Reading adon dawa Chapter 18 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Ta yi takaici akan rabo
tada aka yi da bur sudan aka kawo ta nan inda bata san kowa ba, babu mai taimakonta.
Haka ta yini da yunwa ba abincin safe babu na rana saida daddare tana kallon kalah da
‘yarta suka dafa abincinsu suka juya mata baya suka ci saida suka rage saura suka bata
ta ci ta sude kwano sannan ta iya samun dan barci.
Gari na wayewa bayan kaltum ta yi sallah sai ta shiga wankewa kalah wake, a fusace
lami ta xo ta fuxge kwaryar da waken yake ciki ta sake maimaita mata cewar ba xasu iya
ci gaba da ciyar da ita ba ta je ta nemi sana’arta. Kaltum ta koma gefe ta tsuguna tana
kuka tana ganinsu suka dauki kayan suyar kosansu suka tafi wajen sayarwa.
Hantsi yayi cikinta kuwa ya dau rurin yunwa tana tunanin in da xata nufa gashi bata san
kowa ba a garin sai taji an dafa kafadarta ta baya tana dagowa sai taga wata matashiyar
budurwa ‘yar kusa da dakinsu ce mai suna fatsima.
Ta ce da kaltum”lafiya kike xaune kina kuka ke kadai? ”
Sai kaltum ta fara share hawaye tana murmushin karfin hali tayi sauri ta gyara xancen ta
ce wai ciwon kai ne yake damun ta. Fatsima ta girgixa kai tace “babu wani ciwon kai da
yake damunki mun san komai tun sanda kika xo muke tausaya miki saboda mun san
xaki hadu da wulakanci a wajen kala da ‘yar ta saboda basu da kirki kowa ya san bakin
halinsu ko kadan basu da mutunci gasu da rowa. Ki tashi muje kiyi irin sana’ar da muke
yi.”
Kaltum ta mike jikinta a sanyaye xuciyarta cike da fargaba saboda bata san sana’ar da
suke yi ba, haramtacciya ce ko halattaciya. Tafiya suke yi xugwi xugwi babu wanda yake
Magana a cikinsu har suka isa bakin wata katuwar kasuwa wacce ake kira da suna
makadi. Kasuwar markadi itace kasuwar da ake sauke danyan kaya mota mota irin su
tattasai, tumatur, atarugu, dankali, salad, kabeji da dai sauransu. Sai suka tafi wajen
wata katuwar bola in da ake jibge lalatattun kwanduna da gwalagwajin kayan miya
ma’ana rubabbun kayan miyar da aka tsince aka xubar.
Sai taga fatsima ta samo Kwando ta tsugunna ta fara tsintar masu dan kyau tana Tarawa
a cikin kwandon.
Kaltum ta tambaya cike da mamaki “me xa muyi dashi? ”
Fatsima tace “ke dai kawai ki samo Kwando ki xo ki fara tsintar masu kyau kina Tarawa.”
Kaltum ta aiwatar da abunda fatsima ta umurce ta su yi, suka tottona sosai da hannunsu
ga wari bolar tana yi harda suka tabbatar sun tara da yawa sannan fatsima ta nuna mata
fanfo suka je suka wanke tsaf, suka wanke kwandunan ma sannan tace su dauka aka su
tafi kasuwar adare karamar kasuwa ce. Suna isa adare kuwa Allah Ya kawo wasu mata
suka saya na kowannensu hamsin jine, ya isa su ci abincin yau ko babu nama. Farin ciki
ya kama kaltum ta dinga yiwa fatsima godiya da ta nuna mata hanyar cin abinci badan
ita ba, da batan san yadda xa ta yi ba.
Haka fatsima da kaltum suke yi kullum gari na wayewa saisu nufi markadi a gabansu ake
sauke kwandunan danyan kaya daga mota. Suna tsaye ake ware rubabbun yayin da
suma suke ware masu saukin rubar suna tarawa har sai sun tsince masu dan kyaun wani
lokaci har su sami masu kyau sosai saisu wanke tas su je su sayar a adare.
