Reading adon dawa Chapter 32 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ne sai akai ni Abuja.
madina tace babu komai kada ki damu Allah Ya sa haka shine mafi alkhairi, kaltum na
lura duk hankalinki atashe yake har kin rame ba kamar sanda na ganki ba kwanaki, alh
Adnan din naki kike ki?
haba kaltum idan kikayi masa haka baki kyauta masa ba, suma iyayanki sunga babu irin
godiyar da zasu mishi ne illa subashi ke domin yayi dawainiya dake kowa yasan yana
son ki.
kaltum ta matse hawaye tace ba kiyayyarsa bace ta sani damuwa ba, nauyin sa da
kunyarsa nakeji tamkar babana na dauke shi, ramewa da kiga nayi bai wuce Zafin
mutuwar goggo fattu ba da har yanzu take damuna.
madina ta zabura ta dafe kirji tace InnaLillahi wa inna ilaihi raji'un, yanzu goggo fattu ta
rasu?
kaltum ta matse hawaye tace yau sati biyu kenan a zangon daura akayi jana izarta bamu
dade da dawowa ba, ai acan yan uwan baba suka hadu sukayiwa alh Adnan maganar
auren mu dayaje gaisuwa daga baya ma matarsa taje dana gaishe ta bata amsa ba,
shine yasa nashiga damuwa nasan halin kishinta zata iya babbakawa kishiya wuta.
madina da sumayya suka cigaba da bata shawara da nasihohi masu kwantar da hankali
sannan sukace ta rakasu wajen iyayanta don su musu gaisuwa,
Madina ta karbi numbar wayar alh Adnan tace idan taje gida zata kirashi tamishi gaisuwa
sannan su tattauna don taji ra'ayinsa akan maganar auren.
a haka suka rabu kaltum ta raka su har wajen get inda suka ajiye motarsu suka shiga
suka tafi ita kuma ta dawo gida.
tafiyarsu Madina da kwana uku alh Adnan ya kirawo kaltum a waya, cikin rawar murya
da fargaba ta gaisheshi ya amsa cike da fara'a yace gobe ki shirya danladi yakaiki
gidansu Madina ki yini, da yamma ya koma ya dauko ki,
ta amsa da to na gode, bayan yakashe wayar sai mamaki ya rufe ta nan da nan takira
Madina tana tambayarta yadda sukayi da alh Adnan don yanzu ya kirata yace gobe taje
su yini,
madina tayi dariya tace dadin baki na masa na nuna ina goyon bayan aurenku dari bisa
dari shiyasa yaji dadi,
kaltum tayi dariya kawai ta kashe waya.
washe gari da wuri kaltum ta shirya ta caba ado da wata hadaddiyar shadda gezna kalan
jan duhu wato maroon colour wacce akama surfani da brown din zare, riga da siket da
dankwali, ta saka takalmi da gyale kalan brown, tayiwa iyayenta bayananin abunda alh
Adnan ya umurceta tayi sai sukaji farin ciki ya kamasu tunda har akasamu ya fara yi
mata waya a yanzu,
ta kame a bayan motar danladi yaja bai tsaya a ko inaba sai kofar gidan Doc sumayyah
Tukur,
kamar yanda ta umurceshi ta sake umurtarshi daya tafi ya dawo da la'asar, ta shiga ciki
kai tsaye ta iskesu a falo su uku ne kadai Madina , sumayyah da maigidanta Doc bashir,
sunata hira babu abunda yake damunsu arayuwa sai dariya suke kyalkyalawa, suna
ganin kaltum sai suka hau murna ta durgusa cikin fara'a ta gaishesu sannan ta sami
kujera ta zauna.
Dr bashir yace af dama wannan ce kaltum matar mambela dan ADON DAWA?
su dukka suka tuntsire da dariya.
sumayyah ta harareshi kaji har sunan ADON DAWA ya rike, kamar dashi akaje bur
sudan?
shigowar Abba da kaninsa Anas ita ta katse hirarsu aka hau gaggaisawa,
kai tsaye Abba ya wuce gaban Madina ya ajiye himilin ledoji a gaban ta,
ta dubeshi tayi murmushi ta fada cikin sanyanyar murya mai cike da sakon so da kauna
tace Abba bazaka yarda da maganarda nake gayamaka bako?
so kake muyi pada kenan?
nace saye sayen nan naka yayi yawa ka dinga hutawa kaki jiko?
sumayyah Tukur tace a'a mu munaso inke bakya so, da bakya nan ai bai sayo mana ba,
kudi ne dashi, me anfanin kudin in ba aci ba?
