Reading adon dawa Chapter 12 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bullo musu su amince kin ki sauraransa ma balle ki fahimce
shi.
Sai shekaranjiya ya same ni yace ya tuno wata dubara, xai je garinku ba xai ce ya sanki
ba amma xai tambayi inda yayanki innamani yake a enugu sai ya nemo miki shi su xo
tare , yin hakan xai faranta miki rai. Na ce kada ya je, yace in kyale shi xai je ko da kuwa
xai rasa ransa ne a hanya. Ashe ya fada da bakin mala’iku, haka ta same shi.”
Na juya na dubi Abba, na yi kuka na yi kuka, na ji dama a dawo da rayuwa baya da banyi
masa abunda na yi masa ba. Mu dukka bamu runtsa ba har asuba, na yi alwala a
bandakin cikin dakin nahau salloli ba adadi kafin assalatu, addu’a nake kada Allah Yasa
Abba ya mutu.
Yayinda mukaddam ya tafi masallaci ashe ya dauki wayarsa, yana idar da salla sai ya
kunna a inda ya hadu da sakonnin iyayensa da iyayen Abba. Hankalinsu a tashe suke
tambayar ina suka shiga shi da Abba tun jiya?
Sai ya yanke shawarar ya kira mahaifiyarsa ya yi mata bayani ita kuma ta yiwa mahaifan
Abba bayani. Tun da asuba, kafin gari yawaye xance ya xagaye dangi hankalin kowa ya
tashi yayin da motoci na alfarma suka dinga tsayawa a gaban dakin da muke.
Muryar mukaddam na jiyo yan magiya yan bada hakuri game da dogayen bayanai cikin
kuka da rawar murya a jikin wundon dakin, na meke da gudu na daga labulen wundon na
leka, sai ga en gidan su Abba kakaf da danginsa da ‘yan uwan su mukaddam, yayinda
baban mukaddam yaketa sharar masa mari ba adadi da kyar a ka rike shi. Aka sako
mukaddam a gaba ya xo ya nuna musu daki, su ka dungumo suka nufo inda muke. Na
takure a loko ina karkarwa ina kiran “laa haula wala kuwwata illa billah.”
Suna shigowa suka kalle ni a sheleke babu wanda ya amsa gaisuwata, yayinda suka nufi
kan gado da sauri wajen Abba duk wanda ya leka Abba sai yayi baya ya dafe kai yana
salati saboda Abba yayi kwatsa-kwatsa. Ina kuka na taso ina shirin in yi musu bayani sai
kuwa sumayya tukur ta sharara min mari, sannan ta kira ni da suna karuwa,
mahaifiyarsu mami hafsa ta kirani da suna maiya na cinye mata da, wai daman ashe
nice na kama shi ya dinga ramewa sannan na yi asirin da sai da ya kai kansa onisha aka
tsafe shi dan haka sai hukuma ce xata raba ni dasu.
Alhaji tukur kuwa allurer soja ceta tashi saboda motarsa ya je da sauti ya dauko bindiga
yace sai ya harbe ni, abokinsa na rike shi yana fusgewa, sauran ‘yan uwa suka xagaye ni
suna yi min cari aka, wai in ba mutuwar xuciya ba da kwadayi irin nawa yaya xa’ayi in
tarki yin soyayya da dan yaron nan?
Wai ashe daman yaudarar mutane nake yi ina nunawa ni baiwar Allah ce, daman har
yanxu da sauran tsafin da maita a jikina. Ba ni da bakin bayani saboda babu mai sauraro
na.”
Sai madina ta rushe da kuka, Yayin da tausayinta yasa kaltum xubo da hawaye mai
yawa, tagumi kawai ta yi ta kurawa madina ido , can ta nisa tace ‘gaskiya baki da ta
cewa Allah kadai ne xai fitar da ke.”
Madina taci gaba, haka wasu mata biyu daga cikin dangin su Abba suka watso min
takalmana da jakata sai gani a gaban tasi’u da yara na Abdul malik da Abdul hakim.
Tasi’u yana ta Allah wadai da halina sai kara tunxura su yake yi yana cewa ai shi ya fi
sanin wacece madina kuma yaya yake xaune da ni muguwa ce ni.