Xuwan kaltum sai ya xamowa fatsima alkhairi domin a yanxu tafi da samun kudi, mai
makon su siyar hamsin jine har metan jine suke yi saisu hada kudin su je su sayo danyen
kaya su xo su dafa abinci lafiyayya harda kifi ko nama su ci su koshi idan da canji su kora
da lemun kwalba.
Kawance ya kullu tsakanin kaltum da fatsima yayin da haushi da hassada ta kama kalah
da ‘yar ta har suka daina yi mata Magana don bahaka suka soba, sun so kaltum ta rasa
yadda xata yi tayi ta bin su, suna yi mata wulakanci. Ta kai ta kawo ko gaishe su kaltum
tayi basa amsawa idan a taba kayansu ko buta ce sai su kwace su kyareta.
Xuwan kaltum khartum da sati uku da magaruba bayan ta idar da salla a daki sai taji
muryar kalah da lami suna yiwa mutanen gidan sallama a daki daki da alama bulaguro
xasu yi, nan da nan kaltum ta fito daga daki sai ta gansu niki niki da kayansu aka da
alama dai kaura xasu yi. Hankalinta ya tashi ta fito a gigice ta tsaya tana kallonsu tana
sauraron abinda xasu ce mata. Amma sai taga ko kallonta basu yi ba sun kada kai xasu
fice, sai ta fashe da kuka ta bi su har kofar gida.
Ta ce kalah ina xaku je ku bar ni, ni kadai ban san kowa ba a nan sai ku?
Kala ta tabe baki sannan ta kai mata duka kaltum tayi sauri ta kauce.
Ta ce “ina ruwana ki mutu mana iyayenki ne suka ce a kawo ki khartu, ga khartum nan
kiyi xama. Goyonki xanyi ko kuwa nono xan baki? ”
Kaltum ta fada cikin kuka “dan Allah ki kira su awaya, kice gani na xo su aiko da kudin
mota in tafi, ko ki bani number su. Idan kika tafi basu san numer kowa ba sai taki ita
kadai ce suke tunani xasu same ni.”
Kalah tace “ba xan bayar da lambar ba, idan kina da karfi ki xo ki kwata.”
Ta ja hannun ‘yarta lami suka yi tafiyar su, lami tana ta xagin kaltum.
Kaltum ta rushe da kuka ta shiga tsakar gida tana rusawa, kukan kaltum ya sa kowacce
ta fito a gigice suka hau tambayarta me yake faruwa?
Tana kuka tana Magana t ace “kalah ceta tafi ta bar ni alhali ban san kowa ba a nan sai a
bur sudan ni kuma bani da kudin da xan koma bur sudan wajen wadanda na saba.”
Gaje ta yi salati ta salance t ace “af ke ce kaltum wacce iyayenki suka aiko da kudin
jirgin ki suka ce a saka ki a jirgi ki tafi Nigeria? ”
Kaltum tace “kaltum t ace “kala tace basu turo kudin jirgin ba ammam dai sun ce mata
xasu turo.”
Gaje tace a’a sun turo mata kudin jirgin kasa na xuwanta da dawowarku daga bur sudan
sannan suka turo mata kudin jirginki har xuwa kano. Sannan itama kalah suka bata kudi
mai yawa ladan dauko ki. A gabana dan aiken ya bata kudin da hotanki, sai dai in duka
kudaden ta hada xata haye don yanxu haka makka xasu tafi fitar nan da suka yi ta
barauniyar hanya ake shiga kwale kwale cikin dare sai a tsallaka ruwa a shiga jidda.”
Sai jama’ar wajen suka fara Allah wadai da cin amanar da kalah tayi, suna tausayawa
kaltum
Kaltum ta rushe da kuka yayin da ta tsugunna tana ihu ta rasa yadda xa tayi da ranta
gashi bata da lambar wayar iyayenta balle su san kudin da suka turo bai isa gareta ba
balle su turo mata wani. Ita ba a bur sudan ba, ita ba a Nigeria ba, gata a khartum bata
san kowa ba kuma bata da komai……..
