ka lissafa na shekara nawa ya kama zan turawa abokina number ka sai ku yi magana”
Be jira Yusuf din da ya kira wayar ya kashe ba, balle har ya saurare abunda zai fada ya kashe wayar, yana kallon Hajiyarsa zai yi magana ta tari numfashinsa.
“Har yanzu ba a daina biya Vip din nan ba? Shekara nawa Gwarzo? A yanzu ka gama maganar cewar ka girma, ni nasan abunda na ke ai na san waye kai”
“Ba haka ba ne Hajiya, abunda kika kasa ganewa freedom din danki, Hajiya kin kasa bari na yi komai kamar ko wane namiji, kin ki aminta na zauna a gidan kaina, kin hana auren duk yarinyar na kawo, ko fita nai idan na wuce ka'idar da kika ba ni sai kin nuna bacin ranki ko kuma ki nuna min hankalinki ya tashi ba ki san inda na ke ba, duk yadda nake son na fita na fira a waje na wuce 9 ko na kai 10pm sai ki ce min ba haka ba.
Exclusive City, a nan na hadu da Halima, a kujerar da nake biya a yanzu a gurin na same ta zauna, kin sani Hajiya every week muna zuwa gurin mu sha iska, and ta taba fada min ita take biyan gurin ko da bata zo ba, and after mun yi aure ita ta cigaba da biyan gurin, duk yadda na so na cigaba da biya sai ta hana ni, she once told me na bari sai idan bata da rayuwa sannan na cigaba da biya, and nai mata alkawari daga lokacin da na auri wata macen ba zan sake biya ba, alkawarinta nake kokarin cikawa Hajiya gurin nan yana da muhimmanci a gareni saboda mahaifiyar Namra, ko rai aka bata mata a gurin take zuwa tai kuka, idan kika mata wani abun a gurin take zuwa ta zauna tai bacin ranta ta gama sannan ta kira tace idan na taso daga office na biyo ta nan na dauke ta, wani lokacin kuma da kaina nake zuwa nemanta a gurin, ni kaina a yanzu ko anjima ko wani lokaci na kan je can na zauna kuma na samu natsuwa kamar tana raye... ”
Ya yi shiru idonsa tab da kwalla, uffan Hajiya ba ta ce ba har ya mike tsaye ya saka wayar aljihun shaddarsa da ya zuba hannayensa aljihu ya nufi upstairs. Wani irin abun na rashin jindadi ke masa yawo a zuciya, haka yake samun kansa a duk lokacin da ya tuna da matarsa Halima, wacce yake yawan fada mata cewar daga ita ya gama so, mace da yake ganin babu mai hakurinta da kirkinta a duniyar nan.
Ajiyar zuciya ya sauke sau uku zuwa hudu sannan yaja wani dogon numfashi ya busar a bakinsa. Ya kai hannunsa ya murda kofar dakin Baby Namra ya tura ya shiga ciki. Agaban plasma take zaune rike da drawing book da pencil a hannunta tana drawing wani bird da ake nuna a kids channel. Daga bakin kofar ya tsaya yana kallonta zuciyarsa fal da kaunar yarsa, sannan ya karaso kusa da ita yana ayyana abubuwa da dama akan rayuwarsa da nata.
‘Ko da na ayi aure zan yi ne kawai saboda ke, saboda ni da ke mu samu kulawa amman ba dan zan taba son ko wace mace a duniyar nan ba’
Kanta ya shafa yana murmushi kamar yadda ita ma ta dago ta kalleshi tana murmushin.
“Daddy what”
“Ba komai”
Ya fada yana cigaba da kallonta, ita kuma ta maida hankalinta gurin tv ta cigaba da abunda yake. Wayarsa ya ciro ya nemo number Rayyan.
“Rayyan”
“Ranka ya dade”
“Yusuf ya kira ni wai kudin wata sun kare, na ce masa za ku yi magana akan na year sai ka bashi zai fi”
“Okay amman ban gane Yusuf din ba”
“Wanda yake Exclusive City, kudin Vip nake nufi”
“Okay ina da number shi ai bari na kira shi yanzu”
“Okay ya fada maka ko nawa ne na shekara sai na bashi”
“Consider it done”
Daga haka ya yanke wayar ya cigaba da kallon abunda yarsa take zanawa.