Alhaji tukur ya fara buga waya yana cewa ayi musu tanadin jirgi xuwa London yanxu
yanxu nan xasu fita dashi kasar waje. Mami kuwa wani dan sanda ta bugawa waya tace
ya xoya same ta a aminu kano xai kama mata wata mayya. Ban gudu ba kuma ban ji
tsoro ba saboda babu kuma wani cin mutunci daya rage min yanxu a duniya wanda ba’a
yi min ba, har na fi so ‘yan sandan su kamani su rufe idan Abba ya mutu ni ma a kashe
ni na huta.
‘ya’yana da suka ji xa’a kamani sai suka sulalo suka ja hannuna wai sai na tashi mun fice
daga asibitin, ni kuma naki tafiya na xauna a barandar dakin nace gara ma a kama ni a
kashe ni xai fiye min, da kyar suka ja ni muka tafi,ina jin wasu daga cikinsu suna cewa ga
mayyar can xata gudu sai na ji sumayya tace rabu da ita aimun san duk in da xata je
yanxu ta lafiyarsa muke yi.
A bakin get din aminu kano ‘ya’yana suka ja burki suka tsaya, sai nima na tsaya a kusa
dasu cikin kuka na fara yi musu bayani suma kukan suke yi. Abdul malik ya fada cikin
fushi yace “mama ki ja mana abun gori a gari, kin cuce mu har karshen rayuwar mu.” Ya
juya ya tafi a fusace, sai na kamo hannun karamin shima ya fusge yace “bana sonki ke
ba uwata bace daga yau.” Sai na saki baki ina kallonsu suka tafi suka bar ni a tsaye.
Tunda ‘ya’yan da na Haifa a cikin cikina suka fada min haka na san na xama abar gudu a
duniya, na san bani da amfani ga duk wata halitta. Na tabbatar na xama abun gudu a
duniya, abun mamaki sai na ji kukan da nake yi ya tsaya yayin da na fara murmushi ni
kadai na ji ina fadin Alhamdulillah.”
Madina ta fashe da kuka mai tsanani.
Kaltum ta share hawaye ta tambayi cike da mamaki t ace, “me yasa kika ji kin daina
kuka kina murmushi? ”
Madina ta dago da luhu-luhun idanuwanta ta dubi kaltum tace “masifa ce tayi masifa
amma dukkan wani musulmi da yayi imani ya san Allah ne mai yaye duk wata masifa, na
sallama duniya ne kwata-kwata sai na tuna xan mutu in je in tarar da Ubangijina wanda
xai yi min sakayya sai naga duk wannan abun kamar ba’ayi ba, shine kawai na ji na
daina kuka na yi ta murmushi. Menene dadin duniyar ne?
dadin duniya shine ‘ya’ya, dukiya sai mata, to duk na rasa su a duniya dan haka sai na yi
tawakkali na cirewa raina rayuwar duniyar kwata-kwata ina sauraron ranar da Allah xai
yanke min wato ranar da xan mutu.
Ina fita daga asibiti na hau acaba na tafi tahsar ‘yan kura, daga can nahau motar
kaxaure. Ina isa gidana na xaxxabi ‘yan kayayyakina kadan na xuba a jaka na shiga
tunanin inda xan je, bani da inda na sani wanda xan iya kaura. Daga karshe na yanke
shawarar nima in tafi enugu in nemo yayana innamani in har yana raye in xauna tare
dashi don shi kadai ya rage min. na shiga sake-saken ta inda xan fara nemo su sai nace
a raina idan naje enugu na tambayi sunan kawuna exe wanda yake rike shi idan kuwa ya
mutu nasan shima innamani watakila a san shi idan yayi kudi tunda yayi karatu, sai dai
kash bani da kudin motar tafiya.
Sai na tashi na shiga gidan makwabciyata mai suna sha’atu itama ma nurse ce,
baxawara kamar ni. Na iske tayi bakuwa daga Daura suna xaune suna hira. Ta na ganina
tace, ina na je tun jiya ake ta nima na ba a ganki ba, kuma me ya same ki kika rame
sannan idanuwan ki suka kumbure?