Madina ta bude ledojin daya kayan itatuwa ne lemo ayaba da abarba daya ledar kuma
tuffa ce da inibi, daya ledar kuma mayukan shafawane da turarurruka sai wani dan
karamin kati (greeting cart)mai dauke da sakon so da kauna, katin kadai madina ta
dauka ta karanta ta kalli Abba tayi murmushi ta ajiye a gefenta shima irin murmushin ya
mayar mata.
sumayyah Tukur ta dubi Anas tace kaga ka fita daga idona na rufe zan tona maka asiri
idan baka daina turamin sako cikin wayata ba,
sai kowa ya dubesu,
yace yi hakuri 6star ki rufamin asiri, Abba yace sako wani iri kuma?
dr bashir yace eh gaskiya a tona wannan sirrin kowa yaji, ya duk muna zazzaune ka
dinga tura mata sako don gulma?
sumayyah tace ya dade yanason kaltum wai ce min yayi in kira masa ita wancan falon su
gaisa wai in fada mata yana sonta.
su dukka suka kwashe da dariya.
kaltum taji kunya saita sunkuyarda kanta kasa bata sake dagowa ta dubi Anas ba,
madina tace wallahi kuwa kun dace saidai karigada ka makara anbayar da ita da sai na
tsaya maka kanina.
Anas yaji hankalinsa ya tashi yace ai tunda ba ariga an daura ba zan iya shiga filin dagar
adama dani mai rabo ya dauka.
sumayyah tace kadama ka fara shiga filin dagarnan don dakai zata kife wanda za aje
neman aurenta wajenshi shine zai aure ta.
ban fahimce kiba?
Abba ya tambayi yayar sa.
madina tace alh Adnan zata aura nan da yan watan ni,
Abba ya gyada kai yace lallekam babu mai jadashi yaro karma ka shiga bakin rijiya don
ba wajen wasan yara bane, nifa na dauka yayantane da farko sai nace ko babanta ne
ashe shi ya riketa yanzu zai aureta ko sun dace yana da matukar kirki.
Anas ya fice daga gidan, kallo daya zakayi masa ka tabbatar baiji dadin maganarnan ba,
madina taja kaltum dakinta a inda ta dinga nuna mata abubuwan alkhairin da ta samu
dawowarta nan, dinkuna kala kala wadanda Abba yayi mata ta nuna mata wasu
akwatuna masu kyau har guda hudu saiti tace kayan lefenta ne Abba ya fara hadawa,
auren nan da watanni uku, a Abuja zasu zauna sbd acan yasami sabon aiki shine lauyan
babban bankin nan CBN, Madina ta dubi kaltum ta fada cikeda fara a tace kaltum ki duba
kiga yadda Allah Ya canza mana rayuwa cikin dan kankanin lokaci, shi yasa duk halin da
musulmi ya tsinci kansa ya godewa Allah, jarabawa ne idan Allah Ya tashi sakayyah sai
ya juye maka dadin da baka taba zatonsa ba, banda Allah wazai yi mana irin wannan
kyautar?
kiduba kiga yadda ni dake muka canza kada kiyi bakin ciki da duk yadda kika tsinci
rayuwarki, alh Adnan alkhairine da rayuwarki, ko ba a fada miki ba nasan mambela ma
mai kaunarki ne Allah cikin ikonSa da hikimarSa Ya raba ku, ki godewa Allah a duk
halinda kika tsinci kanki.
kaltum ta gyada kai tace hakane aunty Madina nasan da haka ina addu'a kuma zanci
gaba da addu'a har karshen rayuwa ta.
.ADON DAWA P 46
LITTAFI NA HUDU
TRUE LIFE STORY
.
nasan mambela ma mai kaunar kine, Allah cikin ikonSa da hikimarSa Ya raba ku, ki
godewa Allah a duk halinda kika tsinci kanki.
kaltum ta gyada kai tace hakane aunty Madina na san haka ina addu'a kuma zancigaba
da addu a har karshen rayuwata, na godewa Allah kuma bazan taba raina abunda Ya
bani ba.
