Reading adon dawa Chapter 23 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

abu yaci tura, duk abunda take
samu baiwuci ta ci abinci dashiba sauran tasayi omon wanki da sabulun wanka da
sauran su,
idan taci sa a ta tara kudi mai dan yawa tafara tarawa sai wani abu ya bullo mata wanda
dole sai takashe kamar sayan magani idan batada lafiya ko idan takalminta silifas ya
tsinsinke dole ta sayi wani ko idan rigunanta ko lufayanta sun yayyage dole takai dinki.
yau idan akace maka babu mai taimakonka
kodada loman tuwone komai kaiza nema da kanka to babu sauki, kaltum na aiki tukuru
don neman abunda zatasa a yan hanjinta kokuma wanda zata iya shiga jama'a ba a
toshe hanciba saboda wari ko datti bata hutawa saboda haka tarame tayi kurket tayi
duhu rabonta da kitso tun na bur sudan saboda batada lokaci dakuma wanda zaiyi mata
amma ita ta iya kitson har gida gida ake kiranta tanayi ana biyanta.
watan azumi ya kama kaltum bata hutawa yini takeyi tana neman abumda zasuyi buda
baki saboda azumi.
yau babu masu zuwa gyaran jiki don haka jawahir ta sallamesu tace su daina zuwa sai a
satin sallah sannan zasu dawo saboda haka sukafi mayar da hankalinsu wajen tsinta
lemo da abarba sufere wajen rubar sukasa a faranti suje su sayar, kasancewar azumine
ba acika sayan kayan miya ba akan da, anfi sayan kayan marnari .
sak almajirai ga yunwa ga kishiruwar azumi gasu sun yini a Kasuwa.
wataran suyi sa'a su sayar wataran su yini suna yawo ba a saya ba, dagaa lasa an ya
ruba sai afasa saya daman dai masu rangwamen men kudi ne suke sayen irin wannan
masu kudi basa dosar nakan farantin yan talla sai wankanku ajere akan tebur ko acikin
firij.
ranarda rana takwabe musu kuwa babu mai saya idan akasha ruwa sai su zauna su
shanye abunsu babu kudin cefane bare su dafa abincin buda baki da sahur don haka
saisu zarzaya gidanda ake raba sadakar abinci da kwanukansu tun kafin dare yayi
abincin sadakan yakare,
kunu dagurasa ko sinasirne sukebin dogon layi ana raba musu shizasuci kobasu koshiba
su rage na sahur.
kaltum takanyi kuka cikin dare saboda masananciyar rayuwa da take ciki dumin
a bur sudan tawuce irin wannan rayuwarda ta
fatarar abinci. mambela yakara musu jari ita da madina suna sana'arsu kowannensu
abinci ya wadaceshi
sun daina bara asatin da azumi zai kare satin
sallah kenan alokacin watan cinikin jawahir ta
bude ake tururuwan zuwa gyaran jiki da gyaran kai saboda kwalliyar sallah a wannan
satin kaltum suka kaura gidan jawahir har kwana suke yi suna aiki saboda jama'a,
dogon layin babu masaka tsinke sakar gidan saboda mata a lokacin kudi yayi ta shigo
musu baja-baja duk da jawahir ce mai amshewa,
kalilan da ciki take guntsira musu su ta murna.
wasa wasa kuwa suka tara kudi da yawa ana jibi sallah fatsuma ta shawarci kaltum suje
kasuwa su sayi lafaya da takalmi mai kyau suyi kwalliyar sallah kaltum tace ita tara kudi
takeyi akwai abunda zatayi dashi bazatayi kwalliyar sallah ba.
fatsuma tayi tambayarta mezatayi da kudi da har bazata ki sayan sutura da sallah ba
wacce ko almajirai suna wanka su canza kaya ballesuda suke kudi mai dama.
