Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
zata kalli wannan tai mata uzuri ba? Ko da yake yanzu ba laifi Hajiya ba ne laifin Abdulhamid na yi mata maganar da nuna bacin ransa. Bayan kuma ba shi da wata hujja a yanzu domin da yana sonta kuma ta damu da ita da be sake ta da be juna mata baya ba. Hannunsa ya kai ya dafa zuciyarsa yana kara fadawa wani kogin tunanin. Wai yanzu duk wani abu da yake yi ma Halimatu janye zai yi? Ba zai sake mata komai ba kenan? Babu wata alaka da zata sake shiga tsakaninsu? Ya tambaya kansa yana jin wani irin shauki da son ganin fuskarta. ______________________ Anya Abdullahi zai iya jurewa? Da gaske Aljanun murja ne suka taso? Waye yake bibiyar Halimatu kuma a yanzu? 7/21/21, 10:45 PM - Buhainat: *GOBE NA...* By Khadeeja Candy 3️⃣5️⃣ Kasa cewa komai yai  ya tsaya a gurin kamar an dasashi, Sadi kan sai gumi yake hadawa abun ka da marar gaskiya, Murja kuma na can dakinta tana aikin ihu kamar da gaske Aljanun ne suka ziyarce ta har da wani yare take shi ba yarbanci ba, ba kuma iyamuranci ba. “A kaita asibiti, no gurin malamai” Fadi ya fada wiki wiki da ido, sai Aminu yai masa murmushi tare da gyada masa kai alamar gamsuwa. “Za a kaita” Ya amsa masa sannan ya nufi dakinsa jikinsa babu kwari, saman gadonsa ya zauna sai ya rasa abunda zai fara tunani, korarsa da akai a gurin aiki ko kuma tararda dan'uwansa tare da matarsa? Kwantawa yai saman gadon yana ta kallon silin. “Aminu ka ji tsoro Allah abunda kake mana baka kyautawa, ka rika tunawa kana da yara kana da mata, ace magidanci kamar idan ya bar gida ba zai dawo ba sai karfe daya ko biyu na dare...?” “Ke Halima a nan gidana ne ina da yancin shigowa a lokacin da nake so na fita na lokacin da na ke so, ba ki isa ki saka min doka a gidana ba” “Ba doka nake son saka maka ba, abunda kake yi nake kokarin nuna maka illarsa, duk abunda kai wa matar wani sai an yi ma taka, kuma duk abunda kai wa yar wani sai an yi wa yarka....” “Idan iskancin kike so ni ban hana ki yi ba, ga ki ga guri har kya fada min wani wai sai an yi ma yar wani matar wani dan baki da hankali” “Allah ya tsare ni, ban aikata zina ina budurwa ba ba zan aikata da aurena ba, ga hakkin yayana ga na iyayena ga na mijina ga na ubangijina? Wallahi ba zan iya ba” Ya fada tana share hawayenta sannan ta tashi ta bar masa dakin. Tuna wannan yasa shi share hawayensa ya rumgume hannayensa a kirjinsa. A yau na mallakawa murja komai, ita ke saka masa duk dokar da tai mata, be isa ya kai 9 a waje ba, be isa ya dawo gidan ba tare da saninta ba, amman hakan be hana ta cin amanarsa ba. Abunda be taba mafarki ba, domin a lokacin da zai aureta sai da yai bincike mai karfi aka tabbatar masa da tarbiyarta sannan ya aureta, sannan ya yaba da shigarta da hankalinta shiyasa ya aureta ashe be tsira daga abunda yake gudu ba, kuma ta rasa wanda zata aikata da shi sai dan'uwansa uwa daya uba daya! Wani irin abu yaji ya tsaya masa a kirji ya danne masa numfashi har sai da yai saurin kifewa a saman gadon ya runtse ido sannan ya samu  sassauci. “Allah yasa ka gane kuskuren da kake aikatawa da wuri, ko dan yaranka..... ” Maganar Halimatu ta sake dawo masa. “Na gane Halimatu na gane......” Ya fada yana fashewa da kuka wasu hawaye masu zafi suna sauko masa. Kamar an tsikare shi sai ya zabura tai saurin tashi zaune. So da gaske Halimatu take da fada masa cewar Sadi yai ma Namra fyade? Sadi ya daka masa wuka har sau biyu kenan? Yayi saurin tashi zaune, ji yai babu wanda yake bukatar gani a yanzu