zama ta yi a kan gado, ta yi juyi ta sake juyawa, can kuma ta kwanta ta yi lamooo, daga baya ta miqe da sauri ta sauka qasa ta hau cin abubuwan da aka kawo mata ba qaqqautawa, Umaimah na ta yi mata dariya.
Allah Allah take Umaimah ta dan fita ta kwashi lemukan ta sa a jaka, amma umaimah ta gano ta sai tace,
"Kar ki damu qawata kici wannan, in zaki tafi gida zan baki wasu,"
"Dan Allah? Yanzu kuna da irin wannan da yawa kenan? Ai kuwa zan din ga kawo maku ziyara akai akai,"
Dariya Umaimah ta dinga kwasa wajen Jameela.
Suna zaune mai aiki tayi kiran su akan suje a ci abinci cike da zukud'i Jameelah ta miqe, sai bayan ta yi gaba sai ta tsaya sai da Umaimah ta wuce sannan ta bi bayan ta, a table ta gan su zaune, kasa qarasa wa ta yi saboda sumar da tayi a tsaye a wajen, jiri ne taji yana d'iban ta, hankalin ta ya kai qololuwa wajen karkata wajen table din da abinda ke tattare da shi, Umaimah na taba ta dan su yi gaba taji ta taho mata gaba ɗaya kamar zata faɗi, da kyar ta tsaida kan ta ta samarwa kan ta natsuwa, qafa ta daga zata yi tafiya amma taji ta mata nauyi, idon ta kuwa ko qiftashi bata yi dan gani take kamar da ta qifta shikenan ta daina ganin abinda ke gaban ta da ya fi komai kyau a idanun ta da zuciyar ta............
[11/09, 2:28 pm] asiyahabibu93: 💅🏻 MAZAUNA GIDA 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 3:
Wasu 'yan matan tabarmi na ga suna shimfidawa wasu kuma sallaya, wasu kuwa kujerun zaman gida('yar tsugunno) suka dasa guda biyu su ka zauna da samarin nasu, Mamalo na ɗaya daga cikin wanda suka shimfid'a tabarmi domin kuwa saurayin ta Sadeeq mutumin kirki ne yana matuqar son ta auren ta yake son yi, dan ma iyayen ta sun tsaya masu wala-wala da tini ya turo, daya sako maganar aure sai Lantai tace nawa ma Mamalon take? dika-dika shekarar ta sha biyar, me zai tsinta a wajen ta? Dole haka Sadeeq ke hakura ya bar maganar ya yi ta fata da addu'ar Allah ya kai su lokacin da zata qara girma ta kai aure ya aure ta su yi zaman aure.
Qarfe 9: 45 na dare baka jin maganar kowa sai mutsu-mutsu da 'yan dareraiku sama-sama a wajen 'yan mata da samarin layin su Jameelah, soyayyar shan minti kawai ake zubawa a lungun nasu, Jameela da Babawo kamar zasu shige cikin junan su tsabar mannuwa da suka yi da juna,ba qaramin jin daɗin rigar da tasaka mai faɗi wadda ake kira da ziro hannun ka masoyi Babawo ya ji ba, hannun sa ya zura ya na ta zare idanu kamar ya biya sadakin ta.
Mamalo kuwa ran ta in yayi dubu ya baci saboda Sadeeq ba abinda yake yi mata da ya wuce wa'azi akan abubuwan da ya ke ganin matan layin na su na aikatawa, juya kai tayi ta yi fari farrr da ido sannan ta murguda baki tare da sakin siririn tsaki sannan ta ce,
"Wai kai dan Allah Sadeeq yaushe zaka waye ne? Ka duba fa ka gani kowa sai jin daɗin shi yake yi, amma kai ka wani qame a gefe wai kai ustaz, ka mori quriciyar ka tin kafin tsufa ya riske ka,haba malam ! A yi mutum gaba ɗaya shi bai san mene ne soyayya ba? ko dan kalaman nan na soyayya ni baka jiqa ni da su, ko irin yanda saurayi ke fad'awa budurwa yanda yake ji game da ita da yanda zai mata bayan sunyi aure kai baka iya ba, gaskiya ni da sake,ba zan dauka ba, ka waye kawai mu mori rayuwar mu,"
Sadeeq baki sake yake kallon ta a qalla ya bata kyawawan shekaru takwas amma yarinyar nan bata ji nauyin sa ba ta rufe ido tana fada masa yanda zai gudanar da soyayya, lallai wannan zamanin namu na cikin rud'ani, wa'azi ake yi akan yanda lamura suka tab'arb'are, fadakarwa ake yi amma kamar ba a yi.