kaltum taki fada kuma taki saya fatsuma ce tashiga kasuwa tayi sayayyarta tsaf harda
sarka da yan kunne
baya ga lafaya da takalmi coge chanjin kuma
taje kasuwa da ake sayar da wayan tafi da gidan ka (g.s.m)tsohowar waya gwabjejiya
wacce aka daina yayinta ta saya aka makala mata sim card yadda zataji dadin waya da
musa saurayinda take matukar kauna shima a kasuwar markadi yake dako su suke
sauke kwandunan kayan miya daga mota zuwa cikin kasuwa.
ranar sallah kowa ya caba ado cas gwanin sha'awa duk wanda yaga fatsuma sai yayi
mamakinta kamar ba fatsumar jiya bace mai
barkakkiyar riga da kanannandaddiyar lafaya
saboda rashin guga kanta duk gunji yau kuwa tayi tsaf bakinta har shekin dangwalin
yaba yake.
zanen fuskarta wato bille da uku ukun bakinta sunyi radau saboda jar hoda da ta
rarrangada ta dambara baki a bakinta da girarta kaikace tabarya ce masayin kwallin,
ta fito kwas kwas kwas daga dakinsu ta leko dakin su kaltum jama'ar gidansu suka ta
mamaki kyawun datayi a yau suna tunanin inda ta sami kudi haka,
fatsuma ta dubi kaltum ta girgiza kai don takaicin kin daukar shawararta datayi datakiyi
da tuni sunyi anko yayinda kaltum ta fito daga wanka tana shiryawa a tsaye akan buhun
kayanta tsofofin riga da siket ta saka burguza burguza sai ta dauko lafayarta koriya itace
mai rangwamen tsufa duk da tawanke tas tayi musu karin guga tana kwana akansu kallo
daya zaka yi musu ka tabbatar sofaffi
ne don haka batayi kyauba surutu da gori babu wanda fatsuma bata yiwa kaltum ba
akan taurin kan da tayi nakin yarda da shawararta.
kaltum bata damu ba shirinta take yi kawai ta linke dukkanin kayanta ta cusa abuhun ta
hada bakin buhun ta daure tace da fatsuma zo muje waje na fada miki wata magana
suka fito kofar gida suka tsaya kaltum ta dubi fuskar fatsuma taga yadda tayi wuri wuri
tanaso taji labari saita tuntsire da dariya tace fatsuma yau zantashi daga garin nan zan
kaura garinmu bur sudan
kaltum ta dafa kafadarta tace ki kwantar da
hankalinki zan dinga kawo miki ziyira akai akai ko kinaso kibini idan naje indawo in
daukeki muje can mu zauna?
fatsuma ta girgiza kai tace bazan iya zama
da wadannan mutanen naku na ADON DAWA ba,
kaltum ta harareta tace ADON DAWA ba mutane bane ko ba musulmai bane?
fatsuma tace ADON DAWA saike nikuwa sai ADON BIRNI sukayi daria dukansu.
kaltum tace don bakisan suwaye ADON DAWA bane kike fadar haka musulman cikin su
sunada kirki, kyauta, sadaka, zakka, sallah, azumi, tausayi, sunada ilimin addini,
masu kudi kuma kyawawa hanci zuwit..
fatsuma tace tunda kina son mambela fa ai dole kifadi haka nikuma bana son ADON
DAWA,
kaltum tace ashe bakya sona tunda ni inason ADON DAWA, a kabila daga hausa sai
ADON DAWA nafi so,
fatsuma tace inasonki tunda ke bahaushiyace amma fa banason ADON DAWA gashi
kuwa sun janyeki zaki koma wajensu duk abunda nafada miki kinki ji sai kintafi din,
suka isa tashar da kafarsu duk da nisa basu damuba sun saba da tafiyar kafa basajin
wahalarta.
