kuma Baban Jameelaan ne wani abu ya same shi?"
"Ina fa ! Ba abinda ya same shi kuma ni ba wanda ya b'ata min rai kawai so nake tinda sallah ta gabato mutane na ga sun fara kawo ɗinkunan su, wannan ɗinkin da za ka yi na shekarar nan ka dage ka tara kuɗi sosai, sannan albashin ka na makarantar boko in an baka muna rage wani abu mai yawa a ciki, a samu babban asusu ko ka kai banki ka ajiye, kaii ni koma ya za ai kawai ka tara kuɗi mai yawa kafn na haihu, dan kuwa ina son inna haihu ayi suna mai ban mamaki, sunan da tinda ake aurar da yaran layin mu su haihu ba a taba irin shi ba,"
Baki sake yake kallon ta sanda take masa wannan bayanin me kama da wadda aljanu suka taɓa ko suka bawa shawara,tashi yayi daga durquson daya yi kamar wani me neman gafara, cikin qanqance ido ya ce wa Mamalo,
"Ke da wa kuka tattauna kuka yi wannan shawarar?"
Yanda ya yi magana cikin d'aure fuska itama haka ta mayar masa da amsa cikin daure tata fuskar ta ce,
"Ni ban yi shawara da kowa ba, wato ka maida ni mara wayon da sai nayi shawara da wani sannan zan faɗi abinda nake so a yi min da suna na?"
"Hummmmm Allah to ya hore mana abinda zamu yi sunan idan kin haihu lafiya,"
"Ameen Allah ai yana taimkon wanda ya taimaki kan shi ne"
Ta fada a sanda ta ke tashi dan shigewa d'akin su, a gaskiya ta gaji da zama Jameelaah na fin ta a komai na rayuwa, bayan layin su ɗaya kuma gidan su ɗaya, wannn karon ko bashi zataci sai taci itama an buga suna na ban mamaki.
Sadeeq yana zaune yana mamakin sauyawar Mamalo cikin qanqanin lokaci, qarshe mamakin sa ya kau da ya tuna cewa da dikkan alama Jameeelaa ta zigo masa ita ne dan ba haka matar shi take ba, ba tun yau ba ya kula da yanda Jameelaah ke taka mahimmiyar rawar dake gurɓata tunanin Mamalon shi, dan dik abinda Mamalo tayi mara kyau in aka bincika sai an gano da sa hannun Jameelaah a ciki,in ko haka ne zuwan ta wajen Jameelaah ya zo qarshe,dan ba zai dinga gini ana rusa masa ba, dama ba wata cikakkiyar tarbiyya gare ta ba lallab'a wa yake yi ta dalilin soyayyar da take masa ne yasa take jin maganar sa, sai yake amfani da hakan yake bata tarbiyya mai kyau da inganci musamman yanzu da take ɗauke da gudan jinin shi,dan haka dole ya sa ido kar yazo yana tufka wata na warware wa.
Kitchen ya shiga ya dau abincin shi, dan ko arziqin a kai masa ma yau bai samu ba.
***********************
Yau aka sallami Malam Jameel mahaifin Jameelaa daga asbiti yaji sauqi sosai qafa tawarke sai abinda ba arasa ba, tin da safen dama Umar ya ɗauki Bukar suka fita basu dawo ba sai yamma,lokacin da aka sallame su ɗin kenan,bakin Bukar yaqi rufuwa da alama akwai abinda yake son faɗa amma ya kasa,Ramai da Jameelaah ko sun yi tambayar duniya ya qi magana har sun gaji sun kyale shi, Umar kuwa sai kallon shi yake yi yana kad'a masa kai, da dikkan alamu akwai wata a qasa amma za su barsu idan ta yi wari sun ji.
