Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ta ta tabbatar ma da iyayen ta shi take so, shine zaɓin ta ba wani ba. *********************** Gidan Mamalo gidan haya ne mai ɗauke da d'aki biyu sai band'aki da kitchen, d'aki ɗaya aka sanya mata kayan gado, d'ayan d'akin kuma sai aka sanya kujeru da 'yan kayan kitchen ɗin ta na gayu, sai ledar d'akin ta mai kyau. Ba laifi dan bata zaci ma zata samu hakan ba Sadeeq shima yayi qoqari ainun, tinda aka kai mamalo Sadeeq yaqi d'aga mata qafa, dan kuwa a daren ya angwance, Mamalo an kai budurci gidam miji lafiya, ansha kukan shagwab'a kala-kala wanda ya ke burge Sadeeq tsabar jin daɗin hakan ya dage sai lallashin ta yake amma taqi daina kukan, cike da nishad'i Sadeeq ya ce, "Haba masoyiyar Abubakar mai gaskiya, dan Allah ki daina kukan haka ya isa, har fa maqota na iya jiyo ki, taso muje na taya ki ki gyara jikin ki kin ji? Sai muyi bacci inshaa Allahu gobe kika tashi ba zaki ji ciwon komai ba," Cikin kuka da shagwab'a tare da wani irin jin kai da taqama da kuma alfaharin ta kai mutuncin ta gidan aure take magana, "Ni ba zan iya tashi ba,bayan ka gama min abinda kaga dama, tinda su Jameelaa suke zance da Babawo ban taɓa jin ta koka ba, in ba daɗi da take ce min taji ba, amma kai rana ɗaya ka gama yi min rauni, dubi har da jini fa tsabar mugunta," Har cikin ranta take jin daɗin kai budurcin ta da ta yi gidan aurenta dan haka take magana kai tsaye hankalin ta kwance zuciyar ta zaune a qirjin ta. Sadeeq ji ya ke kamar ya tsaga qirjin shi ya saka ta dan tsabar so, shi talaka ne ba shi da kyautar da zai yi mata irin yanda yake jin ana yi wa  wasu matan da suka kai budircin su gidan miji,amma yasan abu ɗaya da zai yi mata zuwa biyu. Kama ta yayi ya ɗora ta a jikin shi yana shafa bayan ta da sigar lallashi ya ce, "Fateemana ! ba abinda zan ce maki sai dai nace Allah ya yi miki albarka, Allah ya qara min son ki sama da wanda nake maki a yanzu Allah kuma ya biya maki dikkan buqatun ki na alkhairi, dole zaki ji zafi kuma dole na ne na maki dik abinda zai sauqaqa maki, kiyi hakuri kin ji? Na maki alqawarin dik abinda kike so indai bai fi qarfi na ba zan maki shi, zan kula dake, zan kare maki dikkan mutuncin ki, kinga amfanin qin amincewa da na yi muyi soyayyar shashanci ko? Yanzu gashi munyi komai cikin nutsuwa da kuma kwanciyar hankali, ba tsoro ba fargaba, ba tinanin wani zai gan mu, babban ribar kuma babu zunubi sai tarin lada," Dik abinda yake faɗa yana mata ma'ana a kwakwalwa da zuciyar ta, yanzu ta fahimci dik abinda yake faɗa mata abaya take ganin rashin wayewa ne, sai gashi a dare ɗaya ya gwada mata shi ɗin kwararren ɗan soyayya ne, ba dan zafin da ta ji ba ai irin soyayyar daya gwada mata bata jin ko a india akwai wanda ya fishi iyawa. Sun dad'e suna ta hira a tsakanin su, yana mata alqawurran jin daɗin da zai bata wanda har cikin ranshi yake faɗan su, dan kuwa bai ɗaukar wa kan shi qarya ba shi a rayuwar shi, iyakar gaskiyar shi yake fada