suka jira har bayan la'asar jirgi kuwa sai bayan magarib zai tashi kaltum ta umurci
fatsuma tazauna acikin wata rumfa wacce aka tanadar don zaman matafiya gasu nan
reras a zauzaune suna jiran jirgi,
zataje tayi fitsari idan ta gama zataje wajen ma'aikatan jirgi ta tambayesu adadin kudin
tikiti da yadda ake sayansa,
fatsuma ta zauna da buhun kaya a gabanta tana duban kaltum hartayi nisa ta daina
hangota tadade bata dawo ba sannan ta dawo tana zuwa fatsuma ta mike tsaye tace
gida zata tafi saboda tafiyar mai nisa ne, ita kadai kada dare ya mata,
kaltum tayi tayi su sake zama suyi yar hira fatsuma taki tace gara ta tafi tayiwa kaltum
fatan alkhairi da Allah kiyaye hanya tajuya ta tafi.
kaltum tayi kuri ita kadai taci gaba da kallon
masu wucewa kowa da dan uwansa yana hira amma bata damuba, zama kadanne ya
rage mata a shiga jirgi tunda magrib ta kusa farin ciki mara misaltuwane ya bayyana
azuciyarta ya huda ya fito ta fuskarta musamman da jirgi ya iso anfara bin layi don
yankar tikiti kaltum cike da fara'a tabude bakin buhunta don dauko kullin ledar da ta
daure kudinta zataje itama tabi layi ta yanki nata tikitin idan ta tuna jirgi zata shiga
yanzu bur sudan tana wayar gari zata ganta kusa da mambela da Madina sai taji farin
ciki ya lullubeta jitake kamar rufe ido ta bude idanuwanta ta ganta a bur sudan,
ta kasa kwatanto irin farin cikinda su mambela zasu shiga idan sun ganta ta luma hannu
acikin kowane sako lungu da kusurwar buhun kayanta taji har yanzu bata jiyo kullen
ledar kudinta ba nan da nan ta fara zazzakulo tsummokaran ciki da sauri tana zazzagawa
tana ajewa akasa har buhunya zama wayam ba komai amma babu ledar kudin
don haka hankalinta yatashi matuka ta sake bin kowani zani daya bayan daya ko kudin
yamakale ajiki amma shiru kakeji bai fadoba, ta tsake wargaza kayanta akasa kowanne
siket riga zani ko lafaya saida ta shimfideshi akasa sanka-sanka babu ledar kudin ta,
saita rushe da kuka na takaici yayinda jama'a suka tabbatar ba lafiya ba tabbas akwai
matsala aka taru ana tambayarta bayani take cikin gigita da dinbun damuwa wasu sun
yarda ta ita sun kuma tausaya mata wasu kuma bayanenta yamusu kama da tatsuniya
gizo da koki ta mallece kawai domin sun saba ganin irin wadannan mutane wadanda
dazarar talauci ya ishesu sai suzo tashar suna ihu suna neman taimako kudin mota suce
nasu ya fadi idan aka hadamusu taimakon sai su zame su gudu daman ba motar zasu
hauba damfarane kawai,
wake daya yake bata gari inji masu iya magana sun shafawa masu gaskiya kamar yanda
suka shafawa kaltum kowa ya kalleta
saiya watsar yawuce abunsa ma'ana sunsaba ganin irinsu tuntuni,
kuka take haikam bayani take bilhakki rokon taimako take yi da duk karfin ta amma
dakyar ta samu jine goma sha daya ta garzaya bakin wundon mai sayar da tikiti cikin
kuka tayi masa bayani game da fayyace masa abunda take nema agareshi tace tana son
ya
taimaketa yabata tikiti tatafi bursudan wajen yan uwanta batada kowa a Khartoum,
ansace mata kudinta kakaf sai yanzune ma jama'a suka taimakamata da jine goma
shadaya ya
taimaka ya karbi abunda take dashi idan jirgin nan yatafi ya barta batasan yanda
zatayiba...
wani takaici yarufeshi tikitin jine dari biyu dahamsin ne zai bata a jine goma shadaya?
kallon tara saura kwata ya mata don haka basai yamata magana ba tasan abunda
ke ransa cikin fargaba ta sharce hawayenta ta sake neman wata alfarma cewar to ya
bata rancen tikiti suna isa bur sudan yasawani ya bita gidansu ya karbi kudinsa..
cikin wata dankararriyar murya ya fada cike da takaici ke matsami daga jikin wundo
kada ki sake dawowa, kika sake lekowa kika min zancen banza sai nasa yan sandan can
sun kamaki, kaji mahaukaciya tikitin gwamnatin ne zan baki bashi ?