Sun gama kwashe komai nasu da suka yi kwanciyar asibitin da shi suka yi sallama da maqotan su da ke asibitin Ramai na gaba ita da Jameelah suna hira Umar da Malam Jameel na baya Bukar kuwa har ya isa gaban mota ya ajiye kayan su kawai yake jira su tafi, bayan sun shiga Umar ya tada mota suka kama tafiya,sai Malam Jameel yaga ba hanyar gidan su aka ɗauka ba,sai kallon wajen yake yi yana son ya tambaya, amma yasan surukin nashi bazai yi wani abu dan cutar da su ba da alama wani wajen za su biya kafin ya kai su gida, dan haka ya ja bakin shi yayi shiru,Hajiya Ramai kuwa ta gaza hakuri dan kuwa gaba ɗaya bata gane hanyar da aka dosa ba sam dan haka sai ta ce,
"Ni fa ban gane nan hanyar ba, ohhh ni Ramatu Kano kenan tinjimin bajimin gari, Kano ta dabo timbin giwa jalla babbar husa, wato wani wajen dik girman ka a Kano har ka mace baza ka san da shi ba, nan kuma inane muke tafiya?"
Bukar ne ya kalli Ramai dake ta zuba ya kwashe da dariya sannan ya ce mata,
"Gidan Yanka kan mutane zamu je Ramai,"
"A kul nakuma ji dan Uban ka, dika-dika shekara ta arba'in da 'yan kai, ban shirya ma mutuwa ba sai na mori alatun duniyar nan nima"
Cike da jin kunyar kalaman ta Malam Jameel ya yi tsaki ya kauda kai,Jameelah ce ta ce,
"Balle kuma ni dana fara jin daɗin rayuwa ta ba, wataqila dai akwai inda zai kai mu,"
"To gamu mun iso sai kowa ya fito,"
"Mun iso ina?"
"Gidan ku da zaku dawo da zama, in yaso Mama gobe sai kuje ku deb'o kayan ku da kuke da buqata a can tsohon gidan, za akawo mota ta kai ku ku kwaso, wanda baku so zaku iya kyautarwa, dan kuwa daidai gwargwado an saka abubuwan buqatar ku anan ɗin, nan gidan mallakin mahaifi na ne wanda ya mallaka min shi a jiya dana roqe shi, dik da ba wani girma ne da shi ba ina fatan zai ishe ku, nan daki biyu ne da parlour sai kitchen da madafin gargajiya, dan Allah da son Annabi ba dan ni ba domin Allah Baba kar kace komai, kawai kamin addu'a ka sanya min albrka, shikenan ka biya ni kai uba ne a waje na baka buqatar yi min godiya sai dai addu'a da sanya albarka,"
Malam Jameel hawayen farin ciki ne ya ɓalle masa, Ramai kuwa zubewa tayi a qasan wajen ta hau zabga godiya, Umar har kunya yaji ta kama shi dan kuwa abun nata yayi yawa.
"Ku shiga ciki ina zuwa,"
Kafin ya gama rufe baki ta kai hannu ta amshe keys ɗin gidan a hannun Umar ɗin, Baban su Jameelaaah kuwa gaba ɗaya kunyar duniya ta gama baibaye shi akan abinda Ramai ke ta yi kamar dama tana jiran hakan ta same su.