mata. Daga qarshe ya fita ya kunna risho ya ɗora ruwan zafi ya juye a bokiti, sai da ya tara wanda zai ishe su sannan ya kai masu dana sirkawa band'akin,wanka ya taya ta tayi ya gasa mata jikin ta sosai, sannan ya riqo ta suka koma d'akin su, zama tayi a saman sallaya ya gyara masu gadon su, sannan ya sa suka sake yin nafila, kafin suka yi bacci, Mamalo dik hakan sabon abu ne a wajen ta, in tai sallahr farilla bata ta nafila sai gashi zama da mutumin kirki ta san ta yi nafila a dare ɗaya. Bayan kwana huɗu da auren su tana ta bacci ya tashi ya yi masu abin karyawa k'wai ne ya soya sai shayi ya dakko bread din daya shigo da shi a daren jiya ya kai d'akin, ragowar kilishin da basu cinye ba ya juye a plate ya rufe, zama yayi a gadon ya tashe ta, tare da mammatsa mata qafafun ta. Bude ido tayi tana qoqarin komawa baccin ta dan kuwa tunda aka kawo ta Sadeeq yake nuna mata shi fa ɗan soyayya ne dama lokaci yake jira. "Yi hakuri ki tashi haka, ki wanke bakin ki mu ci abinci, " Tana jin abinci ta dire a qasa, zama ta yi zata fara ci ya kad'a kai, tare da kama hannun ta ya ce, "Sai kin wanke baki kinyi sallah sannan mu ci abinci dan kuwa  kin makara, na so tashin ki amma na kyale ki ganin irin gajiyar da ki ka yi , taso muje ki yi alwala ko kina so na wanke maki bakin da kaina ne irin na rannan?" Tinawa ta yi da daren jiya sai kunya ta kama ta ta miqe ba musu, ya ko bi ta da tsokana har waje, shagwab'a ta fara yi masa tana son yin kuka sannan ya yi shiru ya kyale ta, kujera ya ajiye  'yar tsugunno guda biyu, ɗaya tata ɗaya tashi, toothpast ya sa mata a brush yana jiran ta fito ya bata, Mamalo na ciki ta rasa yanda zata yi tace ya tashi daga wajen, dan kuwa tutu take ji sai kaiwa da kawowa take a cikin band'akin, jin motsin da take yi kamar mai tafiya ne ya sa ya buɗe ya leqa ta,gani ya yi ta haɗa zufa sharkaf, sai matse hawaye take yi da sauri ya isa gaban ta ya riqe ta, a tinanin shi can wajen ne ke yi mata zafi har yanzu. "Sannu kin ji Fateemaa, bari na sanya maki ruwan d'umi,sai ki kama ruwan dashi,ki yafe ni da na san zaki ji zafi haka da ban yi ba dana hakura" Wata majinar wahala ta sharce, ko kwakkwaran motsi ta kasa yi,fita yake son yi yaji wani irin mugun warin bala'i, Mamalo ta saki wata tusa mai d'anneman wari, kasa shaqa yayi ya fice da sauri daga band'akin yana fita ya shaqi iska mai kyau ya kalli hanyar band'akin, sai a sannan ne ya gane me ke damun ta. D'aki ya shiga  ya zauna, tanaleqawa taga baya nan kuwa ta zage ta dinga zazzage cikin ta, sai da ta gama tass ta fita ta wanke bakinta ta yi alwala, kunya ta hana ta shiga d'akin, tsaye ta yi a bakin qofar, ganin inuwar ta yayi ya kwashe da dariya, "Fatee na shigo abin ki kowa ma yana yi, nima dana tashi sai da nayi sannan nai alwala nai sallah wai ke yanzu a yanda muka riga muka zama ɗaya har akwai abinda zaki ji kunya ta akai irin haka? Habaa ai an riga da an zama ɗaya Mamalonaaa," Kukan shagwab'a ta fara yi har da hawaye, ita bata san