Nan xa mu tsaya, se mun sake haduwa a ADON DAWA NA 3
Shin yaya rayuwar kaltum xata kasance a Khartoum?
Shin wane hali iyayen kaltum xasu shiga idan suka rasa kalah a waya kuma basu ga
kaltum ba, alhalin sun turo mata da isasshen kudin jirgi?
Shin wane hali mambela xai kasance daya sami labarin tafiyar kaltum alahli yana
tsananin sonta, xai kori bakin gidan su madina ko xai hakura ya kyale su?
Shin yaya rayuwar madina xata kasance, a bur sudan xata dauwama ne har karshen
rayuwarta, ko kuwa xata samu ta haura makka, ko dai xata canja shawara ta dawo
Nigeria wajen yaranta kamar yadda ta ji bata jin dadin xuciyarta saboda tafiyar kaltum?
Shin yaya rayuwar kalah da ‘yar ta xasu kasance a makka, xasu samu su haura ko a'a?
Duk amsoshin tambayar nan suna nan tafe a ADON DAWA 3.
ADON DAWA 21
.
LITTAFI NA UKU
.
Jama ar gida suka tashi kaltum tsaye da kyar daga durkuson datayi tana kuka takaraji
bata kaunar taci gaba da rayuwa gara ace bata raye zaifiye mata alkhairi .tafi kaunar
takoma bur sudan wejan madina da mambela akan takoma nigeriya wajen iyayenta taje
ta kwanta akan figeggiyar tabarmarta kukan ma yadaina fita sai ajiyar zuciya takeyi
saboda tsananin tafarfasar da zuciyanta takeyi, tsanani yayi tsanani yayinda damuwa
tarufi tsananin yunwa da takeji idan kanta yajuya saitaji hankalinta yagushe tamkar ba a
duniya takeba
fiye da awowi uku tana kwance cikin halin tunani me kunshe da bakin ciki Saiji tayi ana
zuba mata ruwa tafarka firgigit saita ga dandazon mata a tsaye akanta wasu nazuba
mata ruwa yayinda wasu na yimata fifita dukda fankar da yake kadawa a saman silin,
mamaki yarufe kaltum ta dinga bin daya bayan daya tana fadi aranta lafiya kuwa
meyake faruwa?
Sannu kaltum yaya jiki?
Allah ya sauwake kalamanda suke fitowa daga bakin ko waccensu .magajiya matarda
tabarmar kaltum ke kusa da tata itace tadaga kaltum tsaye ta dowo da ita tabarmarta
saboda na kaltum ya jike da ruwanda aka yayayyafa
ta kwantar da ita ta lullubeta da zani ita dai kaltum mamaki ne ya ke addabarta yayin da
kwakwalwanta ta dinga kokarin tunano mata abunda yafaru takasa tunawa abinda zata
iya tunawa shine lokacin da kala da lami suka tafi akace makkah zasu tafi sun kunshe
kudin da iyayenta suka turo mata sun tafiya dasu .
sai hawaye yaci gaba da surnano mata daga idanuwanta aka fita da tabarma kultum aka
tsane ruwan a waje,sannan kowaccensu ta juya ta nufi dakinta ,suna masu yiwa kaltum
patan samun sauki .