Budewa sukai suka shiga wata uwar gud'a suka ji an rafka, Malam Jameel na ji ya san daga ina ta fito, kad'a kai yayi ya kalli Umar ya ce,
"Ummaru Allah ya saka maku da mafificin alkhairi kai da iyayen ka, gaskiya ba dan roqon da kayi min ba da ba zan amshi kyautar nan mai girma ba,akwai kunyar ka mai yawa a ido na na san halayen d'iyata da naka sun sha bam-bam ta ko ina, amma a haka ka hakura kake zaune da ita cikin so da qauna,Ummaru ba abinda zan ce maka sai dai nace Allah ya yi maka albarka,ya haɗa ka da alkhairi a rayuwar ka a dik inda yake, ya nesanta ka da sharri a dik inda yake, muna godiya kwarai da gaske, kuma ka sanar dani sanda ake samun mahaifin ka agari sai naje na miqa godiya ta, kyauta irin wannan ta wuci saqo"
"Baba ni ne da godiya ni da aka yi ma kyautar mutum, dik soyayya irin ta iyaye da yaran su kuka hakura kuka auramin Jameelaa ai komai nai ban biya ba,kuma bana jin zan iya biya ba,"
Wani irin nauyi kafadun Baban Jameelaa suka yi sai yaji matsananciyar kunyar Umar ta kama shi, sun aura masa yarinya wadda ba kintsattsiya ba amma shi godiya ma yake musu, share k'wallar data gangaro masayayi yace,
"To bismillah muje ciki,"
"Ai Baba da ka turo ta kawai mun wuce gida kaga magrib tayi,bai kamata muna yawo da magrib ba musamman dake tayi nauyin nan,"
Sosa kai yayi daya kula dame ya faɗa nan take ya juyar da kan shi yana murmushin jin kunya, Baban ma murmushi yayi sannan ya shige gidan dan kiran gimbiyar.
Sai santin wajen suke yi tinda yau sune har da parlour nasu na kansu mai dauke da kujeru, ga carpet blue dark irin na gidan Jameelah kujerun kuma light blue, labulayen ma kalar dark blue kamar carpet ɗin sai qaramar TV ta bango dakin su Baban an saka gado da katifa da ledar daki, sai kitchen ɗin da aka saka risho da kananzir a cikk sai indomie k'wali ɗaya da kayan shayi, da sabbin tukwane a kwali shikenan, d'aki d'ayan kuma katifa ce babba sai leda, murna suka dinga yi kamar wanda aka ma albishir da gidan gwamna,ko da Baban Jameelah ya sanar da ita ta shirya mijin ta na waje yana jiran ta su wuce sai ta hau turje-turje ta na fad'in,
"Haba Baba ka bari ayi isha'i mana,"
"Nace ki wuce yana jiran ki ko? Me zaki yi mana in kin zauna ɗin?"
Cike da zumburar baki ta shuri takalman ta tafice, Ramai na ta sa mata albrka.
A mota ta same shi zaune itama sai ta buɗe ta zauna bakin nan an cuno shi gaba kamar cokali, ganin haka sai yaji kamar yace ta koma anjima ya dawo ɗaukan ta,amma inaa bazai iya ba.
Tada motar yayi yana tinanin yanda yau zai lallab'a ta ko ya sha jaraba.
Ko da suka isa gida ma haka tai ta turo baki, kuɗi ya zaro dubu uku ya miqa mata ya ce,
"Ga sauran canjin katifa a sa a susu,"
Washe baki tayi nan tafara yi masa shagwab'a,shi kuma ya yi ta bata hakuri kamar ya yi mata laifi, duk abin alkhairin da ya yi mata da iyayen ta bata san ta buɗe baki ta yi godiya ba qarshe ma sai da ya bata cin hancin dubu uku ta baje baki ta na yi masa bayanin kud'ad'en da take tara wa,in ta saka wannan dubu ukun da ya bata tana lissafi ta sa ya kusan dubu talatin da wani abu kenan, Umar yayi mamakin yanda aka yi kud'in ya kai haka amma sai ya basar, sam bai taɓa kula da ɗauke-d'auken da take yi masa ba,tsabar iya taku wajen sibaren na bayye, in ta ɗauka baya taɓa gane ta zara.