Se nace mata xaxxabi na yi da ciwo ido kuma na je kano tun jiya.
Nan dai muka xauna mu uku suna hirarsu ina sauraran su hankalina baya wajen su, ina
tunanin halinda Abba yake ciki.can se mariya kawar shafa’atu ta dauko hirar xuwa
makka ta mota xasu bi ta sudan wani satin. Sai kuwa nayi carafna tambaye ta na ce,
nawa ne kudin?
Kuma ina ake biyan kudin?
Ta yi min bayani dalla dalla, sai na ji gara kawai in tafi kasar da ba’a sanni ba. Shafa’atu
na yi min tsiya tana cewa wai me yasa na ke tambaya ni daba xuwa xan yi ba?
Na ce wallahi da ina da kudi da nima xuwa xan yi.”
Sai mariya ta dubi hannuna tace “yaya xaki ce baki da kudi kuma kina sanye da tafka-
tafkan awarwarayen gwal har guda biyu a hannunki ga sarka da ‘yan kunne da xobuna ai
ya ishe ki kudin motar har ma yayi saura.”
Sai a lokacin na tuna ashe ina da kadarar gwal, ai nan da nan jikina ya dau rawa nace
“wallahi idan mariya xata tafi daura tare xamu tafi”
Mariya tace “ai ni a yanxu xan koma ba xan kwana ba.”
Shafa’atu sai ta fara tuntsirewa da dariya a xaton ta wasa nake yi. Ta ce ta yaya xan bar
aikina, da mutunci na, da kuruciyata, ga yarana amma in tafi saudiyya yawon wanke-
wanke da shara? ”
Ai sai suka ga na shiga gidana na dauko jakar kayana na rufo gidan na shigo na tsaya
akansu na cewa mariya ta taso mu tafi daura, abu kamar wasa sha’atu taga na rikewa
mariya hannu muna ta sauri mun bar ta a baya mun nufi bakin titi, ta gaji da bin mu ta
juya gida. Tace min “in kin je ma xaki dawo nasan karya kike yi ba wata makka da xaki
je.”
Ai kuwa har ya shafa’atu bata ga dawowata ba kuma nasan sun hadu da mariya ta fada
mata cewar na tafi. Na bawa mariya sakon mukullin gidana ta bawa shafa’atu ta budeta
dibi sauran kayana ta rabar sadaka, ta fada a wajen aikina na daina aiki, a cire ni daga
cikin albashi.”
Kaltum tace daga kaxaure se ku tafi daura?
Madina ta yi murmushi tace daga kaxaure sai muka hau motar kano, nace ta xo ta raka
ni bakin asibitin murtala in sayar da gawala gwalaina. Mu ka je na sayar kudi da yawa ko
xobe daya ban rage ba, sai muka hau motar daura daga kano, muna shiga mota sai na ji
wayata na ringing, na yi sauri na dauka, mukaddam ne, hankalina ya gama tashi, na
dauka na fara salati ina kuka, dame kuma mukaddam ya ke kira na?
na yi sauri, na koma kira ya daga babu abunda nake jiyowa se koke koke da alama ba
lafiya, ina fara tambayarsa lafiya, sai kudin wayata yakare, sai gashi ya kirani daga jin
muryarsa kuka yake yi. Ni ma na fashe da kuka nace inna lillahi wa’inna ilaihi raji’un.
Mukadda lafiya, ina Abba?
Sai ya sake fashe wa da kuka yace “sister madina Abba ne ya………..”
Sai cajin wayata ta kare dif naji shiru wayar ta mutu. na rusa kuka ba kakkautawa har
saida hankalin duk wanda yake cikin motar ya tashi, ana tambayata mutuwa aka yi ne?
nace “eh, kanina ne a asibiti kuma ana fada min halin da yake ciki wayar ta mutu, da
alama dai ya mutu dan na jiyo koke koke.
