na lefe na ne na qara da su, in kina so zan iya shige maki gaba dan na tabbata kin kusan haihuwa dan dai ko ki haihu cikin azumin nan ko bayan azumi da kadan"
Tinani sosai Mamalo ta shiga yi, wanne irin yara Jameelaa take tare da su a makaranta da suke adashin kudi masu yawa haka iyayen su basu damu ba? Dan taga dik yaran ta girme su in ba saurin girma irin na yaran masu kuɗi ba.
"Kinga na baro mutane na zo nan muna ta tattuanawa amma kin yi shiru kina tunani, in ba dan amintar mu bama kin ji na faɗa maki sirri na in ba kya so ki fada min tun da wuri na sani,"
"Ina so nima ki nemar min ɗin dik abinda na samu a suna sai na tara na biya, in ma basu cika ba na nema na biya,"
"To shikenan,ki gaida gida, ya kamata ki samu a bin hawa anan, dan kayan sun yi maki nauyi,"
(Kayan suna jameelaah ta sa aka d'ibar ma Mamalo masu yawa dan ta sake kwad'aita mata karb'ar bashin itama a fantama a bikin sunan ta)
Mamalo sai tunanin hirar su da Jameelaa take yi tunda ta koma gida, zuciyar ta ta gama aminta da shawarar Jameelaa dari bisa dari, ita ta san Mai zaman gida ce bata aikin komai Jameelan ma haka, amma a qallah suna da 'yan uwa da abokan arziqi ta san za suyi mata biki zata samu kuɗi, sai ta biya su in an gama suna, ko da kujerun ta ne ta shirya tsaf bayan suna ta siyar ta cika ta basu kud'in su ,in ta samu daga baya ta sai wasu.
Koda ta koma gida gum tayi bata ce ma Sadeeq komai ba akan wannan maganar, yayi tambayar duniya akan me ya sa take yawan tinani taqi magana, dole ya hakura ya qyale ta ya san halin matar shi ba ta da b'oye-b'oye da wani abu ya faru tabbas da ta fada masa.
***********************
Azumi ya kan kama Safnah ta zo hutu gidan yayar ta, dan haka koda yaushe suna tare da Umaimah, tare suke yin girki kullum Safnah na koya mata na zamani dan tafi kwarewa wajen su, ita kuma Umaimah tafi gwanancewa ana gargajiya, dan kuwa Haroon su yafi so, amma a saka kaya yafi son na turawa, yana son yaga matar tashi na d'ame ko ina na jikin ta ya dinga juyawa.
Haroon shi kan shi yana mamakin gano yanda yake da tsananin buqatar matar shi bayan ya yi aure wanda a da da ya kame kan shi kafin yayi aure har tinani yake anya lafiyar shi qalaou kuwa?
Sai yanzu ya gane ashe zina ma waje ta samu, in kai exposing kan ka a gare ta sai ta mamaye ka, amma in ka kame kan ka daga barin ta sai kaji baka da wata doguwar sha'awa da zata kai ka ga halaka duniya da lahira, idan ka biye wa zina sai ka gama jin daɗin lokaci qalilan saita guje ka,Allah na taimakon bayin shi da suke qoqarin nesanta kan su daga zunubi, amma wanda suke kusanta kan su daga zunubi sai Allah ya barsu da iyawar su tin da sun sauka daga hanyar shi, Umaimah ce taje wucewa ta gaban shi da wasu qananan kaya a jikin ta, Haroon ya kauda kan shi da sauri yace mata,
"Dan Allah je ki saka doguwar riga, azumi fa ake yi ni kar ki min targade a azumi na"
Dariya sosai Umaimah ke yi masa, saboda rigar doguwa ce amma mara hannu sai ta haɗa ta da dogon wando, sannan akwai hula akan ta kuma bata shafa komai ba a fuskar ta na kwalliya,kawai kayan sun haɗu ne kuma sun karb'i jikin ta sosai,turare ma baya baya ta sanya, wai amma shi a haka yana jin wani abu game da ita, wanne irin abu ke damun mijin nan nata ne haka?