***********************
Jameelaa fa yau kwanan ta biyu tana naquda a tsaitsaye dik ta fige tayi zuru zuru tsabar wahala, sai zuwa duba ta ake yi kamar wadda ta riga ta haihun, kowa hankalin shi ya tashi da yanayin da take ciki cikin ya yi girma da yawa gashi haihuwar fari, umar ya kasa ya tsare da shi ake yin komai watarana idan yaga ta na shan wahala zama yake yi ya yi ta kuka kamar ba likita ba,a rana ta uku ne midwife ɗin da Mum ta roqa a asibitin su tazo duba Jameelah anan ne ta yi masu albishir ɗin ta kusan haihuwa inshaa Allahu, ai kuwa nan ta sa Umar dole ya fita, dik da yaso ayi komai da shi tinda shi likitan mata ne, raunin sa akan Jameelan ne ya sanya Mum saka baki a lamarin dan haka ganin Mum na wajen ya sa yaji nauyi ya fita ɗin kamar yanda aka buqata, Mum ma a parlour ta zauna duk da cewa itama cikakkiyar Nurse ce amma ta kasa shiga, ta gan su sau ɗaya a halin da bai kamata ta gan su ba dan haka ba zata sake maimaita wannan gangancin ba ,Ramai kuwa tunda ta zo gidan take ta doka tagumi daga wannan bangaren zuwa wancan , ta kasa ta tsare tace ba mai kai mata yarinya asibiti, ta sha gani a layin su in an kai mace asibiti suna dawowa da qorafe-qorafen midwifes, musamman akan farke ma mata gaban su da suke ba tausayi dan su huta da jiran mai haihuwa, ba zata yarda Jameelaa ta rasa jarin ta ba ah atoh, ranar Mum taga jahilci tsabar shi a waje Ramai, dan kuwa dik bayanin da ake wa Ramai baya shiga kunnen ta, har mamaki ta dinga yi a ranta ta na ayyana ashe dama jahila ce mahaifiyar Jameelaa ,tinda har wa'azi ta yi mata akan maganganun da ta dinga furtawa dik akan haihuwar amma ko ratsa ta basu yi ba.
Suna nan zaune suka ji ihun Jameelaa tare da kukan Baby mai qarfi ya daki kunnuwan su a lokaci ɗaya ,nan take Umar ya zube dan yin sujjadar godiya ga Allah.
Yana dagowa kuwa ya afka dakin, Jameelaa na kwance...
*My FiFul barka-barka Jamcy kala ta haihu*
[11/09, 2:28 pm] asiyahabibu93: 💅🏻 MAZAUNA GIDA 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 24:
Zuwan su ke da wuya Jameelaah taga motocin kai amarya na qoqarin tafiya kuma idan ta fita ba zata samu shiga ba dan babu mai jiran ta tinda basu san da ita ba, kwab'e fuska tayi zata yi kuka, Umar kuwa na ganin motocin sun tafi ya kalli Jameelah ya ga zata yi masa kuka sai ya juya motar shi suka bi bayan motocin kai amarya, ai kuwa cike da murna ta zabaro masa wuya ta manna masa kiss a kuncin shi, murmushi yayi dan ganin ya burge ta.
"My love akwai ki da rigima,sai ki dinga abu kamar wata yarinyar goye,"
"Ni ce me rigima kooo?"
Ta faɗi hakan cike da shagwab'a,a wajen Umar hakan ma wani abun burge wa ne daga wajen Jameelar shi, sai ya ga ta qara yi mishi kyau, kad'a kai yayi ya d'age hannayen shi daga kan motar tare da zaro ido waje ya ce,
"Nii na isa nace dake nake?"
Dariya suka yi atare suna ta hirar su gwanin sha'awa ,Umar kuwa ya qi barin ko wacce mota ta shiga tsakanin motar su da ta ɗaukan amarya, a ran shi kuwa yana ta ayyana,
' Yau dai ga yayan kwabo an samu a gari da shi za a kai qanwar shi d'akin miji.'
Ko da suka isa qarfe shida na yamma yayi, cike da kid'a sauran motocin suka tsaya aka buɗe kowa ta fito,amma motar da amarya ke ciki ba a kunna kid'a ba dan kuwa tace bata so, albarkar aure take nema ba tab'ewar shi ba.