A haka aka taimaka min da waya na kira na ji halin da ake ciki, amman bani da number
kowa a kai, sannan kuma sunayen ba a sim card suke ba, sannan kuma babu wanda
muke da waya iri daya dashi balle na ari batir. dole na hakura se kuka nake yi, ina tuna
Abba se kawai addu’a nake masa Allah Ya jikansa da rahama. Tsarki ya tabbata ga
Ubangijin talikai, haka Allah Ya rubuto mana, a haka yake so ya ganni.
Kaltum kinji dalilin xuwana sudan kenan. Wannan shine abunda ya rabo ni da yarana na
shiga wannan hali.
Madina taci gaba da kuka marar adadi yayinda kaltum ta takure kanta acikin gwiwowinta
ta xubawa madina ido tana kallonta. Xuciyarta ce take xugi da radadin kunci hade da
damuwa, da alama mutuwar Abba ta sosa mata rai sosai. Hawayenta ne ke disowa daya
bayan daya. Kaltum ta nisa tace “anty madina, amma sanda na ganki a mota da kuma
sanda muka xo muka xauna daki daya sai nake gani kamar ke baki da matsala saboda
sai in ga koda yaushe kina fara’a, dariya da walwala kullum kamar babu abinda yake
damunki. Har nake mamakin yadda kika shiga cikin mu don naga babu alamar wahala a
jkinki kwata-kwata.”
Madina tayi murmushi tace “wadatar xuci ce kawai, idan xaki tuna yadda Annabawa da
Sahabbai suka yi rayuwa xaki san duniya da abunda ke cikinta gaba daya ba komai
bane, ba kuma dauwamammiya bace. Shudewa take wataran tamkar ba’ayi ba. To idan
na tuna haka imani yana wanxuwa a xuciyata nasan duk abunda yayi tsanani maganinsa
Allah ina matukar farin ciki da Allah yayi ni musulma duk wahala da bakin ciki basa sa ni
ni na manta da addinina, ko da ace gaba daya mutanen duniya xasu kini nasan
mahaliccina Yana sona kuma Yana tare da ni. Ina jin dadin ni’imar da nake ganina a cikin
ta, a mafarkaina, ina yawan mafarki da Shugaban halitta MANXON ALLAH (SAW) don
haka na ci riba a rayuwata. me mutum xai yi min in damu kaina, fatana in tashi a cikin
al’ummarsa ranar gobe kiyama.”
Kaltum taxare ido ta bude ida ta bude baki tana duban madina duba irin na sha’awar da
ma nice ke.
Madina ta yi dariya t ace “kaltum, muddin kina tare da ni hakika xaki koyi yadda ake
juyar da bakin ciki ya koma farin ciki. Lokacin sallar la’asar yayi muje mu yi salla.”
Sai suka kwashi shinfidarsu suka shiga cikin gida, domin bada faralli.
ALLAH YA KARA MANA IKHLASI AMEEN , E
ADON DAWA
TRUE LIFE STORY
LITTAFI NA BIYU (P 15)
NA JAMILA UMAR TANKO
GABATARWA SADIQ HALIMA (Sadin Maa)
DAGA Al-Hada Hada Hausa Book stories
.
Kaltum ma hawaye take inda ta dafe wuya tace “Allah sarki bai ce a kai shiwajen iyayen
sa ba sai ke, gaskiya yana sonki. Amma dai kin tausaya masa da kika gan shi a cikin
wannan hali? ”
Madina tayi murmushin karfin hali ta dafa kafadar kaltum t ace “na tausaya masa har na
fara nadamar wulakancin da na yi masa a baya. Dan na tabbatar ba son wasa yake min
ba. Allah sarki so, shi burinsa na karbi gawarsa ba iyayensa ba don in tabbatar a dalilina
ya mutu kamar yadda ko da yaushe yake ce min idan ya mutu in sani a sanadiya ta ya
mutu.
Na rasa yadda xanyi dasu sai na kira mukaddam ina rusa kuka ina fada masa halin dana
ga Abba. Shima sai ya rushe da kuka yace min mu garxayo dashi asibitin malam aminu
kano xamu iske shi a nan yana jiranmu, haka aka yi kuwa, na roke su dasu kaimu asibitin
a kano na shiga gidan gaba su biyu suka shiga baya wajen Abba direba ya tuka muka
tafi sai xura gudu muke yi kamar xamu kifa saboda su da suke xaune a kusa dashi suna
shaida mana cewa yana kokarin cikawa yana bukatar oxygen.