"Yanzu dan Allah Fateema abinda kika faɗa bai maki nauyi a bakin ki ba? Ko kunyar faɗa min waɗannan kalaman baki yi ba? Iyayen ki cewa fa suka yi na basu nan da shekara biyu ko uku, ke har yanzu yarinya ce amma shine....."
"A ganin su ba ! ni fa da ka ganni nan ba abinda ban sani ba, in zaka sake jiki muci soyayya ka sake, ba dan ma ina son ka ba ko bi ta kan ka zan yi ne? ina son ka fiye da yanda nake son kaina, kuma bazan iya rayuwa ba kai ba, shi yasa ma kaji ina fada maka me nake so a yanzu, banda haka aje ka zan yi a gefe na nemi wani,"
"Innalillahi wa inna ilaihirraji'un ! me kk ce Fateemah ? Kamar ke ki ka iya fad'in zaki aje ni ki nemi wani saboda ba na yi maki muguwar soyayya? Yo muguwar soyayya mana wannan ai ba soyayyar gaskiya ake gudanarwa ba sam,Wai me ki ka dau soyayya ne ma tukunna? Soyayya fa shine na kare maki mutuncin ki ba na zubda maki mutunci ba kafin aure, inna gama tattabe ki a waje me na tanadarwa kai na a gidan? In muka gama soyayya a waje in mun je gidan meye sabo da za mu yi dan debewa kan mu kewar shekarun rayuwar mu da zamu yi a tare? Kiyi tinani, ni kam anyaaaa Fateema.... anyaaaaa?"
"Anyaaa me? Nace Anyaaaa me? Kana kokwanto akaina ne? Bari ka ji ita soyayyar nan dana ke fada maka ba fa wai wani iskanci za mu yi ba,kawai dan simba da runguma ne, ka dubi yanda Jameela suke yi ita da Babawo mana abun nasu gwanin sha'awa, ji dan Allah in muka jera da ita qirjin ta taff da dukiyar fulani, amma ni sai kace allo, gaskiya ni baka kyautamin sai da safe, ba zan zauna in sha sanyin banza da sauro ba ban amfana da komai ba sai shegen wa'azi , sai da safe,"
Cikin fushi ta shige gida bazar bazar, da matuqar mamaki Sadeeq yabi bayan ta da kallo, kanshi yayi mugun d'aurewa da abinda ya faru yanzu, sai tunani yake yi anya sanda bai samu zuwa ba ba wasu samarin dake zuwa su lallatse ta kuwa?