Sum sum sum kaltum tayi tabar jikin wundonsa batare da ta sake cewa komaiba daman
itama tsausayine yasa ta tambayeshi don daga ganin bakar fuskar nan tasa baki kirin da
jajayen idanuwansa tasan bazaiyi mutumci ba ga wani tulelen ciki da kiba da kyar yake
juyi kuma tun nan kasa tsinke ka huda yace tush haka yake kamar katuwar balobolonda
aka cika da iska saita daina
kuka ta sharce hawayenta da yayi mata face face a fuska batada sauran dabaru ko
tunani bata da sauran wani tunani kuma ta cire burinta data kudira saitaje kayanta da ta
watsar akasa tana kadewa tana linkewa tana zurawa a buhu jikin ta kalau data gama
lenkewa saita koma gefe jikin wani dakali ta jingina da buhunta a gefe tana duban jama
ar da Allah ya musu rahma wadanda ya yalwatasu da kudin sayan tikiti sai yanka suke
suna shiga jirgi,
dukan uku uku kirjinta takeyi tamkar zata fas
ADON DAWA 27
.
TRUE LIFE STORY
.
ta fito waje yayinda takejin wani jiri na takaici na neman yakayarda ita kasa,
kuka yaki zuwa saboda abun yafi karfin kuka, don idan tashin hankali ya afku akayi kuka
to akwai sauran rangwamen masipa, amma idan masifa yayi masifa to kukama takansa
yake abun yafi karfinsa,
nasihar Madina ta tuna wacce a koda yaushe take shawarta ta yawaita addu'a tana
neman tsari daga masifun rayuwa, wanda ko Allah Ya aiko da masifa zata zo da sauki
kuma da maganinta ta shawarceta data yawaita karanta InnaLillahi wa ina ilaihi raju un
ako yaushe musamman sanda wani abu naki yafaru,
nan da nan kaltum ta cafko kalma InnaLillahi
wa inna ilaiyi raju un a harshenta tana fada
tanasake maimaitawa saita farajin wanan kululun nan daya shaketa awuya yafara
lafawa, bugun da zuciyarta ke famanyi ta sausauta tanaji tana gani jirgi ya cika ya tashi
yatafi ya barta, yayinda kuka ya kwace mata tana yi ta nanata kalmar InnaLillahi wa inna
ilaihi raju'un ta dade a zaune anan har karfe
sha daya na dare.
saida wani dan sanda ya zagayo ya sake zagayowa ya tabbatar ba tada niyyar tashi
daga wajen nan sannan ya tsaya ya tambayeta lafiya take zaune haryanzu cikin kuka?
tamasa bayani yace to ai gara ta tashi ta koma inda tafito saboda zamanta anan bai
dace ba, ga dare ya fara nausawa gara takoma ta tara wani kudin zaifi mata sauki saita
dawo ta yanka tikitin ta tafi baki alaikum don ba wanda zai dunkule wannan makudai
kudin ya bata, don kowa takansa yake yi,
kaltum ta mike ta daura buhunta aka tana zubar da hawaye tafiya take amma dakyar
take jefa kafarta ta isa gida zuciyarta tamkar tafashe taci sa'a duk yawancin ankwanta
saboda gajiyar sallah , ta sadada tashiga dakinsu ta ajiye kayanta a lungu tayi sallah ta
kudundune alungu yayinda duk sanda ta rintse ido saita tayhango Madina da mambela
sai ta fashe da kuka.
washegari da safe kaltum taci karo da yan gidan a lokacin da ta fito daga bandaki zatayi
alwalar sallar asuba, mamaki mara misaltuwa zaka gani a fuskokinsu
musamman ma kawarta fatsuma,
lah kaltum baki tafi ba?