"Sai dai kuma in barin gidan zaka yi gaskiya tinda dai naga doguwar riga ce a jikina"
"Assalamu alaikum"
"Wa'alaikumussalam"
"Yauwaa Aunty Hauwaa, thank God u ar here, dan Allah me ye matsalar riga ta?"
"As in, ban gane ba ku fahimtar da ni?"
"Ba komai rabu da ita,me zaku yi mana ne yau?"
Murgud'a baki Umaimah ta yi ita kan ta tana mamakin ina ta koyi rashin kunya haka, daya mata abu sai ta murgud'a masa baki,kallon ta ya yi ya qanqance ido ya ce,
"Dani kk?" Ta sake murgud'a bakin tace masa,
"Eh din"
"Ba matsala na yafe maki yanzu, Allah ya kaimu a sha ruwa Lafiya"
"Asha ɗin mana wake tsoron ka?"
"Ba komai bari dai a sha ruwan"
"Kun ga ku bari in ansha kun lalibo mai tsoron wani a cikin Ku kun ji? yanzu ki tashi muje mu fara shirin yin abin shan ruwa lokaci na tafiya,"
Aunty hauwaa har yau kunyar Haroon take ji in ana maganar da ta danganci soyayya, shiru ta yi tana murmushin yaqe ta faɗa kitchen ɗin umaimah, dan yau a wajen ta zasuyi aikin.
Bayan sun kammala ne suka d'ebi abincin suka baje shi a tsakar gidan, inda suke haɗuwa har Ishaaq a ci, watarana kuma a bangaren su hauwaan suke bazuwa a tsakar gidan su sha ruwa.
Umaimah ce tayi wanka ta sanya doguwar riga sannan ta saka qaramin hijabi kalar rigar, ba tare da tayi wata kwalliya ba, mai kawai ta shafa sai turare shima sama-sama, zama ta yi ta dauki qur'ani tana karanta wa tare da jiran dan lokacin daya rage yayi suje wajen shan ruwa, karatu take ta rerawa cikin muryar ta mai daɗin sauraro, Haroon ya shigo sanye da jallabiyya fara sol da hula itama fara, hade take da wandon ta rigar ya dage shi sama ya fito a ustaz ɗin shi sak. Zama yayi suka ci gaba da karatun a tare suna ta yi aka fara kiran sallah, suma suka kai aya suka ci gaba da bin kiran sallah, bayan sun kammala suka yi addu'ar da ake bayan kiran sallah tare da salatin annabi.
Addu'a suka yi tayi wa kan su, kowa da abinda yake roqa na alkhairi akan dan uwan shi.
"To baqaqen larabawa kuzo muje mu sha ruwa Allah ya amsa,"
Tashi sukai suka bi bayan Safnah, Ishaaq na ganin sun fito ya hau kama ciki shi a dole yunwa yake ji, dariya suka yi tayi suka zauna suka fara da dabino, sannan Ishaaq ya sha kunun gyad'a, Haroon kuma baqin shayin da Umaimah ke haɗa masa kamar na ibada ya sha, baya rabuwa da shan shayi matan kuwa da fruit salad suka fara.
Bayan sun gama karya azumin suka koma kan sallaya da suka shimfida Haroon ya ja sallah suka yi magrib.
Suna idarwa suka ci gaba da cin abincin su suna hira, sosai suke hira ana ta nishadi, can Umaimah tace,
"Dan Allah ka barni na koma gidan Yah umar ganin baby, kaga ga Safnah da Aunty Hauwaa ma sunce zasu je, gobe kawai sai muje ko?"
Kallon ta yayi ya haɗe fuska ya ci gaba da cin abinci, mugun kishin ta yake ji baya son tana fita, in ta fita ji yake kamar kowa ma kallon ta yake yi.