" Aiko da sakel, daga yanzu kullum zan dinga zuwa zance dan ba zan bar wasu banzayen su lalata min ita ba tunda ta na so na kamar yanda nake son ta,"
Tina sanda suka fara haɗuwa da ita yayi, a lokacin sun taso daga islamiyya ita da Jameelah, kula da rashin kamun kai irin na Jameela ne ya sanya bai ce ita yake so ba dik kuwa da kyaun da take dashi, amma yanzu Mamalo na so ta goge masa haddar kan shi, k'wafa ya yi sannan ya ce,
"Dik laifin wannan Jameelan ne, dan komai take yi shi Fateemana take son daukewa, zan yi qoqarin raba su kuwa inshaa Allahu dan na more wa soyayya ta cikin tsafta,"
Muryar Mamalo ya ji cike da tsiwa ta na kad'a qugu a saman kan shi ta ce,
"Wai malam baka tafi bane? Ni to ka tashi zan shiga da tabarma ta,"
Tana wani jijjiga, kallon ta yayi yayi murmushi kawai, hannu ya sa a aljihun shi ya na d'akko abinda zai bata, tana ganin haka jijjigar ta koma rausaya,tana wani abu kamar mai jin kunya, kuɗi ya d'akko a aljihun shi dubu ɗaya sabuwa fill ya miqa mata,cikin sauri kamar zata haɗa da hannun shi ta amshe ta hau godiya,
"Dan Allah ki min alqawarin daina kula dik wani saurayi in ba ni ba,"
"In dai kayi alqawarin kawon kalar wannan kullumm ba wani qato da zan dinga kulawa wannan alqawarin mamalo ne, kasan kuwa bana karya alqawari inna dauke shi,"
"Indai wannan ne kin samu, sai da safe abar qauna ta,"
D'aga masa hannu tayi suka yi sallama ta nad'e tabarmar ta, zata shige gida kenan ta kalli dai-dai inda su Jameelah suke a duhun, dariya ta ji suna yi qasa-qasa, hankalin ta ta tattara gaba ɗaya tare da qura ido qurr, Jameela ce kaɗai take iya hangota, Babawo kam bata ga ina yake ba ma a wajen sai dai tabbas ta san su biyu ne a wajen,haka ta dinga gwale ido ko zata iya ganin shi amma bata gan shi ba, a zaton ta ko ya tafi ma, dan haka kawai sai ta ɗauki hanyar yin wajen Jameelan, da sauri Babawo ya miqe daga qasan Jameela daya shige, ita kuma taja skirt ɗin ta ta rufe qafar ta ta na b'ata rai,cikin masifa ta ce wa Mamalo,
"Meye zaki zo ki wani tsaya mana akai,"
"Wayyoo kuyi hakuri dama da ban ga Babawo ba na zaci ya tafi ne, sai da safe a ci soyayya lafiya, na baki labarin gobe,"
Can qasan maqoshin ta Jameela ta amsa ta, tana tafiya Babawo ya maida kan shi inda ya fito.
Sai da ya kai wajen minti goma sannan ya fito suna ta dariyar jin daɗi, kudi ya debo canji-canji kimanin dubu biyu, ta tsaya tana kallon shi a ranta tace,
'matsiyacin banza kawai kullum sai dai ya zo ya ji daɗi dani amma ba wani kudin arziqi da yake bani'
A zahiri kuwa sai ta kyab'e baki ta ce,
"Nawa ne nan kuma? Kasan na tsani canji-canjin nan ko?"
"Sorry babyna dubu biyu ne fa shine kike bata rai? canjin ne kawai amma ai yafi na kullum yawa yau ko?"
Ɗan sake fuska tayi ta zaci yauma dubun ce, ahhh lallai dole ne ta d'agawa Mamalo kai dan a da kullum ya zo dubu ce ko dubu da dari biyar, to yau gashi an samu ci gaba.
Haske ne ya bayyana ya haske masu idanu daga ita har Babawon,daga baya hasken ya tsaya akan Jameela, mahaifin ta baya son ya daga murya aji yana magana da d'iyar ta shi,dan haka sai ya dinga haska ta yana kada fitilar.
Cike da zumb'ura baki ta tashi tana doka qafa, Babawo kuwa da sauri ya bar wajen yana kare fuskar shi.
Kewaye baban ta tayi ta shige gidan nasu wanda Soron cike yake da yaran gidan samari, suna ta bacci, haskawa yayi ko zai ga Bukar a wajen kwanciyar shi amma ba Bukar ba labarin shi, kad'a kai yayi yana nemawa yaran shi shiriya a wajen Allah, baya taba zagin su ko tsine masu, shi dai fatan shi su shiryu.
Har ya sa qafa zai shige dakin su, yaji hayaniya, ana fad'in,
"Dalla kar ka fad'o min a ka ni, kayi can ga shimfidar ka can Ramai ta yi maka,"
Bukar kuwa sai hayaniya yake yi irin na 'yan shaye-shaye, dan kuwa ba mai gane me yake faɗa, fari tasss aka haife shi kamar Jameela, amma saboda shaye-shaye ya koma baqi, musamman bakin shi da hannayen shi.