Meyasa baki tafiba ?
Amsa ya gagari bakin kaltum saitayi shiru tana tunanin abunda zata fada sai can tayi
dan murmushi karfin hali tace fasawa nayi ai tun jiya da daddare na dawo,
kika fasa meyasa ?
Suka sake tambayarta ko amsa bata basuba taci gaba da alwalarta kawai,
fatsuma tayi dariya tace gaskiya naji dadi dakika fasa don har ina tunanin yanda
zandinga yawo nikadai a garin nan gara muyi zamanmu anan, kaltum ga wuta ga ruwa
ga titina ga wayar sadarwa ga samarin birni mezakiyi a bur sudan?
kince babu wuta baruwa babu network na waya gaku a zaune a makabarta duk
kabarurruka a dakunanku na katako kamar yadda kika fada min...
sai ko wacce ta tsoma bakinta tanayiwa kaltum nasihar tayy zamanta anan kada ta
koma kauye suma yan kauyen addu'a sukeyi sudawo birni.
ta mike sam ta shiga daki batare da tare da tayi musu magana ba, takaicinda ya isheta
ya isheta kauyen nan da suke kushewa ita yafi mata birninnan dasuke muradi
kamar yadda suka saba kaltum da fatsuma suka bazama neman na abinci duk da sallah
ce amma sunyi sammako suntafi kasuwar markadi , ahanya suna tafiya kaltum ta dubi
fatsuma ta langwabar da kai gefe tace bakisan abunda ya sameni bako?
Fatsuma ta dubeta cike da mamaki tace bansaniba me yafaru?
Kaltum tayi ajiyar zuciya tace sace min wannan kudin nawa duka akayi ban gan su ba
shiyasa bantafi ba .
fatsuma ta zabura ta dauki dogon salati game da dafe kirji ta tambaya cikin gigicewa
yanzu wannan kudin an sace su dukka?
Fiye da jine dari bakwai nefa yanzu wa kike zargin ya dauke miki a dakinku ko atasha
aka
dauke ?
Hawaye ya sirnano daga idanuwan kaltum
ta girgiza kai tace bansan inda aka daukeba ni dai nasan ko a daren shekaranjiya ana
gobe zantafi kenan saida naga kudin harna sake kirgawa na daure na mayar asanda
zamu tafi tasha dai ban duba ba wata kilan sanda nashiga wanka aka dauke,
fatsuma tace watakilan sanda kike kirgawa wata ta ganki kina tashi ta dauke,
nidai kina ganin sanda na dauki buhunki bansaka hannu acikiba agabanki na ajiye miki a
tasha natafi, kuma niban hudaba nazakulo da Kinga buhunki huje....
kaltumta zabura tace nifa bance kekika daukanmin kudina bafa ko a mafarki nasan
baza ki min sataba,
suka cigaba dajajatawa har suka isa masana'antarsu wato babbar bolan da suke
sintar kayan miya suka fara gudanan da ayyukansu kamar kullun,
Abbas dai yanakan bakansa na naci dabin kaltum aduk inda take, a yau ma ya riskesu a
inda yake tunanin zai samesu adaidai lokacin daya san zai riskosu , yakwada sallama
cikin wata kamilalliyar murya mai sanyaya zuciya
lokaci guda suka daga kai don gani mai wannan sanyayyiyar murya sai sukaga fuskar
Abbas cike da murmushi irin wannan murmushi fatsuma ta mayar masa gami da amsa
sallamar itama a yayinda abangaren kaltum akasamu akasin haka, domin jitayi ranta ya
baci nan da nan ta tsuke fuska takawar dakai gefe yasake tsungunawa kanta ya rafka
sallama don dama ita yakewa sallama, kuma ita yakeso ta ansa ba fatsuma ba,
kaltum ta fusata ta mike afusace tafada cikin fushi Abbas karabu dani kakyaleni in sake
saboda ni ina da mijina a bur sudan don haka kaje kanemi wata,
fatsuma tarike baki don mamaki game da
fargaban kada kaltum tajawo musu dan kudin da dan turaren da yake basu ya pasa,
fadi take ke kaltum me haka karya takeyi batada miji a bur sudan,kaltum taji tamkar ta
zageshi,
kishi da tsantsar fusata suka damki zuciyarshi yacije lebe yace nikike fadawa wannan
magana kizo kasarmu kinacin arzikinmu dan kin samu anasonki shine zaki zageni?