kamar Halimatu da yayanta. Tashi yai ya fice daga gidan gaba daya, a bakin gate ya samu abun hawa ya fada masa unguwar su Halimatu, kamin su isa duk sai ya tsawalla kamar wanda ya shekara ba ga yaranba. Sai kuma yai rashin sa'a ya tarar bata gidan wai ta tafi dauko yaran daga School. Kai tsaye Scul din ya wuce a can ya sameta ta tana kokarin taron napep tana rike da hannun yaranta. Sai a lokacin yake jin rashin kyautawa ta ya zai barta ita kadai tana daukar responsibility ba yaransa bayan yana raye? Gaba daya sai jikinsa yai sanyi, karasa yai kusa da su, kallo daya tai masa ta dauke kai sai ya koma gaba Namra ya risina ya kai hannu ya shafa fuskarta yana murmushi. “Daddy ina wuni?” Kasa amsawa yai sai ya rumgume ta hawaye na sauko masa. Tun yana yi a hankali har ta kai mutane na kallonsa. “Miye haka? A cikin jama'a muke fa, ka sake ta gida zamu je” Sakinta yai ya dago kai yana kallon Halimatu wacce ke watsa masa wata uwar harara, kamin ya kai hannu ya shafa kan duka yayansa sannan ya mike tsaye ya share hawayensa, ita kuma taja yaranta sukai gaba, yana tsaye a bakin titin yana kallonsu har suka samu Napep suka shiga suka bar shi a gurin. Shi ma achaba ya hau ya dauki hanyar family house dinsu. Ko da be fada ba kana ganinsa kasan yana cikin tsakanin damuwa, kamar yadda mahaifiyarsa ta karanta a fuskarsa. Gashi ya shigo mata har dakin bachinta babu sallama balle gaisuwa. “Aminu lafiya kake?” A lokacin daya dago kansa sai hawaye ta gani a fuskarsa. “GOBENA Hajiya tunani nake yadda zata kara kasancewa....” “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, miya faru kuma?” “Hajiya yanzu na gane, ba dan na rabu da Halimatu na rabu da arzikina ba, saboda na cutar da ita ne, hakkinta ba zai bar ni ba, samun irinta a duniyar nan sai an tona, kullum nasiha take min bata tana nuna min gazawarta, da gangan Hajiya da gangan nake kauracewa Halimatu sai nai wata uku hudu ban neme ta ba kuma a haka take hakuri da ni......” Ya fada yana fashewa da kuka kamar mace har zaman kujerar ya gagare shi sai da ya sauko kasa. Sai a yanzu yake jin wani irin zafi da bakincikin abunda Sadi yai ma yarsa da kuma matarsa ashe akwai zafi wani ya kusanci matarka, sai yanzu yasan zafin da uba yake ji idan aka lalata masa Y'a. “Aminu ka fada min abunda yake faruwa mana, ka gada min hankali” “Hajiya yau an kore ni gurin aiki... Amman bashi ya fi bata min rai kamar kama Sadi da nai da Matata Murja.... ” Idan akwai abunda yafi sakin baki da mamaki sai da Hajiya ta yi shi. “Kasan me kake fada kuwa Aminu?....” A nan labarta mata komai idonsa ko gani basa yi daidai saboda hawaye. A take Hajiya ta saka kuka. “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, yanzu Sadi da matarsa da yaransa zai yi matar dan'uwansa haka?” “Hajiya kin tuna lokacin da na saki Halimatu saboda ta fada min Sadi yai ma Namra fyade? Daga ni har ke ba mu tsaya mun yi tunani ba....” Hajiya ta dafe zuciyarta tana hawaye. “Indai har haka ne Sadi ba zai gama lafiya ba, wane irin da na haifa?” A wunin ranar daga Hajiya har Aminu wuni sukai cikin jimami da damuwa, sai da Dare Sadi ya shigo gidan shi ma dan Hajiya ta kira shi ne, har lokacin ba shi da natsuwa da kwanciyar hankali, Hajiya ta rufe da fada tana kuka, amman sai kokarin kare kansa yake. “Hajiya Wallahi Aljanunta ne suka gaso kuma tana fisge fisge shiyasa na kaita daki na kwantar da ita” “Kaji tsiron Allah Sadi idan babu duniya akwai kiyamar Allah, wace irin lalacewa ace kana tare da matar aure mai auren ma matar