Dika-dika shekarar Bukar sha Uku amma ba irin iskanci da dabar su basu saka shi yi, dan yana qarami da shi suke amfani ya je ya masu 'yan qananun sata,sannan ya yi masu aiken siyan kayan maye, daga nan har ya fara sha shima.
Kad'a kai Baban su jameela yayi ya qarasa shigewa d'akin su dan kuwa ba zai je kallon takaici ba, tinda ya dawo gida to Alhamdu lilLAAH.
Ya na shiga ya doki qafar ta ta tashi tana gantsaro girji tare da yin hamma,
"Malam lafiya ka ke tashi na da wannan tsohon daren? Kasan nayi aiki na gaji fa gashi gobe ma zan ci gaba da aiki kamar kullum, in ban bacci da wuri ba kasan bana samun jin daɗin yin aiki na,"
"Yi hakuri dan tashi ki duban lokaci a agogon nan,"
Wani haushi ne ya kama ta, agogon ne bai iya ba ko me?
Cikin fushi ta kalla tace.
"Qarfe sha daya da rabi na dare mana baka iya agogon bane ko me?"
"Yauwaaa alhamdulillah kema kin faɗa da tsohon daren nan, sannan kin ce qarshe 11 na dare,to a tsohon daren sai yanzu yaran ki ke dawowa daga waje daga macen har namijin, ya kamata kenan? Haba Ramai, yarannan fa amana ce Allah ya bamu a hannun mu fa, Allah ya aminta damu fa kenan tunda har ya azurta mu da yara dan mu kula da su mu basu tarbiyya mai kyau, amma shine ke kike sakaci da basu tarbiyyar,ni dai Allah ya sani ina yin iya bakin qoqari na amma ba ki bani had'in kai, kin kyauta min kenan tsakani da Allah,"
Tin da ya fara maganar ta ji farkon amma qarshen bata san me yake faɗa ba, dan kuwa baccin ta ta koma a zaunen, dan indai ta shi ne kar suyi bacci ayi ta magana akan yaran wanda ita kuwa bata ga abinda suke yi mara kyau ba,ba zata iya matsawa yaran ta ba ta hana su sakewa sammm.
Malam Jameel yaji haushi kuwa matuqa amma haka ya danne, ya bi gadon nasu tare da yin addu'ar bacci ya kwanta sannan ya tofa mata itama, dan bai taba gani tayi ba shi kuma baya gajiya wajen yi mata kafin ya kwanta, cikin dakiya da jure ɓacin ran da yake ji ya ce wa Jameelah,
"Ki rama sallolin da ake bin ki kan ki kwanta dan bana jin ko azahar kin yi, in Allah ya so ya amsa, in bai so ba ya barki da abun ki, Allah ya shirye ku, kuma kiyi addu'ar bacci kafin ki kwanta,"
Cike da zumbura baki ta amsa shi.Fita tayi tayo alwala ta yi zaman ta a kan sallaya tana ta tinanin abin da ya faru ɗazu da Babawo yazo sai murmushi ta ke ta zabgawa tanashafo dik wani sashe na jikin ta daya taba.
'Gaskiya Babawo ya iya soyayya sai kace a indiyan fim'
Sai da ta dad'e a wajen sannan ta miqe ta ninke abin sallan, ta sauya kayan jikin ta zuwa na baccin data siyo a gwanjo, dan ita tana son harkar hutu, ta yi kwanciyar ta a dan bargon da take shimfidawa kalar pink, a rayuwar ta tana son ya zamana tana da d'akin ta na kan ta, ta yi masa ado irin yanda take gani a wayar Babawo a films.
Tsaki ta doka ta sake gyara filon ta mai mugun tauri sannan ta juya wa dakin baya, nan da nan kuwa bacci ya dauke ta......