Madina tace Allah Ya yi miki albarka idan kika rike wannan bazaki taba danasani ba a
rayuwar ki, kiyi addu a kibarwa Allah zabi Shine abunda na rike tuntuni kuma bana
nadama, ta bude wata katuwar leda ta zazzabo mayuka, janbaki da hoda turarurruka da
atamfa ta zuba ta mikawa kaltuma tace gashinan na baki kije kitayin kwalliya naga kina
son ado.
kaltum ta rike baki tace haba aunty kin juyemin kusan dukka ai yayi yawa ki rage nima
duk karshen wata alh Adnan yana bani kudi inje well care super market in sayo kayan
kwalliya.
Madina tace ai ina da su dayawa keda Shahida na rabawa wannan, bakiji ina yiwa Abba
kashedi ba?
cewar ya isheni haka, shiga gowa fita goma sai yayi min sayayyah bansan irin kyawun
da yakeso inyi ba koso yake in koma indiya don kyau oho.
kaltum tayi murmushi tace Abba yana son ki ko minti daya kayi dashi zaka gane hakan,
Madina tace kwarai kuwa nasan dahaka tuntuni daddy Tukur ma yasha kirana har
falonsa ya yita bani hakuri a bisa wulakancinda sukayi min a rashin sani sannan ya
rokeni in saki jiki in kwantar da hankalina inyarda in auri Abba tunda ya tubure duk
duniya babu wacce yakeso saini, kuma ba haramun bane raya sunnah ne saboda
Manzon Allah (s a w)Ya auri nana Khadija (R.A)a bazawara kuma ta girmeshi ya
nuna min kuskuren da nayi a baya dana hana Abba ya bayyana musu halinda yake ciki,
ai ba zasu hana ba saboda sun yarda da tarbiyyata sunsan bazan cuci dansu ba, daga
karshe ya roke ni da rike dan su amana fiye da yadda na rike Tasi'u, inso Abba kamar
yanda duniya ta shaida Abba yana so na, irin wadan nan nasihohi mahaifinsa yake min
aduk lokacin da muka hadu.
kuma duk bayan kwana biyu ina zuwa gidansu Abba inyiwa mummy hafsat duk abunda
takeso kamar share-share da girke-girke,
nida Tasi'u kuwa general tukur yayi mana katangar karfe haka tsakaninsa da Abba,
saboda ya fara takurawa rayuwarsa koda yaushe saiya tari Abba a hanyah yanayi masa
hayania harda cewa sai yaga bayansa sannan nima ya dinga bina kenan har tsakar falon
mummy hafsat wai ni matarsa ce, shine ran daddy tukur ya baci allurar soja ta tashi
yasa sojojin nan suka wurgo shi waje sannan muka sami lafiya.
kaltum tayi ajiyar zuciya tace har ya bani tausayi ma daman haka dunia take hakkin
wani masifa ne idan ka cuce mutum tun a duniya Allah Ya ke fara nuna sakayyah dubi ni
da goggo fattu fa saida Allah ya kaskantar da ita kafin ta bar dunia, tayi nadama hade da
danasani ai ina tsoron daukar hakkin wani.
madina tace haka alkhairi yake idan ka gina alkhairi zaka girbe shi sbd bayan tafiyata
sanda gaskiya ya bayyana sai yan anguwa suka para tausayin 'yayana su kayi ta
kyautata musu musamman ma shahida ko abinci aka hana ta agidansu sai makwabta su
kirata su bata suce Madina muma ta taimakemu alokacinda bamuda shi, su bata sutura
suce madina ta cire kayan jikinta ta bamu idan mukayi sha'awar kayan, kin gani da abun
tsiya na shuka alocinda makwabta dana tsallake na tafi na bar 'yayana sai an zageni a
gabansu kuma baza ataimakesu va.
kaltum bata dawo daga wajen Madina ba harsaida ta sami nutsuwa da kwanciyar hankali
saboda nasihohi da ta dinga yi mata, data isa gida da farin ciki kaltum ta nunawa
mahaifiyarta abubuwan alkhairan da Madina ta bata sannan ta kira alh Adnan a waya ta
shaida masa ta dawo.
sai yayi mamaki da yaji muryarta radau tana walwala harma da kirkiro masa hira take
sai ya tabbatar da Madina tayi masa gini mai karko a zuciyar kaltum, don haka ya sake
tabbatarwa Madina macece mai nutsuwa da sanin ya kamata.