"Ni dai na amince maku ku je amma ban san me gidan naki ba ke Umaimah ko ya amince ko yana jin mulki, dan naga mulkin masu gidan ya motsa,"
Bai san sanda ya sa dariya ba wai mulki,cikin dariyar ya ce,
"Yah ni ban san yawan yawo ne fa,"
"Ziyara daban yawo daban, in kana so ba sai kawai ka kaisu da kan ka ba, in sun gama su maka waya ka dakko su, ko me kace?"
"Allah ya kai mu goben yah,".......
❤
[08/09, 10:18 pm] Aunty Hameeda: 💅🏻 MAZAUNA GIDA 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 29:
Azumi nada kwana 25 Jameelaa tai wa Mamalo waya dan tabbatar da amincewar ta akan karbar bashin da za su ci bikin suna dashi, a cewar ta gwanda su Karb'a da wuri su sai kayan da zata saka a kai dinki, in yaso daga nan ma sai su sayi duk wasu abubuwan da za a raba abikin suna wanda ba zasu ɓaci da wuri ba.
Mamalo ta tabbatar mata da amincewar ta akan karb'ar bashin, a take kuwa ta bugawa qawayen nata waya ta yi masu bayani kuma cikin qanqanin lokaci kowacce a cikin su ta aminta da a sake bata tinda ba ta yi wasa da wancan da aka bata ba ta dawo da shi akan lokaci,kuma ma dai su basu da wata lalura da shi kamar yanda ita mai iyali take da buqatar kud'in.
Godiya tayi ta masu sannan ta tura account no da zasu tura mata kuɗin, bata jima a zaune ba kuwa ta ga alert na kimanin dubu dari biyu sun shiga wayar ta,Mamalo ta sake kira dan taji ra'ayin ta akan irin kayan da take so, cikin tsananin farin ciki da nuna godiyar ta Mamalo tace,
"Na gode qawata Allah ya saka da alkhairi ya bani ikon biyan wannan bashi,to ni yanzu ai kune idon gari, kin san kayan da ake yayi kawai ki siyo min a kai ɗinkin,"
"To shike nan zan dinga rubuta komai aka siya na ajiye saboda ki ga nawa aka kashe kuma a ina aka kashe su, zan ajiye a waje na dan kar lissafi ya b'ata watarana, inshaa Allah sai dai ki ji na aiko maki telana ya gwada ki,"
"Na gode sosai qawar rufin asiri,"
"In Allah ya kaimu ki ka haihu lafiya kuwa har qawaye na 'yan gayu sai na gayyata dan in d'aga darajar ki kema a wajen matan lungun mu, zaki ga yanda sunan ki kema zai yi aji ya zama abin bada labari a unguwar mu baki ɗayan ta,"
Mamalo cikin washe baki ta hau godiya,bayan sun yi sallama Jameelaa ta buga tsaki ta ce,
"Ke dai za ai suna me kyau yarinya amma ai ke kan ki kin san ba zan bari ayi wanda zai fi nawa ba ko? Tin da ba hauka nake yi ba,"
Umar ne ya shiga parlourn ya zauna gefen Jameelaah tare da fadin,
"Ke da wa kike magana kuma?"
"Ba kowa tasbihi nake yi,"
"My love kina burgeni gaskiya, kina da yawan ibada da tsoron Allah, Allah dai ya qaramin qaunarki,"
"Ameeen Abban Humairah,"
"Dan Allah ina son zani asibiti gobe, naga tana yawan kuka naje naji meke damun ta,"
"Subhanallahi haka kawai take kuka ko sai an taba wani wajen?"