Magajiya ta tura kofarsu tarufe,ta kashe fitila ta kuntsa ta tsakiyarsu hajiya zaliha ta
kwanta duk en dakinne ,tabar wa kaltum tabarmanta .kafin kiftawar ido da BismiLlah
gurnanin munshari yafara tashi a dakin nawanan nadukan na wancen ,hade da
kyawawan mafarkai,
domin burin ko waccensu ta ganta haye makkah ta hada daurin gumama akanta tana
talla tana kuma aikawa nageria ana
rabawa danginta suna tsalle suna murna ,suna cewa hajia wance tayi kudi a makkah.
yawanci da abunda ka kwanta a ranka shi kake mafarki ,don haka yawancinsu
mafarkinda suka sunduma kenan .
ita kuwa kaltum a bangarenta bahaka bane da zarar ta ritse ido saitaga madina a
idonta ,da ta bude saitaga kamar mambelane agabanta ,sai hawaye metarin yawa ya
surnano daga idanuwanta,tayi doguwar ajiyan zuciya tana shesshekar kuka .
kaltum mehaka ?
Wata murya taji daga gefinta ,saita zabura ta waiga a tsorace .magajiya tagani a zaune
duk da duhunda yake dakin
wannan amsa tagagari bakin kaltum.
magaji ta sake tambaya. "me yake damunki kike qoqarin kashe kanki?
Ke ba musulma ba ce?
Ba ki san kaddara ba, baki yarda da kaddara mai dadi da mara dadi ba daga ubangiji?
Idan an rabo ki da bur sudan ba a kai ki nigeria ba aka kawo ki khartum, ba sai ki hakura
ki zauna ba har kiga yarda Allah zai yi dake ba. tunda Shi ya tsara miki haka, ya fi ki
sanin dalilin yin hakan. mu
dakike zaune da mu ba mutane bane, kuraye ne,cinye ki zamu yi?
ki yi hakuri, ki fauwalawa Allah lamuranki, ki kai karan duk wanda ya zalunce ki gurinSa,
shi zai yi miki sakayya. Allah ba ya zalunci, ba ya tare da mai zalunci, kuma yana bayan
duk wanda aka zalunta. ki tashi kiyi alwala,kiyi sallar isha'i don bakiyi sallah ba ,kiyi
nafilfili ki fadawa Allah halinda kike ciki ,don Yafiki sani.kikai karar kalah da yar ta wajen
Sa,Yagaugauta yimiki sakayyar cutarki da sukayi ,domin addu'ar wanda aka zalunta
karbabbabiyace.
Allah na gaugauta karbar addu'ar wanda aka zalunta,sannan ki koma gefe ki zubawa
sarautar Allah ido ,kiga yadda zaiyi dasu nan gaba,
kaltum tayi shiru tana sauraron magajiya tana gaskata abunda take fadi saidai kash
kaltum batada kwarin da zata iya tashi tayi sallar farillah ma,balle nafila,saboda tsananin
yunwa datake addabarta .
magajiya ce ta sake magana tana umurtar kaltum data tashi tayi sallah .dole ce tasa
kaltum yunkura ta tashi zaune ,saidataji dif.bata gani jiri .ta dade a zaune sannan ta dafa
kasa ,game da cije baki tayunkura zata mike tsaye sai tayi taga taga zata fadi,saita
koma jabar ta zauna .
magajiya tambayeta cike da kulawa kaltum,anya kuwa ba yunwa bace take damunki ?
Kaltum ta kada kai cikin jin nauyi tace yunwa nakeji aunty
Magajiya tace , Allah tsarki ,yarinya me kawaici badan jiri ya daukeki bazaki fada min ba
kenan?
To tashi a hankali ki rarrafa ga tukunyanta can a bakin kofa bude da sauran shinkafa kici
farin ciki ya lullubeta zuciyar kaltum ta mike a hankali ta karasa bakin kofa ta laluba ta
bude tunkunya ba ta yi wata wata bata tsundum hannu a cikin tukunyar,kasancewar
shinkafar ba ta da yawa, ta fara kaiwa cikinta hakkinsa yayin da 'yayan hanjinta suka
dauki ruri da kokawa,ni ban samu ba ni ban samu ba.