HALIMATU POV.
daga karshe na yanke shawarar fadawa Abdulhamid gaskiya, na san duk yadda zai ji zafi da tashin hankali ba zai kai kamar lokacin da abun ya faru ba, kwana biyun nan na lura yana cikin damuwa wata kila saboda abunda Abdallah yai masa ne a kwana baya duk da be fada min ba amman ni kaina na lura da hakan, abunda zuciyata take yawan fada min idan ban fada masa gaskiya ba, idan ya ji a wani gurin ba zai ji dadi ba ba kuma zai fahimce ni ba. Amman kuma ta ina zai ji? Wa zai fada masa bayan babu wanda ya san wannan sirri daga ni sai Allah sai kuma kawata Hajara?
Doyar da nake ferayewa na aje na rike wukar kamar ita ce zata sama min mafita.
“Zan fada masa gaskiya, ina jin kamar ba zan samu peace of mind ba idan ban fada masa ba, ina jin kamar na ci amanarsa ne”
Ni kadai nake magana da kaina a kitchen kamin na aje wukar na wanke hannuna saboda wayata da na ji tana ringing. Cikin hanzari na nufi inda wayar take, a lokacin da na kai hannu na dauki wayar sai na kasa picking din call din ganin number mai kiran duk kuwa da ba suna, Aminu ne na san ba wata magana mai dadi zai fada min ba, wata kila haukansa zai min ko kuma ya min gargadinsa na iska da ya saba, sai da ya jera min four miss calls sannan na daga, nai masa shiru tare da hade rai kamar yana a gabana.
“Hello Halima”
“Ya akai?”
Na tambaya ina kara hade fuska kamar ance yana ganina.
“Sai an yi wani abun zan kira? Alaka fa har yanzu bata yanke a tsakaninmu ba saboda yara”
“Babu wata alaka a tsakanina da kai Aminu, kuma bana fatar wata alakar ta sake kulluwa a tsakaninmu, wacan da mu kai a baya ma ka dauka cewar labari ne”
“Ta wuce labari Halimatu tun da har kika haifa min yara hudu, maza biyu mata biyu Al-hamdulillah, yanzu ma kira nai na tambaye lafiyarsu, kuma na ji idan akwai abunda suke bukata idan zan taho musu da kaya sai na siyo musu”
Duba wayar nai dan tabbatarwa idan har number Aminu ce da gaske ko kuma a a. Kamin na maida wayar a kunne na ya kira sunana ya kai sau uku cikin tausasshiyar murya kamar ba shi ba.
“Lokacin da nake gidanka ma baka damu da tambayar lafiyar yayanka ba, sai yau? Ko kunya baka ji ba? Yarana ba sa bukatar komai daga uba irinka Aminu, mahaifiyarsu ta ishesu kuma zata iya yi musu komai, karka sake kirana domin ni matar wani ce a yanzu”
Ban jira abunda zai ce ba na yanke wayar, mamaki fal a zuciyata wanda ya kasa boyuwa har ya bayyana a fuskata, sake duba wayar nai a karo na biyu, neman dalilin kiran Aminu na ke a wannan lokacin na rasa? Me yake so? Ko kuma na ce mi yake kokarin aikatawa? Me zai saka ya tambayi yaransa? Gaba kaina sai ya kulle har na girkin na gama ban raba dayan biyu ba, ko dai Aminu yana da wata manufar akan yaransa ko kuma yana shirin lalata min aure ne.
Abdulhamid be shigo ba sai bayan sallah magariba, na masa sannu da zuwa kamar yadda na saba na raka shi har daki na hada masa ruwan wanka domin na san wanka ne abunda mijina yafi bukata a duk lokacin da ya dawo daga gurin aiki. Kamin ya fito na jera masa abinci da ruwa mai sanyi sannan na fiddo masa da jallabiyarsa, da kaina na karbi karamin tawul din na natse masa jiki sannan na shafa masa mai sannan ya saka gajeren wando ya dora Jallabiyar sama. Zaunawa yai ni kuma na soma zuba masa abincin ina ta kallon yanayinsa kamar yadda na lura da kwana biyun nan ya fiye kallona.
A tare muka soma cin abincin kamar yadda muka saba sai da na tabbatar ya kusa koshi sannan na fara bijiro masa da maganar.
“Hubby Akwai wata magana da nake son mu yi mai muhimmanci....”