[11/09, 2:28 pm] asiyahabibu93: 💅🏻 MAZAUNA GIDA 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 5:
Da sauri Jameelah ta ja Umaimah baya cike da in-ina take magana tare da yin nuni da yatsan hannun ta tana Kyafkyafta ido tace,
"Wwaaa... nnee... ne wan can???"
Murmushi Umaimah tayi mai kyau kafin ta bata amsa da cewa,
"Yah Umar kenan dama ina son na nuna masa babbar qawa ta, muje na gabatar dake wajen shi,"
Cikin sauri Jameelah ta hau goge fuskar ta da bayan hijab dinta ta gyara sosai dik Umaimah na kallon ta bata ce komai ba sai murmushi da take yi,cikin wani sabon ladabi daya matuqar bawa Umaimah mamaki suka jera suna tafiya.
"Me yasa kuka koma ne? Ku fa ake jira"
"Mum wai...."
"Na yi fitsari ne,"
Jameelah ta yi saurin katse Umaimah dan kar ta faɗi gaskiyar abinda ya faru,kallon Jameela Umaimah ta yi da sauri itama dan kuwa a gidan nan ba ta tab'a tina sanda taji wani ya yi qarya ba, waje suka samu a saman jerin kujerun dinning table ɗin nasu, kan Jameela a qasa ta sake gaida iyayen Umaimah, cikin jin daɗin tarbiyyar da take da ita suka amsa, Umar sai zabgawa qanwarshi murmushi yake yi, tare da langab'ar da kai gefe irin na masu shagwab'a Umar ya ce,
"Lallai ma Umynaa wato kin yi sabuwar qawa ne ashe shi yasa ki ka dai na so na ko? Ta kwace min ke,"
Sunkuyar da kai Jameela tayi tare da lumshe kyawawan idon ta dan jin daɗin muryar Umar,cikin ran ta ta ayyana,
'Wayyooo Allah na yau gani ga jarumin maza kenan,Allah kasa sanadin haduwa da wannan gwarzon ne ya kawo ni gidannan'
Ɗan taba ta Umaimah tayi dan kwata-kwata bama ta san me ake yi ba ta tafi duniyar tinani.
"Nanna'am"
"Yah Umr na yi miki magana,"
Kallon shi tayi ta sunkuyar da kai qasa, wani iri yaji azuciyar shi game da ita dan kuwa ta yi matuqar yi masa kyau ba kaɗan ba, a zuciyar shi ya furta,
'Masha'Allah'
Shine abinda Umar yace, a zahiri kuma ya sake maimaita mata tambayar shi inda ya ce mata,
"Cewa nayi meye sunan ki,Umaimah na son riga ki sanar dani sunan naki,"
"Jameelaahhh"
Cikin salo mai ɗaukan hankali tayi magnar, a zahiri ta nuna kamar bata san ma ta yi magana dan jan ra'ayinsa ba.
"Wooow masha Allah Jameelaah nice name, u deserve to be called Jameelaah, naji tace ajin ku daya ko? ashe kema hafiza ce kamar Umynaa....naji daɗin haɗuwa da babbar qawar Umynaa Allah ya sanya albarka a qawancen ku,"
"Ameen"
Itace kalmar da kowa ya fada a wajen, bismilla suka yi kowa ya fara cin abinci, Jameelaa a ran ta sai surutu take yi cikin mita take ayyana.