kowacce cuta da maganinta, cikin yan mintina ciwon jirin da ya ke damun kaltum ya
ware,ta sami karfi mikewa tsaye ta bude kofa tafita bandaki .ruwa ya wadata a bandaki
don haka ta bude famfo ta sharuwa ta koshi,ta dauro alwala tafito.atsaye ta kwana
harsaida aka kira assalatu tana nafilfili tana mika kukanta zuwa ga mahaliccinta,tana me
neman agaji da neman mafita akan mawuyacin halinda take ciki .tana mai neman Allah
ya saka mata bisa cutarda kalah tayi mata ita abumda yafi damunta da aka rabota da
wajen su Madina .
misalin karfe bakwai na safe fatsuma ce tashigo dakin su kaltum ta isketa ta a kudun
dune akan tabarma ,bacci mai dadi ya kamata hade da maparkin abun kaunarta
mambela, kasancewar kwanan da ta yi a tsaye tana sallah.
kaltum kaltum tashi mutafi " fatsuma take fada yayinda take girgiza kaltum ,ta firgigit ta
tashi zaune ta murtsike ido.
fatsuma ta dube ta cike da mamaki ,sannan ta tambaya.haryanzu barci ki keyi , ko
jikinne?
Kaltum ta girgiza kai,lafiyata kalau ai "ta mike game da tawo wata cukurkudaddiyar
lafayarta ta lauye jikinta suka dunguma suka fita ,yayinda yan gida kakaf sun dunguma
wajen neman abinci.tafiya suke zugui zugui fatsuma ce mai dan tabo hira,amma ta lura
hankalin kaltum ba a wajenta yakeba .ta dubi kaltum tace ,kaltum wacece madina ?
Wanene mambela?
Nanda nan taji gabanta ya fadi ,yayinda ta waiwayo da sauri ta tsura wa fatsuma ido
tana mamakin yadda fatsuma tayi mata wannan tambaya.
A ina tasan madina?
A ina taji sunan mambela?
fatsuma ta sake maimaitawa, tace, 'kin yi shiru baki bani amsaba'
kaltum ta tambaya, 'a ina ki kasan madina mambela?'
fatima tace, 'mimmikewa ki kayi kika kakkafe kina ta kiran sunan mambela da madina'
sai kaltum ta fashe da kuka, ba tare da tasan amsar da zata bawa fatima ta tabbatar
larurar aljanun nan ce ba su bar ta ba. Ta tuna irin hidima da kokarin da mambela yayi
mata wajen nemo mata maganin aljanu, gashi yanzu bacin rai ya dawo da aljanun, ga
mambela ba ya kusa kuma.
Ta rushe da kuka, ta yi ta rusawa suna tafe a hanya ana kallonsu.
Fatima ce ta dafa ta tana lallashinta tana ba ta hakuri, har suka karasa bakin bolar da
suke tsintar kayan miya suka samo kwando suka tsugunna suna ta tsintar kayan miya
masu rangwamen ruba, amma hawaye ne ya ke kwaranya shaf-shaf daga idanuwan
kaltum.
Fatima ta dube ta, sai ta girgiza kai, saboda tausayin kaltum da ta ke ji, don a halin
yanzu tafi tausayin kaltum fiye da karin kanta. Tabbas fatima abar tausayi ce,
saboda itama da kanwar mahaifiyarta sukazo da zummar zasu sallake makkah
akazubesu anan.kanwar mahaifiyarta tace kowa yayi ta kansa ko lomar tuwo bata
hadasu,kowa nasa yake nema.to amma ita fatsuma ta saba da khartum tana jin dadin
rayuwarta tamkar a presidential bila take ,musamman ranarda taci sa'ar bolannan ta
cika da rubabbun kayan miya tasamu ta cika kwandonta da kayan miya taje ta sayar ta
sayo shinkafa ko taliya da kifi ,ko nama taje ta gida ta dafa tahado da lemon kwalba mai
sanyi ,tabbas wannan ranar ta fiye mata ranar sallah.sabanin kaltum wacce ta tsinti
kanta a Khartoum tamkar wacce akayi mata dabaibayi cikin rami ,
batajin dadin rayuwanta tarasa me yake yi mata dadi musamman daga jiya abinda kalah
tamata .