akai akai kaltum na ziyartar madina haka itama madina tanasa sumayyah ko abba su
kawo wajen kaltum su dade suna tautaunawa da neman shawarwari akan abunda ya
shafi aurensu daci gaban rayuwarsu gaba daya har wata rana madina tazo da daddare
ita da abba koba a fada maka kaga ango da amarya masu matukar kaunar juna sun
burge kaltum matuka yanda taga suna tafiya suna hira wasa da dariya saisu ka mika
mata katinan bikin su,
daya na walima daya daya kuwa sunan alh Adnan dana malam saleh ne shine na daurin
aure,
farin ciki ya lullube kaltum bata san lokacinda tafashe da kuka ba ta rungume Madina sai
ita ma ta fara kuka irin wannan hawayen farin
cikin ne ya surnanowa abba daman ance kuka iri irine na bakin ciki shine mai radadin fita
na farin ciki kuwa sanyi kalau zai fito babu zafi idan ya fito shar sai a goge a yi dariya a
tafa.
.
RANAR DAURIN AURE
asabar ce ranar daurin auren barister Abba Tukur da Madina a farfajiyar gidan general
tukur shine uban amarya kuma daman Uban angone don haka tuwona maina kenan.
kamar yanda kowa yasani babban goro sai magogin karfe ba kasafai zakaga jifgin
talakawa ba a al'amuran attajirai kamar yadda ganeral tukur da iyalansa suke da
matsayi abokansu ma masu matsayine, danginsu masu kudi ne, abokan aikinsu daga ma
aikatan daban-daban sun hallara ma'ana manyan sojoji sunzo don general tukur haka
manya furofesoshi sunzo saboda da barista hafsat tukur jami'a daban-daban, sannan
manyan likitoci daga manyan asibitoci daban daban sun hallara saboda Doc sumayyah
da maigidanta Doc Bashir,
injiniyoyi ba abarsu abaya ba saboda engr Anas, sai dimbun dalibai daga jami'ar
unguwar sun hallara,
saboda Madina don kirkinta alh Adnan da malam saleh suma suna daga gaba gaba,
kusada ango maroka da makada suna nasu aikin yan jarida da hotuna da bidiyo suma sai
dauka suke kowa yana fadar albarcin bakinsa na alkhairi saboda farin ciki.
masu iya magana na cewa da dai dan wani tarkataccen wani, a lokacinda dubbannen
jama a suke cikin shagalin cin alewa da goro bayaga lemuka da abinci iri iri a wajen
daurin auren Abba da Madina.
shikuwa agidan Tasi'u a cikin tashin hankali suke saboda Tasi'u nacikin gidansa
hankalinsa inyayi miliyan ya tashi haka ya tashi hankalin iyalansa saboda rike kai yayi
yana ihu yayinda ya dinga faduwa kasa fuk sai an yayyafa masa ruwa sannan ya farfado,
'ya yan madina su dukka uku basu iya halattar wajen daurin auren ba suna ceto ran
mahaifinsu haka ma matansa tun suna ganin shirme yake don suji haushi yakeyi har
suka fara tsorata suka tabbatar ba wasa yakeyi ba da gaskene, suka rugo suka kamasa,
suka dauka a surutunsa baya fasa tsinewa sa'ada wacce itace tayi sanadiyyar rabuwarsa
da Madina, ya dau alwashin Madina na tarewa agidan Abba itakuma zata tare a gidansu
ma'ana zai saketa, rirrikeshi sukeyi hakuri ake bashi shikuma tamkar dalmar wuta ake
dana
masa a kahon zuci musamman dayaji an mika sadaki lakadan dubu hamsin aka shafa
fatiha, jama'a sun shaida Abba ya zama mijin Madina saiyaji tamkar ya cire kayansa ya
danna waje da gudu aka rirrike shi.
Madina dai batasan abunda yake faruwa va tana can agidan sumayyah itada mata yan
uwanta suna ta shagalinsu don kaltum da jakar kayanta tazo sai ta shafe kwanaki uku
cur rakiyar amarya har Abuja za aje da ita,
alh Adnan ya yarje mata, yinin biki tayi kyau walima tayi kyau an ragargaza wa azi da
karatun alkur ani haka ango da abokansa sunyi reception hadadde amarya da ango sun
caba ado sunyi kyau matuka ko makiyansu vaza su kushesu ba, komai ya wadata babu
yunwa babu kishir ruwa an bubbuga abubuwa daban daban aka rarrabawa wadanda
suka halacci bikin da hotunan amarya da ango a kalandu da memo, t shirt hankacib,
barguna, atamfofi , bokitin roba agogo da dai sauran su.