Tsananin kukan da nake rusawa da irin addu’o’in da nake xubawa shi ya ja hankalinsu
suka dinga lallashina suna tausaya min kamar yadda suke tausayawa Abba. Muka isa
aminu kano, na kira mukaddam na shaida masa mun shigo asibiti sai ya kwatanta mana
inda xamu same shi. Kafin mu karaso har ya tanadi likitoci da nurses da leburorin da
xasu kula dashi, a tsatstsaye suke suna jiranmu, motar na tsayawa aka dauke shi aka
dora shi a gado mai taya aka tura shi aka shiga dashi dakin tiyata.
Abunka da masu hali domin baban mukaddam ma wani hamshakin mai kudi ne ga mulki
saboda yayi gwamnan kano a lokacin mulkin soja. Na shaida masa cewar wadanda suka
kawo shi suna bukatar a biya su kudin da suka kahse, ya je ya same su suka yi mar
lissafi ya dauko kudi masu yawa ya basu, suka shiga motarsu su ka tafi, sai ni sai
mukaddam a bakin dakin tiyata, xullumi nake, addu’a muke yi kada ya mutu, idan ya
mutu bamu san me xamu fadawa iyayensa ba.
Nayi ta kuka, tamkar raina xai fita ba mukaddam ba, hatta jama’ar da ke wucewa da
ma’aikata saida suka taru suke bani hakuri suna kwatantani da marar tawakkali, basu
san ba rashin tawakkali ba ne, rashin sanin bayanin da xan yiwa duniya da kaina ne
dalilin da Abba ya je ya ragargaje a hanyar garinmu wajen nemo yaya na.
Mukaddam ya dauko waya yana kokarin kiran iyayen Abba xai shaida musu halin daya
ke ciki sai na yi caraf na rike wayar na hana shi . tambayata yake me yasa baxa’a fada
musu ba, halinda yake ciki ba?
Ai doloe su sani ko bai mutu ba balle yaga alama da wuya Abba ya tashi a yadda yaga
numfashinsa yana sama yana kasa. Ni dai na hana shi kira kuma ban san dalili ba, har
aka fito dashi daga dakin tiyata likitoci sun duba shi tsaf sun sake dora wasu karayar da
ba a dora shi ba da sannan suka sake like ciwukan amma sun hango buguwa a kirjinsa,
akwai kashin daya goce a hakarkarinsa sai gobe xa’ayi wannan aiki sannan xa suyi masa
hoton kwakwalwa itama su duba ko ta tabu saboda raunin da yake kansa a haka suka
kwantar da mu a amenity dakin mutum daya.
Mukaddam yabiya kudin daki mai tsada lafiyayya mai AC, fanka, firij da kujerun alfarma.
Mukaddam ya fita ya sissiyo mana abinci da abin sha , shi ma be iya ci ba balle ni, balle
kuma shi marar lafiyar wanda babu abunda yake yi sai suma an sakala masa roba a
hanci ana xuko numfashi, sai Karin ruwan da ake yi masa leda leda.
Ina xaune a gabansa a kan kujera yayin da nake rike da hannunsa na gaji da kuka sai
addu’a nake tofa masa Allah Ya tashi kafadarsa.
Yayinda mukaddam yake lungu yana ta sa addua’ar hankalinmu a tashe bamu Ankara ba
sha biyun dare agogon dakin ya buga ya yin da daidai wannan lokaci wayata da wayar
mukaddam tadau ruri. Ina duba tawa naga sunan sumayya tukur yayin da mukaddam na
duba tasa lambar mami hafsa tukur ce, maman Abba . sai gaba dayan mu muka mike
tsaye muka dafe kirji, muka xaxxare ido muka kalli juna. Na ce sumayya ce, yace, mami
ce, sai na yi saurin na karbi wayarsa dan kar ya danna . suka yi ta ringing har suka katse
yayin da na murtsika wayoyin na kashe gaba daya, duk na bi na rude, ban san me ya
kamata na yi ba.