Sai da aka fara shigar da ita wajen aunty Hauwaa aka gabatar da ita tare da yi masu nasiha akan zaman tare da hakuri da juna,a nan 'yan uwan Mum da Dad suka miqa ta amana wajen Aunty Hauwaa, Aunty Hauwaa kuwa wadda bakin ta yaqi rufuwa saboda murna sai maimaita fad'in,
"Na Karb'a, na Karb'a da babban hannu,da hannu bibbiyu ya Allah ka taya ni riqewa da gaskiya da amana," take yi.
"Ameen ya Allah," mutanen wajen suka amsa.
Nan aka rankaya har aunty Hauwaan zuwa gidan Amarya,Amarya Umaimah kuwa na cikin mayafi tana kuka Jameelaah ta kutsa cikin mutane ta na so ta isa wajen ta ganin ta ɗauke da ciki ya sa mutane suka dinga bata waje, dan kuwa har wani sake turo shi gaba take yi,dangin Mum da basu san ta bane suka fara kallon isa da mallaka irin na Jameelaa.
Wata daga qannen Daddy ce tace ai matar Umar ce wannan,nan wasu suka washe baki aka hau gaggaisawa, wasu kuma suka d'aure fuska, a ganin farko suka gano bata da mutunci, gaida su ta hau yi tare da qoqarin durqusawa amma suka hana ta, a cewar su sun yafe durquson, bata kusa da Umaimah suka yi aka qarasa shigewa da ita gidan na ta,
Karatun qur'anin da aka saka ne tin kwana da kwanaki ke ta tashi, dan kuwa Haroon da Ishaaq sun ce gidan na buqatar karatun da wasu addu'o'in ma duba da cewar gidan yayi shekara da shemaru a rufe ba a san meke zaune a ciki ba.
Jameelaah sai walqita ido take yi dan ganin ta inda zata ga abokan ango sun bayyana tana ta washe baki,Umaimah ce ta ja ta kusa da ita sosai ta yi mata rad'a,
"Ya jikin Baba? Mum tace bai ji daɗi ba? Ya naki jikin,"
"Da sauqi dika sai da na tabbatar likita ya kula da shi na taho,yanzu ke ba lokacin tambaya bane banga angwayen ba fa Ina suke ne?"
"Ni ina zan sani? Ki daina yi min maganar angwaye gabana faɗuwa yake yi,"
Dariyar yaqe tayi kawai ta ci gaba da zaro idanuwa waje,cikin ran ta ta ce,
'Akan me zan daina zancen angwaye in basu wa zai bamu kud'in siyan baki gashi na ji an ce masu kuɗi ne? Kenan zuwa na ya tashi a banza?'
Qawayen su na islamiyya ne suka iso, suna ta yafito Jameelaah dan an ce kar ai hayaniya tinda an saka karatun qur'ani,sai dai an rage volume sosai, ta na ganin su ta ɗauke kai ta qi zuwa,kallon marasa hankali ma take yi musu dan kuwa a ganin ta ta kere musu nesa ba kusa ba amma suke abu kamar makafi,ganin ta qi kula su ne ya sanya suma suka ɗauke kai suka share ta.