amarya da manyan aminanta a jirgi suka tafi
Abuja sauran jama'arne suka tapi a motoci,
kaltum na makale a kugun amarya itada shahida don haka sun sami tafiya a jirgi
koma dai ame sukaje kowa dai ya isa lafiya kuma kowa ya dire akatafaren gidan amarya
da yake unguwar maitama, gida ne matsanancin girma dauke da falo biyu kicin daya
dining area, dakuna uku kowanne da bandakinsa aciki ga farfajiya mai fadi inda zai ci
motoci uku sai boys quaters daga bayan gidan,
ba girman gidan bane keruwar gidan, tsara shi shine keruwar gida saboda gidan nan ya
tsaru da ga ginin har kayan ciki anzuba kayan
kalarda ya dace komai nagidan ruwan zuma ne brown, yadda kowa yaga gidan nan haka
ita ma Madina saida aka kaita tagani koda wasa Abba bai shawarce taba ko a labari bata
san sanda ya gina ba balle lokacinda zai zuba kayan ciki babu sisinta ya zuba mata
komai sabo,
hawaye kawai take zubarwa na farin ciki saitayita godewa Allah a zuciyarta.
farin cikinda kaltum da shahida suke yi har yafi na kowa saikace su aka mallakawa
gidan,
kowa yana san barka musamman sumayyah tayiwa Madina murna tayi mata fadan zama
lafiya,
kwanaki biyu akayi cur a gidan amarya aka kalkalewa amarya da ango gidansu tas tas
sannan aka tapi aka barsu su kadai,
Abba yace saboda zaman kadaici da kuma girman gidan zai samo mata masu aiki biyu
babbar mace daya da yarinya karama donsu tayata aiki,
Madina tace Allah Ya sauwake ita bata bukatar yan aiki zatayi aikin ta dakanta haka
bazai hanata ta kula da mijinta ba kuma,
dole tasa Abba ya hakura da zancen yan aiki saidai koda yaushe suna rigima idan yazo
tayata aiki, shi yana tausayinta wai aikin gida yayi mata yawa ita tana tausayinsa bataso
yasha wahala tafi so ya koma ya zauna ta dafa ta kawo masa yaci, daga karshe suka
tsayarda shawara guda daya cewar duk sanda zata shiga kicin Abba zai jawo kujerarsa
ya zauna yana tayata hira amma bazai tayata aiki ba, saboda bayaso tayi nisa dashi dole
ce take fita dashi wajen aiki daga ya taso daga aiki baya zarcewa ko ina sai gida wajen
Madina, haka ita ma batajin dadin zuciyarta idan Abba ya fita bata samun nitsuwa har
saiya dawo gareta don haka Abba ya dawo dan lele ko jariri sai haka, tabbas hasashensa
yazama gaskiya ba dukka mace vane zata iya biyayyar da Madina takeyi ba musamman
ma yanzu data kara wayewa a wajen sumayyah ta kara, kozuwa da wahalar rayuwa ta
sake tabbatar wa Abba mai kaunarta ne duk duniya babu mai kaunarta fiye dashi, ta
sake tuna amanarsa da mahaifansa suka bata ta dinga tuna irin hatsari da tuggun da
Tasi'u ya dinga jeho masa don ya tsoratar dashi yafasa aurenta amma baiyi ko gezauba,
uwa uba irin dukiyarsa daya kashe don ya dadadawa rayuwarta yana kan kashe mata
ma don duk abunda ya mallaka baya kyashin bata har sai tace ya isa haka,
bayan aurensu da watanni biyu ranar litinin da misalin karfe goma sha daya na safe
Madina na kishingide akan doguwar kujerar dake tsakiyar falonta tana rike da
tsadaddiyar wayar ta wacce aka yi mata lakabi da Black Berry tana turawa abun
kaunarta Abba sakon soyayya da tsantsar bege sai taga wata lamba ta shigo, ma'ana
ana kiranta saidai tana matukar mamakin ganin sunan mai kiran dai dai wannan lokaci
tayi firgigit ta tashi zaune ta amsa cike da fargaba ta fada cikin girmamawa, alh Adnan
ina kwana?
ya amsa cike da fara a, yace ina mai gidan ki tun dazu ina kiransa vai dauka ba.?