Mukaddam na kokarin nuna min bai dace na kashe wayoyin ba saisu xaci ba lafiya ba ko
mun hada baki mun kashe shi musamman idan suka xo suka iske mu tare dashi a asibiti
cikin wannan halin, sai na cakumi kwalar rigarsa na matse shi a jikin bango Magana nake
yi cikin fushi da kururuwa ina kuka, nace kai ne duk munafukin da ka janyo mana,
saboda me xa ka kaishi tasha yahau mota ya tafi garinmu baka sanar min ba, baka
sanarwa iyayensa ba?
Dan haka baxa ka amsa wayarsu ba, in kuwa har Abba ya mutu ka sani gawa biyu xaka
kwashe domin ni ma sai na kashe kaina.
Kaltum ta tambaya “kuma ke lokacin da gaske kike xaki kashe kan ki? Duk wanda ya
kashe kansa dan wuta ne fa.”
Madina ta share hawaye ta yi dan murmushi tace “ba kashe kaina xan yi ba, bacin rai ne
kawai da tsantsar jin haushin mukaddam.”
Kaltum t ace “yaya kuka kare? ” madina t ace “kinsan kasa kwacewa yayi daga shaker
da na yi masa yana ta bani hakuri har saida Abba yayi Magana. Nan da nan muka
dungumo da gudu wajen gadon da yake kwance muna kiran sunansa idonsa a rufe
amma sunan madina ya ambata a hankali nan da nan na rike hannunsa na matso da
bakina saitin kunnensa na ambaci sunansa nace “Abba, ka ganni bude idanunka ka
ganni. “sai yayi ta kokarin bude idonsa amma ya kasa. Hawaye ne kawai yake tsiyayowa
daga idanunsa.
Ya fara Magana cikin sanyin murya wacce take fita a hankali y ace madina, ki yafe min
abubuwanda nayi miki sannan ki sani duk abunda ya same ni dominki bana nadamar son
da nake miki. Burina da fatana ki yadda da gaskiyar son da nake yi miki don kina xaton
yaudararki nake, ina so ki kasance akan gawata yayin da Allah Ya dauki raina tamkar
yadda mace ta gari take yiwa mijinta addu’a bayan ya mutu nima ki yi min saboda na
lissafa ki dan haka na ci burin na aureki Allah baisa kin fahimta ba.”
Na sulale na durkusa na dora hannuna duka biyu a ka ina rusa kuka gami da salati fadi
nake Abba na amince xan aureka, ka tashi kar ka mutu ka bar ni. Ya na cikin magana sai
jini ya ambulo daga baki da hancinsa, a guje na xura na kira likita. Ya na xuwa sai yace
xa su yi masa wata allura kafin gobe a shigar dashi tiyata idan iyayensa sun xo. Dan
mukaddam yace musu iyayensa ne xasu saka hannu, tun daga nan Abba bai sake
farfadowa ba barci kawai yake bai san inda kansa yake ba.
Jikina ya dauki karkarwa har saida na bawa mukaddam tausayi ya jawo ni ya xaunar da
ni akan kujera yayin daya durkusa a gabana yana xubar da hwaye yace, “sister madina,
naga kin rikice kin damu da yawa, na san abunda kike tsoro kada iyayensa su xo su ji a
dalilinki haka ta faru da shi kin manta da Allah ne Yake shedar bayinsa a nan duniya da
gobe kiyama?
Kin manta iyayen Abba musulmai ne, dole su yadda da kaddara mai kyau da marar
kyau?
In har bakya so su ji abunda ya faru na amince ba xan fada ba ki dauki jakarki ki fice
daga asibitin nan, kafin gobe su xo su ganki.”
Na girgixa kai na ce “idan na gudu shine xa su fi xargina su ce da sanina hakan ta faru
saboda dole sai ka fada musu a inda yayi hatsarin saboda ga motarsa nan daya fita da
ita a hannunka bada ita yayi hatsarin ba kuma dole likitoci sun dauki statement din yan
sanda da suka kawo shi cewar a hanyar onisha suka dauko shi. Don haka gudu ba nawa
ba ne duk daran dadewa gaskiya xata fito. Mukaddam, a ganin ka yaya iyayen Abba
xasu ji a ransu idan aka ce musu Abba ni yake so har ma dalilina xai rasa rana?