Tarar numfashina yai.
“Ya jikinki....? Na manta dazun da muka tashi ban tambaye ki ciwon marar ba”
Wani dif na ji numfashina yai dogon zango, kamar wacce zata suma sannan ya dawo min kamar an jefo shi.
“Na ji sauki, akan hakan ne nake son mu yi magana”
“Uhm ina jinki”
Yadda yai maganar da yadda ya fuskance ni sai ya saka ni tsoro da fargaba kwarjinisa duk sai ya cika ni, har na kasa furta komai.
“Ina jinki”
Spoon din hannuna na aje na kama hannunsa na rike na saka idona cikin nasa.
“Ban san yadda zaka dauki abunda zan fada maka ba, ban san ya za ka ji a zuciyarka ba, ban san wani irin kallo za kamin ba, za ka iya cigaba da zama da ni akan kaddarar da ta same ni ko a'a, ban sani ba iyakar abunda na sani shine bana da kwanciyar hankali idan ban fada maka.....”
Idona ne ya cika da hawaye sai nai saurin kawar da fuskata daga barin kallonsa.
“Me kika aikata?”
Yawun bakina na hade na sake kallonsa a karo na biyu sannan na ce
“Ban aikata komai ba, darajata aka taba....!”
“Ban gane ba”
Shiru nai na kasa cewa komai sai hawaye na ke shar kamar ba gobe, shi kuma bayan kallona babu abunda yake.
“Zaka iya tuna lokacin da ka tafi Abuja karbar wasu takardu? Ka bar ni ni kadai?.....”
Cikin natsuwa irin ta masu gaskiya na zayyana masa komai, ba natsuwa irinta ta masu kwanciyar hankali ba, kallon kallo muka ko yi ma junanmu akuya kallom kura, idona na hawaye ina kallonsa, yayinda shi ma yake min kallon da ban san na minene ba, yarda ko akasin hakan ko kuma tausayi? Sosai nake Kallona na kasa dauke idona daga kansa, so nake ya fada min cewar ya aminta da ni tausayi da kulawa da kauna nake son gani a fuskata, so nake na ga idonsa sun cika da hawaye saboda mu yi kukan a tare mu yi jumamin a tare.
Be ce min komai ba, be kuma daina kallona ba, be nuna min wata alama ta yarda ko akasin hakan ba, ban tsinka jimami a idonsa ba balle har na iya hararo tausayi a zuciyarsa.
Ni din ce da kaina na tsargu na mike tsaye na bar masa gurin, ina jin zuciyata na min wani irin zafi kamar zata fashe, idonuwana kuma suna ta min yaji saboda hawaye daya hana ni gani daidai. Dakina na dawo na kwanta saman gadona na mika hannuna na janyo fillo ya dora kaina dayan hannun kuma na rika shafa gadon da shi kamar ban san abunda nake ba, kwancin ya gagareni sai na sauko na zauna a kasa na dora kaina a saman gadon.
Uwa ce ni, amman a yau ji nake kamar ace akwai wata uwar a kusa da ni ta rarrashen ta fada min komai zai wuce, ina son naji wata kalma mai dadi ina son na ji an fada min cewar wata rana zan yi dariya wata rana zan yi farinciki, ina ma a ce Mama ta san da maganar nan da ita kadai zata iya ba ni hakuri ita ce kadai zata taya ni mu yi kuka tare kamar yadda nai da Namra.
“Kaicon ki Halimatu? Wace ƴa ce za a yi mata fyade kuma ayi ma uwarta? Nai kukan yata kuma nai nawa? Yau kenan ya gobena zata kasance?”
Mikewa nai tsaye ina kara magana da kaina kamar wata tabbabiya.
“Ya isa shikenan komai ya wuce, abunda ya faru ya riga ya faru ba zan iya canja shi ba, ba kuma zan iya goge shi ba, shikenan ai kaddarata ce wannan”
Ina kaina nan na fadi kasa zaune na fashe da wani irin kuka da ban san ta ina hawayen ke fito min ba. Na kan yi kuka har na samuwa natsuwa ko kuma na samu sukuni amman a yau sai na nemi natsuwa da sukunin na rasa, kukan ya ko ya tsaya min kamar yadda hawayen ma ce min sallamu alaikum. Wani kalar sara na ji kaina na yi idonawa har rufewa suke saboda ciwo, har kuma lokacin hawayen ba su daina min zuba ba. Karfin hali nai na tashi na shiga kitchen na dauko flask din na hadawa kaina tea da cup nai ta feta har ya sha iska sannan na kurba kadan, wani abun mamaki sai na kas hadewa kamar wacce tasha wani abun mutuwa, kuka ya subuce min.