'Matsalar masu kudi kenan a tashi a hada ku cin abinci a babban teburi tsabar rowa, in ba rowa ba dan kar naci na qoshi da ba sai a bamu mu je can d'akin mu ci hankali kwance ba? ji kaji ma malam yanzu a banza zan barsu'
Ɗan juya ido tayi ta d'ibi shinkafa kadan a spoon ta kai bakin ta, tana taunawa a hankali, kowa a tinanin shi tsabar kamun kai ne ya sa take yin hakan,ganin haka sai Mum ta kiran mai aikin gidan ta ce,
"Kin ga haɗa masu abinci ki kai masu d'akin Umaimah su ci a can, baquwar tamu ta kasa sakewa ta ci abinci da mu"
'Alhamdu lilLAAH kaiii babar su Umaimah na da hangen nesa,yanzu ba sai na ci kaji acan na gyatse abuna ba? habaa da an wani hadani da wannan mai kalar mutanen boyen ta ya abinci zai shigen'
Bayan an kammala haɗa masu abincin an kai masu Umaimah ta kama hannun ta akan su shiga daki su ci, cikin jin kunya ta miqe basu qarasa shiga ba taji Umar na cewa,
"Gaskiya na ji daɗin ganin qawar Umynaa, tana da hankali da nutsuwa ga kuma kunya, "
"Gaskiya nima na yaba da hankalin yarinyar, ana fadin yaran unguwar basu da tarbiyya gaskiya naga sab'anin hakan akan ta, yarinya kintsattsiya haka? Lallai iyayen ta sun bata kykkyawar tarbiyya,"
"Kwarai kuwa, Allah ya musu albarka to,"
"Ameen dai"
Ai wato suna shiga d'akin Jameela ta yi arba da abincin nan ga lemuka kala biyu kowa da nashi ga nama ga shinkafa da miya da salad, wayyooo ji ta yi kamar bata taba cin kowanne a cikin su ba, zama ta yi ta aje hijabin ta a gefe ta duma hannu ta hau yagar naman tana ci tana santi, tasss ta tashi da abincin bayan Umaimah tace ta qoshi, wata gyatsa ta sake ta hau yi wa Umaimah surutu,
"A gaskiya kuna jin daɗin ku Umaimah, kullum wai haka kuke cin abinci mai daɗi a gidan nan?"
Murmushi kawai Umaimah tayi wa Jameelah,kafin ta yi magana kawai sai Jameela ta fara share hawaye cikin kuka ta ce,
"Allah sarki Ramai na da Babana, na zauna na cika cikina da mai daɗi irin wannan, ko su me suka samu suka ci da rana? Wataqila abincin siyarwar da Ramai ke dan dorawa dan siyarwa shi zasu ci yau, Allah kenan mai yarda ya so, mu muna nema ku kuma kun gama samu,"
Tausayin ta ne mai qarfin gaske ya kama Umaimah da sauri ta rungume ta tana lallashin ta, tare da yi mata alqawarin zata ɗebar mata abincin da taci ta kaiwa iyayen ta,
"In aka gani a gidan ku fa ba za a maki faɗa ba? ai sai su ce na zama makwadaiciya Umaimah,basshi kawai kin san soyayyar dake tsakani na da su ne ya sa na ji sha'awar na gan mu muna ci tare, amma ban fada maki dan ki debar min ba,"
"Na sani kar ki damu, inshaa Allah sai sunci nima hankali na zai kwanta, tashi muje parlour,"
"To ai ni tafiya zan yi ma, da kin barshi kawai,"
A hanyar su ta tafiya parlour suka rabu, Jameelah ta yi parlour Umaimah ta yi hanyar kitchen sanye da zumbulelen hijabi......