wanne irin mutum Allah ya haɗa ta da shi ba, komai daga zuciyar shi yake faɗan shi ba wani boye-boye, ita dai gaskiya yana bata kunya. Haka rayuwar su mamalo ta ci gaba cikin girmamawa da qauna tare da soyayyar junan su,yanzu ta fahimci menene darajar kai budurci gidan aure lafiya, da kuma me ake kira da asalin soyayya, dan kuwa Sadeeq A ne har ma zuwa Z, a cikin sati ɗaya da kwanaki da suka yi yanzu da shi ta tabbatar da cewa soyayyar aure ita ce dahir. *********************** Daga makaranta ta dawo ko abinci bata yi ba kan ta fita, tinda ta saba in ta koma daga school ko kafin ta fita mai aiki ke masu abinci acan shi yasa a cikin kwanakin nan da suka yi da Umar a sabon gidan su ko gas bata taɓa kunnawa ba duk abinda take so koda ruwan zafi ne kuwa shi zai dafa mata ya kawo mata har inda take da buqatar shi, jikin ta dik ciwo yake yi mata sai kawai ta zube a kujera bacci mai daɗi ya ɗauke ta, Umar ne ya shiga da sallama yaji shiru gidan,  ya na qarasawa parlour ya ganta a zube a kujera da alama a gajiye take, kuma yunwa na damun ta. Bai tsaya b'ata lokaci ba wajen tub'e kayan shi ya shiga dafa masu abinci, yana cikin girkin ta tashi ko da ta jiyo shi a kitchen kwala masa kira tayi, da sauri Umar ya fito  cikin wani ladabin da ban taba ganin ya yi ma mahaifan shi ba, ta ce, "Kawon ruwa da maganin ciwon kai, kaina ciwo yake yi," "Ina dafa mana abinci yanzu ko zaki bari ki ci abinci sai ki sha maganin, kin san magani ba abinci baya ci," Harara ta watsa masa kafin ta ce, "Kai zaka faɗan me zan yi? Ni ban ruwa da maganin ciwon kai dalla na sha" Ai kuwa cikin sauri ya je ya kawo mata abinda take buqata kamar wani bawa da uwar gidan shi haka Umar yake bin umarnin Jameelah cikin ɗan qanqanin lokaci................ *Shin wa zai sanar dani meke faruwa a gidan Umar da Jameelaa ne?* [11/09, 2:28 pm] asiyahabibu93: 💅🏻  MAZAUNA GIDA   💅🏻 WRITTEN BY HAERMEEBRAERH PAGE 20: Cikin taqama da izza ta shiga gidan tana sallama,Mamalo ce goye a bayan Sadeeq sai tiqar dariyar ta take yi duniya ta yi musu daɗi,cikin nishi Sadeeq ya ce, "Kin san me babe? Ba qaramin nauyi ne da ke ba, bayana kamar zai balle nidai yanzu na tuba ki yafe ni ba zan qara ba sakko haka kar ki b'urma min bayan," "Sai ka yi minti ɗaya kana zunkud'a ni zan sauka, gobe ba ka qara leqani in ina wanka ba, " "In banda abin ki dan na leqa ki me ne? Ni fa mijin ki ne, dan ma ban maki wankan ba gaba ɗaya, ko baki da labarin Annabi yana wanka da matan shi? Suna wanka a mazubi daya hannayen shi na gogar na Nana Aishaa, irin soyayyar nan nake so muna yi,ba soyayyar da ta wuce ta gidan Rasulullah daɗi da wayewa ko baki son na jiyar dake daɗin da ke cikin gidan aure ne?" "Kaiiii ni ko nake so," "To inshaa Allah na maki alqawarin jiyar dake daɗi ko wanne iri ne in dai ina da hali da ikon yin hakan" Mamalo dan jin daɗin maganar shi bata san ta sauka ba ta rungume shi, sai ji ta yi yana qoqarin yi sumbatar ta ai ko tsayawa tayi tare da lumshe ido, jira take