Kame-kame ta fara yi dan ganin yanda Umar ya rud'e, ta rasa ma me zata ce masa, daga baya ta ce,
"Ina jin kunne ke yi mata ciwo ko kuma ciki kasan shi ke rud'a yara, ana zaune qalaou in ta rikice da kuka rasa inda zan saka raina na ke yi,"
"Ehh gaskiya ya kamata ki kaita asibiti, goben zan aje ku sai na wuce, in kin gama ki min waya sai na zo na ɗauke ku,"
"Habaaa kana kula da marasa lafiya zan taso ka? Ka bari kawai zamu dawo nan nan da asibiti ka aje mu kawai kaje zamu dawo, inna dawo zan maka waya na sanar da kai,"
"To shike nan Allah ya kaimu,"
"Ameen ya Allah"
Har aka sha ruwa Umar bai ga Humairah ta yi kuka ba, na d'aga hankalin da za a ce bata da lafiya, haka dai ya bar maganar yayi tinanin wataqila da baya nan tayi kukan har Jameelaan tayi tinanin ko kunne ke damun ta, bari ya barsu suje saboda kwanciyar hankalin su baki ɗaya.
Da sassafe kuwa suka shirya dan kar ta samu layi a cewar ta,ai kuwa qarfe 8 a asibiti ta yi musu, yana fita ta wuce ta je ATM ta cire kuɗin siyayyar ta tass ta koma asibitin dan cin lokaci, sai da taga likitan yara aka duba su ba abinda ke damun yarinyar aka haɗa su da paracitamol in case in tayi kuka jikin yayi zafi, tinda tace in tana kuka jikin ta har zafi yake yi sai a bata.
Godiya tayi ta fita sai kasuwa, siyayya ta yi tayi na dik abinda ya dace, harda su sarqa da dan kunne da abun hannu, takalma da jaka, abubuwan da zasu raba abikin sunan dik sai da ta siya, ta wuce wajen telan ta ta bada ɗinki tace ya yi ɗinki dai-dai nata amma ya rage ta sama saboda Mamalo bata kai ta girman qirji ba.
Sai da ta cake masa kud'in ɗinki sannan ta tafi tsohon gidan su ta je ta kai wa Lantai sauran kayan ajiya, tace na Mamalo ne in suna ya zo dasu za ai amfani ta aje mata bata son Mamalo ta san tayi mata wannan siyayyar.
Ai kuwa Lantai ta dinga sa mata albarka tana godiya sai addu'a take Allah ya bar masu qawancen su har aljannah.
Sai da ta kammala komai ta koma gida ana kiran azahar lokacin da ta isa,sannan ta ɗauki waya ta kira Mamalo ta yi mata bayanin komai, Mamalo harda kuka dan farin ciki a ganin ta bata da masoyi yanzu sama da Jameelaa.
Suna yin sallama ta kashe ta kwanta a gefen Humairah da ta yi baccin wuya dan kuwa yarinyar tayi kuka har ta gaji tayi bacci, tinda suka fita bata samu ta shayar da ita ba,sai da suka dawo din tana waya tana bata mama, har bacci yayi gaba da ita.
"Mamalo kin gama cin gudummawar ki na suna a wannan wahalar dana sha, ko a nawa ban wahala haka ba,"
A haka suka yi ta shirye-shiryen suna a boye, daga wannan lokacin Mamalo kuwa dik maqotan ta samu take ta ɗan shiga a gaisa, wai a nata shirmen a haka za a saba har a ɗan samu su yi mata wani abu idan ta haihu (kamar aje su tayi, da can ba ai zumunci dan Allah ba sai dan a bata abun suna, hummmm).
Bayan kwana uku da kammala siyayyar komai da suke da buqata Mamalo ta tashi da naquda, naqudar ta zo mata da sauqi sosai dan kuwa bata dad'e tana yi ba Sadeeq ya kai ta asibiti suna shiga d'akin haihuwa da mintoci Mamalo ta haifi yaron ta mai matuqar kama da mahaifin shi, sai dai wani babban abun tashin hankalin Mamalo bata haifi yaron nan a raye ba, dan kuwa ko kuka bai yi ba da aka haife shi, ai kuwa tana farfadowa daga azabar haihuwa ta dinga washe baki tana a miqo mata abinda ta haifa ta gani, kowa a wajen shiru yayi,
Midwifes ɗin da suka amshi haihuwar Mamalo ita da wata a d'akin sune suka mata bayanin komawa da ɗan ta yayi, wata qara ta saki ta hau jijjiga idanun ta suka qaqqafe, a guje suka fita dan kiran Dr. Jariri kuwa na hannun Mahaifin shi wanda ke ta kuka saboda rasa babyn shi da yayi, ga kuma halin da Fateeman shi ke ciki.