idan kaltum ta tona bola ta tsinci kayan miya ,saita kifa kai a gwiwarta tayi kuka harta
gaji,sannan ta cigaba da tsinta ta tuno cewar inbata tsinta ba babu ita babu cin abincin
yau.
duk da haka bata tsinci abun kirki ba ko rabin kwando baiyi ba sabanin na fatsima wanda
har yafi rabin kwando a haka suka tashi suka tafi famfo suka wanke suka nufi kasuwar
adare.
sun dade suna zagaya kasuwar da kwado akan su suna tallata hajar su, da kyar suka
samu aka saye bada wani kudin kirki ba ma,
Na fatsima da ya fi yawa yafi yawan kudi.
a hanya fatsima take tsuye kaltum akan abun da taja musu yau sun makara basu kai
kayan miya da wuri ba har kowa ya gama siya asanadiyyar koke-koken data zauna
tanayi tun dazu
kaltum batayi magana ba tafiya take zokai-zokai abun duniya ya ishe ta babu abunda
tafi bege tafi bukata a zuciyarta irin ta rufe ido ta ganta a bur sudan ba haka bata kula
irin gidan kusa da membela .
kwalla ta cika mata ido da ta tuno rayuwarta da yan gidansu na bur sudan ga kawayenta
yadda suke wata yawarsu .bata damu rashin wuta da ruwa irin na bur sudan ba,haka
bata kula da irin gidan katakon dasuke rayuwa ba ,bata duba yanzu a babban birni da
take ba,ga wutar lantarki koda yaushe ba a daukewa ,fanka fil fil fil najuwa ,ga ruwa a
famfuna yana kwaranya koda yaushe .
kaltum bata damu data koma nigeria ba don taga iyayenta da kannen ta ba,balle kuma
alhaji adnan duk ta shafesu a cikin ranta basa lissafinta ta cire ran sake ganinsu a
rayuwarta har abadh .
fatsuma ce da katse tunaninta da take yi tace zo muje musayo danwake muci tunda kudi
bazai isa mu je mu auni shinkafa ba mu dafa
kaltum nabiye da ita har gaban me murhun me danwake.
baiwar Allah fatsuma ta karbi dan kudin dake hannun kaltum ta hada danata me yawan
suka sayi danwaken chanjin suka sayi ruwan sanyi ,saboda yunwa a wajen suka
tsugunna suke ci basu damu da mazanda ke zazzaune a wajenba haka basu damu da
motocinda ke wurwucewa ba ana lekensu ana nuna su ,basu lura da kasar musulunci da
shari'a sukeba
burinsu su warware hanjin cikinsu daya kanannade ya cure a gefe daya saboda
yunwa.har wasu samari biyu da suka zo wucewa suka yada musu da magana cikin
harshen Larabci.
kaltum data fi su jin larabci ta fi fahimtar abun da suka fada musu, don haka nan da nan
yanayin fuskarta ya sauya, sanyin jiki ya far mata. ta bi su da kallo har suka kure.
samari biyu kyawawan fararen larabawa dayan ya dubi dayan,
sannan ya juya ya nuna masu su kaltum ya yamutse fuska ya ce, 'dubi wadannan
'yammatan a tsugunne a gefen titi, suna ciye-ciye saboda tsabar ba su san darajar da
Allah ya yi musu ba ta 'ya'ya mata. rayuwa suke yi kamar dabbobi babu kamun kai'
dayan ya ce 'yan nigeria ne, ai zasu yi abun da ya fi haka ma. kai daga gani ba sai ka
tambaya ba, duk haka suke rayuwa suna bata mana tarbiyyar kasa. ga su da nacin
jaraba ko an kwashe su sai sun dawo ba za su zauna a kasar su ba.
ko ina dimbin arzikin kasarsu yake sukazo suka kunace mu suna cutarmu don duk yadda
ka hada huldarka dasu sai sun zalunceka .