Zama suka yi suka yi da'ira a tsakiyar parlourn, nan da nan suka fara karanta qur'ani daga bakunan su cikin suratul Rahman, basu tsaya ba sai da suka yi shafi biyu, sannan qanwar Hauwaa mai suna Safnah ta fara yin addu'u'o'i masu matuqar ratsa zuqata saboda da hausa take yin su, tana nema wa ango da amarya zaman lafiya da kwanciyar hankali, da zuri'a d'ayyiba,sannan Safiyya ta amshe itama ta fara zubo kalar nata addu'o'in kusan kowa dai a wajen sai da ya yi masu addu'a sai abun ya basu sha'awa su kan su,Jameelaa ta kula sun maida gidan kai amaryar islamiyya, ana zuwa kan ta tace,
"Allah ya bada zaman lafiya ya kawo qazantar daki,"
Ta ja baki ta gume shi gum dan ita bata ga amfanin waɗannan abubuwan ba gidan kai amarya an maida shi kamar wata islamiyya meye hakan?ai kyawun ta a baza masu kid'a irin na soyayyar nan me ratsa zuciya amma sun wani tsaya karatu kamar qauyawa ta na can ta na zancen zuci bata ma san kowa a wajen ya bi ta da kallo ba, saboda a qalla kowa yayi addu'ar da tafi haka balle ita babbar qawar amarya, kiraye-kirayen sallar magrib aka fara yi, nan 'yan uwa da qawayen Umaimah su kai ta yi mata Allah ya sanya alkhairi suka hau fita dan tafiya gida ,sai d'akin ya zama daga Jameelaa sai Safnah da Safiyya da kuma amaryar, Umaimah ta ɗan saba da su dan tin da aka fara bikin sun haɗu ya fi sau biyu dan haka da ta ga zasu fita sai tace da su,
"Dan Allah kar ku barni ni ɗaya mana,"
Cannn dai Safiyya tace bari muje muyi sallah zamu dawo in mijin ki bai shigo ba kenan, dariya suke tayi qasa-qasa dan sun shirya guduwa ne dama.
Safiyya ce ta fara fita sai da Safna zata fita ta gane wayo suke son yi mata, da gudu Safnah ta amshe mayafin ta ta fita tana dariya, riga da skirt ne jikin ta sun amshi jikin ta sosai saboda safna akwai ta da diri mai kyau, ɗan acuci mazan ta da ta yi da gashin ta mai uban yawa ba tsaho ya qarawa d'aurin d'ankwalin ta kyau, tafe take tana ɗan gudu tana dariya suka ci karo da Umar dake jingine a bakin motar shi ya b'ata rai ganin yanda 'Yan matan wajen ke ta kallon shi suna qusqus, yana nan kafe kamar an kafa shi yana jiran hajiyar tashi ta fito su tafi,dan kuwa tunda ta shiga yake zaman jiran ta sallah kawai yayi ya dawo ,a tsayen yake ta azkar din shi.
Bata kula da tsaiwar shi a wajen ba sai ji tayi ta bangaje mutum, da sauri ta juya dan bashi hakuri, sai taga yana yi mata kama da Umaimah sosai, sai ta rage dariyar da take yi tace,
"Dan Allah kai Yayan umaimah ne?"
Cikin d'aure fuska Umar ya ce mata,
"Eh ni yayan ta ne meye?"
Sai kawai ta ja mayafin ta da ya zame tin a gidan Umaimah ta qarasa yafe jikin ta da shi sannan tace,
"Ga qanwar ka can tana yi ma mutane kuka dan an kawo ta gidan miji bayan ita tace tana so,ka shiga ka bata hakuri ko taa sako maka matar ka, dan kuwa tana can ta qanqame ta ta hana ta fita,"
Kawai sai ya fara dariya ya san halin Umaimah sarai da shagwab'a, girgiza kai kawai yayi ya na dariyar shima can qasan ran shi kuwa tausayin qanwar tashi ne fal ran shi a hankali ya ce,
"Yanzu in banda abinki baiwar Allah ina ni ina shiga gidan surukai? Zata fito ne na san Jameelaah da ta gaza hakuri zata mata wayo ta gudo,"
"Ashe ma baka san Umaimah ba har yanzu, a iya ganin da na mata na gano wayo ne da ita itama,ko yanzu da kyar na kwaci kai na plan muka haɗa na guduwa amma Safiyya na fita ta gano mu ta damqe ni da kyar na kwace na gudo,"
Daga haka fa Safnah da Umar sukai ta hira, daga baya tace ta shiga ciki bata yi sallah ba sai watarana.
A cikin hirar su ne ya ji cewar ita ɗin qanwar matar wan mijin Umaimah ce sun zo bikin ne suma, amma tana makaranta a Zari'a tana karantar mass com.