yayanka? Bayan kai ma kanka kana da aure da yara? Ko ka amsa ka aikata ko kar amsa wannan maganar zata tsaya a tsakaninmu daga ni sai kai sai Aminu, ba zamu fitar da wannan sirrin ba” Duk wani abu da Hajiya ke fada, Aminu dai be ce uffan ba, kansa n kasa har sai da Sadi zai tashi sannan ya dago ya kalleshi. “Tun yaushe kuke tare?” Jimmmmm yai kamar ba zai amsa ba, sai kuma ya ce. “Tun kamin ka aureta, class mate dita ce” “Allah yai maka yadda kai min” Ya fada masa sannan ya mike ya fice daga dakin ya bar su daga Sadi sai Hajiya. HALIMATU POV. Tsawon wata uku kenan ban sake saka Abdallah a ido na ba, hakan kuma ba karamin saka ni yai a damuwa ba, na rubuta masa sakon karta kwana na bashi hakuri amman be maido min da amsa ba, na kira wayarsa several times be yi picking ba. Ba zan iya zuwa gidansa saboda na bashi hakurin abunda ya faru ba, sai dai ban abunda zan masa da zai saka ya sauko daga fushin da yake da ni ba, a iya zamana da Abdallah be taba fushi da ni na tsawon lokaci haka ba, ko da ban bashi hakuri ba yana saukowa da kansa balle har na bashi hakuri. Da kaina na zauna ina ta tunani da tariyo abunda ya faru so nake na gane idan maganar da na fada masa mai zafi ce sosai da har zata saka ya gujeni haka. Amman kuma ai na huta da shi, ni da nake neman maraba ma? Dan ya nesance ni a yanzu ai na huta ko? Wata zuciyar ta aika min da tambaya, a maimakon na jidadi sai na ji akasin hakan, wata kila saboda na dan saba da shi ne shiyasa na ji babu dadi a yanzu, wata kila kuma saboda abunda na fada masa ne yasa nake jin babu dadi, haka dai nake ta sake sake na ni kadai na kulla wannan na wance wacan.    Yau ma after na shiryawa yarana sun tafi school na shirya na fito da zimmar leka gidan kawata Hajara wacce na dade ban ziyarce ba, a yau can nake son zuwa yau so nake ba bude nata cikina ina son na ji irin shawarar da zata ba ni ina son na ji yadda zata kalli abun. Na yi kyau matuka ni kaina na san na yi kyau domin bakar abaya ce a jikina wacce take yi ma ko wace mace kyau, gashi na tsirka da jan mayafi, sam ba zaka gan ni kace Halimatu bace domin na rame sosai ni kaina ina ji a jikina domin yanzu bana jin nauyin jikin kamar da kusan dukan tufafina sun min yawa. Napep na tara na shiga na fada masa inda zai kaini ina cikin napep din ina tunani ban san mun isa unguwar ba har sai da mai napep din ya tambayi inda zai sauke ni. “Idan ka dan kara gaba kadan ya isa” Na fada masa ina kallon wata motar da nake kyautata zaton mu take bibiya, ko na nace ni domin tun daga lokacin da nai arba da wannan mutumen ba kasafai bake fita ban ga mota tana bibiyata ba, kuma ba kalar mota daya ba, wani lokacin zai sauke gilashin motar ya kalleni amman ba zai ce min uffan ba, wani lokacin kuma ta cikin motar yake bibiyata, tun abun na bani tsoro har na fara sabawa, ban san mi yake nema a gareni ba, a iya sanina ban yi ma kowa komai ba balle ace wani ya saka ni a gaba dan ya cutar da ni. Bayan na biya nai napep din na tura gate din gidan na shiga sai da muka gaisa da mai gadin sannan na nufi cikin gidan.   