taji saukar sumbar shi sai taji saukar cizo a kumatun ta, ai kuwa da qara da zare ido ta buɗe idon ta, tana ganin yana mata dariya ta bishi da gudu, suka fara zagaye gidan, gajiya Jameelaah tayi da ganin shirmen nasu (inji ta fa ba ni na fada ba) ta buga qofar kitchen da qarfi. "Ana ta maku sallama kuna nan kuna wasan yara," Kallon ta Sadeeq yayi, ya yi murmushi, "Habaa qawar mu ba dai wasan yara ba sai dai wasan masoya  bismillah," Mamalo kallon ta tayi ta ɗauke kai, dan kuwa fushi take da ita parlour ta shige abun ta ta zauna,Sadeeq ne ya yi magana qasa qasa ya ce, "Sai ki shiga ki bawa qawar taki hakuri, kin san har yau fushi take akan rashin zuwan ki kai amarya? Kusan kullum sai tayi maganar," Tinawa da me ya faru ranar ta yi sai ta yi murmushi sannan tace. "Kar ka damu zan shawo kan ta yazun nan qawata akwai son jin gulumsy" Shiga ta yi ta faɗa jikin Mamalo da ke ta zumb'ura baki, dan yanzu Sadeeq ya shagwab'a ta,kowa ma yi masa shagwaba take yi, sun shaqu da shi fiye da tinanin mai karatu, kamar sunyi shekaru a zaman auren su. "Keeee qawata bari b'ata rai in kika ji gulumcyn daya hana ni zuwa kai amarya ai sai kin ji daɗi kema" Mamalo na jin maganar gulma ta fara washe baki ta na fad'in, "Fesa min ! fesa min da sauri na ji," Sadeeq ne ya shigo ɗauke da plate mai dubulan da alkaki na kayan gara, sai pure water a wani plate din ya sha gayun shi ya yi kyau da alama fita ya ke son yi, ajiye musu yayi, sannan ya kashewa Mamalo ido ita kuwa ta kafe shi da idanu kamar ranar ta fara ganin shi. "Yah ne amarya ta, ko akwai magana ne? Fita zanyi na barku dan in dai kuna tare na san ba za a kula ni ba,gwanda naje waje nima," Tashi Mamalo tayi tace, "Muje na raka ka, dan kuwa ba kai qarya ba, yau akwai hira, mun gode fa naga ka riga ni kawo mata abin tab'awa" "Anything for u my Fatee" Dariya tayi suka je daga waje, suna fita Jameelaa ta kad'a ido sama ta na ayyana, 'Wai su masoya dibi yanda yake wani mammane mata, Mamalo har kin isa miji ya tattala ni kema a wani tattala ki? Mu zuba ni da ke' (Wasu haka nan suke a rayuwar su ba su son suga zaman lafiya da soyayya na wakana a tsakanin masoyan da suka shaqu kai ko ba ma soyayya mai qarfi indai da zaman lafiya haka kawai sai wata taji bata son ganin wadannan mutane zaune lafiya da junan su, sai ta yi dik yanda zatai ta raba zaman lafiyar nan, ya Allah ka nesanta idon maqiya akan dikkan ma'aurata da masu niyyar aure) Sai da Sadeeq ya tsotse lips din Mamalo da kyau sannan ta koma tana ta nishadi da jin daɗin irin salon soyayyar Sadeeq da bata gajiyawa da kallon sabuwar ta a  kullum. "Ban labari qawata," Nan kuwa Jameelaa ta zayyana mata kooomaiii, da ya faru a ranar, hatta da yanda suka kwanta bata boye ko sakaya ba, ga qarya da ta haɗa labarin nata da shi dan ta bawa Mamalo haushi, Mamalo kuwa sai taya ta murna take da samun miji kamar Umar, bayan kuɗi ashe mutumin kirki ne haka, faɗa ma Mamalo Jameelaa ta yi wai ya sai mata fili a unguwar iyayen