Madina tace yana wajen aiki ko baya tare da wayar akusa dashi nima dai munyi awa
rabonda muyi magana.
alh Adnan yace ba mamaki to, don Allah idan yakira kice masa yayi kokari ya kawo ki
ofis dina ina neman ki.
ta dafe kirji tace alh lafiya?
badai matsala dai aka samu da kaltum ba?
alh Adnan yace karki damu va matsala vane sai alkhairi.
cikin sanyi jiki tace to shikenan zan fada masa zamu zo insha Allah.
yace to daga nan zuwa karfe uku na yamma ina ofis idan ya wuce uku to saidai
kusameni a gida.
suna ajiye wayar sai Abba ya kira tayi caraf ta dauka cikin laulausar murya tace my heart
inaka shigane alh adnan yayita kira va ka amsa ba?
Abba yayi murmushi yace my life Wallahi aikine yayi yawa yanzu na dauko wayar naga
missed calls dayawa hardana alh Adnan din nace sai na kira gimbiya ta tukunna
zankirawo su daya vayan daya, lafiya yake nemana?
Madina ta lumshe ido tace to dai da baisameka ba niyakira yace infada maka ka kai ni
ofishinsa yana nemanmu kaga nan kiran mahimmanci ne kuma da gaggawa.
Abba yace to Allah Ya sa alkhairine bari inkirawo shi inji, ki shirya zanzo yanzu na
daukeki muje.
ba ayi awa ba saiga Abba a gida ya tarar da Madina ta shirya tsaf a zaune a falo tana
jiransa, ya dube ta yayi murmushi yace my love kinyi kyau,
ta lumshe ido tace na gode ai kai daman konayi wanka ko ban yi kwalliya ba sai kace
nayi kyau,
yace tashi mu tafi na kira shi yace mu kwantar da hankalinmu ba matsala bace bazai
wuce dai zancensa da kaltum bane, ya kama hanun ta ya jata suka pita, ya bude mata
murpin mota ta shiga sannan ya xaga Shima ya shiga suka pice.
basu sha wahala ba wajen hawa suna shiga suka iskeshi a luntsumemiyar kujera yana
juyi yayin da yake ta rubuce rubuce akan wasu file yana ganinsu sai yayi dariya yana
nuna musu kujeru,
suka zauna bayan sun gaisa sai ya jawo wayarsa ya kira wata lamba cikin harshen
turanci yake magana yace kazo ofishina gasu sun zo.
Madina ta kalli Abba shima ya dube ta cike da mamaki gaba daya suka kalli alh adnan
sai yayi murmushi yace kada ku damu so nake mutumin yashigo Ya tabbatar min kuyake
nufi sai inyi muku bayani, idan kuma baku bane shi kenan.
Madina ta gyara zama tadafe kirji tace alh lafiya dai ko waye mutumin yasan mune me
muka yi masa?
Abba ya dafa kafadarta ya fada cikin laulausar murya my love ki kwantar da hankalinki
kinsan fa kina da hawan jini banaso ki dinga yawan damuwa meyasa kike firgita alhali
kinsan babu wanda kika yiwa laifi kuma ke kike yiwa jama'a nasiha su yarda da
kaddara....
kafin ya rufe bakinsa aka turo kofa aka shigo, gaba dayansu su dukka suka dago ido
suna duban mai shigowa,
idonsa ya dira akan Madina itama ta dubeshi saitayi wuf ta mike tsaye kamar an
zabureta ta fada cikin yare wanda yayi kama da inyamuranci sai shi ma ya mayar mata
da amsa sai suka ruga da sauri suka rungumi juna suna rusa kuka.
hankalin Abba ya tashi ya fada cike da damuwa Madina lafiya kikaje kika rungumi kato?
Kin san shi ne?
kuka ya hanata bayani shi kuwa daman mutumin ko hausa bayaji balle ya fahince
abunda Abba ke fada,
alh Adnan ne ya hauyiwa Abba bayani yace wannan mutumin da kake gani mun dade
muna harkar karuwar arziki tare daga enugu yake, muna safarar man fetur ne shekara
da shekaru muna abota, mutum ne mai amana har Allah Ya sa ya auri musulma muka
masa nasiha ya musulunta, sunan sa ada innamani yanzu kuwa Abdullahi, dazu yazo
ofishina sai kawai yayi ido hudu da kalandarku ta bikin aurenku gata can sai naga yatafi
da sauri ya fisgo yana kallo har hannayensa yana rawa na tambayeshi lafiya dai ko?
saiyace tayi masa kama da kanwarsa data bata shekara da shekaru yana neman ta
daman ance masa tana kasar hausa ta auri musulmi .to shine na kira wayarku alokacin
babu tantama nasan Madina ce yar uwarsa, tunda na sami labarin tarihin rayuwarta ashe
kuwa itace din, shi ne yasa kagasun rungumi juna suna kukan murna .