Na jidadin tararda ita ba tare da kowa ba, domin ko mijinta ya fita aiki balle kuma yara da sun tafi school. Tana ganina ta washe hakora “Yau garinmu inji maki baki” Da dariya na zauna saman cushion muka gaisa sai ta tashi ta hado min abun karyawa, ban musa ba na karba daman da safen nan koko kawai na sha, sai da na ji na koshi sannan muka dauko labaran duniya har take min zancen komawa makaranta na cigaba da karatuna. “Ni yanzu ba wani karatu dake gabana, karatun da nai ya isheni aikin nake son samu, na dogara da kaina iyeyena ma suna bukatar taimako na ga yara a gabana ga kanena ga ni ni kaina, kuma kin san karatu dole sai da wanda ya tsaya maka...” Ya janyo fillon kujera ta rumgume tana kallona. “Zan tsaya miki ki yi karatu Halimatu, ko nawa ake kashewa zan kashe miki so nake ki yi karatu ki kai matakin da ko aiki zaki samu ba karami zaki samu ba sai babba wanda zai zama na har wasu ma'aikatan a karkashinki suke, ya zamana kina iya daukar nauyin yan'uwanki da ke kanki da iyayenki da kuma yaranki” “Thanks for the opportunity amman har ga Allah a yanzu bana sha'awar karatu bana jin ma kwakwalwata zata iya daukar wani abu a yanzu” “To aure kike so?” “Bana da kudirin aure a yanzu Hajara, kin fi kowa sanin irin kalubalen da nake fuskanta a rayuwar aure, kwata kwata Yanzu aure baya burgeni, aiki dai nake son samu saboda na dogara da kaina domin bana da mai taimaka min a yanzu, Abdallah da nakr ganin yana dauke min wani nauyi shima ya fara guduna” Fuskar mamaki tai “Kamar ya?” Ban rage ba ban kara ba daga abunda ya faru tsakanina da shi wanda nake ganin shine silar fushin da yake da ni. “A gaskiya baki kyauta ba, amman shi kuma ya dauka da zafi” “Na san ban kyauta ba, tun daga lokacin abun ke ta damuna har yanzu na ta masa sako na ta kiranshi amman be daga ba be kuma maido min da amsa ba, Wallahi abun yana da damuna” Na fada idanuwa na taf da hawaye. “Kina son Abdallah Halimatu....” Wani kallo na watsa mata a kaikaice. “Ko ki yarda ko karki yarda son Abdallah kike Halimatu kuma kin yi kuskure tun farko da kika auri Abdulhamid bayan kin san Abdallah yana sonki ga kuma tarin kyautatawar da yai ta miki, yanzu gashi zaki cutar da kanki” “No ba ki gane ba ne, ba son Abdallah nake ba” “To miyasa kike kuka saboda ya kaurace miki?” Na kai hannu na share hawayen da suka zubo min. “Ai ya kyautata min da yawa ko? So ya kamata na ji babu dadi idan ya kwaurace min ko?” “Hakan be isa ya saki a damuwa ba, akwai son Abdallah a rayuwarki wata kila ba ki sani ba, wata kila kuma kina boyewa ne kawai, so abunda nake ganin yafi kije kai tsaye ki same ni a gidansa ai ba zai kyale ki a can ba, ki bashi hakuri idan ki kai hakan kin wanke kanki” “Kina ganin idan naje matarsa ba zata zargi wani abu ba?” “Ke fa jininsa ce Halimatu, taya matarsa zata yanke alakarku? Ke wai ni yar a manta ma ban fada miki ba kinji Aminu ya saki matarsa?” “Haka Asma'u makociyata take fada min a chat, ko me hada su kuma?” Hajara ta tabe baki. “Me zai hada su kuwa ban da bakin halinsa, wace macen ce zata dauki abunda kike dauka? Ai babu macen da zata iya zama da Aminu” Na yi murmushi ina tuna lokacin da yake ce min wai babu namijin da zai iya zama da ni sai shi saboda bakin halina da sa'idon da nake masa. “Wata kila shiyasa ya fara munafurci, kin ga yadda yake kula da yaran nan a yanzu kamar ya lashe su? Wallahi idan ya gan ni har wani sunsun da kai yake kamar mazuru” “To ko so yake ya dawo dai.... ” Na tofar da yawun bakin. “Allah ya kiyaye haba Hajara ai dai kya min fatar kwarai ko? Wallahi ni yanzu ko a kafa aka daura min Aminu ba zam iya jansa ba, ke idan na ganshi har wani tashin zuciya nake ji” Na fada ina yatsina fuska sai Hajara ta saka dariya. “Balle ya ga kin yi slim kin yi kyau abunki Ma-sha-Allah” Mun dade muna fira da ita kamin na bijiro mata da zancen mutumen nan da ke bibiyata, ita ma kanta ga tsorata da lamarin har ta ce mai reporting ma yan sanda saboda gudun abunda zaije