‘Ke fa uwace Halimatu, idan Namra ko Amal ko Adnan ko Amir suka shiga damuwa gurinki za su zo, ke za ki sama musu mafita, so be a strong woman....’
Shine abunda zuciyata yake fada min, kai na gyada ina karfafawa kaina kuiwa sannan na shiga bandaki nai wanka har kan nawa da ke ciwo sai da wanke dan kaiwa na samu salama. Daure da tawul na fito na nufi gaban madubi na zauna ina ta kallon kaina, hawayen idona be daina zuba ba kamar yadda ruwan kaina suke zuba. Ina jin motsin shigowar Abdulhamid gabana ya yanke ya fadi, daga jikin kofar dakin ya tsaya yana kallona.
“Amman Halima ba su bar wata alama da za a gane cewar yan fashi sun shigo gidan nan ba? Ba su fasa komai ba? Ba su dauki komai ba? Ba su harbi kowa ba? Kuma duk a unguwar nan ba su shiga ko'ina ba sai nan? Kuma ba su zo ba sai ranar da bana nan?”
Ta cikin madubin na aika masa da kallo sai murmushi ya bayyana a fuskata, still hawaye na sauko min.
“Wacce zan fara amsawa a cikin tambayoyinka?”
“Halima babu yadda za ayi 6arawo mai makami ya shigo gidan nan be bar wata alama da zata nuna cewar ya shigo ba, and if gaskiya ne miyasa ba ki fada min tun farko ba sai yanzu, and miyasa kika yi kokarin zubar da cikin? Ba ki fada min ba sai da kika fara gano cewar na gane halin da ake ciki shiyasa kika kirkiri wannan? Na kasa yarda cewar ke ce Halima!”
Wannan karon juyowa nai na fuskance shi.
“Ni din ce dai Abdulhamid, ka yi tunani iya yadda zuciyarka ta kawo maka, Halimatu ce! Karka damu wannan din ma yana cikin kaddararta, na yarda wani sabwar kaddarar ce ta fuskance ni kuma ta bude min sabon shafi, na shirya karbar ta da hannu biyu, na sani bakinciki baya taba dawwama, kamar yadda jindadi ba ya dawwama, ko dai bakincikin ya tafi ya bar ni, ko kuma ni na mutu na bar shi, kuma gaskiya a duk inda take gaskiya ce zata bayyana ko da bayan raina...”
Takowa yai ya karaso kusa da ni ya dafa ni ya tayarda ni tsaye ya kalle ni da idonsa da ke zubar da kwalla.
“Saboda ina kaunarki na aureki, har ga Allah na yarda da ke..... amman zuciyata ta kasa natsuwa da wannan, duk wani kuduri da nake da shi akanki ne, duk wani buri da nake da shi akan ki ne, na san kin yi jihadin aurena bayan kin san bana iya komai, wannan kadai ya isa ya nuna cewar kina kaunata, amman be isa ya wadatar da cewar za ki iya tsare kanki ba, wannan abun da ya faru laifina ne na cutar da ke, taya son rai yasa na cilasta miki aurena bayan na san ba zan iya sauke hakokinki ba, komai kika aikata ba ki yi laifi ba Halima saboda ni ne ba mutum ba, da ace ni din namiji ne kamar kowa da duk hakan be faru ba da baki rasa komai ba”
Hannayensa ya kai ya riko fuskata ya matso da tasa fuskar daf da tawa yana hawaye kamar yadda ni ma nake.
“Wannan sirrinmu ne, babu wanda zai ji? Karki fadawa kowa mu bar wannan a tsakaninmu, na miki alkawari ba zan ta a fadawa kowa ba, babu wanda zai ji wannan abun daga gareni, kuma zan cigaba da zama da ke kamar yadda muka saba, na sani ni ma wannan jarabawata ce, and i think this is the only way da zan iya repay na aurena da kika a yadda na ke marar lafiya, saboda Allah ya kaddaro min haka a rayuwata, na yafe miki har Allah na yafe miki kuma ina fatar Allah ya yafe miki....!”