*A yi hakuri da wannan na yi busy ne thank you mutanen kwarai da hakuri da ni.*
[11/09, 2:28 pm] asiyahabibu93: 💅🏻 MAZAUNA GIDA 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 7:
Sosa kai tayi sannan tace,
"Baba na jima ina so in gyara dik wani halayen da nake yi marasa kyau malamin mu ya yi mana wa'azin daya shigi jikina kuma ya tsoratar dani, sannan Allah ya amsa addu'ar ka akan nema mana shiriya da ka ke yi a kullum ba ka gajiyawa,ana haka shine na nemi izinin Ramai na je gidan wata qawata dan muyi karatun qur'ani ina so na gyara hadda ta,dayake ita qawar tawa tana da hadda sosai dan kuwa ita ke yin na ɗaya cikin mu arba'in da wani abu a ajin mu, muna zuwa sai na ga ashe masu kuɗi ne, shine mukai karatu da zan tafi iyayen ta da ita kan ta suka haɗa min abin arziqi, na qi Karb'a maman ta tace ai dik abokiyar d'iyar ta d'iyar ta ce, shine na amsa yayan ta ya dawo dani gida, kuma maman ta ta qara mana k'warin guiwar yin karatu tare"
Nazari sosai Baban nata yayi ma maganar ta, amma sam bai gano qarya a ciki ba, dan haka fara'a ta bayyana a kyakkyawar fuskar dattijon har ya samu kan shi da fad'in,
"Alhamdu lilLAAH, na gode Allah dana ga wannan rana,Allah ya shirya min dan uwan ki shima ya gyara rayuwar daya tsindima kan shi a ciki yaro qarami amma haka za ki ga yana layi a titi dan lalacewa, Allah ya dawwamar dake cikin farin ciki da kuma shiriya,"
"Ameeen Babana,"
A haka suka kashe bakin shi, ta dage ta dinga yin duk wani abu da zai tabbatar masa da cewa ta shiryu da gaske kamar yanda ta ce ɗin, shi kuwa baba haka ya saka mata ido dan ya ga ko wani makircin suke qullawa amma har dare bai ga ta je zance ba, dik kuwa da naci irin na Babawo da ya zo har leqawa tsakar gidan ya yi ya hau kiran ta, tana nan rungume da qur'ani ta na jin shi amma ta qi fita.
Washegari da assuba bayan tayi sallahta sai ta d'auki qur'anin ta ta hau karatunta ta nata muraji'a, Baba kam daɗi kamar ya d'aga shi sama haka ya dinga sakin murmushi.
Bayan ta gama karatun ta ta shirya dan zuwa wanka sai ta saka hijab daya rufe mata jiki gaba ɗaya taje tayi yi wankan ta ta dawo tayi shirin zuwa makaranta,a hanya suka hadu da Mamalo,cikin ɗauke kai irin na masu kishin qawancen nan Mamalo ta ce,
"Wai ina ki ka shiga jiya daga zuwa gidan su Umaimah kamar wadda ta yi tafiya wani gari?"
"Ba zaki gane baaa yarinya,nace ba zaki gane baaaaa, amma nan da wani lokaci kaɗan zaki gane komai, yah kin tara kud'in anko muje mu siyo ko ki na nan ba ki da ko sisi?"
"Eh na tara dubu uku da dari biyu,"
"Ba laifi in an tashi muje.mu siya,ke ni har na sai takalmin da zan saka ma jiya,"
"Habaa dai ! lallai ke babba ce qawata,"
Murmushi tayi saboda ita wannan yabon da take samu daga qawayen ta na lungun su yana mugun d'aga mata aji ainun, sai ta dinga jin kamar ita ɗin wata Zahrah Buhari ce.
Bayan sun isa makaranta ne ta samu waje ta zauna a nutse, yi tayi kamar bata ga Umaimah ba ma dan kar ace ita take manne mata, Umaimah bata damu ba ita sai ta zira hannu ta tabo ta, murmushi suka sakar ma juna, sanan suka miqawa muna hannu suka gaisa a mutunce, Umaimah ta ce,
"Ya ki ka je gida jiya? Dik da na san lafiya qlou zaki isa tunda Yah Umar ne ya maida ki,"
"Kwarai kuwa, lafiya qlou na isa gida, dan kuwa Yah umar akwai mutunci,"
"Sosai ma kuwa, sai ma kun saba zaki ga hakan,"
Jameelah murna ce ta kama ta da jin kalmar sabo a tsakanin ta da Umar a ranta ta ke ayyana,
'Wayyyoo Allah ka matso da ranar sabawar mu nan kusa'
A zahiri kuwa sai ta dafe qirji ta zaro idanu waje ta ce,
"Ni Jameelah ni me zai kaini sabawa da namiji kamar Yah Umar? Ai ni din ba ajin shi bace, ko ke ɗin ma dan kina qanwar shi ne amma da sai nace yafi qarfin kula ki bare ni 'yar talaka jikar talakawa"
Murmushi Umaimah ta yi sannan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 3 Chapter of 30