Me yasa ka bari Abba ya jefa kansa cikin wannan hali nima gashi nan ya jawo min? sai na
rusa kuka.
Mukaddam ya gyara xama ya bani labarin yadda abun ya faru daga farko har karshe.
LABARIN ABBA.
Mukaddam yace “tun muna yara idan kika lura Abba na sonki, ba son soyayya ba, yana
matuakr son ya xauna dake. Baya gajiya da sauraron labarinki haka baya gajiya da
kallonki, baya gajiya da yabon kirkin ki ko a bayan idonkine. Haka kawai kike burge shi
yadda ya ga kina da tsafta, kina kula da gidanki, yaranki da mai gidanki, yace baki da
kwadayi dan bakya roko sai abunda aka baki ki ke karba, baya ga rikon addininki bakya
wasa da sallah. Abba ya shaida min cewa ko ya girma xai yi aure sai ya duba mace me
tsafta da ladabi irinki sannan xai aura.
Bayan mun girma ya shaida min yana matukar damuwa da irin wahalhalu da wulakancin
da mijin ki da kishiyoyinki ke yi miki, hakan bai sa kin fice ba saboda biyayyar aure. Idan
muna xaune muna hira, sai ki ji ya tambaye ni yace, “mukaddam, anya kuwa a xamanin
nan xan samu mace kamr Madina? ”
sai n ace masa “rabo ne ai, kai dai kayi addu’a kawai. Abba yayi ‘yan mata da yawa
amma tun kafin aje ko ina sai dangantakar ta kwabe saboda bata da hali irin na madina.
Kinsan gidansu rayuwar turawa ake yi bai tashi ya ga mahaifiyar sa na yiwa mahaifinsa
hidima ba komai sai kuku da masu aiki ke yi, ke kuma ya ga komai ke ki ke yiwa mijin ki
hatta tsinke xaki mika sai kin taso da gudu kin durkusa har kasa sannan ki bashi haka
idan ya kiraki da gudu xa ki bar abinda kike yi ki je ki durkusa. Ba ki da lokacin kowa sai
kin salami mai gidanki ko kadan ba kya bata masa rai baki da kiwar aiki.
‘yan mata da dama sun so Abba sai sun fara sai ya daina yace baya son su, har Allah Ya
kawo lokacin rabuwarku ki ka bashi tarihin rayuwarki, ki kayi matukar bashi tausayi
musamman daya ji kince kin rasa inda xaki nufa baki da iyaye. Sai yace min yana
tausayinki yana matukar son yaga ya tallafawa rayuwarki kin koma cikin farin ciki kamar
kowace mace mai miji da iyaye.
Daga nan bai sake cewa komai ba sai da aka dade, sannan na lura yana cikin damuwa
na, na yi juyin duniyar nan ya ki fada min abunda yake faruwa sai ranar da muka je
kaxaure wajen ki kika kore mu nima ranar ya shaida min halinda yake ciki nayi ta bashi
hakuri kafin mu rabu yayi min alkawari xai hakura dake amma sai ya kirani a tsakar dare
yace ya kasa hakura dake gashi tunaninki ya hana shi barci. Muna ta addu’a amma abu
sai karuwa yake yi.
Ya ce min ya fi so ya auri matar daya ke tausayinta dan ya riketa amana. Burinsa ya raya
sunna kamar yadda Manxon Allah (SAW) ya auri Nana Khadija a baxawara, ta grime shi,
burinsa ya haifar miki da farin ciki, fatansa ya sami soyayyarki, ta iyayensa duk mai
sauki ne yasan yadda xai bullo musu su amince kin ki sauraransa ma balle ki fahimce
shi.
Sai shekaranjiya ya same ni yace ya tuno wata dubara, xai je garinku ba xai ce ya sanki
ba amma xai tambayi inda yayanki innamani yake

Please Login or Register in order to submit comment