Likita ne ya shige dan duba Mamalo, ko wanne taimako daya dace a bata an bata, sai dai inaaa shi alqawarin Allah in ya cika ba mai hanawa, kowacce mai rai zata dandani d'aci na mutuwa, Mamalo ta koma ga mahaliccin ta sakamakon kid'imewa da ta yi dan jin ɗan ta bai zo da rai ba, komai dawo mata yayi a lokacin ta hau tinanin kuskuren data tafka na amsar bashi mai yawa gashi yaro ya mutu kuma bata sanar da ko da mijin ta bane abinda ta aikata,wanda aka amshi bashin domin shi ko qamshin duniyar ma bai shaqa ba ya koma, hakan ne ya sa zuciyar ta bugawa ta bi bayan ɗan nata.
Sadeeq kuwa qaramin hauka ya hau yi masu a asibitin, da kyar aka samu ya nutsu, ya zauna a qasa ya dafe kan shi ya dinga rusa kuka, tabbas yayi rashi, yayi babban rashin abar son shi, ba zai taba samun kamar Fateen shi ba.
Da kyar ya iya ɗaukan waya ya kira Malam Buba mahaifin Mamalo ya sanar da shi rasuwar Mamalo da abinda ta haifa, Malam Buba shima kid'imewa yayi 'yar tashi guda ɗaya tilo yanzu ta zam babu, Lantai kuwa da ya sanar mata suma ta dinga yi.
Mahaifan Sadeeq sun samu halartar gidan su Mamalo sun miqa ta'aziyyar su ga iyayen ta,Sadeeq kuwa baya imm baya imm imm yanzu da ya zauna tinanin irin rayuwar jin daɗin da suka gudanar a gidan su yake yi shi da Fateen shi.
Jameelaa bata tashi jin rasuwar Mamalo ba sai washegari, kuka ta dinga yi tana kumawa cikin ranta tana fad'in
'Na shiga uku ni Jameelaa na lalace na d'akkowa kaina jaraba da bala'i, yau ya zanyi da bashin waɗannan bayin Allah dana amso ba tare da sanin kowa ba? Ga shi ba wanda ya san ma na amso mata sai mu ya mu kawai balle na kafa shaida, dan Allah Mamalo ki tashi na san baki mutu ba, wayyooo Allah na ta mutu ta barni da bala'i,'
Mutane sai riqe ta ake yi sanda ta shiga gidan ta tabbatar da gaske Mamalo mutuwa ta yi, wasu sun zaci tsabar shaquwar dake tsakanin su ce ta janyo ta shiga halin damuwar da take ciki, nan kuwa ba su san me ke cikin ran ta ba na damuwar inda zata samu dubu ɗari biyu ta biya bashin da suka ɗauka take yi.
Umaimah ma ta samu zuwa gaisuwar rasuwar Mamalo, mutane sun samu zuwa sosai saboda abun ya girgiza kowa, maqotan ta sai yabon ta suke yi, suna tina yanda take shiga a 'yan kwanakin, (dik da basu san abinda ke kai ta ba amma sun bada shaida mai kyau akan ta)
Bayan sallah qarama da sati ɗaya Qawayen Jameelaa suka fara doka waya suna tambayar ya suka ji shiru, qarya ta zabga masu da cewar har yanzu qawar ta ta bata haihu ba, ko da ta kashe wayar tinani ta dinga yi ko sata zatai a wajen Umar ne ta biya su? To ta yaya zata saci har dubu ɗari biyu bai gane ba? Ko da da take sata ma qananan sata take yi ba manya haka ba.