Allahu akbar Allah abun godiya kalmar da Abba yake ambato kenan alokacin da alh
Adnan yake bawa Abba labarin abunda yake faruwa ita ma Madina cikin yarensu ta bawa
yayanta tarihin rayuwar ta sannan ta gabatarda mai gidanta Abba,
yayanta ya rumgume Abba yana farin ciki sai godiya yake yi masa nandai suka dunguma
suka tafi gidan Madina don yaga muhallinta shima kuma ashe matansa biyu daya ba
musulma ba ce tana enugu amaryar ce musulma beyarabiyace tana nan cikin Abuja a
maitama, basu da nisa ma,
rayuwa ta dawowa Madina sabo fil mai tafe da tsagwaron farin ciki tana kuka tana bawa
yayanta tarihin yadda Abba ya tarki tafiya enugu nemansa saiya yi hatsari a hanya
saigashi cikin ruwan sanyi Allah Ya hadasu.
Kun ga yadda na yiwa Abba Mutumci na
ADON DAWA 47
.
TRUE LIFE STORY
.
rayuwa ta dawowa Madina sabo fil mai tafe da tsagwaron farin ciki tana kuka tana bawa
yayanta tarihin yadda Abba ya tarki tafiya enugu nemansa saiya yi hatsari a hanya
saigashi cikin ruwan sanyi Allah Ya hadasu,
tun sanda Madina tahadu da dan uwan ta bata ta taba kwana ta yini ba batare data kira
shi awaya taji muryarsa ba, haka shima bai taba kwana 2 baizo ya ganta ba indai yana
gari haka yake ta ambulo mata dukiya domin mutum ne mai dinbun dukiya da
kyaututtuka da ya kamata yayiwa iyayensa da danginsa sai yake jifgewa Madina domin
ita kadai ta rege masa, ita yake gani yaji dadi, yafita shiga damuwa daya rasa ta, ya fita
wahalar neman inda take yafita dauriyar addu ar Allah Ya sa ya ganta.
ta dinga buga waya kano tana shaidawa masoyanta cewar taga yayanta innamani kuma
babban farin cikinta ya musulunta shima,
farin ciki ya rufe kaltum, sumayya, mummy Hafsat, general tukur da 'yayana,
har kano tazo dashi yaga 'yayanta da iyayen Abba,
yayi musu godiya Madina ta nunawa su sumayyah sabuwar motar da ya bata, lalle Allah
mai kyauta duniya da lahira mai yanta bawa Ya azurta talaka a dare daya babu abun da
madina take yi sai sallah da gode wa Allah babu abunda tanema ta rasa a duniya yanzu
sai dai ta nemi lahirarta, ta sami dan uwa da miji masu sonta haka ta sami arziki marar
iyaka, tanaci tana wadata 'yayanta tana kyautatawa masu kudi badan basu dashi ba
sannan tana taimakon mabukata saboda tasan illar talauci da yunwa.
Madina ce ke zaune cikin falonta na kano bangarensu a cikin gidan surukanta aka fitar
musu tana karatun kur ani Abba na gefe yana
sauraronta har lumshe ido yake saboda daddadar kira'arta sai wayarsa ta hau ruri
Madina ta tsaya da karatun ta dube shi ta lumshe ido tace amsa wayar sai inci gaba.
yace alh Adnan ne harta katse ma kafin in amsa,
Madina tace kirashi saboda Kiran wayar alh Adnan alkhairine mutum ne mai hada
khairan baya sharri,
Abba ya kira lambar nan da nan ya sameshi bayan sun gaisa saiyace ina Madina?
inason ganinku.
Abba ya gyara zama yace ga madinar a kusa dani sai Abba ya mikawa Madina kan wayar
cikin fara a da ladabi ta gaishe shi yace da ita kuna gidane anan gida a Abuja?
madina tace a'a muna kano shekaranjiya muka zo sai mun yi sati biyu zamu koma Abba
mai gidanane yake hutu sai.
alh Adnan yace yauwa

Please Login or Register in order to submit comment