shi, saboda first nyt ɗin su,Mamalo bata san wani first nyt ba, kawai ta make,dan ita ko bata ji abu ba bata ragewa gulma daɗi sai ta kai aya a sauraro. "Gaskiya na mana murna da samun mazan da bamu taɓa tsammani ba, tsakanin Yah Umar ɗin ki da Sadeeq ban san wa ya fi zama mutumin kirki ba,Allah ya bar qauna dai," "Ameen," Hira sukai tayi Jameelaah na cin kayan gara, Mamalo ta sa mata tabarma da pilo a waje, dan zata ɗora girki tinda ga baquwa sun yi kuma kar Sadeeq ya dawo ba abinci, taliya da miya tayi da ɗan kifi tayi daɗi sosai, amma data kawo ma Jameela sai Jameelaa ta yatsina fuska ta ce, "Yanzu kina amarya zaki dafa taliya da miya da kifi? Ina nama? Ko kaza? Sanan ba ganye dibi ɗazu ma fa ruwa kuka ban ba wani ɗan lemu haka babu kayan marmari, gaskiya ni kam sai naje gida naci abinci," (Kun san taliya akwai tsinka yawu, koda baka cin taliya ina da yaqinin ka ga an baɗe ta da miya sai kaji yawun ka ya tsinke, ko da mai da yaji, yanda kuka san lemon tsami haka take da tsinka yawu) Jameelaa ma ba a barta a baya ba wajen tsinkewar yawu, sai tayi sauri ta wawuri cincin ta danna a baki, tana ci tana kallon Mamalo da jikin ta yayi sanyi, saboda kalaman Jameelaa, kuma itama sai yanzu ta kula a matsayin ta na amarya kuma wadda ta kai budurcin ta ba wata kyauta da ya bata, ta dai san ya yi mata addu'a, amma kyauta ai ko ta goro ce tana da daɗi, sannan gashi ko wata basuyi ba wanne ma wata ko sati biyu basu rufa ba amma abinci ba nama sai kifi, kifin ma na rufin asiri. Jan plate ɗin ta yi rai ba daɗi, ta fara d'ibar taliyar zata kai baki, wani yawu jameelaa ta had'iya maqwatt,dan ganin kyaun taliyar a ido, kuma ta san girkin su Mamalo akwai daɗi, (Girki na ɗaya daga cikin qualities na matan kano tabbas ba qarya) "Yi hakuri qawata naga kamar ran ki ya ɓaci, bari na ci ko kaɗan ne, matso dan Allah ki saki ran ki," Taliya Jameelaa ta fara d'iba ta kai bakin ta, ta na taunawa kuwa kunnen ta ya riqe qauuuu dan daɗi, amma haka ta basar ta sosa cikin dabara, sai da suka cinye taliya tass sannan ta sud'e hannu, dan kuwa ajiye cokali tayi tsabar bata son b'ata lokaci. Hira sukai tayi  Jameelaa na ba Mamalo labarin 'yan uwan mijin ta masu kudi, da irin zaman da tayi gidan surukan ta yanda ake ji da ita ake lallab'a ta, da yanda take zuba mulki, sai abinda tace ayi wai shi ake yi a gidan, da qaryar wai da shekarar data wuce Baban mijin yaso ya kai ta Hajji amma Allah bai nufa ba, yace dai tayi ta addu'a Allah ya kira ta, bana da ita za a je. Mamalo murna kamar zata zauce, tsakani da Allah take taya Jameelaa murna, amma Jameelaa gani take kamar Mamalo irin murnar qarya take yi ɗin nan amma a qasan zuciyar ta haushi take ji, nan mamalo ta bata labarin irin jin daɗin da Sadeeq ke bata, da alqawarin da ya yi mata kala-kala, Jameelaa ta so Mamalo ta bata labarin daren farkon su, amma tai ta nuna mata kunya take ji, bazata iya fadan sirrin auren su ba. Sai dai ta bata labarin yanda Sadeeq ke son ta yake ririta ta