Umar yana tsaye yana ta murmushin hirar su da Safnah Jameelaa ta fito, lokacin ana ta kiraye-kirayen sallar isha'i ranta a mugun b'ace ta taddashi,ba ango ba abokan ango ba alamar ma za ta ga ango a wannan lokacin,sam ba haka suke biki ba su a cikin gari,ta yaya za a kawo maka amarya tin biyar na yamma har takwas na dare amma baka zo ba to sai yaushe za ka zo?
(An yi karatun qur'ani ta ce su qauyawa ne amma an zo bangaren kuɗi ta ce su ba haka suke yi ba a cikin gari,komai dama akwai lokaci na musamman da aka qirqire shi)
Ga wata muguwar yunwa da take ji har ta na jin kamar za ta yi amai saboda rabon ta da abincin kirki tin safe, sai uban ruwa da tai ta d'irka da Lacasera.
"Muje gida"
Ta ce masa ta na hura hanci ta na b'ata rai kamar zata kai masa duka, umar kuwa da sauri ya kalle ta ya ce,
"Gida ko asibiti?"
"Ni ka kai ni dik inda zan samu abinci yunwa nake ji marowatan banza kawai ku tara mutane amma ko wannan shegiya shinkafa babu balle mutum ya saka ran samun nama ko wani abu makamancin hakan,"
Ta qarasa maganar cikin datse haqorin ta dan haka baiji me ta ce ba, kawai dai ya ga tana b'ata rai ta zauna a kujerar me zaman banza (as she is) ta na qunquni.
Gidan Mum ya ɗauki hanya zai kai ta ya san a can za ta ci abinci kuma ko Allah ya sanya alkhairi ta yi musu duba da cewar tinda aka fara bikin bata je ba, bata yi masa musa ba amma ta d'aure fuskar nan kamar hadari, suna isa suka tarar da gate a bude yake, sa kan motar yayi ciki ya parker suka shiga riqe yake da jakar ta da abun ruwan ta dan kuwa ta yi gaba a yunwace take, suna shiga kowa ya bisu da kallo, cikin sauri ta zauna yaraf tana maida numfashi, ganin kallon da ake yi mata ne ya sa ta wayance ta ce,
"Yau na ga shagwab'ar Autan Mum, Mum Kinga yanda Umaimah ta dinga kuka kuwa tana qanqame ni dik jikina ciwo yake yi sosai, ga yunwa da nake ji, da kyar na k'waci kaina na taho,"
Dariya sosai wasu suka hau yi ana maida zance kowa na fad'in abinda ya gani da abinda ya faru, wata daga cikin qannen Mum ce tace,
"Ai gwanda kukan ta akan naki fa Jameelahh ke da ki kai ta kuka kamar zaki shid'e sanda za a kawo ki?"
Rufe fuska ta yi alamar wai kunya take ji, Mum ce ta shigar mata tace,
"Kinga rabu da su taso muje ki ci abincin ki kin ji 'yar albarkan Mum,"
Da kyar ta bi bayan Mum ita a dole wai kunya take ji, kitchen suka je da Mum sai da ta zaɓi abinci tsabar gashi nan kala-kala anan kitchen ɗin aka zuba mata taci ta yi nak,sannan tace zata wuce asibiti daga nan ta ga Baban ta a kunyace tace,
"Mum yah Umar fa shima yunwa yake ji bai ci abinci ba tun da safe da muka baro gida,"
Murmushi Mum tayi tace,
"Ai muna parlour ana hirar nan ya shiga ya d'iba ya wuce d'aki, bari na zuba maki ki kai asibitin ki gaida mai jiki idan kun je gobe inshaa Allahu zan shigo, sai na duba shi,"
"Allah ya kaimu Mum, ai da kin bari naje gida na yi masu girki tinda naga kamar akwai baqi sosai kar na kwashe kuma yazo
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 15 Chapter of 30