To zan nuna miki ko ni wanene, ya juya yatafi afusace.
fatsuma na kwala kiran sunan shi tana bashi hakuri yayinda kaltum ke tunzurashi tana
cewa ya tafi din wazai tsoratar babu abunda
zai sameta sai alkhairi,
fatsuma ta fara yiwa kaltum fada itama dayake zuciyar akusane saita hargitsa suka hau
hayaniya kamar zasu cinye kansu,
ranar dai kowa gabanta takama ba a tafi tallar tareba haka basu daura tukunya dayaba
sai washegare fatsuma tabiyo wa kaltum suka hadu suka tafi tare kowaccensu ta huce
sai hira suke suna wasa suna daria,
gidan jawahir mai kunshi suka fara zuwa don suji sanda zasu fara zuwa aiki tunda tace
musu sai bayan sallah zasu dawo sai suka tarar ana zaman makokinta, Allah Ya mata
rasuwa ranar biyu da sallah sukata kuka da ihu ana basu hakuri sannan suka yi shiru a
gidan, suka nufi kasuwa jikinsu a sanyi kalau suna isa wajen sana'ar su sai suka iske
labari yasha bamban don yau ana kwashe bolan da suke tsintar kayan miya yau a
manya-manyan abun kwashe shara ana tarawa sai aje ajuye a motar kwashe shara,
suna isowa wasu ma'aikata masu uniform suka taso sukace oh kune daman masu tsintar
rubabbun kayan miya ku wanke ku sayarwa mutane suci ko?
Don haka yanzu zamu wuce daku wajen hukuma a hukunta ku,
hankalinsu yatashi sai suka hau rokonsu afuwa da alkawarin sun daina daga yau, da kyar
suna koke-koke aka kyalesu suka tafi akace kada su sake dawowa, daga wanna ranar su
kaltum basu sake zuwa bola ba sai suka shiga tunanin sabuwar sana'ar da zasuyi su
dinga samun abinci,
aranar kaltum da fatsuma suka jeru ajikin bangon kofar gidan su yunwa ya addabi
hanjinsu fatsuma ta daga kai da kyar ta dubi kaltum tace meza mu dingayi muna samun
abinci ?
Kaltum tace ni bakuwa ina na sani, kece yar gari kikasan kowa suma suka sanki,
fatsuma ta zabura ta mike tacewa kaltum taso muje wani waje kaltum na biye da ita
abaya har suka isa wani gida alungu gidan wata hajiya Maryam mai saro kaya daga
makkah sababbi da gumama, ,
fatsuma ta lankwashe kafa ta langwabe kai ta koro mata bayani cewar suna neman
sana'a suna so tabasu tallah ta dinga biyansu
dayake tasan kanwar babarta asabebe tasan
gidansu saboda haka tasan ko sun cuceta ta san inda zata zakulosu, ta amince ta daura
musu tallah, idan sunyi ciniki dayawa ta biyasu dayawa idan ciniki kadane ta biya su
kadan,
bayan sati guda ne sukaje daukar tallah sai hanasu dauka tayi, tayi musu korar kare
batare da sunsan abunda yake faruwaba, kuma bata fada musu daliliba suka koma
wajen mai sayar da gurasa suna yimata tallah, bayan kwana biyu ta koresu,
duk Abbas ne yake hada musu tuggu ashe,
kwanci tashi watannin kaltum bakwai cur a Khartoum haka shekarunta uku kenan
rabonta da Nigeria,
wulakanci da walagiigi sai karuwa sukeyi maimakon suragu al-amura sun cunkushe
musu har gara da abincin da zasukai bakinsu yazam wahala kasancewar anhanasu
tsintar kayan bola sannan jawahir mai kunshi da gyaran jiki ta rasu har maigidan yasake
aure ko gidan ba a shiga balle su sami wadanda
zasuyi wa gyaran jiki,
Abbas sisinshi ya daina basu tunda batasonshi tuggu iri iri yake hada mata duk wata
hanya da yasan kaltum zata bi ta sami
taro ko lomar tuwo sai yaje ya toshe ya batata da bakin shi,
gobe idan ta dawo sai kaga anyi mata korar kare ta shafawa fatsuma, '' idan bera da
sata daddawama da wari, idan babu rami mai yakawo zancen rami ?