da kulawa da ita. Wajejen la'asar Umar yayi wa Jameelaah waya akan gashi nan zai zo ɗaukan ta, amsa masa tai da wata murya mai daɗi da rausaya, sai ta juya ta hau magana da turanci, Mamalo kam kallon ta take da sha'awa da burgewa, sannan da taya ta farin ciki. Sai da suka gama magana ta tura masa saqo akan ya siyo fruits leda biyu da kayan kwalama dai in ya zo ya ba Mamalo ɗaya, wai suna cikin babu, ta tausaya masu. Umar sarkin tausayi da son taimako haka kuwa ya tsaya ya siyi fruits masu yawa da cimar zaqi, ya qarasa gidan su Mamalo, sun gama shiri ta d'ebarwa Jameelaa kayan garar ta danna a jaka, dan kuwa tana son kayan gara sosai kamar bata dauki komai ba haka ta fita dan bata so umar ya gani sai ta b'oye,Mamalo ta saka mayafi ta raka ta har waje. Bayan sun gaisa da Umar ne ya d'akko ledar ya miqa mata, aiko ta sake baki ta na kallon shi cike da mamaki kafin daga baya ta hau yi masa godiya, sai Jameelaa ta kwab'e fuska irin na tausayawa dinnan, Umar sai yaji Jameelaa ta burge shi yanda ta tausayawa qawar ta har take son a taimaka mata. Mamalo da murna ta koma cikin gida, tana jin daɗin kayan da aka kawo mata,gyara su tai ta saka wasu a qaramin fridge din ta dake parlourn su, sannan ta yanka wasu ta zauna ta fara sha. Bayan su Jameelaa sun koma gida ba irin qaryar da bata zabga ba akan Mamalo, wai mijin ta baida kuɗi,na abincin da suka ci ma da rana ita ta zara a jakar ta ta bayar, ta hau matse kwalla wai ita zatana yawan zuwa dan ganin qawar ta bata sha wahalar gidan miji ba ko dame ta samu ta taimaka masu da shi. Da kyar Umar ya lallashe ta,yana jin son ta na yawo a jikin shi, mace mai tausayi mara son kan ta ai tayi a rayuwa. Tana a rungume da shi take murguda baki dan ta san dole zai dinga bata kuɗi dan ta bawa mamalon daga nan zata na sokewa. *********************** Hauwaa na zaune tana chatting da wani saurayi da ta yi sabo a whatsapp, suna ta exchanging pics na batsa sai juye-juye take tsabar yanda take jin sha'awa na motsa mata, ta rasa yanda zata saka ranta,taji budewar qofa da sauri ta rife wayar ta gyara kwanciyar ta,tare da b'ata rai, daga baya kuma kawai ta sai washe baki kamar gonar audiga............... *Ban taɓa tunanin wasu groups ɗin suna karanta novel ɗin nan ba turawa kawai nake yi sai da na ga masu tambayar page 20 within awa ɗaya da tura page 21-22...a min afuwa na yi mantuwa ne na zaci a page 20 ɗin aka tsaya....i beg of you to pray for my wellbeing and dacewa da samun kyakkyawan qarshe na yafe comments ɗin*😔au rab'ewa, ana kame-kame....................