ya dawo, kuma ban ki ta taba domin dan'adam abun tsoro ne a yanzu. Na dauki shawararta na zuwa bawa Abdallah hakuri dan haka daga gidanta sai na wuce gidansa kai tsaye da kwarin guiwa na. Na dade ina knocked din kofar falon kamin matarsa Suwaiba ta bude min, muna hada ido sai yanayinta ya sauya. “Ah ah ahhh Abun kuma yanzu har cikin gida Haba Halimatu?” Ina ta tunin abunda zan fada mata sai na ji muryar Abdallah yana amsa mata. “Ni nace ta zo....” Sakin kofar tai wanda hakan ya bani damar shigowa cikin falon, sai na hango shi zaune saman sofa sanye da Jallabiya laptop a jikinsa da alama wani aikin yake. Daga inda nake nai tsaye na kasa cewa komai sai ya aje laptop din ya nufo ya ratsa gefena ya fito daga falon, sai nima na juya na fice a harabar gidan muka tsaya ni da shi, yana ta kallona kamar zai cinye ni, ni kuma na gagara ce masa komai na gagara daga ido na kalleshi kwarjinsa da kimarsa ta cika min ido ga wani uban faduwar gaba da nake ji kamar mai jin tsoro. “Kin lalata komai Halimatu, kin aikata kuskure, taya zaki auri Abdulhamid bayan kin san ina sonki? Why? Saboda ki musguna min? Haka Hajiyata ta fada min, kin san me? Da Hajiya ta fi kowa son ki saboda ina sonki kuma gana ganin kamar kina so na, daga lokacin da kika ja ra'ayi Abdulhamid a kanki sai ta lamarin ya lalace, gashi yanzu aurensa be haifa miki da mai ido ba, kuma ya haifar mana da matsala gaba dayan mu, baki tunani idan za ki yi abu Halimatu baki tunani.... ” Ya fada yana hada duka hannayensa ya daki kaina. Dagowa nai na kalleshi idona taf da hawaye zan yi magana ya tari numfashina. “Sai kuka da an miki abu sai kuka.. ” Yayi saurin juyawa sai kuma ya juyo. “Ya akai? Miyasa kika zo nan?” Na fara matsar yatsuna ina hawaye. “Zuwa nai na baka hakuri akan abunda na fada maka a asibiti wanda ya saka kake fushi da ni....” “Yanzu kin fara jin son na a cikin ranki? Shiyasa har kika damu da fushin da nake da ke? Bayan komai ya lalace?” Ya juya ya fara tafiya. “Ka yi hakuri dan Allah Wallahi ba abunda ke raina kenan ba” Juyowa yai ya kalleni “Ni bana fushi da ke ba zan iya fushi da ke ba....” Haka kawai ya fada min ya cigaba da tafiyarsa har ya shige cikin falon. Ni kuma na juyo hawaye wasu na bin wasu na fito daga cikin gidan, ina tafiya ina jin ana bina a baya a lokacin sa na waiga sai sake arba da fuskar mutumen nan da ya saba bibiyata. Faka motarsa yai ya fito ya miko min handkerchief. “Pls...” “Waye kai? Me kake nema a gurina? Idan ma sace ni za kai ni bani da wanda zai karbo ni, idan kuma yarana zaka sace ban da kudin karbo su” Murmushi na gani a kyakkyawar fuskarsa. “Zaki iya shiga motana na kai ki gida, sai ki aminta da ni” “Ba zan shiga ba, miye hadi n dake kai rista ni musulma” “Soyayya ai babu ruwanta da addini, haka dai aka fada min mai irin addinin suna da kirki da karanci ba kamar yadda na same ki ba” “Wani yayi amfani da hakuri na ya cutar da ni, wani yayi amfani da soyayyata ya cutar da ni, kai kuma kana son kai amfani da addinina ka cutar da ni, to ba zan yarda ba ban yi kowa komai ba ba zan yarda ayi ta cutar da ni ba” Ina fada masa haka na cigaba da tafiyata. “Idan cutar da ke na zo yi kar Allah ya bar ni da raina a yau” Tsayawa nai cak kamin ya juyo na kalleshi da mamaki. “Kai kuma daga ina?” Matsowa yai kusa da ni ya miko min hannunsa. “Sunana Abraham akwapo” Tsayawa nai kallon hannunsa sake sanye da manyan zobuna sai dai ba irin wadanda can ba ne na zinari wasu kala ne na dabam sai dai duka alphabet dinsu A ne. Sai kuma na