Dik wani irin tashin hankali Jameelaa ta shige shi a wannan lokacin,kayan sawar da aka d'inka aka kawo mata a ranar ta fara cigiyar masu siya, haka kuwa aka dinga yi mata tayin walaqanci, a haka ta saida kayan wajen dubu hamsin banda kud'in ɗinki da ta bayar wajen dubu arba'in, kuka kuwa Jameela ta dinga yi wanda ta rasa mai lallashi.
Wanka tayi ta fita ta bar Humairah wajen Kulu Umar ma bai san zata fita ba, gidan su Mamalo ta je, da sallama ta shiga suka gaisa da kowa ta nufi d'akin Lantai,Lantai na zaune ta zabga tagumi tana tinanin d'iyar ta hawaye sirara na bin kuncin ta, dan kuwa bata san sanda zata ji sanyin wannan rasuwa a ranta ba, 'yarta ta kenan guda ɗaya bayan sun gaisa da Jameelaah a mutunce ne Jameelahn ta ce,
"Lantai ki kara hakuri kin ji?hakurin dai zamuyi baki ɗaya dole, Allah dai ya jiqan ta,"
"Ameen Jameelaah ba abinda zan ce maki sai godiya, kin gwada min soyayyar da kike wa Mamalo domin Allah ce, Allah ya albarkaci rayuwar auren ki kema,"
"Ameenn Lantai......immmm.... damaaa.... na zo ne akan kayan dana kawo kwanaki, dama a gaskiyar magana bashi muka ci ni da ita, dan a fita suna lafiya kar a ji kunya, yanzu na zo na amsa na sai da su ko da ba su kai kud'in dana siye su ba na haɗa da kud'in wajena na biya masu kuɗi kud'in su, yanzu dik sauran kud'in ni zan cika na biya gashi banda ko sisi, tinda abunnan ya faru hanyoyin samuna suka toshe gaba ɗaya kamar an datse min su, ko nera dubu Abban Humairah bai sake bani ba"
Cike da bacin rai Lantai ta kalli Jameelah ta ce,
"Kan uban can ! auuuu ina yabon ki sallah zaki kasa alwala Jameelah? Ina ganin Mamalo bata da masoyi sama dake ashe har yanzu halin ki na nan na son abun duniya? Yarinyar ma ta mutu amma ba zaki bar ta ta huta ba?"
Wani irin tashin hankali ne ya rikitowa Jameelah ta ji kamar zata zaga dan tsabar damuwar da take ciki, cikin fitar numfashi sama-sama ta ce,
"Ba haka bane Lantai da gaske bashi muka ci wajen qawaye na ni da marigayiya yanzu haka sai waya suke yi min nayi qarya nace bata haihu ba, dan Allah ki rufan asiri ki ban naje na siyar na haɗa dana hannu na na rage wata asarar,ki barni naji da biyan sauran kudin, in baki biya bashin bane ma zata wahala a qabari, dan kuwa tana cikin azaba dan akwai bashin mutane akan....."
Gaffff naji qarar duka ya sauka a bakin Jameelah, ai kuwa Jameelaah ta buɗe murya tun qarfinta ta zunduma uban ihu ta dafe bakin ta da ya fashe, tana kallon Lantai a tsorace, Lantai kuwa cikin tsananin fushi da bacin rai ta ke nuna Jameelaa da yatsa ta ce,
"In kika kuskura kika sake kira wa yarinya ta azaba a qabari na rantse sai kin kwashe haqoran ki a qasa, dan uwar ki tashi ki bar nan, ki kira kotin qoli ta amsar maki kayan matsiyaciya wadda bata san mene ne mutunci ba,"
Qofar dakin Lantai kuwa nan da nan aka taru ana son jin me ya faru, Jameelaah kuwa sai tayi gum da bakin ta dan tasan tonuwar asirin Mamalo tonuwar nata asirin ne, Lantai ma ba zata so wannan labarin ya fita ba itama, tankad'a Jameelaa waje ta yi, daga dakin ta, sannan ta ce,
"Kar ki bari idona ya sake shiga naki mara mutunci, ki bar nan gidan ko na qarasa maki abinda na fara dan kuwa sai na cire maki haqori"
Jameelaah ba baki sai ido haka ta d'au jakarta ta fita a qofar gidan ta sai ruwa ta wanke bakin ta dake fidda jini ta yi gida.