dayan yabashi ansa da cewa ,ehto baduka yan nigerian bane macuta sunada masu
kirki ,kamun kai ,rikon addini da kyawawan halayya.
kaltum tayi ajiyar zuciya yayin da ta tsame hannunta tsam daga kwanon dan wake ta
mike tsaye gami dacewa ,nakoshi ,ki cinye duka .
fatsuma cike da mamaki da tambayan ranta meyasa kaltum ta barma ta danwake har
goma?
nan da nan ta halakasu ta tsuda kwanon ta kora ruwan sanyi suka kara gaba.
suna shiga sakar gida suka iske damdazon matan gidan kwansu da korkotansu a tsaye
suna ta ce ce kuce .
hayaniya tayi yawa har ba zaka iya tsintar kalma daya ba kamar fada akeyi ko mayarda
zance ,labari ne suke yi ko kuwa jajanta wani abu sukeyi wajunansu?
Allah shi Ya barwa kanSa sani.
fargaba gami da mummunar bugawar zuciyace ta fado wa kaltum asanda taga gaba
daya matan sun yiwo kanta suna fadin ,yauwa ga kaltum din ya
ADON DAWA 22
.
,yauwa ga kaltum din nan yar halak .
ta dafe kirji ta fada cikin,fargaba InnaLillahi wa'inna ilaihi Raji'un .me nayi ,lafiya?
Magajiya tafada cike tausayawa ,tace,sai kikaji abun da ya sami kalah da yar lami?
Kaltum tasake jin mummunar damuwa.tace meyasami kalah da lami?
Sai taga hawaye yana kwaranya daga idanuwan wasu daga cikin su ,saboda
tausayawa .kankace kwabo kaltum tafashe da kuka,yayinda jikinta ya dau karkarwa tana
tambayarsu cikin matsananciyar damuwa mai hade da fargaba amsar da zasu bata .wai
me yake faruwa ne ?
Ku fada mini.
magajiya ta sharce hawaye tace ,kalah da yarta lami ne suka yi hatsari a kwale kwale a
hanyarsu ta hayewa makkah ta barauniyar hanya jiya da tsakar dare,
kalah na asibiti rai ahannun Allah ,yayinda lami da sauran mata uku Allah Ya a
musu rasuwa kalmar innalillahi wa inna ilaihi
raji un ce ke fitowa daga harshen kaltum ,ta tsulale ta tsugunna yayinda ta hada kai da
gwiwa tana rusa kuka .
magajiya tace kowa anan yasan hakkinkine yakama kalah da yarta kowa yasansu kalah
suncuceki ,Allah baya Ya fe wa wani laifin
wani,sai kin yafe musu susami rahama kaltum kiyafewa lami wacce ta rigamu gidan
gaskiya,kalah kuwa da bakinta take cewa anemo mata ke tanemi gafararki yanzuma
daga asibiti muke bata anbaton kowa sai akiraki tanemi gafararki tasan ta cuceki mun
duba duk inda zamu samoki tunda safe bamu gankiba
kaltum tafada nan da nan nayafe musu asabebe tace tashi muje asibitin taji da kunnenta
ko hankalinta zai kwanta kaltum ta mike da sauri yayinda kowaccensu ta zaro gyalenta
tafiya sukeyi fakam-fakam cikin sauri suna tayar da kura kai kace garken shanu aka
bude aka korosu kiwo .
kowaccensu ka duba sai ka rantse daga kabari ta fito butu-butu wasu da goyo wasu da
yayayyun 'yaya sunrike hannunsu mata fiye da ashirin ne suka taho duba kalah.
nan da nan ma aikatan suka taho da sauri suka tare bakin kofarda kalah ke kwance .
tambayarsu suke lafiya?