Inji akuyarda kura tace ta tsallako babu rami abun nufi shine duk wata tsanarda
sangwama da akeyiwa mutanenmu yan Nigeria su suke jawowa kansu saboda sau tari
idan suka gingimo wata badakalar saikaga ko a labari ko a mafarki yan wannan kasar
basu tabajinta ba abubuwa rashin gaskiya da rashin da'a akasashen jama'a mutanenmu
ke nunawa, wadanda abun kunya ne da bata sunan wadanda babu ruwansu kuma
mutanen kirki ne kamar su kaltum sun zaune agidan amma basusan me
yake faruwaba, kashin kaji aka shafa musu aka hadasu akayi musu hukunci iri daya koda
yake wasu masu irin mugayen dabi'u ba yan Nigeria bane wasu yan Niger
ne,Ghana ,Togo ,Cameroon ,Chad ko Kenya amma sai ahadasu ace yan nigeria ne,
jama'a da gwamnatin Khartoum ta fara gajiya da rashin bin doka da rashin da ar yan
gidansu kaltum aka kira malam Abdulkadir mai gidan su kaltum, ance yamusu gargadi
bisa munanan halayen da akace suna kamar zubarda shara a ko ina, kafa teburin
sana'o'i ko ina, sayarda rubabbun kayan dasuke tsinta abola kamar irin sana'arsu
kaltum,
maza suna haura gidaje suyi sata haka ana ganin mata suna fita karuwanci yan kasa
suna daukar su amotoci atafi dasu.
malam yatarasu mazansu da matansu ya shaida musu abunda aka umurceshi daya
gargadesu dashi duk da wasu ya sani wasu kuma bai saniba wasu gaskiyane wasuma
karyane koma ma menene aka kara acikin maganar gaskiyar tafi yawa haka ba bukatar
bincikensu waye suke aikata wannan badakalar kosu waye babu ruwansa burinsa kawai
su daina idan bahaka shizai kori kowa agidanshi,
sai su kayi kamar sun gamsu suka yi ta bashi hakuri,
gobe wani sabon rashin mutuncin zasu suka,
yasake kiransu yayi wa'azi yayi lallashi ya jawo ayoyi daga AL QUR'ANI MAGIRMA yayi
fadan da kumfar baki,
in shaa Allahu jibi ta'andanci saiya karu
saboda sabbabbin mutane suke zuwa su yada zango agidan ba yan zangon daura
kadaiba ko yan daura harda kanawa,zazzagaw
a,zamfarawa,sakkwatawa.gida yazama gidan baitil mali bangaren maza daban saboda
malam yace kowa azauna
sadaka ga wuta ga ruwa ga dakuna lailaye da
siminti ba biyan ko sisi abinci ne kawai zaku nema shine suke bin gurbatacciyan
hanyarda suke zubarda mutuncin su data kasarsu abunda yake tambaya anan shine wai
mutane idan suka bar kasarsu cikin en uwansu inda akasansu sai suyi tayin abunda suka
ga dama don ba asansu ba balle ayi musu gori ko ayiwa yayansu gori?.
me yasa mutanane basa kare mutuncin kasarsu aduk inda suka tsinci kansu ?
dadine ace yan kasa kaza basu da gaskiya ko karuwai ne marasa tarbiya ne.