kalli fuskarsa. “Ni musulma ce miyasa kake bibiyata? Zan kai report dinka a gurin police yau” “Okay” Ya juya ya shiga motarsa na yi zaton tafiya zai yi amman sai ya fito rike da wani kamin littafi yai rubutu akai ya mika min. “Sunana Abraham ga number motata nan da number wayata da address din gidana ko da sun bukaci gani na” Ni kan a tsaye da nake mamaki ya kusan kashe ni. “Waye kai....?” Sai yai murmushi ya saka hannayensa aljihu. “Za ki ba ni damar kasancewa abokinki?” Shiru da nai ban bashi amsa ba ban kuma daina masa kallon mamaki ba yasa shi sake sakar min murmushi. “Ina mika kyakkyawar gaisuwata a gurin yaranki” Sannan ya shiga motarsa yai mata key ya bar ni a gurin tsaye da mamaki.... _____________ Wake irin tunanin da na ke 🤔 7/21/21, 10:45 PM - Buhainat: *GOBE NA...* By Khadeeja Candy 3️⃣6️⃣ Na kasa jefarda takardar kuma na kasa fadawa kowa cewar ya bani takardar kamar yadda na kasa fadawa yan sanda. Shi kuma be fasa chusa kansa a cikina ba, har kara ma da bibiyata kawai yake amman a yanzu har yarana yake yi ma siyayya ta kudi mai yawa ya kai musu a scul a gida kuma ya aiko min da ita, a kullum ina fargabar idan Mama ta tambayi wanene shi wa zan fada mata ba? Bayan karyar da nai mata cewar wani ne dana hadu da shi yake min haka yai ma su Namra, amman idan aka samu akasi yarana ko kuma Mama da kanta ta ganshi fa? Duk wanda ya gan ni da kafiri zai yi mamaki abunda ya hada ni da shi ina diyar musulmai. Sai dai a yadda na fahimta kamar shima yana gudun mutane domin baya min magana a inda yakr ganin jama'a da yawa, sai idan ina a kebance kamar idan zan hau napep ko na sauka ko zanje wani gurin sai kuma da dare zai aika yace ana min sallama. Duk kuwa da ban tana fitowa da sunan amsa sallamar da yake min ba, hakan be hana shi aiko min lokaci zuwa lokaci ba, kamar yadda yake yawan bibiyata yana rokon na saurareshi. Ni kuma na kasa saurarensa saboda bana jin aminci a tare da shi wata kila saboda ba addinin mu daya da shi ba oho, sai dai a yadda na lura yana da kamun kai da taka tsantsan da kuma natsuwa wacce ba ko a musulman mu ba kowa kake samu da wannan ba.   Ba ni da wata fargaba a yanzu sai ta abubuwa uku,wannan Abraham din sai kuma Aminu wanda shi ma ya saka ni a gaba da yawan bugo min waya da sunan zai gaisa da yayansa tun yana kira ina dagawa na bawa yaransa har ta kai yanzu idan ma ya kirani sai dai na mika musu wayar su su yi magana da shi, hakan kuma be hana idan ya kare magana da su yace su ba ni wayar idan ni kadai ce ko kuma da kanen sai na yanke kiran idan a gaban Mama ne kuma na kan dauka saboda ta gargade ni cewar na daina kin karbar wayarsa ko dan darajar yarana, ina yi mamata biyaya ne kawai saboda ina gudun bacin ranta gudun kar tace ban dauki shawararta ba, amman har ga Allah bana kaunar jin sunan Aminu ma balle jin muryarsa, shi kuma yanzu har wani zillon rashin kunya yake domin wani sa'in har cikin gida yake shigowa ya gaishe da Mama da Baba sannan ya fita, ga wata bakar al'ada da ya tsiro ta daukar yaran yana tafiya da su gidansa ko wani gurin daban su wuni can sai dare zai kawo su gida. Idan na nuna zan hana sai Mama tace min ba haka ba. Wani lokacin sai dai nai ta jin haushin a zuciyata kawai amman ban isa na nuna a fili ba saboda kar mama tace saboda ita nake yi.   Na tattara komai a yanzu na aje a gafe, babu da bukakata da damuwa kamar abu na ukun nan wato neman aiki, duk inda naji wata ma'aikata ko wani kamfani sai na mika takarduna, sannan na saka addu'a a gaba

Chapter 28 of 55