Ita dai yau ta shiga uku ina zata nemo dubu ɗari da goma ta biya bashi? Ko wajen Mum zata ta roqa ne? Ko zuwa zata yi ta kai dubu arba'in wajen malamai su juya mata da kan Umar ya mata kyautar wannan maqudan kuɗin a dare ɗaya, ko kuma yau zuwa za ta yi ta sha maganin mata da ake cewa gida ko mota ko kyautar kujerar makka wataqila idan Umar ya gigice zai yi mata kyautar da zata wanke mata takaicin bashin da suka gingimo ba mai biya????
*A cikin shawarwarin nan da take yi, wanne ne kuka zaba?*
*Ina ma masoyan Mamalo ta'aziyya rasuwar takuyi hakuri, haka labarin yazo, na san ba za kuji daɗi ba amin afuwa*
[08/09, 10:18 pm] Aunty Hameeda: 💅🏻 MAZAUNA GIDA 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 30:
Zaune take ta saka sarqar da Umar ya bata ta zinare a gaba tana ta kallo, tinani take yi ko saidawa za ta yi ne ta fidda kud'in mutane dan rufuwar asirin ta, dik da dama ba son komawa makaranta take yi ba balle a gano maqaryaciya ce ita,dan kuwa in ta bari magana ta fita ajin ta ya zube a wajen kowa da take huld'a da shi a makarantar,ko a wajen qawayen ma bata isa magana ba sai dai su rabu, dan ba su son harkar qaranta su.
Kukan Humairah ne ya dawo da ita daga dogon tinanin da ta tafi, can ta hango ta gefen gado da dikkan alama fad'uwa tayi, sai tsala ihu take yi kuwa kamar zata tsaga gidan, Kulu ce ta shiga dakin tana tambayar lafiya? Ita kanta kulu ta kula da yanda gaba ɗaya yarinyar bata samun isasshiyar kulawa daga wajen mahaifiyar ta sam.
Kuka Jameelaah ta fashe da shi dama ta kai iya wuya wajen quluwa da shiga damuwa, a gigice kulu tace,
"Subhanallahi uwar d'aki na me ya same ki haka ki ke kuka? Me ya same ta itama naga gefen kan ta yayi ja kamar ta bige? kawo ta nan na gani,"
Kuka kawai suke tsalawa daga Jameelahn har jinjirar ta, ji take ko zata sanar wa Umar me ya faru ne dan ya biya kuɗin a huta, amma ba zata so ya gane ta amshi bashi da sunan Humairah ba ba zai ji daɗi ba tinda komai ya yi iya yin sa dan yaga ya wadata su da duk abinda suke da buqata,cikin kuka Jameelah tace,
"Dan Allah Kulu kin san inda ake saida gwal?"
Kallon ta kulu tayi da mamaki tace,
"Eh na sani, amma uwar d'aki na me zai kai ki saida kadarar ki?"
"Ba ruwan ki ni dai kawai ki nuna min muje yanzu kafin Abban ta ya dawo muje mu dawo,"
"Ai kuwa sai dai ki bari ya dawo yaci abinci ya koma, sannan muje dan kuwa ya kusan dawowa,"
Wasu hawaye ne masu zafi suka sake zuba mata, tabbas ta dakkowa kan ta masifa har da bala'i, amma kuma ta
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 18 Chapter of 30