Yana kaiwa nan ya hade yawun bakinsa ya dauke hannayensa daga fuskata ya juya yana cigaba da hawaye ya fice. Ban yi zaton akwai wani sauran karfi a jikina ba, a take kafafuwana suka fara rawa sai gani a kasa zaune jikina na ta rawa kamar wacce ta fito daga cikin kankara.!
ABDALLAH POV.
Cikin wani irin bachin rai ya shigo gidan, tun daga yanayin parking dinsa ma ya isa a gane hakan balle kuma idan a kai arba da fuskarsa, zuciyarsa har wani bugawa take da karfi kamar zata fito.
Dukan yaransa suna falo kasancewar yau Thursday babu islamiya school, suna masa sannu da zuwa amman be amsa musu ba kai tsaye ya nufi dakin Mahaifiyarsu. Tana zaune saman gado tana waya ganinsa da kuma yanayinsa yasa ta katse wayar tana kallonsa.
“Me yake damunki Suwaiba?”
Da karfi ya aika mata da tambaya sai da hantar cikinta ta kada.
“Me na aikata?”
“Ba ki san abunda kika aikata ba? Ba a nan muka gama maganar Halimatu ba? Akan me za ki dauki wannan maganar ki kaita social media a page irin wannan?”
“Ba ni bace ni ban kai komai a page ba.. ”
“Ba ke bace wacece? Taya za asan da labarin idan ba ki fada ba? Har da sunan Namra? Da maganar School fees? Haka kawai ki dauki maganar da an riga an yi ta ki saka a media? Wace irin shawara kike nema? Kin san mutane sai zagina suke, a ina za su sama miki mafitar? Kina tunanin idan Halima ko Abdulhamid suka ga wannan ya za su ji? And look at the way da kika fadi labarin is like zargina kike ma? Kin ja ana ta tsina mana alrbaka ni da ita”
“Maganar kenan Halima Halima....”
Ya kara matsowa kusa da ita yana nuna mata wayarsa da ke hannunsa.
“Yes Halima Halima, Halima yar uwata ce, kuma ni ba mazina ce ba ne, ban nemai matan waje ba ma babu yadda za ayi na nemi yar'uwata yar'uwar ma matar dan'uwana, ko a lokacin da Halima take gidan Aminu ban neme ta ba balle yanzu da take auren dan'uwana, ni ba mahaukaci ba ne kuma na jahili ba ne ba zan taba neman aikata Zina da Halima ba har abada! no matter how much I love her, ki shiga hankalinki karna sake jin sirrin gidan nan a media”
Yana fadar hakan ya juyawa ya fice daga dakin cikin bacin rai. Second to last sentence na sa ya fi komai rudata ya yanke mata hanzari kuma ya jefata a duniyar tunani.
‘No matter how much I love her....’
Those that means Abdallah yana son Halimatu? Zargin da yan comments suke ya zama gaskiya kenan? Cewar da suke yana son ta ne wasu kuma na fadar cewar yana tarayya da ita ne ya zama gaskiya kenan? Ada kam sam ita bata kawo ma kanta wannan tunanin ba, ta fi zargin ko Abdallah yana son kanenta ne, amman yanzu kam gaskiyarta fito. Da sauri ta kunna data ta shiga page din da ta tura neman shawara ta shiga kara duba Comments din followers.
_Al-hamdulillah, mun dawo fatar dai Yan Team Halimatu da Abdullah da Abdulhamid da Ahmad har ma da Aminu ba su yi fushi ba 😊_
7/21/21, 10:44 PM - Buhainat: https://chat.whatsapp.com/C40KoSeXq9l35nIiFXS1Rz
*GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
2️⃣3️⃣
Na kan dora komai a mizanin kaddara, na yarda dukan abunda ya same ni ko zai same ni rubuttacen al'amari ne daga gurin mahaliccina, wani be isa ya goge min ba kamat yadda ban iya na yayewa kaina ba.