masu iya magana sukace shadda bata wari banza dole muma da halinmu shiyasa ake
tsanarmu, babban tabon ma shine ha'inci da rashin gaskiya
Duk yanda kahada hulda da mutanen mu sai
ancuceka wannan itace illarmu babba a kasashen waje da cikin gida,
wani sabon salo kuma wanda su kaltum basu san shiba shine gudun gardi irin nawasu
makarantun kwana da akeyi a wasu makarantun kwana na yan mata da akeyi garada ne
suke tubewa tsirara su hauro dakunan mata da talatainin dare suyi ihu gardi.
asabebe alokacinda taji motsi a bayanta tana juyowa taga sarkacecen mutum akan
akwatinta bayan ya tsinke musu wayoyinsu da suka jona a chaji a bakin kofar dakin
yafice da gudu yahaura katanga yayinda gida ya rude da kururuwa matan kowanne daki
sun firfito tsakar gida a firgice, dole malam Abdulkadir da sauran mutanen anguwa suka
firfito hankali a tashe ana hashaskawa ba a ganshiba,
a safiyan wannan ranar ne kuma fada ya kaure tsakanin wasu mata biyu akan shiga
bandaki harda dambe da fashe fashen kai, nan ma dakyar aka kirawo wasu mazan suka
rabasu don haka yansanda suka diro
gidan suna kama duk wanda suka samu idan
kukaga irin gudunda kaltum da fatsuma su kayi da tsalleka katanga saikuyi mamaki
amma da kyar sukasha bayan gurgurjewa da bubbugewar dasukayi a kafafuwansu, wani
sharcecen yankane a gwauri kaltum dajini jage jage amma bata lura ba saida suka isa
maboya suka tabbatar sunsha sannan ta duba tagani asanadiyyar radadi mai tsanani da
takeji awajen hankalinsu yayi matukar
tashi a sanda suka yi arangama da jinin mai yawa,
fatsuma ta fashe da kuka mun shiga uku kaltum yaya zamuyi da jinin nan kada jinin
jikinki fa ya kare ki mutu,?
ADON DAWA 28
.
TRUE LIFE STORY
.
kaltum ta matse hawayenda ya cika mata
ido tace Allah Ya biye bakinki fatsuma,
dama jinin jikina yakare in mutu in huta, banajin dadin duniyar nan banaso na koma
nigeria haka ma yanzu banaso nakoma bur sudan dama in mutu abayan garin nan kada
intashi daga inda nake yanzu,
suka rushe da kuka lokaci guda, fatsuma tace gara muyi addu'a mukoma kasarmu ke ai
iyayenki sunsan bakya makkah harsun aiko miki da kudin jirgi ki koma, nifa da iyayena
suke zaton ina makka inajin dadi kanwar babatace ta dauko ni asabebe muguwace ta
gaske.
harkokinta kawai takeyi na iskanci, dama akamata yanzu akaita nigeria idan taje gida
zata fada inda nake nima azo a dauke ni, fatsuma ta sake rushewa da kuka tace kaltum
kiyafe min don Allah nina jawo miki duk wannan abun da kin tafi dabakyanan akayi
wannan rigima, dabaki yage kafa abanza ba,
mamaki mara miraltuwa zaka iya gani a idanuwan kaltum ta dubi fatsuma da sauri tace
me kika jawo min ?
ai ni baki jawomin komaiba kalah tajawo min ta tafi tabarni...
fatsuma ta girgiza kai tace bawan nan zuwan naki nake fada ba kaltum da tuni kina bur
sudan nice nadauke miki kudinki a jakarki don kada kitafi ki barni.
kaltum taji ta tsani fatsuma harbataso tasake ganinta ta runtse ido don takaici yayinda
taji zuciyarta kamar zata fashe da alama fatsuma ta gane haka sai taja da baya ta
lankwashe kafa ta zurawa kaltum ido tana jiran hukuncinda zata yanke mata,
kaltum tayi shiru ba tare data furta komai

Please Login or Register in order to submit comment