[11/09, 2:28 pm] asiyahabibu93: 💅🏻  MAZAUNA GIDA  💅🏻 WRITTEN BY HAERMEEBRAERH PAGE 21: Kame-kame ta hau yi tana qoqarin boye wayar ta sai dai ta yi rashin sa'a dan kuwa a qasa wayar ta faɗi a kife, har rige-rige suke yi ita da Ishaq wajen d'aga wayar daga qasa, cike da tashin hankali ta amshe wayar a hannun shi ta na zazzaro ido wata iriyar zufar tashin hankali na tsattsafowa daga saman baki da hancin ta,yanda take lamuran ta ne ya sanya Ishaq son ganin meye a wayar ta shiga tashin hankali irin haka, da sauri Hauwaa ta faɗa jikin shi ta ajiye wayar a gefen su ta hau kissing ɗin shi sosai, tare da yunqurin cire masa rigar jikin shi, Ishaaq ma a yau ya shirya tsaf dan ganin ya gwadawa matar tashi soyayya kamar yanda qanin shi ya shawarce shi da ya yi, wasu had'e-had'en magunguna na gargajiya ya sha ya yi tatul wanda wani abokin shi ya bashi bayan ya yi masa bayanin matsalar shi dan haka tuni ya manta da batun waya ya biye mata. Sai da ta ga ta mantar da shi maganar wayar ta sake shi zata wuce ta kwanta, shi kuwa janta yayi ta baya ya fara yi mata wasanni, mutuwar tsaye tayi saboda abinda Ishaaq bai taɓa yi ba kenan, da sauri ta juya ta tura shi baya, idon ta taf hawaye saboda bata son ya fara abinda ba zai iya qarasawa ba, haka rayuwar su take tun farko sai an d'akko abu rumi-rumi kamar gaske sai ya rigata ya barta da abu ajiki tai ta fama da wahala. Qara matsawa yayi ya rungume ta, cikin kuka ta sake qoqarin janye jikin ta amma bai bata dama ba, cikin wata iriyar muryar da Hauwaa bata taɓa jin mijin nata da irin ta ba ya ce, "Dan Allah kar ki guje ni ki bani dama na nuna maki jiya ba yau bace sannan goben mu ba zata ci gaba da zama kamar jiya ba za ta ci gaba da zuwa da kyawawan sauyi na alkhairi har abada" Kuka ta fashe da shi tare da sake k'wace jikin ta a nashi ta ce, "Please Ishaq let go of my hands, kar ka min haka na gaji, ba zan iya ba kullum kai kenan ka gama jagwalgwalani ka biya taka buqatar ni ka barni ko mutuwa zan na mutu baka da asara? Dan Allah ka barni, na gaji da wahalar dani da ka ke yi ba zan iya ci gaba da irin wannan rayuwar ba Ishaq," Ishaaq bai san sanda wani tausayin ta ya shigi ranshi ba,nan take ya fara zubda hawaye, da qarfi ya riqe ta gam a jikin shi ya ce, "I am so so sorry Hauwaa ki yafe min ,yanzu ne na san ina cutar da ke wanda hakan bai taɓa zuwa a tunani na ba balle na yi yunqurin gyarawa,amma inshaa Allahu daga yau an wuce wannan wajen, daga yau zaki samu dik wata kulawa daga wajena da ke da abinda ke cikin ki, ina son ki shirya tafiyar nan da zamuyi dake zanyi ta, in naje can zan sake samo wasu magungunan, yau na samu wani na sha kiyi hakuri mu gwada mu gani in yaso in ba a dace ba sai in munje can naga kwararren likita, ina fatan zaki yafe min?" Da sauri ta faɗa jikin shi tana kuka sosai mai ban tausayi, a hankali ya fara aika mata da saqonnin da ada ita ke yi masa irin su shi sai dai ya tsaya mata kamar gunki, cike da shauqi da son abinda yake yi mata take miqa masa ragamar jikin ta........... Hauwaa ta sha mamaki ainun ashe mijin ta gwarzo ne haka dama bata sani ba? shine yake son ya kashe ta da yarintar ta ya jefa ta a halaka (ki jefa kan ki dai,ita zina zaɓin rai ce ai,idan ka so sai ka aikata ta, idan baka so ba ka bi hanyoyin da musulunci ya ce ka kare kan ka daga gare ta ga lada ga biyan buqata) baccin shi yake hankali kwance, dan kuwa shi kan

Chapter 12 of 30