Wannan ma yana cikin kaddararki Halimatu, haka zuciyata take yawan fada min kuma ina samun natsuwa sosai idan na tuna cewa ko wane abu da izinin Ubangijina yake samu na. Iyakar kokarin da nai na danne zuciyata ne daga kokarin aikata wani abu marar kyau wanda wani bangare nata yake hararo na ke ganin kamar mafita a gareni. Tun daga lokacin ba mu sake hada shimfida da Abdulhamid zai ba, ma'ana dai be sake leko dakina ba kamar yadda ni ma ban sake taka kafata dakinsa ba matukar yana a cikin gidan, ban fasa masa girki ba be fasa ci ba, ban kasa mika masa ko wace irin gaisuwa ba, sannu da dawowa, Allah ya tsare daman halina ne. Sai dai ban sake ganin walwalar fuskarsa ba kamar yadda walwalarsa ta hana tawa walwalar.
Idan ina zaune a falo baya zama, idan kuma yana zaune na zauna sai yai kamar ya tsargu a take zai tashi ya shige dakinsa.
Ban taba ganin laifin Abdulhamid min akan wannan ba, idan na saka kaina a matsayinsa ni kaina na san kwatankwacin abunda zan yi kenan, ba lallai ne ya gasgata ni ba, kamar yadda ba kowa zan fada haka ya yarda ba, sai dai abunda yafi min ciwo kallon da yake min na cewar na ci amanarsa.
Ina ji ina gani zaman gidan yaki yai min dadi, na kasa sakewa, kwanciyar hankali yai min kwara walwala ta yi min bankwana, kuka da damuwa suka kwankwaso min kofa.
Har ta kai bana iya bachi idan lokacin bachin yai, sai dai na raya dare da sallah ko kuma na zauna nai ta kallon sillin ko da kuwa bana tunanin komai bachin ba zai dauke ni, da rana kuma sai na tsargu ina ganin kamar ni ce kadai nake cikin matsala. Da kaina na fita chemist din dake unguwar na siyo maganin mura na ruwa a duk lokacin da na ji ina bukatar bachi sai na sha, wani abun mamaki a take bachi zai dauke ni kuma sai na manta da duk wata damuwa dake tare da ni.
Da dare kawai ba, da rana ma idan na ji damuwar ta matsa min na dan kan sha sai kuma na samu salama da natsuwa, na sani akwai illa abunda nakr sha, kuma na san ba abu ne mai kyau ba, mace kamar ni mai yaya hudu ace na buge da shan kayan maye domin na samu bachi, wannan ma yana saka ni damuwa sai dai babu yadda na iya idan ban yi hakan ba ban san abunda rashin bachin zai janyo min ba. Gaba daya yanayi na ya canja ni kaina na sani, bana sakewa kamar da ga ciwon ido ya saka ni a gaba har ta kai bana iya daga idon sosai.
Tun lokacin da abun ya faru ban sake fita da sunan zuwa unguwa ba ko wani gurin, Hajara ma ban sake labarta mata komai ba, a ganina duk wanda zan fadawa ba zai sama min mafita ba dan haka babu amfanin fallasa sirrin nawa.
Yau ma kamar jiya ta kama weekend sai dai yau Sunday ba Saturday ba, Abdulhamid tun safe ya fita kamar yadda ya sabawar kansa yanzu da fita ranar weekend ya wuni a wani gurin sai dare zai dawo, bayan da can ba haka ya saba ba. Lamarinsa na ya bani tausayi ta wani bangaren kuma sai ya bani tsoro na kan yi tunani anya ko wace mace zata iya sadaukarwar da nai? Auren mutum kamar Abdulhamid a lokacin da tawa kaddarar ta same ni sai ya juya min baya? No be kamata nai wannan tunanin ba, shi ai ba shi da lafiya rashin lafiyarsa babbar damuwarsa ce sai kuma ni na kara masa wata, ya fa kamata na gane wani abu a duk lokacin da wani ya rabe ni sai wani abu marar kyau ko kuma na bakinciki ya same shi, misali kamar Kabir ko yana ina ma yanzu?
Ni kadai nake zaune a falona ina ta sake sake da tunani kala kala wasu masu amfani wasu kuma marar amfanin. A tsorace na kalli kofar falon saboda knocked din da akai, haka nake yawan tsorata ko iska ya kada sai gabana ya yanke ya fadi. Sai da na sake jin an kwankwasa kuma na ji kamar hayani a waje sannan na tashi na nufi kofar na bude. Kanwata ce Hafiza tare da Namra da Aiman da Adnan da Amal da kuma wata yarinyar da ban waye ta sosai ba.
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 55