rawa yake ta kara wayar a kunnenta sannan ta nufi wani bangare na gida cike da shauki tana amsa wayar.
HALIMATU POV.
Ban lura da jini dake zubo min ba har sai da na zauna a saman manyan cushion din dake falo, shi ma saboda Hajiyar ta yi magana ne.
“Subhanallahi kin ji ciwo ne?”
A lokacin da na duba sai na lura da jinin ya bata duk sawun kafata yake jini ya bata gurin. A iya sanina dai ban ji ciwo ba ban fadi ba balle na ce na ji ciwo ne,
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 15 Chapter of 55