Asabe ce ta koro musu bayani ,wannan itace kaltum da kalah kecewa anemo tunda tsafe
suka bar asabebe da kaltum suka shiga ragowawar aka tura keyarsu baya .akarkashin
wata itaciya suka tarufi, takaici ya ishesu baza arasa tsaki da harare harareba harda yan
tsirarun ashariya duk sun kutuntumawa ma'aikatan cikin harshen hausa tunda basaji ,
fargaba da kidimewane suka hadu a zuciyar kaltum dai dai lokacinda tayi ido hudu da
kalah yanayin jikin kalah zai tayarwa da duk bil adama hankali musulmi harda wanda ba
musulmiba saboda mugayen raunukan da ke jikinta kama daga kanta zuwa kafarta duk
bandejine,
karkarwa kawai kaltum keyi yayinda taja burki tayi turus tana duban kalah.itama tana
dubanta hawaye masu zafine ke kwaranya daga idanuwansu,
yayin da bakin kowaccensu ke karkarwa. kalah na kwance reran an nadeta da farin
bandeji, wanda ya yi nashe-nashe da jini. kafafuwanta dukka biyun, da hannunta data
dorin karaya ne. fuskarta luhu-luhu a kumbure idan ba an fada maka ita ba ce babu
yadda zaka kalleta sau daya ka gane ta. da kyar kalah ta daga hannun ta fada cikin wata
shamulalliyar murya marar kuzari, 'zo nan kaltum, zo wajena, kun ga yadda Allah ya yi
da ni. na cuce ki, amma kaina na cuta' kaltum ta matso a hankali ta raba ta zauna a
gefen gadon kalah tana mata duban tausayawa,hawayen dai bai tsagaita ba daga
idanuwan kowaccensu, su ukun har da asabebe.
kalah ta kara da cewa,
'me za'a yi da halina, me za'a yi da zalunci, cin amana da damfara?
kaltum, na damfari iyayenki ,nacuce ki ,najawo kaina.shin me kudin nan dana cuce ku ya
karamin yanzu?
mezamu fada wa Ubangijinmu nida lami ?
kuka me yawa ya ruftowa kalah takasa
cigaba da bayani asabebe nashafa hannunta tana bata hakuri tana cewa daina kuka
kalah fuskarki duk dinkine kada ya sake kuburi yihakuri kaltum tariga tayafemuku,
kalah ta fara magana cikin nadama Allah ya yafemin ,kaltuma kiyafe min inkinje gida
kicewa alhaji adnan yayafemini domin naci amanarsa akwai wani Inuwa agent dan Daura
ne wanda duk shiyakawomu nan shi alhaji adnan yaje yasamo har Daura ya tambayi
inda kike inuwa agent yace ya dade baiyi wannan harkarba ta kawo mutane sudan saidai
zaisa a binciko inda kike bansan inda
inuwa yasamo labarin bur sudan ba andai tabbatar masa kina cen saisuka shiga tunani
yanda za ayi adaukoki da farko shida alhajinne suka shirya tahowa bur sudan dinsu taho
dake sai gani kwasam nabugowa inuwa agent waya inaso yakaiwa 'yaya na wayarsa
muyi magana dasu don basuda waya sai kuwa yaji dadi daganin numbata
daganan sai labari ya canja cewar intaikesu in dauko musu ke daga bur sudan in dauraki
ajirgi kitafi kano nan da nan na kalallamesu da dadin baki danaji maganan kudin jirgi na
nunamusu ciwon 'ya mace na ' ya mace ne, d'a ai na kowa ne, na daukan musu alkawari
zan kawo musu kaltum har gida kada ma su bata lokaci da kudin jirgi har na mutane biyu
zuwa da dawowa ga wahalar zuwa bur sudan godiya iri iri da shi albarka suka dinga mini
basusan abunda na kudurta azuciyata ba
mukayi lissafin kudin jirgin kasanda zai kaini bur sudan da wanda zamu dawo Khartoum
ni dake da kudin abincinda za muci a hanya sannan da kudin jirgin sama nawa da naki
daga Khartoum zuwa kano hatta da kudin taxi

Please Login or Register in order to submit comment